Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
wadannan mutane biyu da suka rage face sarki muraka na birnin samhar da kuma sarki Ridwan na birnin kilmaz. Kowannansu ya yi gagarumar shigar yaki suna zaune bisa ingarmun dawakai dokin sarki muraka bakine shi kuma na sarki Ridwan farine. Sarki Barluza ya dubi wadannan sarakai biyu ya yi musu jinjina. A wannnan lokacin gimbiya falmin na tsaye daf da mahaifinta kuma a yaune ta fara ganin wadannan sarakuna guda biyu, don haka sun kura mata idanu itama ta kura musu idanu zuciyartana yi mata wasu-wasi akan wanda yakamata ta zaba ya zamo abokin rayuwarta. Duk da cewa tasaon cewa bata isa ta yiwa kanta zabi-ba tunda wanda ya lashe wannan gasa shi ne zai aureta. Sarki barluza ya dubi gimbiya falmin cikin murmushi yace "Ya ke 'yata yanzu a cikin wadannanjaruman sarakunan wanne ne yafi kwanta miki a rai?" koda jin wannan tambayar sai ta maida masa da martanbin murmushi tace. "Ya kai Abbana ka sani cewa ni mace ce me son tausayi da jin kai ga talakawa don haka nafi 36 Jarumi da Gimbiya son ace sarki Ridwan ne zai zamo ango na saboda yafi sarki muraka saukin zallunci, duk da cewa dai shima din ma'abocin danne hakkin talakawane da kuma son dukiya" Sa'adda sarki barluza ya ji wannan batu sai fuskarsa ta sauya zuwa yanayi na damuwa yace. "Nima na fi sonki da sarki Ridwan amma kuma baka safai muke samun abinda muke so ba a rayuwa Yana gama fadin hakan sai ya bar gimbiya falmin ya nufi inda su sarki muraka suke ya je har daf da su ya dube su yace "Ya ku wadannan zaratan jaruman sarakuna a cikin jaruman gasa guda dari uku da sittin ku biyune kacal kuka sai da ranku domin zuwa tsaunin mutuwa to kusani lokacin fara gasarku ya yi, sai ku hanzarta zuwa kogon dukiya ku debo zinare da lu'u-lu'u duk wanda ya kawo wannan dukiya kafin rana ta fadi daga cikinku tamkar bayar da sadakin auren 'ya tane gimbiya falin kuma nan take zan daura masa aure da ita” Sa'adda sarki muraka da sarki Ridwan suka ji wannan batu sai suka dubi junansu suka yi murmushin mugunta sannan suka juya baansu suka dubi bokayensu wadanda suma suna zane bisa dawakansu. Kawai sai bokayen biyu suka kada linzamin dawakansu suka juya suka nufi kofar fita daga cikin gidan sarautar. Sarki muraka da sarki Ridwan ma sai suka bi bayansu, gimbiya falmin da mahaifinta suka bisu da kallo har suka bace musu da gani. 3-7 Jarumi da Gimbiya Haka dai wadannan mutane hudu suka ci gaba da tafiya akan dawakai suka nausa cikin daji inda wannan tsaunin mutuwa yake. Boka samasa da sarki Ridwan ne akan gaba. Sarki muraka da bokansa Aryan na biye da su kuma tazarar da take tsakaninsu bata wuce kamu goma ba sarki muraka ya dubi boka Aryan yace "Ta kowane hali fa nine zan lashe wannan gasa" Cikin mamaki Aryan yace. "Ya shugabana dame ka dogara ka fadi haka?". "Abinda na dogara bisa binciken da ka yi shi ne zan shiga çikin koğon kuma zan fito a raye to idan har shima sarki Ridwan ya samu wannan nasara to ba zan bari ya koma fadar su gimbiya falman ba" Boka Aryan yace. "To yaya zaka iya hana shi zuwa?" Sarki muraka yace "Kashe shi zan yi saboda gimbiya falman tawace ni kadai ba zan taba bari wani na ya mallaketa ba" Yana gama fadin hakan ya juyo baya ya hada idanu da sarki Ridwan. Ridwan ya yi masa murmushi amma shi sai ya daka masa harara ya juya yaci gaba da tafiyarsa. Sarki Ridwan ya dubi boka samosa yace "Maganarka gaskiyace akwai mugun nufi a cikin zuciyar wannan abokin hamaiyar tawa domin naga hakan a cikin idanunsa" Boka samosa yace. "Nima naga hakan sai ka kula". Nan dai aka ci gaba da tafiya ana ta ratsa daji batare da an fuskanci wata matsala ba har rana ta take, bisa dole suka yada zango. Sarki Ridwan da Boka samasa suka sauka a karkashin wata katuwar bishiya suka daure dawakansu suka yi shimfida 38 Jarumi da Gimbiya suka zauna kuma suka bude jaka suka fito da abinci guzuri suka fara ci. Sarki muraka da boka Aryan kuwa sai da suka yi nesa kadan da su sannan suka soma yada zango a karkashin wata bishiyar daban suma suka yi shimfida suka zauna suna cin abinci kuma suka fara hira inda boka Aryan ya dube shi yace. "Ya shugabana daga nan inda muke fa tafiya ce ta zango daya da rabi kacal mu isa tsaunin mutuwa. Kasani cewa idan muka isa can ni da bokan sarki Ridwan a kasan tsaunin za mu tsaya mu jira saukowarku, don haka duk taimakon da zamu iya baku daga nan zuwa bakin tsaunin mutuwa ne" Cikin mamaki sarki muraka ya dubi boka Aryan yace "Ashe duk bala'in da za mu tunkara a cikin tsaunin mutuwa babu ruwanku da shi?" Boka Aryan yace 'Kwarai kuwa tunda tsafi baya tasiri a cikin wannan kogon abinda zai ceceku kawai shi ne karfin damtsenku, jarumtakarku da kuma irin nasibinku a rayuwa kai dai kawai duk yadda za ka yi kayi domin tabbatar da cewa ka debo wannan dukiya kuma ka fito a raye" Sarki muraka ya yi ajiyar numfashi yace. "Wannan kamar anyi an gamane lallai sai na sami nasara debo wannan dukiyar kuma sai na fito a raye daga cikin kogon dutsen na tsaunin mutuwa". A can bangaren su sarki Ridwan kuwa hirar da ta karke a tsakaninsu da Boka samaso ya dube shi yace "Ya shugabana babban tashin hankalina shi ne idan ka rasa rayuwarka a cikin tsaunin mutuwa ba Jarumi da Gimbiya zan iya komawa birnin kilmaz na kai wannan labarin ba domin wasu za su yi zargin na akan ni na hallakaka domin na gaje kujerarka don haka na hakura da rayuwar can sai dai na tafi wata kasar na zauna na karasa ragowar rayuwata" Sa'ar da sarki Ridwan ya ji wannan batun na boka samasa sai ya kyalkyale da dariya sannan yace "Ya kai wannan boka ka yi sani cewa ba'a iyawa mutum a cikin wannan duniyar, ko ka koma ko kar ka koma hakan ba zai saka aki yin zarginka ba bisa mutuwata. Abinda na ke so ka sani shi ne ba zan mutu ba a cikin wannan tafiyar haka kuma babu tabbacin zan sami nasarar lashe wannan gasa" Cikin mamaki Boka samosa ya dube shi yace. "Ya shugabana kai kuwa mene ne dalilin da ya sa ka fadi haka?" Sarki Ridwan yace "Saboda duk abinda zai sameni a rayuwa nakanga kwatankwancinsa a mafarki kafin wannan abin ya faru-a zahiri, yanzu yaushe ne za mu ci gaba da wannan tafiya?" Boka samosa yace. "Ai da zarar rana ta danyi sanyi kadan za mu ci gaba da wannan tafiya tunda kafin ranat ta fadine ake so akai sadakin Gimbiya falman" Sarki Ridwan ya yi murmushi gami da jinjina kansa yace "Lallai yau akwai gwagwarmaya wacce zata zamo abar tarihi a wannan nahiyar gaba daya". ** Kamar yadda boka samasa ya fada haka al amarin ya kasance wato rana na soma yin sanyi sai duk su hudun suka mike tsaye suka yi shiri suka hau dawakansu suka ci gaba da tafiya suna masu 40 Jarumi da Gimbiya tunkarar tsaunin mutuwa ko tafiyar sa'a guda basu yi ba suka iso wani babban fili wanda babu bishiya ko guda daya a wajen. Kasar wajen gaba daya yashi ce kuma wurin ya yi tsit! Tamkar babu wani abu me rai da ya taba wanzuwa a wajen. Sarki maraka da boka Aryan ne suka fara isowa wannan wurin don haka sai suka tsaya cak suna nazarin wajen koda ganin haka sai sarki Ridwan da boka samosa suka ja linzamin dawakansu suka tsaya cak! Boka Aryan da boka samosa suka sauko daga kan dawakansu suka damki wannan yashi suka shinshinashi domin su gano ko akwai wani mugun abu a wajen amma sai suka kasa ganokomai. Kowannansu sai ya fara amfani da sihirin tsafinsa domin ya gano sirrin wajen amma sai dukkaninsu sihirin tsafin na su yaki ya yi aiki. Al'amarin da ya matukar basu mamaki kenan kawai sai boka Aryan ya dubi sarki maraka yace "Ya shugabana ba zan iya ketare wannan wajen ba face ka fara ketare shi saboda bansa irin bala in dake cikin wannan yashin ba". Shima boka samosa sai ya yi wa sarki Ridwan irin wannan bayani, koda jin hakan sai sarki Ridwan ya sauko daga kan dokinsa ya zare takobinsa ya nufi cikin wannan yashin kai tsaye ba tare da jin tsoron komai ba. Da ganin hakan shima sarki muraka ya sauko daga dokinsa ya nufi wajen da sarki Ridwan ya nufa. Boka Aryan da boka samosa suka zama 'yan kallo. Jarumi da Gimbiya Muraka da Ridwan suka shiga cikin wannan yashi kowannansu na rike da takobinsa suna taka sawayensu a hankali cikin tafiya cike da nutsuwa irin ta jaruman da suka yadda da kansu. Kwatsam sai su kaga hannayen wasu mutane ya fito daga cikin karkashin kasa ya kama kafafuwansu, cikin zafin nama kowannansu ya kaiwa hannayen da suka rukoshi mugun sara amma sai sukaji kamar Karafa suka sara ba hannun bil'adama ba domin wata irin kara ce ta tashi kal! Gami da tartsatsin wuta. Ko gezau hannayen ba su yi ba kuma ko kwarzane ba su yi ba, maimakon ma su saki Kafafuwan sarki maraka dana sarki Ridwan sai suka sake rikesu gam suka fara jansu da karfin tsiya izuwa cikin karkashin kasa, kafin su ankara kafafunsu sun shige cikin kasa tsawon guiwoyinsu. Koda ganin haka sai sarki Ridwan da sarki maraka suka saki takobinsu suka kama hannayen da suka rikesu suka rinka janyosu da dukkan karfinsu, nan fa kwanjinsu ya tashi dukan jijiyoyin jikinsu suka tashi suka kumbura, kawai sai gani akai sun cisgo hannayen daga cikin gangar jikin dake cikin kasa, sai ga jini na zuba a jikinsu. Faruwar hakan ke da wuya sai wasu samudawan mutane su kimanin dari suka suka faso ta cikin karkashin Kasa suka yiwa sarki maraka da sarki Ridwan kawanya. Koda ganin wadannan samudawan mutanen sai boka samasa da boka Aryan suka firgita ainun saboda kwarjinsu da kuma kirarsu ta karfi babu komai a jikinsu face warki na fata, kafafuwansu 42 r Jarumi da Gimbiya babu takalma a wuyansu akwai wata sarka wace aka yita da kashi, su dai wadannan mutane sun fi kama da masu cin mutane domin kamanninsu ma ya fara fita daga hayyaci na bi'adama su kansu su sarki muraka duk da kasancewarsu gwarazan jarumai sai da suka firgita bisa ganin wadannan mutanen amma da yake idan mutum yaga mutuwa murara sai ya tareta domin neman matsera sai ko wannansu ya gyara tsayuwarsa ya dunkule hannayensa biyu domin fara gumurzu. Lokaci guda sai samudawan suka yi ca akansu aka ruguntsume da azababbane fada ya zamana cewa samudawan na kai musu naushi da bugu suma suna kai musu. Babban abinda ya dagawa su sarki Ridwan hankali shi ne duk basamuden da suka nausa sai suga ya shanye dukan tamkar shafarsa suka yi shi kuma idan ya naushe su sai kaga sunyi layi suna neman faduwa saboda karfin naushin. In ba don ma suna da tsananin juriya ba da na ci da cikin kankanin lokaci za su zube kasa. Cikin kankanin lokaci aka hadawa sarki muraka da sarki Ridwan jini da majina. Tun suna iya kare naushi da bugu gami da maida martani har takai cewa an kai su kasa ana ta yi musu luguden duka. Tuni sarki muraka ya galabaita har ya fara aman jini, idanunsa sun fara warkalewa alamar zai suma, koda sarki Ridwan yaga halin da sarki muraka ya shiga sai ransa ya baci ya kurma wani uban ihu mai tsananin firgitarwa wanda yasa su kansu samudawan suka dan ja baya Jarumi da Gimbiyа Kawai sai sarki Ridwan ya daka tsalle sama tamkar daga kan sifirin aka wurgo shi kawai sai ya dira akan kawunan samudawa biyu da kafafunsa kawai sai ya ji kawunan na su sun gurma suka sulale kasa matattu. Nan take ya gane cewa ashe lagon samudawan shi ne tsakiyar kansu cikin zafin nama Ridwan ya ci gaba da naushin tsakiyar kawunan samudawan suna faduwa tamkar ana sassabe a gona. Adaidai wannan lokacine sarki muraka ya dawo cikin hayyacinsa koda yaga yadda sarki Ridwan ke ta dukan samudawan a tsakiyar kawunansu suna zubewa matattu sai shima ya mike tsaye wuf! Ya tashi ya kifa kan samudawan. Kafin cikar rabin sa'a sun kashe gaba dayan samudawan dayan su bai tsira ba. Faruwar hakan ke da wuya sai sarki Ridwan ya durkushe kasa yana haki kamar ransa zai fita, shima sarki muraka sai ya zauna a kasa yana numfashi saboda jikinsa gaba daya ya yi tsami,sakamakon naushi da bugun daya sha. A daidai wannan lokacin boka samasa da boka Aryan suka rugo da gudu izuwa garesu suka kama yi musu jinjina bisa ganin irin gagarumar jarumtakar da suka yi. Boka Aryan ya yiwa sarki muraka rada a kunne yace. "Baka yiwa sarki Ridwan godiya ba alhali badan shi ba da yanzu tuni ka dade da mutuwa a lokacin da kuke yin gumurzu da wadannan samudawan” Koda jin haka sai sarki muraka ya murtuke fuskarsa ya bude baki a fili yace "Tsakanin abokan gaba babu taimako ko godiya Jarumi da Gimbiya Yana gama fadin haka sai ya mike ya dubi Boka Aryan yace. "Bamu da lokaci ka zo mu ci gaba da tafiya tunda so ake a kawo sadakin gimbiya kafin rana ta fadi" Dajin haka sai boka Aryan ya mike da sauri yabi sarki muraka suka haye dawakansu sua zaburesu da gudu. Koda ganin haka sai sarki Ridwan da boka samaso ma suka ruga izuwa wajen na su dawakan suka haye suka bi bayansu sarki muraka da gudu. Har su sarki muraka suka isa bakin tsaunin mutuwa ba su sake haduwa da wani mugun abu ba, da zuwansu sai suka ja linzamin dawakansu suka yi carko-carko suna kallon tsaunin. Shi dai wannan tsaunin na mutuwa tsawonsa daga kasa zuwa sama yakai kamu tamanin koda sarki muraka da sarki Ridwan suka kalli tsawon wannan tsaunin sai hankalinsu ya tashi domin ba sy ga yadda za su iya haye saman wannan tsaunin har su shiga ciki kogon dutsen ba tare da amfani da karfin sihiri ba tunda tsafi baya amfani a wannan dajin. Idan takamar mutum ya iya hawa saman dutse to ai kafin ya kai karshensa hannunsa zai gaji idan kuma ya gaji to subutowa zai yi ya fado kasa ya mutu a banza. Boka samasa da boka Aryan suka koma gefe daya suka zauna a waje guda suka yi tagumi duk da cewa tunda aka fara wannan tafiya ba su yi wa junansu magana ba ko sau daya amma sai kowannansu ya ji yana so ya yi maganar. A 45 Jarumi da Gimbiya wannan lokacin sarki muraka da sarki Ridwan sun tsaya a gaban tsaunin mutuwan sun kura masa idanu kawai kowannansu yana tunanin dabarar da zai yi ya hau kan wannan tsaunin ba tare da ya fuskanci wani hadari ba da zai zamo sanadin ajalinsa. Boka Aryan ya dubi boka samasa yace "Abokina ashe duniya abar tsoroce?" Cikin mamaki Boka samasa ya dube shi yace "Kai kuwa mene ne dalilin da yasa ka fadi haka?" Boka Aryan yace. "Bomai mulkin mutum da daukakarsa komai tarin dukiyarsa yana ji yana gani wani abun zai gagareshi. Yanzu dai gashi sarakunan nan biyu babu abinda suka rasa a wannan duniyar amma sun rasa ta yadda za su hau kan wannan tsaunin, wannan ya isa babban darasi akan kowa. Babban abin hadarin ma shi ne saboda kawai su mallaki mace guda daya suke so su hau kan wannan tsaunin kuma babu tabbacin za su iya isa karshen tsaunin har su debo dukiyar da ake bukata kuma su sauko lafiya a raye" Koda jin wannan batun sai boka samosa ya bushe da dariya yace. "Na rantse da gemun mahaifina ni dai idan ni ne daya daga cikinsu hakura zan yi da wannan gasar tunda ina da sarauta kuma ina da kudi duk وو irin kalar macen da nake so na aura zan iya samu Boka Aryan ya yi murmushi yace "Ai shi dan adam da buri yake mutuwa saboda shi buri baya karewa, tunda a nahiyarnan kaf babu wata budurwa mai kyawun gimbiya falman tofa 46 Jarumi da Gimbiya duk wanda ya mallaketa a wannan zamanin ya zama zakaran gwajin dafi kuma ya ajiye tarihin da har abada ba za a taba mantawa da shi ba" Boka Aryan na gama fadin haka, sai suka hango sarki Ridwan ya gyara zaman takobin dake rataye a gadon bayansa sannan yasa hannayensa biyu ya kama tsaunin ya fara hawa kansa. A hankali yake hawa tsaunin idan ya yi taku uku zuwa saman sai ya tsaya cak ya dan huta. Ya yin da sarki muraka yaga yadda abokin hamaiyarsa ke hawa kan wannan tsaunin sai shima ya yi koyi da shi ya kama hawa tsaunin. Haka dai suka ci gaba da hawa kan wannan tsaunin suna hutawa har suka kai rabin tsawon tsaunin. Koda suka kallo kasa suka ga tsananin nisan kasa sai hankalinsu ya tashi saboda sun tabbatar da cewa ko yaya suka subuto kasa sunansu gawa. Abu na biyu kuma shi ne idan ba su hanzarta isa saman wannan tsaunin akan lokaci sun debo wannan dukiyar ba to rana zata fadi su fadi a wannan gasar. Koda suka tuna da hakan sai suka ci gaba da hawa kan tsaunin. A wannan lokaci sun nannade tafin hannunsu da tsumma amma saboda zafin ranar da ya daki dutsen tsaunin tsumman ya fara farfashewa kuma tuni tafin hannayen nasu ya cika da kanta. Dama sun cire takalman kafafuwansu don kada santsi yasa su subuce su fado kasa. Ai kuwa nan danan 'yan yatsun Kafafunsu suka kumbura kuma 47 Jarumi da Gimbiya suka yi bakikirin kamar kuna saboda zafin ranar dake jikin dutsen tsaunin. Dukkaninsu sun jike sharkaf da gumi tamkar a cikin kogi aka tsomasu, sai da suka shafe kusan rabin sa'a suna ci gaba da hawa wannan tsaunin wani lokacin idan daya daga cikinsu ya zame ya yi kamar zai fado kasa sai kaji abokinsa ya kurma ihu amma bisa mamaki sai aga bai fado din ba ya ci gaba da hawa can saman tsaunin. A haka dai suka sami nasara hayewa can karshen tsaunin bayan sun sha bakar wahala. Da isar su saman tsaunin suka yi arba da katon kogon dutsen dake kasan sai hankalinsu ya dugunzuma ainun, zuciyoyinsu suka karaya suka ji nadama ta zo musu bisa shiga wannan gasa da suka yi. Ba komaine ya haddasa hakan ba face ganin wasu irin halittu masu kama da dodanni kimanin guda dari uku wadanda suka lullube kogon dutsen samansa da kasansa. Su dai wadannan dodanni kawunansu irin na batoyine, idan suka wangame bakunansu sai kaga ai zasu iya hadiye karamar giwa, hanayensu da kirjinsu sirarane amma cikinsu babbane tamkar an hura balan-balan. 'yan yatsun kafafuwansu da hannayensu dogayene cike da jijiyoyi babu kyan gani dauke da zakwa-zakwan farata masu kaifi da tsini tamkar karfe aka fike, sannan kuma suna da fuka-fukai a jikinsu. Duk da cewa sarki muraka da sarki Ridwan a matukar galabaice suke sakamakon tsananin wahalar da suka sha a wajen hawan kan wannan 48 Jarumi da Gimbiya tsaunin suna yin arba da wadannnan halittu sai kowannansu ya yi wuf ya mikezaune aka fara kallon-kallo a tsakaninsu da su. Ga shi dai kofar kogon dutsen a bude take kuma su sarki Ridwan na iya hango tarin dukiyar zinare da lu'u-lu'u tsubi guda a ciki amma kogon ba zai shiga ba. Ridwan da muraka suka kalli junansu, a karo na farko tunda suka fara wannan tafiya dayansu bace uffan da abokin tafiyarsa ba face kallon harara da tarin kiyayyar zuci da zahiri amma sai sarki muraka ya bude baki yace "Ya kai abokin hamaiyata kayi sani cewa ba zamu iya shiga cikin kogon dutsenan ba face mun hada karfin da karfe" Ridwan yace. "Ta yaya kenan kake nufi?" Muraka yace "Za mu rike garkuwoyinmu a sama, sannan mu hade jikinmu waje guda daya a gaba, daya ya fuskanci baya muna rike da takobbanmu. A haka za mu tunkari cikin kogon dutsennan da gudu suna kawo mana hari muna mai da martani cikin zafin nama da jarumtaka. Idan har muna da rabo da sa'a to lallai zamu sami damar shiga cikin kogo a haka amma fa komai zai iya faruwa, idan ba mu yi nasara ba dayan mu ba zai tsira da ranyuwarsa ba" Sa'adda sarki Ridwan ya ji wannan shawara wacce sarki muraka ya zo da ita sai ya yi shiru yana tunani da nazarinta. Abu na farko daya fado masa a rai shi ne anya kuwa sarki muraka ba so yake ya yi amfani da damarsa wajen taimakon kansa ba? To idan ma ba haka bane ai zai iya yaudararsa a lokacin da ya 49 Jarumi da Gimbiya bashi hadin kai suka sami nasarar shiga cikin kogon ya yaudareshi ya cutar da shi, wata zuciyar kuma sai tace da shi to ai kuma wannan dabarar da sarki muraka ya zo da ita, tabbas ita ce kadai hanyar da za su iya bi su shiga cikin wannan kogon dutsen koda gama aiyana hakan sai sarki Ridwan ya mike tsaye shima muraka sai ya mike tsayen suka kalli junansu,Ridwan yace "Kawai mu yi hakan" Nan take kowannnansu a ciro garkuwarsa daga gadon bayansa ya riketa da hannun hagu sannan suka zare takobbansu da hannayen dama suka hada bayansu. Ridwan ne ya fuskanci gaba shi kuma muraka ya fuskanci bayansu. A daidai wannan lokacin mugayen halittun masu kama da dodanni suka fara yin wani-irin gurnani mai matukar firgitarwa kuma faratan hannayensu da kafafuwansu suka fara kartar dutsen kogon. Nanfa tartsatsin wuta ya fara tashi sakamakon haduwar faratansu da dutsen. Al'amarin daya dugunzuma hankalin Ridwan da muraka kenan ganin idan faratan suka karci wannan dutsen sai ya murmushe, kenan idan suka taba jikin mutum mene zai faru? Kawai sai sarki Ridwan ya kurma uban ihu irin na manya jarumai wadanda ba su san tsoro ba, ai kuwa shima sarki muraka sai ya kurma ihu. Lokaci guda suka falfala da gudu izuwa kofar kogon dutsen. Kaico,bala'i ba a sa masa rana, gobara daga kogi maganinta sai Allah. Lokacin da wadannnan gwarazan jaruman sarakai biyu suka nufi kofar 50 Jarumi da Gimbiya kogon dutsen sai gaba dayansu wadannan halittu guda dari uku suka bude fukafukansu suka taso a sama suka lullubesu suka rinka kai musu sara da suka da faratansu na hannu da kafa. Sarki Ridwan da sarki Muraka suka wanzu suna kare kansu da garkuwoyin hannunsu kuma suna kade wasu haren da takubbansu kuma ba su fasa kutsawa ta cikinsu ba da gudu da dukkan karfinsu. Nan fa wuri ya yamutse in banda karar haduwar faratan halittun da garkuwoyinsu da takubbansu babu abinda kunne ke ji sai kuma karar rurin halittun. Duk da kasancewar su sarki Ridwan gwarazan jarumai masu zafin nama, karfin damtse da juriya sai gashi halittun sun takurasu harma sun fara samun nasarar uankar sassan jikinsu da sukarsu da kaifin faratansu da tsininsa. Sarki Ridwan da sarki muraka suka rinka kurma ihu sakamakon tsananin zafi da zogin da suka ji a jikinsu a lokacin da jini ya rinka zuba a jikinsu, harma jiri ya debe su amma saboda bakin na ci da juriya amma ba su fadi kasa ba. A hakan suka ci gaba da bakin artabu suna banke halittun har suka samu suka shige cikin kogon da karfin tsiya, suka zube kasa cikin matukar galabaita. Suna shiga sai halittun suka јa da baya suka daina binsu kuma suka bace bat tamkar ba su taba wanzuwa a wajen ba. Da kyar sarki Ridwan da sarki muraka suka bude idanunsu suna ganin dishi-dishi koda suka ga jini na zuba a sassan jikinsu kuma jiri bai daina dibansu ba sai kowannen su ya yi sauri ya kama 51 Jarumi da Gimbiya yagar tufafin jikinsa yana daure raunin dake jikinsa domin tsayar da jinin dake zuba cikin matukar sauri. Ba komai ne yasa suke wannan saurin ba face kar rana ta fadi kafin su kai wannan dukiya birnin soman a matsayin sadaki na auran gimbiya falman. Cikin hanzari kowannansu ya dauko damin dukiyar dinare da lu'u-lu'u dake cikin buhu guda alhalin dukiyar dake wajen tafi buhu dubu dari biyar, cikin takaici duk su biyun suka kalli tarin dukiyar saboda babu damar su kara daukar koda buhu dai-dai domin ba zata dauku ba sakamakon nauyinta. Kowannansu a zuciyarsa yace to wai shin ma wannan dukiyar bata fi gimbiya falman daraja bane a wajenmu? Ko shakka babu wani sarki a wannan nahiyar daya mallaki wannan tarin dukiyar. Suna ji suna gani suka hakura da wannan tarin dukiyar suka fito daga cikin kogon dutsen suka nufi Karshen tsaunin domin saukowa kasa. Anan fa suka tsaya cak suka kalli junansu cikin mugun nufi, kowannensu yana goye da dukiyar daya debo, lokaci guda kowa ya kai hannunsa kan marikin takobinsa amma sai suka kasa zaro takubban. A zukatansu kowa so yake ya kashe abokin gabarsa domin ya zamana cewa shi kadaine zai sauko daga kan wannan tsaunin a raye, bisa mamaki sai duka su biyun suka bushe da dariya. Sarki muraka yace "Ya kai abokin hamaiyata ka yi sani cewa idan muka ce zamu yaki juna bayan duk wannan bakar wahalar da muka sha ta dauko wannan dukiyar to tabbbas ragas za mu yi, 52 C Jarumi da Gimbiya dayanmu ba zai cika burinsa ba, zai fi mu sauka kasan tsaunin sannan mu raba wannan gardama" Sa'adda da sarki Rudwan ya ji shawarar da sarki muraka ya zo da ita sai ya yi guntun murmushi a gareshi yace. "Tabbas na aminta da wannan shawarar taka" Yana gama fadin hakan sai kowannansu ya bude jakar guzurinsa ya dauko igiya mai karfi da matukar tsawon gaske cikin sauri suka daddaure igiyoyin a jikin dutsen tsaunin suka ziraro su kasa suka iso har can inda su Boka samasa suke, koda Boka samasa suka ga igiyoyi guda biyu sun fado kasa daga saman tsaunin sai farin ciki ya lullubesu domin sun tabbatar da cewar sarakunansu sun samu nasarar dauko abinda suka zo nema a tsaunin mutuwar cikin hanzari Boka samasa da Boka Aryan suka mike tsaye kowannensu ya daga kansa sama domin ya hango sarkinsa amma saboda nisan tsaunin daga can saman basa iya hang komai. Sarki Ridwan da sarki muraka suka kama igiyoyin guda biyu suka fara saukowa kasa daga saman tsaunin kowannansu na goye da buhun dukiyarsa ta zinare da lu'u-lu'u a matsayin sadakin da zai bayar na auren gimbiya falmin. Sai da suka shafe sa'a uku suna saukowa kasa daga saman tsaunin sannan su Boka samasa suka fara hangosu nan fa farin ciki ya kara turnukesu suka soma kyalkyala dariyar murna. Haka dai su sarakunan biyun suka ci gaba da kama igiyar suna ta saukowa kasa. Ko wannansu sai da hannayensu suka dade suka rinka yin kara saboda rike igiya amma saboda 53 Jarumi da Gimbiya jarumta da naci basu saki igiyarba suna ta kara saukowa kasa. Tsayin daya rage bai fi sauran kamu ashirin ba da kasa sai kaiwa sarki muraka ya shammaci sarki Ridwan ya zaro wata wuka mai kaifin tsiya ya cillata izuwa kan igiyar sarki Ridwan take wukar taje ta yanke igiyar da yake rike da ita ya suboto kasa, shi kuma Boka Aryan ya shammaci Boka samosa ya daki kirjinsa da kafarsa, boka samosa ya fadi

Chapter 3 of 5