Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 5
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels JARUMІ DA GIMBIYA ABDULAZIZ SANI MADAKIN GINI Jarumi da Gimbiya JARUMI DA GIMBIYA Su bakwai ne dukkaninsu sun-yi shigar bakaken kaya sama da kasa, idanunsu Skadai ake gani. Kowannnensu yana rataye da takobi a bayansa kuma suna dauke da wadansu taurari na karfe ma su kaifi da tsini a jikinsu ma su dan yawa. Lokaci guda su bakwai suka dira akan rufin sama na gidan sarautar suka karewa gīdan gaba daya kallo. A kalla akwai dakaru kimanin guda dari uku a tsaitsaye a ko wanne lungu da sako na harabarr gidan masu tabbatar da tsaro. Jaruman bakwaíu suka kalli junansu sannan suka kalli shugabansu wanda akwai alama ta zanen jar tsuntsuwa a jikin rawaninsa, kawai sai shugaban ya nunawa ko wannen su zai nufa da hannu. Nan take suka dako tsalle kasa daga saman gininn kai kace fuka-fukai ne a jikinsu duk da cewa tsawon ginin daga saman zuwa kasa ya kai kamu ashirin da biyar. Lafiya kalau kowannensu ya sauko kasa ba tare da anji motsin durowarsu ba, nan fa suka fara watsawa dakarun gidan sarautar wadannan taurarin na karfe suna zubewa kasa matatta, kai kace wata guba suke busa musu dan ko motsin kirki basa iyaye. Abinda zaifi daure maka kai shi ne zafin naman wadannan jaruman guda bakwai domin ko gani su ka yi badakare zai fada kan wani abu da zai 3 Jarumi da Gimbiya samar da kara wacce zata tona asirin zuwansu sai kaga sunyi sauri sun rukoshi da hannu, sun ajiye shi kasa a hankali. Haka da jaruman bakwai suka ci gaba da bazar da dakarun tsaro na wannan gidan sarauta har suka karar da su, su dari uku nan. Kai tsaye shugaban na su ya tunkari turakar Gimbiya sazira. a Kofar shiga turakar a rufe take kuma dakaru biyune tsaye a wajen. Koda suka hangoshi ya durfafosu sai suka yunkura a lokaci guda. Daya ya zare takobinsa domin ya tare shi, dayan kuma ya kai hannunsa izuwa kan wani kaho dake rataye sama domin ya dauko shi ya busa amman sai shugaban dakarun sumamen ya yi wuf ya zaro taurarin Karfe guda biyu, cikin zafin nama ya watsa musu. Taurarin karfen suka cake akan goshinsu duk su biyun suka sulale kasa matattu. Ita dai wannan babbar kofar ta shiga dakin Gimbiya sazira a rufe take ta ciki da sakatu da makullai. Shugaban dakarun sumame ya sunkuya ya leka ciki turakar ta cikin kafar kubar kofar sai ya hango kuyangin su da yawa a kwance cikin wani katon falo suna ta sharar bacci. Kofar shiga cikin ainahin dakin barci na gimbiya sazira na gaba kadan. Koda ganin hakan sai ya rikide ya zama haske ya shige ta cikin kofar. Yana baiyana a falon ya sake tunkarar kofar dakin gimbiya kai tsaye. Karar takun sawunsa yasa kuyanginta suka fara farkawa daga bacci amma duk wadda ta bude ido tayi arba da shi sai ta kasa mikewa tsaye kuma ta kasa bude Jarumi da Gimbiya baki tayi magana saka makon wata hoda da ya rinka busa musu daga cikin wani lofe dake bakinsa kuma ya toshe hancinsa da rawaninsa. Nanfa kuyangin suka rinka komawa suna kwanciya sakamakon bacci me nauyi da ya rinka daukarsu. Da isarsu kofar dakin Gimbiyar sai ya tsaya cak domin gimbiyar ya hango ta cikin tagar-dakin zaune akan gado ta kura masa idanu. Babu-alamar tsoro ko wata fargaba a tare da ita. A wannan lokaci tana sanye da wata doguwar farar riga barci me bayyana kyakkyawar surar jikinta. Gashin kanta a tsefe yake ya zuba har kasan kwankwasonta. Macece me dara-daran fararen idanuwa hancinta dogone a kasansa dan karamin bakine, kirar jikinta ta kalanguce, kaurin jikinta madaidaici, fatar jikinta mai haskece, sumul sumul tamkar ko kuda bai taba sauka a jikinta ba, tamkar ana tabata jini zai fito. Nan take wannan shugaban dakarun sumame ya dimauce bisa ganin tsananin kyawun Gimbiya Sazira saboda dama bai taba ganinta ba, labarinta kawai yake ji. _Bayan sun yi kallon-kallo na 'yan dakiku ashirin zuwa-talatin sai Gimbiya sazira ta sauko daga kan gadonta ta nufo bakin kofar dakin kai tsaye ba tare da wata fargababa. Tasa-hannunta ta zare sakatar kofar dakin guda hudu ta budeta ta dube shi fuskarta da murmushi irin na mugunta tace "Kaine shugaban dakarun sumamen da ake bani labari na birnin samhar ko?" mamaki ya kama shi ya kasa cewa komai. Jarumi da Gimbiya "An gaya mun cewa sarki muraka yasa an baku horo na wata shida kai da yaranka ku shida domin kawai ku zo nan birnin kamlaz ku sace ni, tabbas na yaba da kokarinku da kuma kaifin sihirinka na tsafi tunda har kuka iya ratsowa cikin gidan sarautar nan harma kai ka sami nasarar shigowa 6angaren turakata. Nasan kun sami nasarar kashe gaba dayan dakarun dake tsaron wannan 6angaren da nake kuma ka sakawa kuyangina bacci me nauyi. Tofa ka sani ba'anan gizo yake sakar ba, idan kana ganin za ka iya daukata da karfin tsiya ko da karfin sihirin tsafi ka kaini wajen sarki muraka babban makiyin mahaifina to ga fili ga mai doki. Daga ni sai kai mu jarraba mu gani, babu wanda zai kawo min taimako, taho mana, zo ka dauke ni idan ka .isa יי Mamaki ya kara kama shugaban dakarun sumamen ya dubeta da murmushi na raini ya bude baki yace "Ya ke wannan 'yar sarki ke kuwa me kike takama da shi har da kike tunanin zaki iya kare kanki daga farmakina?" Gimbiya sazira ta yi murmushi tace. "Ina takama da duk abinda kake takama da shi, amma kasan wani abu sai an gwada sannan ake sanin bambanci a tsakanin aya da tsakuwa. Kai nake jira kawai idan kuma ka karayane, to ka juya ka fice mun na yi baccina da ka katse mun" Koda jin wannan batun sai shugaban dakarun sumame ya fusata ya nufo Gimbiya sazira da nufin ya kamata da hannunsa. Cikin zafin nama ta damki hannun nasa ta murde ta doki gadon bayansa ya tafi taga6 Jarumi da Gimbiya taga zai fadi amma-sai ya tsaya daram ya juyo suka dubi juna yana mamakin irin wannan jarumtaka tata. Kafin ya ankara sai kawai yaga ta dako tsalle daga inda take tsaye tamkar kibiya aka harbo ta kawo masa wawan naushi a fuska. Koda ya goce hannunta ya samu wani gunki me siffarta dake tsaye sai gunkin ya rushe ya zube kasa. Nan fa suka kacame da azababben fada suka wanzu suna kaiwa junansu naushi da bugu hannu da kafa. Abinda ya yi matukar daure masa kai shi ne duk irin salon fadan da ya yi sai yaga itama ta iya irinsa. Zafin namansa da juriyarsa duk sai suka zamo iri daya. A duk sa adda ya sami nasarar naushin jikinta sai yaga ta shanye naushin kuma ta rama nan take cikin dakiku kadan suka hadawa juna jini da majina. Sai da suka shafe dakiku ma su yawa suna wannan gumurzu ya kasa kaita kas kuma ya kasa galabaitar da ita. Bisa dole duk su biyun suka ja da baya saboda gajiya suka yi carko-carko suna kallon juna sakamakon gajiya sai haki suke yi. A wannan lokacine hankalin shugaban dakarun na sumamen ya tashi saboda yasan cewa idan ya kara bata lokaci shirinsu na sace Gimbiya Sazira zai wargaje saboda daya 6angaren na gidan-sarautar-za su iya sanin abinda yake faruwa-anan tunda asuba ta kusa. Kuma har ya hango ragowar abokan aikinsa dakaru shidan sun iso babbar kofar shigowa turakar Gimbiya sazira sun tsaya suna jiransa. Bisa dole ya yunkura cikin zafin nama ya nuna Gimbiya sazira da hannayensa biyu, wata irin iska mai karfin gaske Jarumi da Gimbiyа ta sauka akan ta tana kokarin zukota gareshi. Kawai sai itama ta nuna iskar da hannayenta biyu, take wata jar iska ta tari tasa iskar suka kama hautsinewa. Ya yi iyayinsa amma ya kasa zuko gimbiya har shi da ita suka jike sharkaf da gumi, kawai sai ya saki hannayensa kasa, itama ta saki suka kama haki suna kallon juna kai kace sa'a uku suka shafe suna yin aikin karfi. Shugaban dakarun sumame ya juya zai fita daga cikin turakar sai tace "Idan ka koma birnin kilmaz ka gayawa sarki muraka cewa tunda ya kasa satoni to ni zan zo da kaina na sace dansa Yarima Andaz". dajin haka sai ya juya ya dubi Gimbiya sazira yace. "Ba kasa satoki na yi ba, kwanaki goma aka bani na kai ki can birnin kilmaz kuma yau kwana biyu kacal don haka zan ja da bayane domin na sake yin shiri. Ina mai tabbatar miki da cewa kafin cikar kwanakin goma sai na kaiki gaban sarki" Gimbiya sazira ta bushe da dariya sannan tace "Duk irin shirin da za ka je kayi nima zan yi irinsa anan, ba zaka taba samun nasara a kaina ba, kuma ka sani nima na yi alkawarin da girman gemun mahaifina kafin cikar kwana gomannan sai na shiga har cikin birnin kilmaz na sato Yarima Andaz. Ka sani na sani a tsakanin mahaifina sarki Ridwan da sarki muraka duk wanda ya sami nasarar sace jinin daya tamkar mallake kasarsane, ba zan taßa bari ku mallake kasarmu ba saboda tsohuwar gabar da take a tsakaninmu tun iyaye da kakanni. Kafin ka fita daga nan ina so ka bani amsa amsar tambayayona 8 Jarumi da Gimbiya guda biyu, wane kai a cikin kasar-kilmaz-kuma saboda me ka siyar da rayuwarka domin ka farantawa sarkinku rai? Wane alkawari ya daukar maka har da ka yi wannan kundumbalar haka?" Shugaban dakarun sumame ya yi kamar ba zai ce komai ba sannan yace "Ni ba kowa bane a cikin birnin kilmaz face jarumi me zaman kansa. Ba-zan iya baki amsar tambayarki ta biyu ba, sai mun sake haduwa a karo na biyu" Yana gama fadin haka sai ya juya ya fice daga cikin turakar, Gimbiya ta biyoshi da gudu amma yana isowa inda abokan aikinsa suke su shida sai su duka suka daka tsalle sama suka dira a cikin rufin saman gidan. Nan take itama Gimbiya sazira ta dako tsalle sama tamkar daga cikin baka aka harbota ta dire akan rufin gidan amma sai ta neme su sama da kasa ta rasa. Cikin tsananin bakin ciki ta diro kasa bisa kafafuwanta ta koma cikin turakarta. Adaidai wannan lokacine taji an busa kaho, alamar angane cewa baki sun shigo gidan. A wannan lokaci asuba ta kawo kai. Sarki Ridwan ya na kwance akan gadonsa yana bacci kawai sai ya ji an busa Kaho. Cikin hanari ya mike zaune ya sauko daga kan gadonsa ya dauki alkyabbarsa yasa ya fice daga turakarsa. Yana fita yaga dakaru suna ta rugawa izuwa bangaren da Gimbiya sazira take. Hankalinsa ya tashi ya nufi bangaren da sauri, kawai 'sai ya hango sarkin yakinsa barde kinana ya taho gareshi. Kinana na zuwa daf da shi sai ya zube 9 Jarumi da Gimbiya kasa bisa guiwarsa guda ya kwashi gaisuwa ya mike tsaye da sauri ya kame kamar gunki. Sarki Ridwan yace "Ina 'yata Gimbiya sazira?" Kinana yace "Tananan a turakarta cikin koshin lafiya". "Su waye suka kawo mata hari?" "Wasy dakarun sumame ne su bakwai, sun gudu amma na tura abi sawunsu, sun kashe gaba daya dakarun dari ukun da suke gadin Gimbiya, kuma sun samu nasarar shiga har cikin turakar Gimbiya amma ba su sami nasarar tafiya da ita ba". Cikin mamaki sarki Ridwan yace. "Ta yaya suka kasa tafiya da ita alhalin sun sami nasarar shiga har cikin turakarta?" Sarkin yaki kinana yace. "Banyi bincike akan hakan ba amma ina ganin cewa Gimbiya ce kadai zata iya bamu amsar wannan tambayar" Sarki Ridwan ya yi ajiyar numfashi sannan yace "Sun taba lafiyartane ko kuma sun yi mata wani abun?" Kinana yace. "Ni dai naga jini akan hancinta da lebenta wata kila dai sun dan doketa". "Ka je ka zo mun da Gimbiya bayan ta kimtsa, ku same ni a dakin gani" Kinana yace. "An gama ya shugabana". Sarki Ridwan ya juya ya koma 6angarensa shi kuma sarkin ya kira wani badakare ya bashi umarnin yaje ya sanar da Gimbiya sazira cewar idan ta kimtsa yana jiranta za sy sami sarki a dakin gani, Badakare ya juya da sauri ya tafi isar da sako, 10 Jarumi da Gimbiya shi kuma sarkin yaki kinana ya nufi bangaren da tasa turakar take. ** Lokacin da Gimbiya sazira ta koma cikin wannan babban falo inda kuyanginta ke kwance suna bacci sai ta nunasu da hannunta. Take wani farin hayaki ya lullubesu sai suka farka daga baccin da suka mimmike tsaye zumbur cikin firgici suna kallonta shugabar kuyangin wacce ake kira Dulis ta leka waje ta hango dakarun tsaro kwance a kas matattu ana kwashe gawarwakinsu sai ta firgita ta rugo gaban gimbiya ta zube kasa tace "Tuba nake ranki ya dade, na rantse da darajar mahaifinki ba musan abinda ya faru ba a gidannan" Gimbiya sazira ta dubeta cikin murmushi tace. "Ai ba za ku sani ba, ni kadaice naga abinda ya faru, sarki muraka ne ya turo dakarun sumame domin su sace ni, don haka maza a shirya mun ruwan wanka da abincin kalacina" Durus tace. "An gama ranki ya dade". A daidai wannan lokacin badakaren da sarkin yaki kinana ya aiko ya karaso cikin turakar yana hango Gimbiya sazira sai ya risina ya isar da sako, Gimbiya sazira ta wuce cikin turakarta, badakare ya risina ya mike-tsaye ya juya ya tafi su kuma kuyangin sai kowacce ta kama gudanar da aikin da ta saba yi. Sarki Ridwan na zaune a cikin dakin gani shi kadai yana cin tuffa, sarkin yaki kinana tare da Gimbiya sazira suka shigo. Yana ganinsu ya mike 11 Jarumi da Gimbiya tsaye cikin farin ciki ya bude hannayensa Gimbiya sazira ta fada kan kirjinsa suka rungume juna. Sarki Ridwan ya sumbaci goshinta sannan ya kama hannunta suka zauna tare akan kujerar da yake. Sarkin ya dubi sarkin yaki ya masa wani nuni ga farantin tuffar dake bisa tebur a gabansu. Kinana ya dauki tuffa guda daya bayan ya zauna ya fara ci, sarki ya dauko wata tuffar ya mikawa Gimbiya itama ta karba ta kai baki kamar zata ci sai ta fasa ta ajiye tuffar bisa faranti. Sarki ya dubeta cikin mamaki yace "Me yasa kika ki ci wannan tuffar?" Gimbiya ta yi murmushi tace. "Na ci tuffa da yawa a cikin abincin kalacina da zu kuma a koshe nake sosai". "To ammma dai kya ci ko dan yaya tunda ni ne na baki da hannuna" Gimbiya sazira tace "Ka yi hakuri Abba idan na ci tffarnan koda bata wuce kwayar zarraba zuciyata ta shi zata yi na yi amai" Koda jin haka sai jikin sarki Ridwan ya yi sanyi, sazira ta yi masa wani irin kallo na kurulla domin ta gano wani abu amma sai ya yi sauri ya kauda aknsa ya dubi sarkin yaki kinana yace masa. "Wane sakamako dakarun da ka tura suka bi yan sumame suka samo?" Kinana yace "Sun gano cewa sarki muraka na birnin samhar ne ya turosu su sace gimbiya sazira" koda jin wannan sai sarki Ridwan ya fusata ya mike tsaye zumbur ya dakawa sarkin yaki kinana tsawa yace "Ya aka yi kuka yi sakaki har suka je bangaren da gimbiya take ba tare da kun sani ba?" Sarkin yaki ya dan sunkuyar da kansa kas yace. 12 Jarumi da Gimbiya "Ya shugabana kasani cewa a daren jiya bana nan ka aike ni kauyen Batur kuma ban dawo ba sai gefin asuba, kuma wadannan dakarun sumame suna da karfin sihirin tsafi ni kadaine tsaransu, idan da ina nan ba su isa su shiga bangaren da gimbiya take ba, sai bayan sun gudu sannan na iso cikin gidan sarautarnan Sa'ar da-sarki Ridwan ya ji wannan batu sai ya yi ajiyar numfashi ya koma kan kujera ya zauna a kusa da gimbiya sazira ya dubeta yace. "Ya ke 'yata-a sanina dake baki taba yi min karya ba kuma na yarda da ke dari bisa dari, ina son ki yi mun bayani a nutse kuma ki gaya mini iyakar gaskiya, mene ne ya hana wadannan dakarun sumame samun nasarar tafiya dake?" Ya yin da gimbiya sazira ta ji wannan tambayar sai ta gyara zama gami da gyaran murya. ta dubi mahaifinta cikin nutsuwa tace. "Ya kai Abbana ka sani cewa mafi yawan dare bana yin bacci domin lokacine da nake zama ina karance-karance na littafai na tarihin Kasashen da suke cikin wannan nahiya tamu. Bana kwanciya bacci har sai gari ya waye na yi kalaci sannan nake komawa bacci, ba zan farka ba face idan kai ne ka tura a kirawoni. A jiya-eikin daren ina cikin karantalittafi na tarihin wannan masarautar tamu sai kawai naji motsin dirar wani abu akan rufin sama na Gangaren turakata. Hakan ne yasa na rufe littafina na boyeshi a karkashin matashin kai na gadona. Kawai na zauna ina kallon kofar shigowa turakata, tsawon dakiku masu dan yawa ina zaune 13 Jarumi da Gimbiya a hakan kawai sai na hango wani badakare sanye da bakaken kaya, fuskarsa a rufe, idanunsa kadai ake gani ya nufo kofar turakata. Da isowarsa sai muka hada idanu ta cikin taga, take zuciyata ta buga da karfi na firgita kafin na yi wani motsi ya ratso cikin turakata ya bayyana a gabana. Jikina na karkarwa na dubeshi muryata na rawa nace wanene kai? Mene ne ya kawoka nan? Badakaren ya bushe da dariya yace ni manzone daga sarki muraka na birnin samhar kuma na zo ne na saceki. Na dube shi a nutse nace shin kana da mata? Ya dube ni cikin mamaki yace me yasa kika yi min wannan tambayar? Nace saboda nasan cewa kowane mutum yana son ahalinsa. Tabbas kana da mata kuma kana da 'ya guda daya sunanta Yarsik shekararta goma sha daya a duniya, kana sonta fiye da komai a duniya, shin idan wani ya zo ya saceta ya rabaka da ita ya za ka ji? To ka sani idan ka rabani da mahaifina kaima sai an rabaka da Yarsik. Yana jin wannan batu jikinsa ya yi sanyi ya kasa kamani kawai sai naga ya juya ya fice daga cikin turakata bayan ya nausheni a fuska na fadi kasa. Wannan shi ne dalilin daya saka wadannan dakarun sumamen suka fasa kamani domin su tafi da ni" Sarki Ridwan ya yi shiru yana mai kurawa Gimbiya sazira idanu yana nazari bayan ta gama jawabinta sannan ya yi ajiyar numfashi yace. "Nasan cewa marigayi Boka samasa ya koya miki ilimin sanin sirrin mutum to amma ai wannan ilimin ba ya aiki face ka taba tafin hannun mutum da tafin hannunka, ya aka yi ke kika iya sanin sirrin 14 Jarumi da Gimbiya rayuwar wannan badakare da ya zo saceki?" Gimbiya sazira ta yi murmushi tace. "A daren da boka samasa zai mutu ai kasan cewar na je bankana da shi,kuma mun kadaita da shi a cikin turakarsa, a wannan lokacin ne ya kara kaifin wannan ilimin a gareni ya-tabbatar min da cewa ko kallon idanun-mutum-na-yi zan iya sanin komai na sirrin rayuwarsa" koda jin wannan batu sai hankalin sarki Ridwan ya tashi yace a zuciyarsa kenan yanzu gimbiya tasan-dukkanin-sirrikana na rayuwa da nake boye mata? Kai ban yadda da hakanba har sai na gwadata na gani. Koda gama aiyana hakan sai sarki ya dubi sazira yace. "Shi kenan na sallameki za ki iya tafiya, ni da sarkin yaki za mu tattauna akan yadda za mu tsananta tsaro a gidannan domin kada a sake kawo miki hari" Gimbiya ta yi murmushi ta mike tsaye ta fice daga cikin dakin suka-bita da kallo har ta fita suka dubi junansu suka yi shiru. ** Al'amarin wadannan dakarun sumamen guda bakwai kuwa bayan sun gudu daga cikin gidan sarautar birnin kilmaz sai suka bayyyana tsulum a cikin daji inda suka daure dawakansu. Kowannansu ya yaye rawanin dake kansa. Shugaban na su saurayine matashi ma'abocin kyawu da kwarjini da kuma sura irin ta cikakkun jarumai ana kiransa da suna Lurwan. Kai tsaye ya nufi kan wani dutse ya je ya zauna ya yi tagumi yana tunani. Suma sauran dakarun sumamen su shida sai suka zo suka zazzauna a kusa da shi suka yi jugum! Kai kace 15 Jarumi da Gimbiya zaman makoki ake yi. Tsawon kimanin dakika arba'in dayansu baice uffan ba. Sannan daya daga cikinsu mai suna zainur ya dubi jarumi lurwan yace. "Ya shugabana gaba dayanmu jikinmu ya yi sanyi ai bamu taba sanin cewa gimbiya sazira jaruma bace kamar haka, kuma tana da karfin sihiri da tun farkoma ba za mu yi gangancin biyoka zuwa wannan aikin mai hatsari kamar haka ba" koda jin wannan batu sai jarumi lurwan ya fusata ya dakawa zaunur tsawa yace "Kada ka gaya mini maganar banza mana. Gabadayanku ku shidannan kudade na baku ma su yawa wanda baku taba mallakarsu ba sannan kuka amince kuka biyoni izuwa wannan aikin. Kusani cewa mahaifiyata sarki muraka ya tsare domin na yi masa wannan aikin idan na ki yin wannan aikin kasheta zai yi don haka ta kowane hali sai mun koma cikin birnin kilmaz mun sato gimbiya sazira idan kuma kuna ganin cewa ba za ku iya sake komawa ba to kowannenku ya biyani kudina dana ba shi darham dubu goma-goma yanzu take". Lokacin da barde zainur suka ji wannan batun sai duk su shidan hankalinsu ya dugunzuma suka rasa abinda yake musu dadi a duniya. Lurwan ya sake dubansu yace "Sauran kwana takwas wa'adin da sarki murata ya diba mini ya cika. To ni na baku kwana uku ku gama yanke shawara domin a kwana na uku za mu koma cikin birnin kilmaz mu sato gimbiya sazira, so nake a cikin kwanaki biyunnan na gama tunanin dabarar da zamu yi mu sami nasara ba tare da mun sake fuskantar wata 16 Jarumi da Gimbiya matsalarba. Ku tashi ku fara kafa mana tanti ni zan shiga cikin daji na farauto mana nama da za mu gasa" Yana gama fadin hakan sai ya mike tsaye ya dauki kwari da bakan sa ya nausa cikin daji. Zainur da 'yan uwansa suka bisa da kallo har ya kule a cikin dajin sannan zainur ya dubi sauran abokan tafiyar yace-musu "Anya kuwa jarumi lurwan bai samu tabin hankali ba? A ina za mu iya samo dinare dubu goma-goma da ya bamu mu dawo masa da su alhalin duk munyi bukatunmu da su a can birnin samhar. To ma wai wane irin sabon tunani zai yi wanda har zai iya samun nasara sato gimbiya sazira? Juma'ar da za tai kyau ai tun daga laraba ake ganeta" Daya daga cikin jaruman shida me suna komaru yace. "Mun riga mun siyar da rayukanmu tunda mun karbi kudinsa akan wannan aiki don haka dolene mu cika masa alkawarin in ba haka ba kuwa sai dai mu gudu mu barsa mu bazama zuwa wata nahiyar ta duniya mu hakura da mahaifarmu da danginmu" Zainur yace "Hakan ba zata taba faruwa ba, ku tashi mu fara aikin kafa tanti". Ba tare da wata gardama ba kuwa sai suka mike tsaye suka fara aikin kafa tantuna. ** Al'amarin sarki Ridwan da sarkin yaki kinana kuwa bayan Gimbiya sazira ta fice daga cikin wannan dakin gani ta bar su, su biyu rak sai sarkin Ridwan ya mike tsaye yaje ya bude wata durowa ta karfe dake jikin bangon ya dauko wani akushi na 17 Jarumi da Gimbiya sihiri wanda a rufe yake kuma ba a budeshi. saman akushin akwai kofofi guda biyu rak. A Shi wannan akoshin an sasssakashine daga danyen lu'u lu'u sai sheki yake yi. A gefensa guda bakwai akwai wani bututu wanda inda za'a zuba ruwa ta cikin wannan kofofin guda biyu to zai iya zurarowa waje ta cikin bututun. Sarkin Ridwan ya zo ya ajiye wannan akushin a gaban sarkin yaki kinana sannan ya zauna ya dubeshi yace. "Ya kai sarkin yaki shin kasan ko wannan akushin na mene ne?" Kinana ya yi dan guntun murmushi yace "Ranka ya dade na sani mana, wannan ai shi ne akushin sihiri na mallakar wannan nahiyar gaba daya. A cikin waannan kofofi guda biyu dake samansa kana bukatar ka diga jinin Gimbiya sazira da jinin Yarima Andaz na birnin samhar, idan aka diga jinin wani hayaki zai tashi ya fito ta cikin wannan bututu ya baibaye jikinka. Da zarar hakan ta faru duk kasar daka yaka a wannan nahiya sai ta dawo karkashin ka, kai

Chapter 1 of 5