Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
can gefe daya yana murginawa da kasa, kafin ya tashi tsaye tuni Boka Aryan ya zaro wuka ya lumawa dokin boka samosa dana sarki Ridwan nan take dawakan suka zube kasa matattu. Lokacin da Boka samosa ya mike tsaye ya hango sarki Ridwan na fadowa kasa daga saman tsauni sai ya kurma ihu ya ruga da gudu gareshi domin ya sa hannayensa biyu ya tareshi karya fado kasa amma kafin ya isa wajen tuni sarki Ridwan ya fado kasa tim! Bisa kasa nan take jini ya zubo ta cikin hancinsa da bakinsa. Boka samos ya fada kan sarki Ridwan ya tasoshi zaune ya rungumeshi akan kirjinsa ya kurma ihu kuma ya fashe da matsanancin kuka domin a zatonsa sarki Ridwan ya mutu. A daidai wannan lokacin sarki muraka ya gama saukowa kasa daga saman, yana kyalkyala dariya mugunta da farin ciki a guje boka Aryan ya zo da dawakansu guda biyu suka kama suka hau suka juya da gudu suka nufi birnin saman suka bar Boka samosa rungume da sarki Ridwan yanba ta faman sharar kuka Jarumi da Gimbiya Tsawon dakiku masu yawa Boka samasa yana ta faman rusa kuka cikin matsanancin bakin ciki sai ya yunkura domin ya mike tsaye ya dauki gawar sarki Ridwan ya dorata a kafadarsa kawai sai ya ji sarki Ridwan ya yi tari gami da furza da jini daga cikin bakinsa. Koda ganin haka sai farin ciki ya kama boka samosa ya dubeshi yace "Ya shugabana bari nayi sauri na yi maka magani sannan na ruga na bi bayan su sarki muraka, ka sani ina barin dajinan karfin sirrin tsafina zai dawo don haka zan riga su Boka Aryan isa birnin soman naje na tona musu asiri bisa ha'intarmu da suka yi a wannan gasar da kuma yunkurin kasheka da sarki muraka ya yi. Sa'adda sarki Ridwan ya ji wannan batu na boka samosa sai ya girgiza kai yace "Ai ko kaje ka tona musu asiri a banzane tunda sarki muraka ne zai rigani kai sadakin gimbiya falman wannan itace kaddarata. Ba zan taba mallakar gimbiya falman ba amma ka sani da raina sarki muraka da ransa sai shima ya rasa gimbiya falman kamar yadda nima na rasa yanzu. CI GABAN LABARI Wannan shi ne asalin abinda ya haddasa kiyayya a tsakanin sarki Ridwan da sarki Muraka bayan an haifi Yarima Andaz da shekara uku-ne sarki Ridwan ya yi aure aka haifi gimbiya sazira. Sai dai kowannansu ya girma ya balaga wata rana aka wayi gari gimbiya falman ta tashi da wani ciwo me tsanani wanda aka kasa gane irinsa da kuma musabbabinsa 55 Jarumi da Gimbiya Babu irin likitocin da ba'a taraba domin su yi mata magani amma abu ya faskara dagananne aka fara tuntubar bokaye domin neman maganin cutar da kyar wani boka dake can birnin sin ya gano matsalar ya sanar da sarki cewar sarki Ridwan ne ya yi wani sihiri ya binneshi a karkashin tsakiyar teku cikin rami me zurfin kamu dubu, aljanun da suka yi wannan aikin kuma duka an hallakasu kuma duk duniya sune za su iya ciro wannan sihiri su lalata shi. Gimbiya falmin ba zata wuce sati uku ba a kwance tana jinya zata mutu. Lokacin da sarki muraka ya ji wannan jawabi sai ya kamu da tsananin bakin ciki ya fashe da matsanancin kuka. Daga wannan rana sai kulluum cutar gimbiya falmin ta rinka kara tsanani babu alamar sauki, sarki muraka ya tare a cikin turakar gimbiya falmin dare da rana yana kallonta yana kuka tare da dansa Yarima Andaz, haka suka kasance har tsawon sati uku sannan rai ya yi halinsa. Bayan an binne gawar gimbiya falmin ne sarki muraka tare da dansa Yarima Andaz suka kadaita da wannan boka na birnin sin wanda ake kira da suna boka linjolin sarki muraka ya dube shi yace "Ya kai boka linjolin ka sanar da ni abinda zan yi na murkushe sarki Ridwan na yi masa kisan gillah kuma kasarsa ta dawo karkashin mulkina?" Ya yin da boka linjolin ya ji wannan batu na sarki muraka sai ya yi doguwar ajiyar zuciya sannan ya dago kai ya kalleshi sannan ya kalli Yarima Andaz yace "Ya kai wannan sarki ka yi sani cewa a wannan gidan Jarumi da Gimbiya sarauta naka akwai wani akushi na sihiri hakane?" Sarki muraka ya gyada kai yace. "Hakane akwai shi" Boka linjolin ya се "Wannan akushi ya kai shekaru dari uku da goma sha daya ajiye a cikin dakin mahaifinka a samansa akwai kofofi guda biyu kuma agefansa akwai wani bututu wanda zai iya fitar da hayaki. To kasani cewa akwai irin wannan akushi a can fadar sarki Ridwan, a cikin ku duk wanda ya samu nasarar sato jinin daya daga 'ya 'yanku ya diga a cikin kofar akushin guda goma wani hayaki zai tashi daga cikin akushin ya lulluße shi, da zarar hakan ta faru zai samu nasara-kashe abokin -hamaiyarsa-ya mallake Kasarsa". Koda jin wannan batun sai sarki muraka yace "Na rantse da darajar gemun ubana da kuma kabarin kakana sai na tura an sato mun gimbiya sazira 'yar sarki Ridwan sai na debi jininta dana dana na diga a cikin wannan akushi domin cikar wannan burin nawa". sa'adda da yarima Andaz ya ji wannan batu na mahaifinsa sai farin ciki ya kama shi yace "Ya kai Abbana ni kuma na yi maka alkawari bayan ka sami wannan nasara sai na yi gunduwa-gunduwa da sassan jikin gimbiya sazira na zuba shi a cikin akwati na aikawa da mahaifinta ya gani domin daukar fansa kisan daya yi wa mahaifiyata". Sarki muraka ya yi murmushi ya rungume yarima Andaz yace "Babu shakka sai mun cika wadannan burika na mu Jarumi da Gimbiya Sarki muraka na tsaye a cikin turakarsa yana kai kawo cikin alamun tashin hankali sai ga boka Rimasu ya shigo cikin turakar da sauri ya zube kasa ya kwashi gaisuwa. Sarki muraka ya kama kafadarsa ya tasheshi tsaye suka dubi juna yace "Ya kai Rimasu da ga amintacce na Boka Aryan ka yi sani cewa jiya da daddare na yi wani mugun mafarki wanda ya yi matukar girgiza hankalina. Tunda na farka daga bacci kafin ketowar alfijir har kawo yanzu ban sake rintsawa ba" Sa'adda boka Rimasu ya ji wannan batu sai ya yi guntun murmushi ya kama hannun sarki muraka ya ja shi izuwa kan wata doguwar kujera suka zauna ya tashi ya dube shi a nutse yace. "Ya haba ya shugabana yau shekara dari uku kenan da kafa wannan masarautar, tunda aka kafata kakannin nakane suka malketa har abin ya zo kanka, tsawon wannan lokaci ba'a taba cinka da yaki ba, akan wannan dalilin wani mafarki na banza zai sa hankalinka ya tashi" Yana gama fadin haka sai ya dubi wata kuyanga da ya hango a can kusa da kofar turakar zata wuce ya "Maza aje a kawo wa sarki abincin kalacinsa" Nan fa Boka Rimasu ya daukewa sarki muraka hankali da hira me dadi har aka kawo abincin kalaci suka ci suka sha tare suka yi hani'an sai da boka Rimasu yaga hankalin sarki ya kwanta sosai ya saki jikinsa da shi sannan ya dube shi yace. "Ya shugabana bani labarin mafarkin da ka yi jiya da daddare koda jin wannan tambaya sai 58 Jarumi da Gimbiya fuskar sarki muraka ta sauya izuwa damuwa ya yi gyaran murya yace. "Ya kai amintaccen bokana kuma dirkar birnin samhar kayi sani cewa mafarkin da na yi shi ne wata kyakkyawar barewa ta shigo har nan cikin fadata ta ci abincin da nake ci a cikin kwanukan abincina mai albarka, kowa na kallonta amma an rasa wanda zai dakatar da ita ko ya kasheta, ina ji ina gani ta juya ta fice daga cikin fadar amma kafin ta tafi sai da ta zo gaban dana yarima Andaz ta cijeshi a hannu Yarima ya kurma ihu ya fadi kasa yana karkarwa tamkar maciji ya sareshi. A daidai wannan lokacin na farka daga bacci a firgice, wannan shi ne dalilin daya sa na aika a kiraka domin nasan fassara wannan mafarkin" Boka Rimasu ya bude baki da nufin ya yi magana sai yarima Andaz ya shigo cikin turakar fuskarsa cike da alamun damuwa. Sarki muraka ya tareshi suka rungume juna sannan ya janye jikinsa daga cikin nasa ya dube shi yace "Ya kai dana menene ya faru naga babu annuri a fuskarka?" Yarima Andaz ya numfasa yace "Ya kai Abbana yau kwana biyu kenan da muka tura jarumi lurwanu tare da dakarun sumame guda shida izuwa birnin kilmaz domin sato gimbiya sazira amma shiru kake ji kamar maye ya ci shirwa.nifa na yi wani mafarki wanda ya yi mini nuni da ba zamu sami nasarar cikar burinmu-ba akan sarki Ridwan" koda jin wannan batu sai boka Rimasu ya yi caraf yace. 59 09 Jarumi da Gimbiya "Wannan mafarkin naka ba gaskiya bane, ya kai yarima ka yi sani cewa nasara tana tare da mu a wannan masarauta domin bamu taбa samun akasinta ba, ka je ka kwantar da hankalinka,kwanaki goma ba za su cika ba face jarumi lurwan ya zo da gimbiya sazira, yana kuma kawota za mu dauki akushin sihiri mu diga jininka da nata a ciki domin hayakin daukaka ya rufe mahaifinka mu sami damar cika burinmu" Lokacin da yarima Andaz ya ji wannan batu sai farin ciki ya lullubeshi ya rungume boka Ramisu yace "Da zarar ka fita daga nan zaka iske kyauta ta musamman יי saboda wannan kyakkyawan albishir da ka yi mini" Yarima na gama fadin haka sai ya juya ya fice daga cikin turakar yana mai farin ciki mara misaltuwa. Sarki muraka ya dubi boka Rimasu yace "Maza ka sanar da ni fassarar mafarkin da na yi da wannan barewa" Boka Rimasu ya yi ajiyar numfashi gami da sunkuyar da kansa kasa sannan ya dago ya dubi sarki yace "Wannan mafarkin ba zai fassaru ba a yanzu dole sai naje na yi bincike a kansa kuma binciken zai iya daukata kwana shida, ka huta lafiya ya shugabana sai na sake dawowa gareka"Boka Rimasu na gama fadin hakan sai ya juya ya fice daga cikin turakar shi kuma sarki muraka sai ya bishi da kallo cikin matukar mamakin dalili kuwa shi ne boka Rimasu bai taба jinkirta yi masa fassarar mafarkinsa ba sai yau. Duk mafarkin da ya yi indai ya sanar da shi to nan take yake fassarashi mene ne dalilin da yasa Jarumi da Gimbiya boka Rimasu yaki fassara mini wannan mafarkin yanzu? Sarki muraka ya tambayi kansa. Lokacin da Yarima Andaz ya baro turakar mahaifinsa sarki muraka sai ya wuce kai tsaye izuwa cikin turakar mahaifiyarsa marigayya gimbiya falman. Ita dai wannan turaka an kawatata ainun- da kayan alatu na kyale-kyale duk da cewa ba a gudanar da komai a cikin wannan turaka amma kullum sai an tsaftaceta tamkar me turakar na nan a raye, daga safe zuwa dare zaka iske an kunna turaren wuta a cikinta me kamshin gaske kuma zaka ga kuyangi suna ta kai kawo a cikin turakar suna gabatar da hidimominsu. Da shigowar yarima Andaz-cikin wannan turakar sai gaba daya kuyangin da suke hidima suka fice suka ja kofa suka rufe. A tsakiyar wannan turaka akwai gunkin gimbiya falmin wanda ya kasance kato kuma dogo, gunkin ya sassaku ainun kamar zata bude baki ta yi magana kamanninta sun fita sosai, kawai rai ne da babu a jikin gangar jikin. Yarima Andaz ya karaso daf da wannan gunki na mahaifiyarsa ya daga kai ya kura masa idanu tsawon 'yan dakeku sai hawaye ya zubo masa ya bude baki yace. "Ya ke ummina kiyi sani cewa a wannan duniya babu abinda nake so sama dake, an kashe ki a lokacin da nafi bukatarki a rayuwata, baki da buri face na ganin aurena amma babban makiyinmu sarki Ridwan ya yanke wannan burin naki, na 61 Jarumi da Gimbiya rantse da soyayyar da nake yi miki ba zan taba yin aure ba face na saro kan sarki Ridwan na zo da shi gabanki a sannan ne zan cika miki burinki na yi aure. Ina mai tabbatar miki da cewa sauran kiris wannan al'amarin ya tabbata da zarar gimbiya sazira ta fado hannunmu" Yana gama fadin hakan sai ya sake matsawa jkin gunkin ya rungumeshi ya fashe da kuka. Wannan shi ne abinda ya faru a birnin samhar bayan sarki muraka ya yi mafarkin data dugunzuma hankalinsa. ** A can birnin kilmaz kuwa bayan tafiyar gimbiya sazira cikin daji a cikin siffar kuyanga Dulus sai ita kuyangar Dulus din ta ci gaba da zartar da komai kamar yadda gimbiya ta saba aiwatarwa batare da kowa ya gane a itace ba. Amma fa hankalin kuyanga Dulus a tashe yake tun daga lokacin da sarkin yaki kinana ya taba kafadunta taga ya yi mata wani irin mugun kallo alamar bai yadda da ita ba, sai dataga an shafe sama da sa'a uku bai sake dawowa gareta ba sannan hankalinta ya dan kwanta. A farkon yammaci ne sarki Ridwan ya turo aka sanar da Dulus cewa yana so ta sameshi a cikin lambu na gidan sarautar domin su yi gani na musamman. Koda jin wannan sako sai hankalin kuyanga Dulus ya dugunzuma ta rasa abinda yake yi mata dadi a duniya. Dalili kuwa shi ne bata taba e 62 Jarumi da Gimbiya raka gimbiya sazira lambun ba bare taga irin abubuwan da suka saba yi da sarki a can ba. Tunaninta shi ne idan fa har bata yi abubuwan da gimbiya ta saba yiwa sarki ba to tabbas zai gano ba ita bace kuma idan ya gano hakan hkuncin kisa ne zai tabbata a gareta, gashi a wannan lokacin jakadiyar sarki ce ta zo da kanta ta tsaya tana jiranta su tafi tare don haka babu damar da Dulus zata iya shiga cikin daki ta dauko tsuntsuwar sihiri ta karfe ta aiketa izuwa wajen gimbiya sazira domin samo mata mafita. Zuciyar kuyanga Dulus na bugawa ta mike tsaye tabi jakadiya suka fice daga cikin turakar suka nufi cikin gidan sarautar Gangaren da lambun yake. Suna cikin yin wannan tafiyar ne jakadiya ta lura da gimbiya cewar tana cikin alamun damuwa ko fargaba, don haka sai ta dubeta tace "Ya shugabata wai shin me kike tsoro ne akan fuskantar sarki yanzu a can lambu?" koda jin wannan tambayar sai zuciyar kuyanga Dulus ta buga da karfi amma sai ta basar tace "Ya ke jakadiya ba wani tsoro nake ji ba face bana son sarki ya bijiro mini da maganar aure, kinsa na yi alkawari ba zan yi aure ba face idan tsufane ya riski sarki yadda ba zai iya tafiyar da mulki ba, to lallai ba zan hau kan karagar mulki ba face ina da miji" Jakadiya tace. "Ai kuwa sarki ba zai taba lamintar wannan uzuri naki ba" Gama maganar ke da wuya suka karaso kofar shiga lambun kawai sai suka hango sarki Ridwan tsaye a cikin lambun yana jiran karasowarsu fuskarsa cike da annuri ita kuwa Jarumi da Gimbiya kuyanga Dulus zuciyarta ce ta ci gaba da bugawa da karfin gaske akai-akai kai tsaye sarki Ridwan ya tunkaro kuyanga Dulus da nufin ya rungumeta kamar yadda suka saba kawai sai yaga ta kauce masa ta nufi izuwa inda kujerun lambun suke ta zauna akan kujera me daukar mutum daya ta sunkuyar da kan kas tayi tagumi. Cikin tsananin mamaki sarki Ridwan ya taho gareta ya tsaya a lokacin da tazarar dake tsakaninsu takai taku uku ya dubeta yace "Ya ta yau kuma mene ne ya faru naga kina guduna? Kuma babu walwala da annuri akan fuskarki? Jikinki babu kwari tamkar baki da lafiya, mene ne yake faruwa?" Kuyanga Dulus ta daga kai ta dube shi fuskarta cike da alamomin damuwa tace. "Na yi mafarki ka aurar da ni ga mijin da bana so, shin gaskiya ne kana da wannan tunanin a cikin zuciyarka?" Koda jin wannan tambayar sai mamaki ya kama sarki ya dubeta ya kauda kai sannan ya yi ajiyar zuciya sannan ya je ya zauna akan wata kujera dake fuskantar tata suka kurawa juna idanu yace "Kafin mahaifiyarki ta rasu ta nemi alfarmar kada na aurar da ke ga mijin da ba kya so, na yi mata alkawarin hakan kinga kenan mafarkinki ba zai taba zama gaskiya ba, nasan alkawarin da kika daukarwa kanki cewa cewa ba za ki yi aure ba har sai na yi tsufan da bazan iya tafiyar da harkokin mulki ba to kasancewar wannan alkawari naki ba zai taba cika ba saboda ba haka Kaddararki take ba, tabba nan ba da dadewa ba za ki auri dan sarkin da babu kamarsa a wannan nahiyar tamu Koda jin 64 Jarumi da Gimbiya wannan batu sai mamaki ya kama jakadiya da kuyanga Dulus suka kalli junansu sannan Dulus tace. "Ya kai Abbana a nahiyar nan gaba daya babu wani dan sarki wanda yafi Yarima Andaz na birnin samhar, tsakaninmu da su kiyayyace ta tsawon daruruwan shekaru ta yaya zan aure shi ko kuma akwai wani 6oyayyen dan sarkine wanda-ya fishi?sa'adda sarki Ridwan ya ji wannan tambaya sai ya bushe da dariya sannan yace "Babu wani boyayyen dan sarki wanda yafi Yarima Andaz, lallai shi za ki aura amma wata kila a wannan lokacin ni da sarki muraka duk ba ma raye" Koda jin haka sai hankalin Dulus dana jakadiya ya tashi suka kurawa sarki idanu sarki Ridwan ya yi murmushi ya mike ya nufi wajen da- Gimbiya take, itama sai ta mike tsaye yana zuwa daf da ita sai ya mika mata hannunsa da nufin ta kama ta rike domin su fice daga cikin lambun. Nan take zuciyar Dulus ta yi mugun bugawa da karfi fiye da koyaushe ta yi kamar ba zata ba shi hannunta ba amma sai ta mika masa hannun, yana dora hannunsa akan nata sai shi da ita suka ji kamar an jona musu wutar lantarki ba shiri kowannansu ya janye hannunsa kuma suka kurawa juna idanu cikin alamu na rashin yadda, kawai sai taga sarki Ridwan ya yi murmushi yace "Gimbiya baki da lafiya akwai zazzabi a jikinki, wannan gadone kika yi a wajen mahaifiyarki saboda itama idan bata da lafiya a hannunta nake ganewa, maza ki koma turakarki zan turo likitana ya duba 65 Jarumi da Gimbiyа lafiyarki" Yana gama fadin haka sai ya juya ya fice daga cikin lambun ya nufi bangaren tasa turakar, jakadiya ta bishi da sauri a baya ita kuma kuyanga Dulus ta bisu da kallo kawai, har a sannan zuciyarta bata daina bugawa da karfi kuma tana ji a jikinta asirinta ya gama tonuwa. ** A can daji kuwa lokacin da jarumi lurwan tare da Gimbiya sazira suka isa inda abokan aikinsa suke dakarun sumame shida yana dauke da naman damisa akan kafadarsa sai jaruman shida suka cika da tsananin mamaki sakamakon hango shi da sukai tare da bakuwar mafauciya daga can nesa ya yin da suka matso kusa da su sai daya daga cikin yaran nasa wanda ake kira karzim ya kurawa gimbiya sazira idanu yana yi mata wani irin kallo mai nuna alamun rashin yadda, jarumi lurwan ya jefawa karzim wannan naman damisar ya cafe ya dubeshi yace. "Maza a gasa mana wannan nama domin tarbar babbar bakuwata" Yana gama fadin hakan ya wuce cikin tanrinsa ba tare da wata fargaba gimbiya sazira ta bi jarumi lurwan cikin tanrin. Lurwan ya kwanta akan shimfida ya mike Kafafuwansa domin ya huce gajiya. Ita kuwa sai ta zauna a gaban wata butar ruwa, ta dauki kofi ta zuba ruwan tasha ta dubeshi tace. "Kafin mu gama yarjejeniya akan harkallar da zamu kulla ina so ka ban amsar tambayata" A cikin mamaki jarumi Lurwan ya dubeta yace "Wacce amsa kike so na baki?" 66 Jarumi da Gimbiya "Ina so ka gaya mini dalilin da yasa ka siyar da rayuwarka ka zo nan birnin kilmaz dmin ka sato gimbiyata? Ka sani cewa fada mini gaskiyarka shi ne kadai zai sa na aminta da kai mu yi wannan harkallah. Duk da cewa na dade ina da burin samun 'yancin bauta da kuma samun tarin arziki zan iya hakura da su muddin na fahimci cewa ka boye mini gaskiyarka" Lokacin da jarumi lurwan yaji wannan batu sai ya mike zaune ya dubi gimbiya sazira cikin wani irin yanayi na rashin yadda sannan yace. "Kinyi mini tambaya bisa abinda ya shafi sirrina wanda idan na saran dake shi bani-da tabbacin anan gaba ba za ki iya ha'intataba" Sa'adda gimbiya sazira ta ji wannna batu sai tayi murmushi ta ce "Ai sarkinka ya gama ha'intarka tunda ya yi garkuwa da wacce kafi so a duniya-ya yi maka dole ka taho sace gimbiyata" Koda jin wannan batu sai jarumi Lurwan ya-yunkura cikin bakin zafin nama ya zaro wuka daga cikin jakarsa ya dorata akan wuyan gimbiya yace "Wacece ke? Ya aka yi kika san wannan sirrin?" Tayi murmushi ba tare da tsoron komai ba tace. "Ni ce wacce ka zo ka sace Gimbiya sazira, za ka dauke kaifin wukarka daga kan wuyana ko sai ka hallakani na zama gawa yadda naka aikin zai lalace sarki muraka ya kashe mahaifiyarka" Koda jin haka sai jarumi Lurwan ya yi sauri ya janye wukarsa daga kan makogwaron gimbiya ya kura mata idanu cikin tsananin mamaki, jikinsa na tsuma kawai sai gimbiya ta rikide ta dawo izuwa ainihin siffarta koda ya yi arba da ita sai zuciyarsa ta buga 67 Jarumi da Gimbiya da karfi fiye da lokacin daya ganta jiya da daddare a cikin turakarta, nan take ya ji ya kamu da tsananin sonta a cikin zuciyarsa amma daya tuna cewa wutsiyar rakumi ta yi nesa da kasa sai ya danne zuciyartasa ya yi mata dole akan ta manta da abinda ta aiyana masa. Jarumi Lurwan ya dago kai ya dubeta yace "Amma fa ina mamakin abinda ya hana mahaifinki ya turo dakaru su biyo sawunki alhalin bakya cikin gidan sarautar yanzu" Sazira ta yi murmushi me taushi a gareshi wanda ya sake dimautashi a karo na biyu tace "Wacce na zo maka da siffarta itace take wakiltata a cikin tawa siffar acan fadarmu don jaka babu yadda za'a gane cewa bana nan, ya kai wannan jarumi ni nasan abubuwa da yawa wanda kai baka sani ba kuma a shirye nake na taimakeka domin ka kubutar da mahaifiyarka daga hannun azzalumin sarkinku wato sarki muraka amma sai idan nima zaka taimakeni" Ya dubeta cikin mamaki yace. "Wane irin taimakone zan iya baki?" "Ina son da zarar ka kai ni wajen sarkin ku yaga ya mallakeni, hankalinsa ya kwanta a cikin dare kai kuma sai kabi daren ka sace wannan akushin sihirin wanda aka ajiye shi a cikin dakin tarihi na masarautarku tsawon shekaru dari uku da suka gabata, lallai ina son ka tafi da wannan akushin sihiri izuwa cikin wutar ibilisai da take ci a Karkashin dutsen larzo a bayan birninku". Saadda da gimbiya jawabinta sai hankalin sazira tazo nan jarumi Lurwan a ya 68 Jarumi da Gimbiya dugunzuma ainun saboda dalilai guda biyu, dalili na farko shi ne yasan cewa wannan aiki da take so ya yi mata yana da mugun hatsari, babu tabbas zai iya tsira da rayuwarsa kafin ya sami nasara. Abu na biyu shi ne idan har ya sami nasarar jefa wannan akushin sihiri a cikin wutar ibilisai dake cikin dutsen larzo to tabbas sai masarautarsu -ta fadi kuma har abada mulkin kasar ya bar hannun zuri'arsu sarki muraka. Ya yin da gimbiya sazira taga jarumi Lurwan ya yi shiru yana ta tunanin wannan babbar harkallah da ta zo masa da ita sai ta katse masa tunanin tace "Nasan ba komai kake tsoro ba face rushewar masarautar ku to ka sani a yanzu haka nima na sato akushin sihiri na tamu masarautar kuma can zan kai-shi cikin wutar ibilisai na jefa shi ya narke ba domin komai ba face ina son kawo karshen zalluncin mahaifina sarki Ridwan da kuma karshen zalluncin sarki muraka, idan ba haka muka yi ba har abada ba za'a sami zaman lafiya da adalci a wannan nahiyar-gaba daya ba, lallai ina son ka bani hadin kai dari bisa dari domin mu ceto rayuwar al'umma yakin gaba daya". Lokacin da Gimbiya sazira ta zo nan a jawabinta sai jikin jarumi lurwan ya yi sanyi ya sake yin shiru yana tunani. Ya mike tsaye ya kama yin kai kawo a cikin tantin ita kuma sai ta mike tsaye ta kura masa idanu kawai. Daga can sai ya juyo ya dubeta yace "Rai na fansane ga al'ummar da zata ta so nan gaba a wannan nahiyar, na rantse 69 Jarumi da Gimbiya da soyayyar da nake yiwa mahaifiyata na baki raina da jikina domin tabbatar da wannan batu" Jin haka sai farin ciki ya lullube gimbiya sazira don haka bata san lokacin da ta ruga izuwa ga jarumi Lurwan ta rungume shi ba, mamaki ya turnuke jarumi Lurwan ya kasa riketa da hannayensa biyu yace a cikin ransa ya aka yi wannan 'yar sarkin mai daraja da daukaka haka ta hada jikinta da nawa alhalin naji ance in banda mahaifinta da sarkin yakin garinsu babu wanda ya taba hada jikinsa da nata. Kawai sai yaga gimbiya ta janye jikinta daga cikin nasa ta dubeshi cikin murmushi tace "Kai ne namiji na farko da na yi gumurzun fada da shi, tun a daren jiya da muka fafata jarumtakarka ta burgeni, a yanzu kuma dana zo na ji yadda ka sallama rayuwarka don ceto ta mahaifiyarka da kuma yadda ka sake bayar da rayuwarka domin gyara rayuwar 'yan gobe sai na ji na kamu da matukar kaunarka, idan har mun rayu a cikin wannan kyakkyawan kuduri to lallai kai ne mijin da zan aura, maza ka fita ka baiwa yaranka umarni su yi shirin tafiya domin mu isa birnin samhar kafin dare ya raba" Tana gama fadin hakan sai taje ta kwanta akan shimfida tana kallonsa cikin murmushi, wani irin farin ciki mara misaltuwa ya lulluße jarumi Lurwan gami da mamakin wai yau shi ne gimbiya sazira ta kaleshi ido da ido tace tana son sa. Mutumin da shi a rayuwarsa bai taba ganin wata 'ya mace ya ji yana sonta ba alhalin da yawa sun ce suna son sa yaki. Jarumi da Gimbiya To ya aka yi yanzu ya ji ya kamu da tsananin son gimbiya sazira farat daya alhalin har yanzu zuciyarsa tana tabbatar masa da cewa wannan fa abune wanda ba zai taba yiyuwa ba domin tazararsa da gimbiya sazira tamkar tazarar sama da Kasane. Wannan shi ne abinda ya faru a daji tsakanin gimbiya sazira da jarumi Lurwan bayan sun hadu a wajen farauta. A can fadar birnin kilmaz kuwa tun sa'adda sarki Ridwan ya rabu da 'yarsa gimbiya sazira a bayan sun hada hannu ya ji kamar wuta ta jashi sai zuciyarsa ta cika da wasu-wasi ya fara zargin anya kuwa wannan 'yarsace sazira. Dalili na farko da ya sa masa wannan shakku shi ne gimbiya bata taba kin rungumarsa a duk sa'adda suka hadu koda kuwa haduwa ce ta dari a rana. Dalili na biyu shi ne me yasa ya ji kamar wutar lantarki ta ja shi a lokacin da suka hada hannu? Tunanin wadannan abubuwane guda biyu suka sa sarki Ridwan ya rasa sukuni, kawai sai ya sa aka kawo masa doki ya yi hawa shi kadai cikin batar da kama ya nufi gidan boka Rimasu kai tsaye. Boka Rimasu

Chapter 4 of 5