Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 4
gari inda gidan gonar dan uwansa take wato mahalfin Lashmaira, Yana isa ya iske matarsa ta haifi Lasmaira, dan uwannasa nata na ruke da jaririya yana ta murna da yiwa Allah godiya. Koda ya hango dan uwansa Sarki bisa doki kuma acikin shigar yaki sai hankalinsa ya dugunzumaya mikawa Ungozomar jaririyar ya ruga ya tari Sarki ya tambyaeshi yana mai cewa “shin harin surname aka kawo manane? Cikin alamun tsananin damuwa Sarki y ace ai inda harin sumamame ne dab azan so na sanar da kai ba ni zanje nayi maganinsu, shu’umar macjiyar nance Burukul karsum ta shigo take ta cinye mutane, koda jim wannan batu sai mahalfin Lashmaira ya juga da baya aguje ya shiga cikin wani daki agidan gonar, jim kadan sai gashi yya dawo acikin gagarumar shigar yaki, kawai sai ya tukari inda dokinsa yake da nuffin ya kwance shi ya hau. Koda ganin haka sai Sarki Abu zaiyan ya **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** ruga gareshi ya riRe dokin nasa ya dubeshi alokacin da kwalla ta cika masa ido yace "haba yakai dan uwana shin ka.manta ne da wasiyar da mahalfmmu yabar mana cewar kada mu kuskura muyi gaba da gaba da wannan macijiya banzo na sanar da kai zuwan tab a dan kaje ka yafeta saboda tuni na dauki mataki, na tara malaman garinnan suna ta yin addu'a kuma na tura dakaru da yawa suna yafi da ita" Lokacin da sadauki Hizanu mahalfn Lashmaira yaji wannan batu sai sai shima kwalla ta cika masa idanu ya dubi Sarki Abu zaiyan yace "yakai dan uwana shin ka mantane cewa nine Sarkin yakin wannan garin" haKline akaina na futa na tari wannan muguwar macijiyar nasan baka sone na mutu shiyasa kake so ka hanani naje na yafeta, shin su dakarun daka tura su yaketa basu da 'yan uwane agarin? Suna da 'yan uwa suna da mataye da 'ya'yaye kamar yadda nima nake dasu, raina baffi nasu darajaba, saboda ni su zaka turasu su hallaka amma ni kaki turani? Koda sadauki Hiziyan yazo nan ajawabinsa sai Sarki Abu zaiyan ya rungumeshi kuma ya fane da kuka yana mai cewa "yakai dan uwana haKika duk --- abin da ka fada gaskiya ne amma idan baka manta ba mahaifinmu ya gargademu akan cewa duk mutumin da yai gaba da gaba da wannan shu’umar macijiyar sai ta hallalashi, Hizanu ya janye jikinsa daga cikin na Sarki Abu zaiyan yace “wannan gaskiya ne amma kuma ya gaya mana cewaa duk ranar da ta shigo garinnan babu abinda zaisa ta dainafarma ta juga da baya ta fice face anyi mata rauni ajikinta kuma kasani cewa ni kadaine zan iya yiwa wannan macjiuar rauni. Koda jin. Koda Sadauki Hiziyan yazo nan a zancensa sai jikin Sarki yayi sanyi ya kasa cewa komai, nan take Hiziyan yaje gaban mahaifiyar Lashmaira tana rike da jaririyarta a hannu ta fura mata idanu alokain da kwalla ta ciki mata ido, Al ‘amarin da fara karya zuciyar Sadauku Hiziyan kenan ya sumbaci mahaifiyar Lushmaira sannan ya sumbaci jaririyar sannan yace “yake matata idan ‘yata ta girma na umaree kid a ki gaya mata cewar ina mai neman ga fararta bisa na maid a ita marainiya tun kafin ta taso ta san mahaifinta, ki gaya mata cewar na sallama rayuwata ne dan na cici rayuwar miliyoyon al’umma musulmai idan Allah ya rayata kuma ta **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- isă aure ină son ta auri găgarumin Jarumi wandă yâyi jărumtăkă kwătănkwăcin wăcce năyi ko wăddă tăfi tăwă, wănnăn shi ne burină kumă shi ne fătănă dă nă dăde ină yiwă wănnăn jăririyă tămu”. Să’addă Sădăuki Hizănu yăzo năn ăzăncensă sai hawaye ya zubuwă măhăfiyăr Lushmăiră ta sumbăci goshinsă tă ace “Ubăngiji Allăh ya cikă măkă burinkă, yăkăi mijină kayi săni cewă wănnăn yăki dă zăkă je kayi yănzu dă wănnăn macijiya ăikin ne nă săhăhădă sabodă hăkă zăkăyi mutuvă irin wăddă akeso ăbăr alfăhări ăgăreni dă kumă ‘yărkă damă dukkanin musulmăi kayi săni cewă wănnăn hawaye dă kăgă ină zubărwă bă wăi ină zubărwă băne dăn zăkă mutu bă ăaid ăn kăwăi tsănănin săbo,shăkuwă, dă făunăr dăke tsăkanină dă kăi. Kodă tăzo năn ăzăncenta sai ta rungume shi ă jikinta dă kyăr Hizănu ya 6ăn6ăreta dagă jikinsă ya komă wajen dăn uwansă Sărki Abu zaiyăn sukă rungume jună sună kwăllă sănnăn sukăyi bănkwănă nă fărshe. Năn take Sădăuki Hizinu ya kămă dokinsă yăh ăye kumă ya zăbureshi dă gudun zuwă cikin gări cikin săuri --- shima Sarki yabi bayansa aguje, Alokacin da Sadauki Hizanu ya isa ciki n gari sai ya iske garin acikin mugun hali, domin mutane sun dīmauce iface iface da guje guje yai yawa ya cika dodon kunne gidaje ma bata barsu ba domin bi take ta kansu tana rugujewa kamar antsalitse man shanu akan dutse haĀika girman wannan macicijiyar ya wuce tunanim mai tunani. Jinin mutane kuwa sai malala da gudu yake aĀasa tamkar teku ta баlle, Koda ganin wannan ala’amarin sai Sadauki Hizinu ya fusata ainun ya kama kwarara uban ih ya zaburi dokinsa da gudu izuwa hanya da yaga mutane sunfi tahowa dagudu, ashe kowa macijiyar nan na wannan bangaren, Koda Sadauki Hizanu ya iso inda macijiyar take tana tahowa da gudu mutane na ta kokawar neman boya shi sai ya tsaya cak ya riĀe linzamin dokinsa alokacin da dokin nasa ya tsorata ainun ya kama tirjiya da haniniya bisa ganin macijiyar, Koda macijiyar taga Hizau ya tsaya cak agabanta ko alamar tsor babu a tare das hi sai itama ta tsaya ta dāga kanta cansama izuwa **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** Kololowa suka fara kallon kallo ,kawai sai Hizanu yayi bisamilla yana mai zare takobinsa cikin bakin zafin nama macijiyara ta kawo masa sura da bakinta da nufin ta hadiyeshi. Hizanu ya wuf ya bar kan dokin yana maid aka tsalle can gefe daya aikuwa sai macijiyar ta gatsa dokinsa Hizanu ta rabashi gida biyu tamkar wuka akasa akai yankashi nan take jinin dokin yai fallatsiakan fuskar Hizanu yayi masa wanka duk jikinsa ya rine da jinin dokin, cikin hanzari Hizanu ya goge jinin fuskar ya gyara tsayuwarsa yana mai fuskantar macijiyar acikin shakka da fargaba domin ya fuskanci cewar masifar wannan macijiyar ya wuci duk yanda yake tsammani aikuwa sai macijiyar ta jeho jelarta ta baya izuwa kan Hizanu da nufin ta makeshi, cikin shammace. Kawai sai taga Hizanu ya daka tsalle sama ya dira ajikinta yana mai falfala gudu domin ya isa inda kanta yake, kai kace kanwani tsauri yake hawa. Koda macijiyar ta gane cewa so yake ya isa inda kanta yake domin ya cutar da ita sai ta rinfa mako jelarta don da bugoshi fasa amma saboda bakin zafin manasa sai ya rinfa shawagi **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- akanta yana kaudewa jelar tata sai dai kaji shu... faf.. fat..tana zane. jikinta da kanta amma ta kasa makoshi kasa, sai da aka dauke lokaci mai tsawo a haka gashi dao Hizanu ya kasa isa inda kan macijiyar take ita kuma ta kasa makoshi kaasakuma saranta yake da takobi amma kamar dutse yake sara sai dai kaga taratsatsin wuta na tashi. Tta kanta macijiyar al'amarin yai tsananin bata mamaki domin bata taba haduwa da akadrrin jamuri ba wanda ya zame mata alakakai ta kasa hallakashi acikin abinda bai wuce dakalka dari da tamaninba sai yau. Koda macijiyar ta rasa yanda zatayi da Sadauki Hizanu sai wata dabara ta fado mata ta kama birgima akasa, ind ba don Hizanu na mutukar zafin nama bad a tuni ta turmusheshi aksa tayi rugu rugu dashi, Koda yaga ta fara wannan birgima sai ya falfala da azababban gudu ya nufi inda wata doguwar ganuwa take, nan fa suka kasa tsare tana kai masa cafka da bakinta yana gocewa kuma tan a kai ma sa maka da jelarta yana kaudewaduk abinda nacijiyar ta buga sai ya wargazaa haka har suka isa inda ganuwar take --- **TURBAR GASKIYA** sai Hizanu ya kama hawa wannan ganuwar kamar yanda kadangare ke hawa bango aikuwa sai itama wannan Macijiyar ta fara kanamade wannan ganuwar ta rinka yin sama suka kasa tsere ita da hizanu yana azababbabab gudu akan ganuwar tana biye dashi yazamana cewa tazarar da ke tsakaninsu bata wuce kamu biyar ba, Kokarin macijiyar shine ta kamo kafafunsa da bakinta ta fara hadiyeshi amma sai abu ya gagara har suka kusa isa karshen Ganuwar Ita wannan ganuwar an ginata ne da wani rin dutsen wuta mai tsananim kaurin gaske dalilin da yasa Macijiyar ta kasa rugozata kenan domin agaba daya birnin na Baitul Haura! babu wani gini mai kaurin wannan ganuwa. Hizanu yasan da hakan shi yasa yaja macijiyar izuwa can, abinda bata sani ba shine dabara yayi maya doin ta kawo kanta kusa dashi yasamu inda zai yitmata illa, koda ya isa karshen ganuwar sai ya sake jikinsa ya nufo kanta yanda shi ma kansa ya san idan ya runtumo sai ya karairaye saboda nisan dake tsakaninsu saman ganuwa da kasanta, Hizinu yana sama ya saita talobinsa izuwa dio guda na wannan macijiyar. Aikuwa **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- kafin macijiyar ta dauki wani mataki tuni tsinin takoin nan ta shiga cikin idon nata, take ruwan ido ya fashe jini ya kama bulbulowa Macijiyar tayi wani irin ruri mai tsananin frigitarwa alokacin shi ma hizanu ya kama iho alokacin da yaga ya taho fasa lu...kawai sai macijiyar tayi amfani da jelarta ta cafke Hizanu da kanannadeshi kawai sai ta dinga matseshi yana ji yana gana: ta dinga karairaya masa dukkan fasusuwan j'ku.sa, jun yana ihu da motsi har sai da ya daina. Ita kuwa wannan macijiyar bata daina wannan ihu da ruri ba sakamakon tsannain zugi da take ji, said a ta tabbatar da cewa Hzanu ya zama gawa samani ta warbar da gawarsa a fasa ta kama jan jiki a hankali a hankali ta nufi hanya fita daga cikin birnin gaba daya cikin tsannain bafkin ciki ta zama mai ido daya. Duk wannan abu day a faru Sarki Abu zaiyan na labe abayan wani rusanshe gini yana kallo. Tun sa'adda yaga macijiyar ta sami nasara r kanannade dan uwansa Hizanu sai ya fara kuka domin yasan cewa muuwazaiyi. Koda macijiyar ta fluce daga birnin gaba daya saiSaarki Abu zaiyan ya ruga izuwa inda **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** gawar Hizanu take ya dauketa ya rungumeta a kirjinsa ya fashe da matsanancin kuka tamkar ba zai daina ba. Tun daga ranar da wannan abu ya fau macijiyar Burkul karsum bata sake shigowa cikin wanan birnin ban a Baitul Haural dare da rana tana cikin kogi na dajin siril maut . wannan shine asalin yadda mahalfin Gimbiya Lushmairat ya sara rayuwarsa. Said a sui Sarki da Yarima suka shafe sa'a daya da rabi suna wannan bakin gumurzun har suka face daga cikin gidan sarauta suka tsinci kansu a tsakiyar filin birnin inda wannan doguwar ganuwar take, koda yarima yay Arba da wannan ganuwa acan nesa dashi kad'an sai ya mike zumbu ya fallala da gudu izuwa inda ganuwar take aikuwa sai yarima ya kama hawanta tamkar Kadangare na hawa bangokamar yanda marigaye Sadauki Hizanu yayi ya hauta ashekarun baya da kyar sarki ya dinga kwakkwayan Yarima har ma yaringa zamewa kamar zai fado kasa amma saboda naci da juriya sai yaci gaba da bin yarima. A wannan lokaci gaba daya mutane garin suka fifo suna kallin ikon Allah cikin tsannan **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** mamakidomin a tarihin wannan ganuwar in banda marigayi sadauki babu wanda ya taba hawanta har ya kai Karshenta, idan ana so a nau ganuwar ta dole sai anyi amfani da igiya , haka dais u Sarki da yarima suka ci gaba da hawa kan ganuwar Koda suka iso rabin tsawanta sai Sarki ya kakare wato ya kasa ci gaba da hawan har said a ya isa can samanta ya dirge acikin gininta, Koda yarima ya leko Kasa yaga irin nisan dake tsakanin ta sama da Kasanta sai ido ya raina fata, hankalinsa ya dugunzuma ainun domin bai gat a hanya da zai iya saukowaba, shi kansa Sarki da ya makale atsakiyar tsawan ganuwa idan ace zai saki hamunwansa ya fado Kasa hallaka zaiyi, jama'arjama'ar dake gurin suna kallon abin dake faruwa sai suka kama sallallami domin suna ganin cewa tabbas a yau dai Sarki da yarima sun tafka babban ganganci wanda zai zamo sanadin ajalinsu, lokacin da sarki ya dubi Kasa kuma ya dubi can sama inda yarima yake sai hankalinsa ya dugunzuma ainun domin ya fahinci cewar Yarima ba zai iya saukowa ban an fa ya fara tunanim mafita , kawa si ya daga kan sa sama gami da daga hamunsa guda daya dayan kuma na rike da ganuwar yayiwa yarima **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** day a sallamo kasashi kuma ya café shi. Koda ganin haka sai zuciyar Yuarima a karaya yaga ceva ta yayay Sarki zai iya café shi da hamun daya alhalin shi kansa ma lilo yake ajikin ganuwar a inda yake. Nan fa yarima ya npke a lokacin da Sarki key a fitoshi da hamu Adai dai lokacinne labara ya riski Gimbiya Lushmairat cewar ga yarima da sarki sun hau kan ganuwar har ma yarima ya fure karshenta, koda jin wannan batu sai Gimbiya ta mike zumbur ta ruga da gudu izuwa filin da abin yake faruwa. Tsakanin gimbiya da Yarima Zaiyan ba'a ga maciji banda kushe da hassada babu wani fahintar juna ba wani abu bane ya janyo hakanba face yadda Lusmaira take yiwa mazaje gori agarin tana cewa duukkkaninsu matane babu namiji ko guda daya daya tunda an rasa jarumi da zai iyayin irin Jarumtakar da mahalfhta yayi, wannan tsa duk inda suka hadu da yarima sai 'yar tsama. Bugu da Kari shi ne Yarima Zaiyan ne koda wasa bai taba nuna son Lushmairat ba duk da cewar kar samarin garin sun kidime sun d'mauce saboda ita wasu ma har nema suke su **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** zauce dan basu da aiki sai sai begen ta da rera mata wafoki abinda ya daurewa Lushmaira kai kuma ya fusata ta ainun shine ko a hanya suka hadu da Yarima sai yak au da kai kamar baiganta ba wanni lokacin bangazar juna suke ta wuce, kai in ba don ma alakar musulunci bad a Magana ma basa su dinga yi ba duk da kasancewarsu 'yan uwa juna, Ita tana takama da kyaunta da kuma kasancewarta jinin sarauta shi kuma yana takama da jarumtakarsa da saurauta. Har Gimbiya Lashmaira ta isa filin gurin Yarima da sarki sun kasa saukowa daga kan wannan ganuwar kuma asannann hankalin kowa ya dugunzuma ainun an rasa yadda za ayi a ceto rayuwarsu Sarki wasu sun fara bayar da shawara a samo igiyoyi a cilla musu su kuma su daura ajikin ganuwar amma kuma Sai akaga cewar yin hakamma abune mai vuya domin kafin su samu nasara cafkar igiyoyin ko kuma a afokarin kama igiyoyin zasu iya subutowa fasa, musamman Sarki wanda tuni ya fara gajiya saboda reto yake ajikin Ganunwar, Koda gimbiya Lashmaira ta fahinci abinda ke faruwa sai tayi murmushi nan take ta **ABDUL'AZIZ SANIM/GINI** --- kwalawa wasu dakaru si goma kira wadanda suka kasance majiya karfi ta umaree su das u ruga su dauko raga. Cikin abinda balfi rabin sa'a ba suka je suka 'dauko raga, da zuwansu sai tayi musu jagora suka je daidai inda ganuwar take suka yi Kawanya ruke da ragar A samanne ta daga kanta can sama kuma tayi musa nuni das u fado cikin ragar, batare da fargabar komai ba Sarki ya fara sallamowa Kasq shima yarima sai ya dako tsalle ya subuota Kasq shu... Kusan lokaci iguda duk su biyun suka fado kan wannan ragar a cikin foshin lafiya, koda ganin haka sai mutane suka rude da kabbara akq kama farin ciki da yiwa Allah godiya. Koda yarima ya dira daga kan ragar sai ya matso gaban Lushmaira ya dubeta fuskarsa a murtuke yace "me yasa kika cec rayuwata alhalin kincc kin tsani duk samarin garinan? Koda jin wannan tambaya sai gimbiya ta dubeshi cikin murmushi akaro na farko tun da saninsa da ita tace "na ceci rayuwarka ne saboda dalilai guda biyu, Dalili na na farko shi ne ina son na ceci rayuwar Sarki a matsayinsa na Kanin mahaifina **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- kuma wanda yako mutukar kaunata tamkar shi ya haifeni, dallii na biyu kuwa shi ne na cece ka ne kawai saboda. naga kayi irin jarumtakar da mahaifina yah au kan wannan ganuwar ne ya fure karshenta kamar yadda kayi ya sallamo fasa ya soke idon macijiya Brukul karsum ya ceci rayuwar al’ummar birnin nan wato ya sadaukar da rauwarsa domin ceto rayuwar jama’a. kai ne mutun na biyu da ya iyahawa karshen wannan ganuwar, yanzu abin day a rage agareka na daina kyararka da tsanar ka shi ne ka soke daya idon macijiyar Burukul karsum. Koda gama faďin hakan sai gimbiya Lushmaira ta juga da koma izuwa cikin gari, jama’a kuwa sai suka rugo izuwa wajen yarima suka dāgashi ana kabbara ana yi masu jinjina bisa wannan jarumtaka da sukayi tahawa kan wannan ganuwar wanda ta gagari kowa hawa, Ana cikin wannan haline manzo ya iso daga birnin Hizuba daya daga cikin masu gadin ne yayi masa jagora a fasa suka durfafo inda su Sarki suke yana ruke da wasika, da isowar manzon gaban Sarki sai ya zube fasa cikin gimamawa ya kwashi gaisuwa saman ya mikawa wasikar. **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** Sarki Abu zaiyan ya karbi wannan wasikar da hannunsa ya budeta ya karantata yana gama karanta wannana wasikar sai ransa ya baci nan take zuciyarsa ta kuma tafarfasa kamar zata fone. Koda ganin haka sai yarma yai wuf ya zare takobinsa da nufm da nufm ya sare kan wannan amnzo day a kawo waskar saboda zargin ko safon ne ya dake cikin wasikar ya aibata Allah. Cikin hanzari Sarki ya ruke shi y ace “ai ba akashe manzo ko afilim yaki idan basu taba addininmu ba, Mafarkim da kayi ne ya tabbata, lallai lokacin yaki ne yazo domin bukatar da suka zo mana da ita indai nki biya musu ita sai munyi yaki dasu. Nan take Sarki ya sake karantawa su Yarima wannan wasika afilim kowa yaji, bayan y agama karanta wasikar sai ya dubi wani hadimansa yace dashi “akai wannan Manzo masauki a bashi abinci” sarki ya sake duban wani Hadiminnsa daban yace “kai kuma kaje ka sanar da ‘yan majalisa su sameni a Dakin Gani kuma kaje Unguwar ‘yan gudun hijira Ka gaya masu har iyalansu suzo fada, Hadimin ya duka yace angama ya shugabana” **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** nan take shima ya ruga domin cika wannan umarnin na Sarki, Sarki da Yarima kuwa tare da wasu tsararun Dakaru sai uska nufi Fadar Kai tsaye. Lokacin da 'yan majalisa suka cika a dakin Gani gaba dayansu ga Sarki da Yarima zaune agabansu sai aka bude taro da addu'a saman Sarki yai gyaran murya yace "To wasunku dai sunji abindake cikin wannan wasikar da Sarakunan da suka makwantaka damu suka rubuto ga wanda bai jib a yanzu zan mainatabayan nan kuma ai ku kawo shawarwari bida abin da kuke ganin zai fishshemu. Nan take Sarki ya zaro wannan wasika ya sake karantawa afili kowa yaji, nan fa Dakin gani yayi tsit aka rasa wanda zaice komai sai yarima ne ya numfasa ya mike tsaye ya dubi 'yan majalisa daya bayan daya yace "ni atawa shawarar kada mu kuskura mu mikawa wadannan jama'a mutun miliyan bakwai wadanda suka karbi addinimnu tare da dukiyoyinsu da ivalanu, dalilina shi ne idan muka mika sum un nuna muna jin tsoro wadannan abokan gaba namu sun sami logomnu kenan da nan gaba masu zo su iya kawo mana **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- hari, abu na biyu idan muka mika wadannan mutane addinin musulunci zai sami rauni a Nahiyar nar gaba daya, yakamata ace duk kanin musulmi bazai ji tsoron komai da kowa ba akan addininsa tunda ya tabbatar da cewashi ne akan TURBAR GASKIYA baza muje tsoron abokan gaba ba koda kuwa gaba daya wadannan kasanshin da ke kewayae da mu zasu yi mana rubdugu, mun dogara ga Allah kuma kun yi sani cewa duk wanda ya dogara ga Allah zai iya masa abinda ya gagareshi”. Koda yarima Zaiyan yazo nan azancensa sai dakin taron ya rude da kabbara kowa ya nuna cewayana goyan bayan dari bisa dari, Al’amarin day a jefa Sarki da yarima cikin tsananin farin cikikenan, Sarki ya sake yin gyaran murya a akaro na biyu sannan yace yanzu idan har yaki nan ya tabbata ina son Yarima ya jagoranci rundunar mayakanmu saboda kun sani cewa tun da mutuwar Dan uwana Sadauki Hizanu ban dana wani Sarkin yakin ba in har Yarima ya samu nasarar wannan yaken to shi ne Sabon sarkin yakimnu”. Ko da jin wannan batu sai fadar ta rude da kabbara da kuma fatan samun nasara, shi kuwa **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- Yarima ji yayi kamar aan yaye masa dukkanin bakin cikin san a duniya sai ya ayyana aransa cewa komai rintsi da tsamanin sai ya san yanda yayi ya samu nasara awannan yakin. Nan take Sarki ya salami ‘yan majalisar bisa cewa za aika da wasikar raddi ta yaki gasu Sarki Madhan. Bayan ‘yan Majalisa sun waste daga cikin dakin Gani ya rage daga sarki sai Yarima kadai sai Sarki ya tura aka kirawo masa wadannan mutane su miliyan bakwai wadanda sukayi hijira daga kasashen makotan guda uku suka karbi addinin Musulunci, gaba daya wadannan mutane sai suka taro a fada gaba Sarki da yarima. Sarki ya dubesu ya ce ‘yaku wadannan baki namu masu alkarka kuyi sani cewa Sarakunan kasashenku da kuka baro sun aiko mana da wasika akan mu basu ku da ivalanku da dukkanin dukiyarku ko kunta su zo su yakemu, shin kun zaci ku ci gaba da zama damu anan da dukiyayoyinku da ivalanku? Koda jin wannan tambaya sai gaba dayan mutanen sukayi shiru aka rasa wanda zaice kala, kawai sai suka dare suka bayar da hanya a tsakiyarsu. Nan take sarki da yarima suka hango --- **TURBAR GASKIYA** wata mace acikin bakaĕtin tufafi idanunta kawaĕ ake gani, Koda tai so daf da Sarki da yarima ai ta rissina ta gaishesu cikin girmamawa saman ta yaye fuskarta, Koda Sarki da yarima sukai arba da fuskarta sai suka cika da abin al’ajabi saboda ko a tarihi basu taĕa ganin macen da ta kaita kyau ba, kai hatta inda gimbiya Lashmaira zata zo ta tsaya a kusa da ita da sai kyawun Lushmaira ya disashe ta zama mummuna. Kyakyawar budurwa ta buĕe baki cikin zazzakar murya mai dan karan dadī da zaĕti tace “ sunana Shadilat, mahaifina kuma shine attajirin da yaĕt gaba dāyan attajiran dake wannan nahiyan arzki kuma yana zaune acikin birnin Hizuba, sam̃nai ya kasance dan uwa ga Sarki Madhan, ko shi kansa Sarki Madhan bai san da wanzowata ba a duniya domn tun daga ranar da aka haifeni mahaifina ya boyeni bai yarda wani mahaloĕti ya sake ganin fuskataba ko jikina face shi da mahaifiyata har na girma na zama cikakkiyar budurwa idan kuwa mahaifina zai fita dani izuwa kasuwa ko wani guri sai na rufe idanuna yadda babu wanda zai iya ganin fuskata **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** hatta wadannan mutane da suka kasance abokan hijirata basu taba ganin fuskar tawa ba gaba daya wadannan jama'a da kuke gani basu samu dammar yin hijara daga garuruwansa said a taimakon mahalfina domin kuwa said a ya biya dakarun kowane bimiyakai wannan Sarki mai adalci mahalfina ya shaidamin cewa anan garinne kadai zan iya baiyana kaina ga jama'a na zauna lafiya nayi rayuwa yadda kowane da adam yake yi aduron fasa cikin zaman lumana idan bah aka ba kowa masoya su za su sace ni, ayanzu mahalfinawa yana so ya kwaso dukiyarsa gaba daga birmin Huzuna ya dawo nan da zama domin ya karbi addinin musulunci wato addinin gaskiya amma ya kasa saboda Sarki ya zuba masa matakan tsaro ya sa ido akanshi sosai sama da komai na rayuwar sarki matakan tsaron da yasa masa sun yawaita har takai da koda numfashinsa akan idonsu yakeyi dan haka bai isa ya Ketare suba. Daga cikin dukiyar mahalfina abin da nazo dashi nan nake juyawa akasuwa daga cikin arzikinsa baffi kaso daya daga cikin goma ba ina tabbatar maka da cewa in dai mahalfina ya samu dammar dawowa nan tare da manyan hadimansa **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- da dukiyarsa sai wannan birnin mai albarka ya habaka a akasuwanci ninki yadda yake a yanzu, ina mai neman alfarma guda daya jal a wajenka yakai wannan Sarki mai daraja, Koda jin haka sai Sarki ya dube Shadilat cikin tsananin mamaki alokacin da gaba dayan sauran 'yan gudun hijirar keta kokarin leken fuskarta suna dimaucewa bisa ganin tsananin kyawonta da yadda boye kanta acikin sub a tare da wani ya taba ganin taba az ahiri, Sarki yace "yake wannan ma abociyar kyawun fuska kekuwa wace irin alfarma kike da ita haka kike son nayi miki ita? Koda jin wannan tambaya sai fuskar Shadilat ta fadada da murmsuhi nan take kyawunta ya ninku na da alokacin da Wushiryarta ta bayyana, Shidilat tace "Yakai Sarki mai adalci kayi sani cewa ni tun ina kara mata da na taso babu abin da yake burgeni sama da jarumtaka don haka sai nakawai naji burina na zama jaruma mai dakakkiyar zuciya, juriya, naaci, da iya yaki, tun asannan mahalfina aya dauko hayar wani mayaki ya koyar da ni har nagirma amma duk da haka ban yarda da kwarewata domin mahalfina ya bani labarin Sarkin yakin garinnan wanda ya rasu **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** wanda ake kira da suna Hlzanu. Mahalfin nawa ya gaya min cewa idan har ina son na sami gagarumar jaraumtaka sai na sami im horon da Sadauki hizanu ya samu kuma babu mai kwatan kwacin irin horon nasa face kai da ka kasance dan uwansa, mahalfin nawa ya sanar da ni cewa shi ya kori Macijiya Baurkul karsum a lokacin da ta shgo birnin nan take fokarin ta hallaka kowa. Koda Shadilat tazo nan ajawabinta sai idon Sarki ya ciko da kwalla nan take al’amarin da ya sa jikin kowa yayi sanyi kenan a fadar, Koda Yarima yaga Sarki ya sunkuyar da kansa fasa har hawaye ya fara zubo masa sai shima zuciyarsa ta karaya ya kama hannun Sarki ya damke a alokacin das hi ma idanunsa sun ciko da

Chapter 2 of 4