Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
da sarki muraka ne kadai kuke da irin wannan akushi na sihiri a wannan nahiyar, kuma wannan ne dalilin da ya saka yake son a sato masa 'yarka gimbiya sazira, kuma kaima shirinka kenan ka saka a sato maka Yarima Andaz, a yanzu haka ma ka tura sarkin barayi na wannan nahiyar gaba daya ya tafi birnin samhar domin ya sato maka Yrima Andaz harma ya tabbatar maka da cewar kafin kwana bakwai zai kawo maka shi, ka basa rabin ladan aikinsa darhami dubu dari da hamsin bisa 18 Jarumi da Gimbiya alkawarin idan bukatar ta biya zaka cika masa ragowar darhami dubu fari da hamsin". Lokacin da sarkin yaki kinana ya zo nan a jawabinsa sai sarki Ridwan ya kamu da tsananin mamaki ya dubeshi yace "Ya kai kinana ya aka yi duk kasan wannan sirri alhalin tun da na gaji sarautarnan ban taba gayawa kowa batun wannan akushin sihirin ba kuma duk abinda zan yi ni kadai nake yinsa a sirrance. Wannan fa burine wanda mahaifina ya mutu da shi kuma ya bar mun wasiyar na cika shi koda zan rasa rayuwata" Sarkin yaki kinana ya sake yin murmushi a karo na biyu sannan yace. "Kada ka manta cewa kamar yadda ka gaji sirrin wannan gidan sarauta namu haka nima na gaji sarautar sarkin yaki na wannan birnin namu. Babu abinda mahaifina bai sani ba na dangane da mahaifinka amma shima sai ya yi shiru bai nuna yasan komai ba. Nima yanzu in ba don ka tambayeni ba da ba zan taba nuna maka na san wani abu ba, ina son ka sani cewar sarkin barayi ba zai taba iya sato maka Yarima Andaz ba, kuma duk duniya babu wanda zai iya sato maka shi face mutum daya" Cikin matukar mamaki sarki Ridwan yace. "Wanene wanda zai iya sato mun Yarima Amdaz? Na rantse da kabarin mahaifina ko nawa yake so zan biya shi" Kinana ya yi ajiyar numfashi yace "Wanda zai iya sato Yarima Andaz yafi kowa kusanci da kai kuma baya bukatar sisin kwabo daga hannunka to amma kai ba zaka bari ya je ya 19 Jarumi da Gimbiya kai kansa birnin samhar ba" Koda jin wannan sai sarki Ridwan ya mike tsaye cikin tsananin mamaki ya nuna kinana da hannu yace. "Kana nufin kace da ni 'yarta gimbiya sazira се kadai zata iya zuwa birnin samhar ta sato mini Yarima Andaz?" Kinana ya gyada kai cikin murmushi yace "Tabbas ko shakka babu itace kadai zata iya yin hakan saboda abinda baka sani ba shi ne boka samasa ya bata horon yaki dana jarumtaka a sirance kafin ya mutu ba tare da kasani ba haka kuma ya tsumata a cikin sihirin tsafi da ko ni da kai bamu da irinsa, duk maganar data gaya maka da zu karya tayi maka. Jarumin da aka aiko daga birnin samhar domin ya saceta bakin gumurzu suka yi shi da ita aka rasa mai samun nasara a tsakaninsu saboda jarumtarkarsu da karfin sihirinsu ya kusan zuwa daya". Koda jin wannan batun sai mamaki ya kara turnuke sarki Ridwan ya yi shiru yana tunani sannan ya dubi kinana yace "Me yasa tuntuni duk baka sanar da ni komai akan 'yata ba sai yanzu?" Kinana yace. "Saboda kai ma kana boye mini komai naka, baka yarda da ni ba kamar yadda mahaifinka ya yarda da mahaifina, kuma ba komaine ya janyo hakan ba face kai kafi son kanka da kowa" Sarki Ridwan ya bushe da dariya yace "Tabbas kafi kowa sanina a garinnan kuma nima nasan cewa ba zan iya gyara halina ba amma tunda ka fito mini a mutum me zai hana muyi wani abu guda?" Kinana yace. 20 Jarumi da Gimbiya "Me kake so muyi?" "Ka taimaka mun na cika burin mahaifina ni kuma na yi alkawari da kabarin mahaifina zan baka kasata biyu na baka rabi ka mulketa" Sarkin yaki kinana ya yi murmushi yace. "Ni a rayuwata ban taba jin ina sha'awar mulki ba, kuma bana sha'awar na tara dukiya mai yawa. Burina guda dayane jal a duniya, matata bata taba haihuwa ba amma kafin boka samasa ya mutu-ya fada mun ba zata taba haihuwa ba face an hada jinin 'ya'yan sarakuna guda biyu na wannan nahiyar an bata ta lasa da harshenta. Ka yi mun alkawari cewa idan aka sami nasarar kawo maka Yarima Andaz zaka ciri jininsa da na Gimbiya sazira ka hada a waje guda a baiwa matata tá lasa, sai munje da kai gaban kabarin mahaifinka ka dafa kabarin da hannunka kayi rantsuwa bisa cewa zaka biya mini wannan bukatar sannan nima zan taimaka maka ka cika wannan burin naka ina tabbatar maka da cewa nasan yadda zamu iya sato yarima Andaz ba tare da Gimbiya sazira taje da kanta ta sato shi ba, hakan shi ne zai fiye maka kwanciyar hankali domin kada garin neman gira a rasa idanu gaba daya. Tura gimbiya izuwa birnin samhar domin sato Yarima Andaz ba karamin ganganci bane" Lokacin da sarkin yaki kinana ya zo nan a jawabinsa sai hankalin sarki Ridwan ya dugunzuma fiye da koyaushe ya mike tsaye ya kama kai kawo yana tunanin mafita. Abu na farko dai shi ne boka samasa ya gayamasa cewar duk matar data 211 Jarumi da Gimbiya dandani jinin 'ya 'yan sarakunan biyu na nahiyar akan harshenta sai ta haifi sarkin da zai mallaki Kasashen nahiyar gaba daya. To ya za'ayi kuwa ya bari wannan damar tabar ahalinsa ta koma ahalin sarkin yaki. Yanzu kuma ya tabbatar da cewa idan bai yiwa sarkin yaki abinda uake so ba to shima bukatarsa ba zata biya ba. Yanzu ina mafita a gareshi? Yana cikin wannan tunanin zuciyarsa ta bashi mafita tace da shi kawai abinda za'ayi shi ne ya je ya yiwa sarkin yaki wannan alkawari a gaban kabarin mahaifinsa amma da zarar tasa bukatar ta biya sai yasa a kashe matar sarkin yaki a sirrance tunda ai sai tana raye sannan ma zata iya haifar dan da zai mallake nahiyar gaba daya. Koda zuciyar sarki Ridwan ta kimtsa masa wannan dabara sai farin ciki ya lullubeshi. Cikin hanzari ya dubi sarkin yaki yace. "Na amince yau da yamma za muje da kai gaban kabarin mahaifina na daukar maka wannan alkawarin" Koda jin haka sai farin ciki ya lullube sarkin yaki kinana ya mike tsaye suka rungume juna yana yiwa sarki Ridwan godiya, yana ta murmushi amma shi sarki Ridwan fuskarsa a murtuke take cike da guzurin mugunta. ** Gimbiya sazira kuwa lokacin da ta baro dakin gani wajen sarki ta koma turakarta sai itama ta rasa sukuni. Ta kasa zama da tsayuwa zuciyarta ta cika kakil da tunani gami da damuwa da kuma fargaba. 2.2 Jarumi da Gimbiya Bisa wannan daliline ta shige can cikin kurya turakarta ta kulo kofa ta zauna ita kadai tana tunanin mafita. Abu na farko da ya fara fado mata a rai shi ne ta sani cewa mahaifinta azzalumin sarkine wanda yake matsantawa talakawansa akan haraji da sauran al'amura na rayuwa. Tun tana karama da ta taso taji bata son wannan dabi'ar ta mahaifinta, a duk sa'adda ta nuna masa kyamatarta akan hakan sai yace. "Shima haka ya taso ya gani mahaifinsa ya na aikatawa" Sarki Ridwan baya taimako kuma baya jin kan talakawansa, kuma duk abinda ya gani a hannun talakansa ya ji yana son abun walau dukiya ko mace tofa ta karkashin Kasa a sirrance zai rabashi da shi. Idan ma bai rabasa da ransa ba duk tasan irin wannan mugayen dabi'un da sarki Ridwan yake aikatawa domin haka sai taji bata son ya kara samun karfin mulkinsa bisa wannan dalilin ta fara tunanin taje har cikin birninsamhar amma ba domin ta sato Yarima Andaz ba sai domin ta kashe shi kawai tunda idan ta kashe shi ai shi kenan burin mahaifinta ba zai taba cika ba saboda sai yana-raye sannan jininsa zai iyayin aiki a cikin wannan akushin sihirin. Abinda gimbiya sazira ta aiyana a cikin ranta shi ne idan har bata samu nasarar kashe Yarima Andaz ba to tabbas ita zata kashe kanta don kada burin mahaifinta dana sarki muraka ya cika tunda dukkaninsu azzalumaine babu wani sarki da ya fisu cutar da talakawa a nahiyar. 23 Jarumi da Gimbiya A yanzu kowannansu kasa yake mulka, idan kuma suka mallaki nahiyar gaba daya, shi kenan zalluncin sai ya ninka na da fiye da kima. Batare da bata lokaci ba sai gimbiya sazira ta yanke hukuncin cewa zata kai kanta wajen wadancan dakarun sumame da su ka zo domin su saceta, ta hakan kadai zata samu damar da zata kusanci Yarima Amdaz ta kashe shi. To amma ya za'ayi tabar cikin gidan sarauta ta tafi har birnin samhar ba tare da mahaifinta ya sani ba? Koda ta zo nan a tunaninta sai hankalinta ya tashi ta ci gaba da kai komo ta fara sabon tunani. Sai da ta shafe kusan rabin sa’a sannan mafita ta zo mata, nan take farin ciki ya kamata ta mike tsaye ta bude kofar turakarta ta kwalawa shugabar kuyanginta kira Dulus. Dulus ta amsa kiranta ta rugo da gudu izuwa cikin turakar Gimbiya ta dubeta tace "Ki rufe kofofin za mu yi ganin sirri" Dulus ta juya da sauri ta rufe kofofin turakar sannan ta dawo wajen gimbiya ta durkusa kasa bisa guiwoyinta biyu. Cikin hanzari Gimbiya ta sunkuya ta kama kafafunta biyu ta jata izuwa kan babbar kujera suka zauna tare. Gimbiya ta dubi dulus cikin nutsuwa tace "Kin sani cewa a cikin kuyangina duka babu wacce na yarda da ita sama da ke, na sani cewa idan nace ki fada wuta sai kin fada, baya ga haka tsawon zamana dake baki taba cin amanata ba kuma baki taba furtawa wani sirrina ba, ina son zan yi tafiya ta sirri izuwa birnin samhar kuma kece za ki wakilceni a ya yin da bana nan domin kada 24 Jarumi da Gimbiya sarki ya gano cewar bananan" mamaki ya kama baiwa Dulus tace. "Ranki ya dade ta yaya zan iya wakiltarki alhalin kama da wane bata wane na sani cewa idan na sanya suturarki na boye fuskata kowa zai dauka cewa kece amma kuma da anga fuskata shi kenan asirina ya tonu" Sa adda gimbiya sazira ta ji haka sai tayi guntun murmushi sannan tace. "Ai wannan karon ba a iya jikinki za ki yi kama da ni ba, fuskarki ma irin tawa zata koma" Mamaki ya kara kama baiwa Dulus tace. "Ta yaya kenan hakan zata faru?". Maimakon gimbiya ta bata amsa sai ta mike tsaye taje ta bude durowar da kayan sawarta suke ta nuna mata wadansu dogayen riguna na musamman masu tsananin kyau wadanda sun kai kala ashirin ta dubi Dulus tace. "A duk sa'ar da kika saka daya daga cikin wadannan tufafin kamanninki za su rikide ne izuwa nawa sak! Idan kina shakka ki jarraba sawa yanzu kije gaban madubi ki tsaya ki kalli kanki" sa'adda baiwa Dulus taji wannan batu sai ta mike tsaye cikin sanyin jiki da fargaba domin zuciyarta cike take da fargaba tana bugawa da karfi. Abu na farko shi ne wai yau itace zata sanya irin suturar da gimbiya ke sawa a matsayinta na baiwa kuma wai zata ci gaba da rayuwa a matsayin gimbiya sazira har tsawon kwana ashirin, lallai kenan zata shiga daula da irin jin dadin da gimbiya ke samu har tsawon wannan lokaci. Koda baiwa Dulus ta tuna 25 Jarumi da Gimbiya wannan al'amari a cikin zuciyarta sai taji wani irin farin ciki ya shigeta mara misaltuwa. Dulus ta isa inda daya daga cikin dogayen rigunan take ta dubi dauki daya daga cikin dogayen rigunan wata shudiya me haske da kyalkyali ta dauko ta. Nan take ta ajiye rigar akan gadon gimbiya ta cire wacce ke jikinta ta dauki wannan din ta sanya. Kawai sai ta nufi inda madubi yake, ai kuwa tana isa gaban madubin sai ta fara kallonta daga kan kafafunta a hankali har zuwa kan fuskarta, tana yin arba da fuskar tata kawai sai taga ta zama gimbiya sazira. Mamaki ya turnuke ta Gimbiya sazira ta taho gaban madubi ta tsaya a kusa da ita sai suka zama kamar Hassana da Usaina Gimbiya ta yi murmushi tace. "Daga yanzu kin fara aikin ki saboda yanzunnan zan yi shiri na bar gari, kinsa komai a dangane da dukkanin gari, kinsa komai dangane da motsina a gidannan kinsan yadda na saba yi zan baki manzo wanda za ki iya aikensa izuwa ko ina nake da zarar kin fuskanci wata matsala". Dalus tace. "Manzo kuma? Ai babu wani mutum da zai iya yin wannan aikin". Gimbiya sazira ta yi murmushi tace "Ai ba mutum bane tsuntsune na sihiri” Tana gama fadin haka sai ta bude tafukan hannunta, take wani tsuntsu na karfe ya bayyana akan hannunta me launin ruwan kwai Gimbiya ta mikawa Dulus dan karamin tsuntsun wanda ko kaďan ba shi da nauyi, Dulus ta karbi tsuntsun tana dorashi-akan 26 Jarumi da Gimbiya tafin hannunta sai-ya zama-na-gaske ya juya-ya fuskanci gimbiya sazira ya bude fukafukansa ya risina a gareta alamar girmamawa, ya sake kamewa ya zama gunki mamaki ya kama baiwa Dulus ta dubi Gimbiya tace. "Ya shugabata ya zanyi da wannan tsuntsun" Gimbiya tace. "Anan kusa da tagar gadona za ki rika ajiye shi, a duk lokacin da za ki aiko shi gareni sai ki dauke shi ki dora shi akan tafin hannunki, take zai zama na gaske sai ki bashi sakon da-zai kai mini sannan ki bude wannan tagar za ki ga ya fice ta cikin tagar, kar ki bar bakin tagar kuma kar ki kulleta har sai kinga ya dawo. Lallai zai zo miki da amsar sakon da ya kai min” Gimbiya na gama fadin haka sai taje ta dauki takobinta da kwari da bakanta ta ratayasu a bayanta sannan ta dauki wata jakar fata da kaya a ciki ta ratayata a kafadarta suka yi bankwana bisa cewar sai bayan kwana ashirin zata dawo. Gimbiya tana janye jikinta daga jikin baiwa Dulus sai ta rikide ta koma kamannin baiwa Dulus din ta juya ta fice daga cikin turakar Dulus ta bita da kallo kawai cikin tsananin mamaki kuma zuciyarta ta ci gaba da bugawa da karfi sakamakonwani tsoro da ya shigeta bisa tunanin idan asirinta ya tonu aka gane cewa ita ba gimbiya sazira bace sarki zai iya sawa a kasheta. Lokacin da Gimbiya sazira ta fito daga cikin turakarta a cikin siffar baiwa Dulus kuma gata dauke da jakar fata sai kowa ya zata cewa gimbiya 27 Jarumi da Gimbiya ta aiketa cikin gari domin tayi mata siyayya kamar yadda aka saba don haka duk kofar data isa sai kaga Dakaru sun girmamata sun bude mata kofa da sauri ta wuce. A haka sai data wuce ta cikin kofofi goma sha daya na gidan sarauta hankali kwance. Koda ta iso kofa ta sha biyu wacce itace ta karshen fita daga gidan sarautar, tana zuwa sai taga anki bude mata kofar ta dubi dakarun fuskarta a murtuke tace. "Baku gani bane za ku ki bude mini kofa alhalin gimbiya ce ta aikeni kasuwa?" Daya daga cikin dakarun yace "Kiyi hakuri Dulus sabuwar dokace ta zo daga wajen sarkin yaki yace duk wanda zai fita daga gidannan sai da izininsa" Koda jin wannan sai zuciyar gimbiya sazira ta buga da karfi domin tana ji a jikinta cewa babu wanda zai iya gano shirinta face sarkin yaki kinana. A yanzuma da ta rikide izuwa siffar kuyangarta Dulus yana yin arba da ita zai gane ba ita bace, kwatsam sai taji muryar sarkin yaki kinana daga can bangaren yana cewa. "Dulus juyo ki taho nan za mu yi magana" Koda jin haka sai zuciyar gimbiya ta sake bugawa da Karfi sosai a karo na biyu, cikin sanyin jiki da biyayya ta juyo da baya, kanta na sunkuye ta tunkaro sarkin yaki ta tsaya cak! A gabansa. Mamaki ya kama sarkin yaki kinana yace "Yau kuma ko gaisheni ba za ki yi ba" Koda jin haka sai tayi sauri ta durkusa kasa bisa guiwarta guda ta kwashi gaisuwa. Kinana ya yi murmushi ya kai hannunsa bisa kafadarta zai tasheta tsaye sai ya yi 28 Jarumi da Gimbiya sauri ya cire hannunsa daga jikinta kuma ya dan ja baya cikin alamun tsoro kadan. Ba komai ya jawo haka ba face tsananin laushin jikinta da ya ji, ta yaya jikinta ya kasance a haka tana matsayin baiwa. Wannan itace tambayar da sarkin yaki kinana ya yi wa kansa kuma ya kasa baiwa kansa amsa. Gimbiya ta mike sunkuye da kanta ta kalleshi kadan ta sake sunkuyar da kanta kas, kinana yace "Wane irin sako gimbiya ta baki izuwa cikin gari?" "Aikena tayi na sayo mata kayayyakin hada miya ta gargajiya" Kinana ya yi murmushi yace "Tabbas na sani cewa gimbiya kullum sai ta ci miyar gargajiya, akwai wani abu na kayan marmari wanda sau daya gimbiya take siyansa a sati, idan aka sayo mata wannan abun sau nawa take cinsa a rana?" koda jin wannan batu sai gimbiya ta yi shiru tana tunani ta kasa bashi amsa, can sai ta dago kai ta dube shi tace. "Babu wanda zai iya baka wannan amsar sai gimbiya da kanta saboda babu wanda ya taba ganin lokacin da take cin wannan-abin marmari" Sa'adda sarkin yaki ya ji wannan amsar sai ya yi murmushi ya dubi dakarun tsaron kofar yace musu. "Ku bude mata kofa ta fita" Cikin hanzari sukа bude mata kofar ta fita, suka janyo kofar suka sake rufewa, sarkin yaki ya yi shiru yana tunani, ba komai yake tunani-ba face yana zargin ko-gimbiya ta rikide ta zama baiwa Dulus domin ta sami damar fita daga gidan sarautar amma daya yi mata wannan tambayar ta biyu ta kasa ba shi amsa sai hankalinsa ya kwanta, saboda yasan idan gimbiya 29 Jarumi da Gimbiya ce mancewa zatai ta basa amsa kasancewarta mace mai yawan mantuwa akan al'amuranta nan take sarkin yaki kinana ya juya ya koma can cikin gidan sarautar. Da fitowar gimbiya sazira daga cikin gidan sarautar birnin kilmaz sai ta ci gaba da tafiya har sai da tayi nisa sosai ta daina hango bayanta sannan ta bace bat tamkar bata taba wanzuwa ba a wajen. Bata bayyana a ko ina ba sai a can cikin kungurmin daji inda mafarauta ke zuwa neman dabobbin daji. Tana bayyana a wannan wurin sai ta hango wata katuwar damisa kawai sai tayi sauri ta zaro kibiya a bayanta ta dana akan baka ta saita damisar da nufin ta harbeta a lokacin da damisar ta juya baya tana tafiya. Kawai sai taga damisar ta tsaya cak a inda ta ke kuma ta juyo gareta suka kurawa juna idanu har izuwa tsawon 'yan dakiku. Daga nan kuma sai damisar ta tunkaro Gimbiya sazira kai tsaye tana tafiya a hankali. Koda gezau gimbiya sazira bata yi ba kawai sai ta kara tabe bakarta ta saita kan damisar da kibiyarta. Koda ganin hakan sai damisar ta falfalo da gudu har tana tashi sama da nufin ta zo ta murkushe gimbiya sazira baifi taku goma ba a tsakaninsu sai gimbiya ta sakar mata kibiya, kibiyar ta huda tsakiyar kan damusar rabinta ya lume a ciki. Maimakon damusar ta fadi a kasa sai ta dako tsalle a sama ta kawowa gimbiya wawusa da faratan hannayenta biyu tamkar kibiya bata soketa ba, cikin bakin zafin nama gimbiya sazira ta kaucewa 30 Jarumi da Gimbiya harin damisar ta sunkuya ta karkashinta tayi sufa izuwa can gefe daya, bayanta ya bugu a jikin wata bishiya ita kuma damisar ta diro kasa akan kafafunta guda hudu ta karci kasa da faratan ta kura ta tashi ta yi tirjiya sannan ta juyo da baya suka sake kallon-kallo a ya yin da gimbiya sazira ke zaune a kasa jikin bishiya. Wannan karon sai da suka yi nazarin juna sosai kowannansu ya kudure mugun nufi a ransa domin samun nasara akan abokin gabansa. duk da cewa wannan kibiyar da gimbiya sazira ta harbi damisar na nan a cikin kan damisar jini na zuba kuma dafin kibiyar ya fara sata jin jiri-jiri amma tana yin wani irin gurnani mai ban tsoro kuma tana wangame bakinta, hakoranta ma su kaifi da tsini na firgita duk wata halitta dake wajen. Cikin shammata sai damisar ta dako tsalle mai karfi a sama daga inda take da nufin ta dira-akan gimbiya ai kuwa itama gimbiya sai tayi wuf ta zaro takobinta ta doki kasa da hannunta guda sai gata a sama cikin sararin samaniya tamkar harbota akai daga cikin baka suka yi mugun gamo ita da damisar a saman. Damisar ta wangame bakinta da nufin ta hadiye kan gimbiya cikin zafin nama ta kaucewa bakin damisar ta soka mata takobinta a tsakiyar gadon bayanta takobin ta 6ollo ta cikin Damisar suka fado kasa tim!. nan take Damisar ta zama gawa ko shurawa ba yi ba. Takobin gimbiya ta nutse a cikin kasa a cikin Damisar Gimbiya na ruke da takobin tata da hannu biyu kawai sai gimbiya ta ji ana-yi mata tafi daga 31 Jarumi da Gimbiya bayanta. Ta waiga da sauri tayi arba da wanda yake yi mata tafin ba wani bane face jarumi lurwan shugaban dakarun sumame wadanda suka zo saceta. Yana tsaye rike da kwari da bakansa ya kura mata idanu yana mamakin wannan gagarumar jarumtaka da ta yi a yanzu ta kashe wannan Damisar farat daya. Jarumi Lurwan ya karewa gimbiya kallo sama da kasa yaga tana rataye da jaka ta tafiya a bayanta Gimbiya ta mike tsaye ta zare takobinta daga cikin Damisar ta goge jinin dake jikin takobin akan gawar Damisar sannan ta zurata cikin kufenta. A sannanne jarumi Lurwan ya dan matso kusa da ita yace. "Na so na gane wannan fuskartaki daga cikin kuyangin dake kwance a babban falon Gimbiya sazira jiya da daddare" koda jin haka sai ta dube shi a fusace tace "Wato kaine shugaban dakarun sumamen da ya shiga har cikin falon Gimbiyata domin ya saceta ko?"Lurwan yace. "Tabbas ni ne ke kuma wacece kuma me yasa kika baro cikin birnin kilmaz kika shigo wannan daji, ina kika nufa daga nan?" Gimbiya ta sake murtuke fuska tace. "In ba don akwai aikin da na fito yi ba yanzu da sai na kamaka da karfin tsiya na kaika gaban gimbiyata na gurfanar da kai domin ayi maka hukunci bisa laifin da ka aikata na yunkurin satar gimbiya" Koda jin wannan batu sai jarumi Lurwan ya kyalkyale da dariya yace. 32 Jarumi da Gimbiya "Ya ke wannan kuyanga ta gimbiya sazira kiyi sani cewa uwargidanki ma na yi gumurzu da ita bata sami nasara akaina ba bare ke 'yar karamar alhaki. Tabbas jarumtakarki ta burgeni da za ki amince ki taimaka mini na cika burina akan gimbiyarki da na kai ki birnin samhar kin sami daukaka daga kuyanga-zuwa ga attajirar da babu kamarta" Lokacin da Gimbiya ta ji wannan batun sai tayi sororo ta sunkuyar da kanta kas tana tunani sannan ta dago kai ta dube shi tace. "Ta yaya zan iya tabbatar da cewa idan na taimake ka naje na sato Gimbiya na kawo maka ita har nan zaka cika wannan alkawarin ba tare da ka yaudareni ba?" koda jin wannan batu sai farin ciki ya kama jarumi Lurwan ya dubeta cikin murmushi yace "Idan har kika kawo mini Gimbiya nan inda nake zan tura birnin samhar a dauko miki dinare cikin buhu goma. Idan kuma muka isa can birnin samhar da gimbiya sazira lafiya zan kara miki buhu arba'in na dinare, yaya kin yarda da wannan sharadin?" Gimbiya ta kada kai tace. "Ban yadda ba sai ka fara bani kafin alkalami sannan zan yarda-na-ci amanar gimbiya naje na satota na kawo maka ita nan” Jarumi Lurwan yace "Shi kenan na yarda da hakan muje cikin tanti mu zauna ki huta sannan mu daddare wannan babbar harkallah" Yana gama fadin haka ya je ya sari naman Damisar ya juya ya nausa eikin daji. Cikin hanari da murna gimbiya sazira tabi shi a baya ba tare da yasan cewa itace wacce yake nema ba ruwa Jarumi da Gimbiya a jallo saboda a cikin siffar kuyangarta Dulus ya ganta. ** A can birnin samhar kuwa sarkin muraka na kwance a cikin turakarsa da tsakiyar dare yana bacci sai ya farka a firgice ya mike zaune zumbur sakamakon wani mugun mafarki da ya yi mara dadi. Hakanne yasa idanunsa suka bushe, bacci ya kaurace masa ya mike tsaye ya kama kai komo. Har alfijir ya keto bai sake rintsawa ba. Tun kafin gari ya yi haske ya kirawo bafadensa ya aike shi da yaje ya kirawo abin dogaronsa wato boka Rimasu nan danan kuwa bafaden ya cika aikinsa. Kafin Boka Rimasu ta iso tuni sarki muraka ya yi wanka ya kimtsa kuma sai ya yi gagarumar shigar yaki ya zauna a cikin fadarsa shi kadai babu dogarai da fadawa sai huci yake yi yana muzurai cikin alamun tsananin fushi. Ba wai mutum ba ko aljan a wannan lokaci ko wacce irin halittama sai tayi shakkar tunkarar sarki muraka saboda kwarjininsa da kuma fushin da fuskarsa ke nunawa. A wannan rana tunda sarki ya farka daga bacci hatta matansa da kuyanginsa babu wacce ta kusance shi saboda shi idan yana cikin fushi kana rabarsa zai iya yi maka mugun lahani koma ya hallakaka. Boka Rimasu ne kadai yake iya zuwa kusa da shi ya kwantar masa da hankali. Sarki muraka ya kasance gawurtaccen jarumi a nahiyar domin a tarihin jarumtakarsa ya ajiye tarihin da babu wani. jarumi daya ajiye irinsa. Abinda ya faru a lokacin daya nemi auren matarsa 34 Jarumi da Gimbiya mahaifiyar Yarima Andaz wacce a halin yanzu-ta samu shekara bakwai da rasuwa. Ita dai mahaifiyar Yarima Andaz sunanta gimbiya Falmin kuma ta kasance 'ya ga wani sarki da ake kira Barluza me mulkin kasar soman a kudancin Kasar samhar A wannan lokacin a nahiyar gaba daya babu-wata budurwa wacce ta kai kyawun gimbiya falmin don haka sai sarakuna, jarumai da matsafa suka yi caa akan neman aurenta bisa wanan dalilin mahaifinta sarki Barizu yasa wata gasa me tsananin wuya hadari bisa cewa wanda ya samu nasara lashe gasar shi ne zai auri gimbiya falmin. Yanayin gasar shi ne akwai wani tsauni wanda aka yi masa lakabi da tsaunin mutuwa. Shi dai wannan tsauni a samansa akwai wani kogo babu komai a cikin kogon face tarin dukiya ta zinare da lu'u-lu'u ance wannan dukiyar tafi shekara dari uku a wajen amma duk wani mahaluki da ya shiga cikin wannan kogo domin ya dauko wani abu a cikin dukiyar baya dawowa a raye. Da yawa wadanda suka shiga wannan kogon basa dawowa kuma ko duriyarsu ba a sake ji. Bokaye da-yawa sun tabbatar da cewa ba aljanune suke hallaka mutum ba a cikin wannan kogon wadansu irin halittu ne masu cin naman mutum sai dai aga sun watso kasusuwan mutum waje sun cinye naman, kuma an tabbatar da cewa tsafi baya tasiri a kansu sai dai tsagwaron karfin damtse da iya yaki. Mutane dari uku da sittine suka taru a kofar gidan sarautar kasar soman domin neman auren 35 Jarumi da Gimbiya gimbiya falman amma da mahaifinta sarki Barluza ya fito ya yi musu bayanin cewa sadakin 'yarsa shi ne zuwa tsuburin mutuwa a shiga cikin kogon dukiya a debo zinare da lu'u-lu'u duk wanda ya zo da wannan dukiya gaban sarki Barluza kafin rana ta fadi to shi ne zai auri gimbiya falmin sai mutanen nan suka fara janye jikinsu daya bayan daya suna hakura da shiga wannan gasa har sai da ya zamana sauran mutum biyu kacal ba wasu bane

Chapter 2 of 5