Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 4
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels **Tuchar Caskiya** **ABDULAZIZ SANI** **MADAKIN GNI** --- SAFIYA CE MAI dauke da yanayi gwanin 'ban sha'awa domin Babu sanyi kuma babu zafi, mutane sun fito daga cikin gidajensu sun fara aiwatar da harkokin kasuwancinsu na yau da kullum kamar yanda aka saba acikin birnin mai tarin al'umma ma'abota addinin Musulunci. kowa ka gani a nutse yaka babu ashararai a ko ina kima babu gdajen da ake aikata masha'a a ko ina, baza ka taba ganin mata da maza ba aguri daya ba kuma indai mace ta kai minzalin balaga zaka gat a rufe ko ina na jikinta sai dai kawai fuskarta da tafikan hannayenta da kafafunta a waje. Kaso tamanin na lukotan wannan mutanen wannan birni yana tafiya ne awajen hidimar addini kamar nafilfilo ama sallatai karanta alkur ani da wa'azi a ko ina har kasuwanci da wararen sana'o'i Babab abin da zai fi burgeka mutun dangane da rayuwar mutanen wannan birnin mai albarka shi ne yadda zaman lafiya ya yawaita atsakainsu saman babu babanci tsakanin mai mulki da talaka, malami da attajiri, kowa daidai yake da kowa kuma komai girman mutun idan **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** ya **Ketare haddin Allah ko ya karya doka sai anyi** masahukunci kamar yanda addini ya tanadar. wannan birnin ya bunkasa da harkokn kasuwanci da ci gaba na Kere Kere, gamio da ma;adanan Kasa kuma yana Karkashin jagoranci wani adali Sarki mai suna Abu zaiyan. Abu zaiyan ya kasance gawurtaceen Sadauki gwarzan mayaki mai tarwatsa maza afilin daga, amma atarihin rayuwarsa sau uku kawai ya 6a yin yaki duk da cewar ya shekara arba'in akan karagar mulki. Ykuna ukun da Sarkin Abu zaiyan ya ta6a yi yayi sune bisa dole da wadansu kasashen kafirai dake mafobtaka dashi kuma sune suka takaleshi, Abin ya samu asali tun a farkon hawan sarautarsa bayan rasuwar Mahafinsa wanda ya gaji sarauta awajns. Shi dai wannan birnin na Abu zaiyan ana kiransa da suna Baitu! Haura! kuma duk Kasashen dake zagaye dashi Kasashen na kafirai ne ma'abota tsafi da bautar gumaka, rana, da sauransu. Ko kadan mutanan Baiti Haura! basa zuwa tallan addininsu izuwa sauran kasashen amma **ABDUL'AZIZ SANJ M/GIMI** --- kutna a hankali mutanan sauran kasashen kafiran suna zuwa har cikin wannan fasa dan karbar addin Islam ba koma bane ya janyo haka face sha awar yanda suka ga mutaneb birnin suke tafiyar da rayuwarsu bisa jin dadī, kwanciyar hankali da nutsawa akan TURBAR GASKIYA. Lokacin da sauran kasashen suka ga hankalin mutanensu suna bijirewa addininsu har ma ana shigo da addinin musulunci cikin kasashen a aboye ana yada su sai suka dauki mataki mai tsauri yazamana cewa duk wanda aka kama yana addinin musulunci sai an kasha shi ko kuma akwace duk abin day'a mallaka,gidansa da dukiyarsa hatta iyayalinsa sai an mashe su bayi, Koda ga nin irin wannan barna sai mutanan da suka musulunta daga cikin wadansu birane uku da ake kira HAUZUBA; DAKFUL, DA HASNAM suka dingayan kaura cikin dare suna koma cikin birnin Baitu haural. Kafin a ankar a 'yan gudan hijira sama da miliyan bakwai sun gudu birnin Baitul Haura! kuma da yawansu manyan mutane ne awadancan birane. **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- Wasu mashahuwar attajirai ne wasu kuma manyan manomane dam asana ilimin sarrafa ma adanan kasa. Lokacin da aka tara wadannan 'yan gudun hijira afadar Sarki Abu zaiyan sai ya karfesu hammu bibbiyu kuma nan take yasa aka raba musa gidaje da gonaki kyauta domin su zauna su fara sabuwar rayuwa, Aikuwa cikin wata daya jal da zuwan wadannan 'yan gudan hijira sai arziki birnin Baitu Haura! ya kara bunkasa ninkin ba ninkin yana ninka na da yazama cwa agaba daya nahiyar ma babu wata kasuwa man girman da kao arziki sama da kasuwa Birnin Baitul Haura! kasuwanin dake cikin binna hizub, Dakful, da Hisnam kowa duk sai suka mutu, bafi suka daina zuwa , arzikinsu ya raunan kuma talauci ya yawaita. Al'amarin day a dugunzuma hankalin sarakunan wadannan kasashe uku kenan, Koda suka yi bincike suka gano cewar wannan masifa da ta samesu a sanadiyar hijirar da jama'arsu sukayi ne suka koma binnna Baitul Haura! sai wadannan sarakuna uku suka shirya taron gaggawaa birinin Haizuba inda Sarki Madihar yake mulki. **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- Sarki Madhan na Birnin Haizub ya dubi sarki Tarmas na birnin Dakful da Sarki Husaka na Birnin Hasnam ya ce “yak u manyan abokaina kun sani cewa muna cikin masifa da tashin hankali bisa yadda tattalin arzikin kasashen nan hamu uku ya lalace muka fada cikin fari yunwa, da talauci kuma duk wannan abuu ya samu ne sakamakon attajiranmu da kwarrarun masana sana’o’in-nu duk snyi hijira sun koma birnin baitul Haura! da zama kuma sun karbe addinin mutanan can, nasara daya muka samu ta share wannan addinin acikin biranenmu to amma fa mun kasha muciji-ne bamu sare kanshi badomin na sado da bokana ajiya yayi bincike ya gano cewa idan har ba bamu share birnin Baitu haura! ba nan gaba sai sun sun mallake duk kasashinnafiiyar nan gaba daya sun Kone allolimnu da muke bautawasun kafa adddinimusu yanda har abada baza akara yin tsafi ba da wani addinin daban awaninan Nahiya sai nasui. Shin haka zamu zuba do muna jt muna gani har mukan ga wannan lokaci, ni yanzu babban abin da bakim dikina ma shi ne dan uwana da muke uwa daya uba daya kuma --- attajirin da duk nahiyar nan babu kamarsa ta fannin dukiya, Abu shadalat ma so yake ya koma Bimin Bautl hural amma na mafa masa matakan tsaro na hana shi zuwa ko inayana fakewa da cewar kasuwanci zashi yayiamma ni nasan cewa so yake ya krbi addinin mutanan birnin Baitul h Rural, yanzu dai meccce shawararku? Mai ya kamata da myyi dan mu ma gance wannammatsala? Kodda Sarki Madhan yazi nan aazancensa sai Sarki Tarmas ya numfasa y ace ni againna babu wani abu day a kamata muyi face mu hada runduna ta mayaka, ina nufin mu hada karfi da karfi na mayakamnu mu kaiwa birin baitul Haural harin mannyar BAZATO,cikin dare mu kama Sarki Abu zaiyan muyi masa kisan gilla agaban mutanensa, daga waman rana duk wanda ya sake yin addinin nasu mu kasheshi muyi musu dole su koma irin addininmu na bautar gumaka, Duwtsu, Rana, da sauransu ka ga kenan sai mu raba birnin nasu kasu uku kowannanemu sai ya yagi rabonsa kun ga kenan mu jifi tsuntsu biyu da hoge daya wato mun kare addinimu da kasarmu kuma mun dawo da tattalin arzikinmu **ABDUL AZIZ SANI M/GINI** --- Yayin da Sarki Tarmas na birnin Dakfuj yazo nan azancensa sai Sarki Madhan yayi ajiyar zuciya saman yace hakika kazoo da shawara mafi alkairi agaremu to amma menen tabbacinka cewar zamu iya sami nasarar yaki akan wadannan mutaneh wadanda tsawan shekaada shekaro tun karfi a harfenu bamu taba ganin iyayemnu da kakannumun sunyi yunkurin yakarsu ba kuma ba musan darilin ba? Bamu san karfin mayakansu batunda ba ataba yin yaki da suba. Sarki Tarmas ya ce Kodai ba musan karfinsu ba amma dai kasan Sarkin yawa yafı Sarkin karfi inda ni ha kaotawa rundunar kaida Sarki Husaka kuka kao naku rundunonin muka hada rundunar kare dangi ai dole ne mu gama dasu. Koda in haka sa sar ki Madman ya sake yin ajiyar zuciya akaro na biyu saman ya dubi Sarki Husaka ya ace Rar kama meeece shawararka? Sarki Husaka ya giyan muy ya yace ni atawa shawarar ba hanli sumame ya kamata mu fara kaimusu ba kamata yayi mu roubuta wasika mu akawa da Sarki Abu zayan muy masa gargadi akan cewa yayi gaggawar bamu **ABDUL AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** mutanemnu gaba dayensu wadanda suka hijira suka koma birninsakuma ya hadosu da duk dukiyar da suka mallaka in ba hakaba za mu zo mu yake shi har gida mu karbesu da karfin tsiya, ina tabbatar muku da cewar Sarki Abu zaiyan mutune wanda ko kadan baya son tashin hankali kuma yana son kasarsa da jama'arsa sun kasance acikin nutsawa da wadata, kun sani cewa indai za ayi wannan yakiwanda baa san ranar daina shi ba sai jama'ar tasa da yawa sun rasa rayuwarsu da dukiyarsu kuma sai fasar ta shiga cikin fari da talauci, Sa'adda Sarki Husaka yazo nan a bayaninsa sai Sarkin madahan da sarki Tarmas suka kamu da tsananin farin ciki cikin hacfın baki suka ce tabbas kazo da shawara da ta kore ta farko. Nan take aka rubuta wasika aka tashi manzo ya tafi izuwa birnin Baitul Harwal. Acan birnin Baitul Haura1, bayan anyi asuba amasallacin anyi aaddu'a kowa ya waste sai Sarki Abu zaiyan ya shiga cikin gidansa domin yaje ya zauna a aharabar gidansa inda ya saba zama dan yin lazimin har izuwa lokacin da rana ta fara fitowa, KOda Sarki yaje inda zai je ya zauna sai **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- y a j yo takun tafiya acan bayan bargar dawakain gidan kuma ya dinga jin karar haduwar takubba alamar cewa mutun biyunie ke yaki. Arude kuma cikin mutufar mamaki Sarki ya karasa da hanzari izuwa wajen yana zuwa yaga ashe dansa ne YarimaZaiyan da abokinsa Safwan suke wasa jini har Sarki ya bude baki zaiyi musu Magana sai ya fasa ya samu guri ya raku6e'inda basa hangoshi yaci gaba dakallonsu cikin murna sakamakon ganin gagarumar bajinta da Yarima Zaiyan yake yi , kaafin Safwan ya kawowa Zaiyan hari guda daya Zaiyan ya kaima sa goma saboda tsananin t safin namaduk da cewar shima Safwam ya kasance Sadaukin gaske kurna yafi Zaiyan cika ido murdewa da girma amma sai gashi Zaiyan din yana daka nada gumba a hamun, shi kansa Sarki Zaiyan lokacin da yaga Yarima yana yin iri n wannan gagarumar bajinta sai ya cika da tsananin mamaki domin bai taba sanin cewa yarima yana da irin wannan jarumtaka ba, nan take ya aiyana aransa cewar sai ya jarraba tasa jarumtakar akan ta yarima domin ya banbancetsakanin aya da tsakowahaka dai Sarki ya ci gaba da kallon gumurzu yarima Zaiyan da abokinsa Safwan ba tare da sun sani --- **TURBAR GASKIYA** ba har Zaiyan yashammaci Safwan ya doki hannunsa takobinsa ta fadi kasa kafin Safwan ya jnya da dauki takobin tasa tuni Zaiyan ya doki kafafunsa cikin bakinsa zafin nama, yai katantanwa asama ya baje akasa. Koda ya yunkura zai tashi sai Zaiyan ya rintsashi da tsinin takobinsa a wuyansa, kawai sai suka ji ana rafka tafi, cikin sauri duk su biyun suka waigo suka dubi inda sautin tafin ya fito koda suka ga ashe sarki ne atsaye fuskarsa cike da murmushi yana tafin sai Safwan ya mike suka ruga gareshi suka kwashi gaisuwa, Sarki ya dafa kafadun yarima Zaiyan ya tashi she tsaye saman ya dubeshi cikin nutsuwa ya ce “yakai dana menene dalilin da yasa kuke bawa kanku horon yaki alhalin ni ban taba ganinku kuna yi ba? Koda jin wannan tambaya sai Yarima yayi ajiyar zuciya fuskarsa ta juye izuwa yanayin damuwa nan take saman yace “yakai Abbana kayi sani ba wani abu bane ya saka ni cikin wannan tunani ban a bahwa kaina horo yaki face wani mugun mafarki da nake yawan yi acikin ‘yan kwanakinhan, abinda ake nuna min acikin mafarkina shine wdansu manyan kasashe gudu uku dake cikin wannan nahiyar sun hada karfi da **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** karfi suna son su rushe wannan birnin namu maj albarka kuma su shafe addinin ,ana hiyar gaba daya kafin Zaiyan ya gama rufe bakinsa tunj Sarki ya tari Numfashinsa yana mai daka masa tsawa yace "akul na kara jin kayi irin wannan furuci domin har abada TURBAR GASKIYA itace hanya mai dorewa, nasani cewa akan gaskiya muke su kuwa suna kan turbar karya don haka bza su taba samun nasara akanmu ba mun saki Allah mu kama abin da suka kama ya kai dana ina so ka sani cewa nima Allah ya nunanimin abin da ya nuna maka acikin barcina fye dad a kwanaki biyar da suka shude kuma tun daga saman kullum sai nayi addu'a na neman tsari daga saharrinsu da kaidinsu. Lallai zamu zauna acikin shiri ko da ta kwana duk wanda ya takalamu zamu tareshi afafata, ba tsoro kuma ba gudu ba ja da baya, haKika ka bani mamaki mutuka bisa ganin irin wannan gagaanunar jarumtaka don haka ni yanzu ina so na wasajini na tare daku. Koda gama fadin hakan sai Sarki ya karbi takubin Safwan ya fuskanci Yarima yace bisimillah, cikin tsananih alamun tsoro Safwan ya dubi Yarima yana mai masa inkiya akan kada **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- yayarda yayi yafi da Sarki saboda yasan ceva ruwa baa san Kwando bane, Shi kuwa Yarima ki ajikinsa bai damuba kawai sai ya gyarasayuwa ya daga takubinsa sama yana mai rufeta da hannun biyu, Sarki ya ya futo Yarima da hannunsa yana mai masa nuni day a fara kawomasa hari, shi ma Yarima ya yafuto Sarki da hannun yana nufin sai dai shi Sarkiya fara kawoharin, Koda ganin haka sai kuwa Sarki ya falfalo da gudu izuwa kan Yarima ya kawomasa wawan sara tamkar yana yafi da wani fasurgumin kafiri, koda yarima ya kaucewa wannan saran sai takubin sarki ta tsarge wata bishiya dake bayan Yarima ta rabata gida biyu, saboda tsananin frigitar da Safwan yayi bai san lokacin day a dafe kai baya durkushe yana mai zazzaro idanuwa da wangame baki tamkar yasa kururuwa ya nemi agajin mutane domin tunda yazo duniya baitaba ganin mutun mai zafin nama da farfin saraba kamar sarki, Nan take yaji kamar ya tsandara thu ko kuma ya kwalawa mutane kira domin su zo su tsaida wannan yafi don kada ayi asarar rai abanza shi kuwa yarima Zaiyan ko alamar tsoro **ABDUL AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** babu atare dashi, kawai sai yayi murmushi kuma shima ya afkawa sarki suka ruguntsume da azababben fadamai tsanamin da ban tsoro yazamana cewa suna kaiwa junansu sara da suka acikin zafih hamai juriya da bajinta. Al amarin day a kara datire Safwan kai shime, ganin yadda Sarki da yarima zaiyah suke wannan yafii da wani irin zafin hama na musamman tamkar jikinsu bana jin da tsoka bane domin ko kadan babu alamar gajiya atare dasu saman kunna irin salon rada daya suke yıt tamkar darina can malamanisu guda ne suna yakine asrin kaiwa juna hatshi, bugu, sara, da suka duk ulokaei guda da dan gami da dan tsalle tsalle da kwance kwance irin ha sofaffun gwanayen yaki, abinda Safwan yake tambayar kansa shi ne yaya akayi jarumtar Sarki da ta Yarima ta ke neman tazo iri daya ne alhalini kowa agarin ya sallamawa Sarki saboda ko daji aka tafi faranta babu wanda yake yin irin jurumtar da yake yı agarin kaf sama dashi. Akwai wata rana da aka tafi yin wata gawartacee wa’ faranta acikin wani kasurgumin daji dan kamo wani shu’ umin Zaki wanda ya gagar! kowa ya hana shigewa ya tsare hanya har **ABDUL AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** ma ya kasha kimanin dakaru sama da dari nan take Sai sarki ya fusata yasa akayi wannan shirin da farauto zakin alokacin da ya isa cikin wannan daji cikin fusata sai ya ajiye makamansa ya tare zakin suka kaure da azababben yaki, shi da zakinan Sarki ya turmusheshi yasaka Zakin anan amakata har said a ya fabakin Zakin gida biyu saman ya vatsar da gawarsa gefe. Daga wannan ranar kowa ya sallamawa Sarki aka rinka yi masa kitari da makashin mazan dawa. Lallai ashe nasu iya Magana sun gaskiya da suka ce barewa bata gudu danta yayi, rarafe. Lokacin da aka shafe kimanin sa'a daya darabi ana wannan bafin yakin tsakanin sarki da Yarima yazama duk su biyun babu wanda ya samu nasarar koda lakutar jikn dayansu ba sai suka gaji ainun, babu shiri suka ja da baya sukayi curko curko suna haki saboda gajiya sai harara juna. suke kawai. Koda ganin haka sai hankalin Safwan ya tashi ya dubi Yanima ya yi masa inkiya da kada ya yarda da suyi fadan hannun shi da Sarki iya ka wannan bajin tar day a nuna ta is, shi sai Yanima jikinsa yayi sanyi ya dubi mahaifasa **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- yace "haba yakai Abbana kayi sani ceva ba zanso ace na cutar da jikinka bad a hannayena, koda jin haka sai Sarki ya dakawa yarima tsawa yace "Idan har kaki fadan hamu dani bil hakki sai na tara maka gajiya koda yaki yazo baza ka iya fita ba domin alokacin kana kwance kana jinya jikinka" Koda jin wannan baru sai hankalin yarima ya dugunzuma ainun domin arayuwarsa bashi da wani buri wanda yafi ya fita film yaki ya fafata da mazaje domin a nanne zai iya sanin iyakar jarumtakars, duk sa adda za afita farauta sarki baya barin yarima yaje a wannan rana sai dai ya bashi wakilicin garin dan tafiyar da harkokin mulki, akwai wata rana ma da sarki ya tafi rangadi tare da tsirarun dakaru izuwa wani daji mai nisan gaskea asannane wani ayarin guda na 'yanfashi ya kawo musu sumame aka kasha gaba daya wanman tsirarun dakarun na sarki amma shikadai ne yazewa wadannan 'yanfashin guguwar annaoba ya rınfa ragargajarsu sai da ya kashesu bake daya alhalin adadinsu ya kai dubu uku da doriya su kuwa dakarun na Sarki ba su wuce su hamsinba, Kawaisai ganin Sarki akayi ya dawo **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- birninsa.tare da gawarwakin dakarunsa akan keken dokinsa duk.jjikinsa yayi kace kace da jini tamkar acikin kogin jini aka tsoma shi, Nan day a bayar da labarin yakin da yayi abaya da 'yanfashi kuma ya fafi a inada akayi wannan mummunan karo das u ya kuma bada umamin dan aje adauko ganimar 'yan fashin. Aikuwa.daakajeakagataringawarwakin 'yanfashinsaihankalin'yan aikinyadugunzumasuka rude da ganin yawansu kuma duk ace mutun daya ne yazama sanadiyar yimusumasaukia afiyama,dukiyardaaka samukuwaatare da 'yanfashin ba karamin yawa gareta badomin sai akayisawubiyubayan wadandasuka je na farkosundawodkaturawasudansujesukwasolallaisumasungaabinmamakimaitarinyawa. Lokacindayarimayajewannandajeyagaringagarumarbajintardamahalfinsayayisaitakaiciyakamashiharsaidayazubardakwallasabodabafincikicewabashiakayiwannangagarumingumurzuba. Batareda fargabasaishimayarimaya dunkuehannuwansayanamaitunkarasarkida --- **ABDUL'AZIZ SANIM/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** gyara tsayuwa, nan take kuwa suka kaurace da azababben fada suna kaiwa juna naushi da bugu da hannu da kafa sai gashi dukkaminsu sun shanye dukan tamkar jikin nasu bana jini da tsoka banc, idan Sarki ya gabzawa yarima wawan naushi a fuska sai kaga har kataantanwa yake saboda karfin naushin amma sai ya shanye shimaya maida mada martani, Nn da nan suka hadawa juna jini da majina, al’amarin daya kara dugunzuma hankalin Safwan kenan yaji kamar ya rugu yaje yak era mutane su zo su raba wannan yaki amma sai ya kasa saboda yana ganin cewa idan ma ya bar wajen kafin yake ya samu mutanen, to tuni daya daga cikinsu ya kashe daya nan fa Safwan ya fara kuka ya shiga rokan sarki da Safwan akan su daina wannan fada su kuwa ko kallonsa basu yi ba kamar ma kara zugashi sukayi don ci gaba sukayi da gabzar junansu ka kace tsofaffun abokan gaba ne sukc son su kawi karshen gabar tasu, Tun sarki da yarima suka tsaye suna kai duka said a suka durkushe akasa suna layi ammu saboda bakin nacı da tsananin juriya basu daima Kofarin kai naushi ba har said a da kai cewa ko daga hannayensu basa iyawa sannan **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** suka zube kasa wanwar suna numfarfahi kamar ransu zaifita. Lokacin guda kuma sai suka mike zaune suka dubi juna suka bushe da dariya a tare kawai sai sukayi rarrafe kamar kananun yara suka nungume juna suna dariyar farin ciki, said a suka dan jima amanne da juna samon sarki ya janye jikinsa daga jikin na yarima ya dubeshi acikim nutsuwa yace ‘yakai dana kayi sani cewa daga na sami nutsuwa da kwanciyar hankali tunda nasan cewa na sami magajin da zai iya ruke karagata, lallai zanyi alfahari da kai domin wannan albasar tayi halin rowe. Mayi maže alkawarin duk ramar da yafi ya zo mana kaine zaka jagoranci dakarunimi.’ KOda jin haka sai farin jiki ya lullume yarima ya sake rungume mahalfinsa yana mia yi mada godiya domin shi arayuwarsa bashi da wani buri wanda yafi ya fita film daga a fafata musamman dan saboda gorin da ‘yar kanin Sarki wato Lushmaira take yi masa. Lushamaira wata kyakkyaawar budurwa c eta gaban kwatance wadda babu kamarta afagen kyau a birnin baitul Harwal, Samari da yawa sun nemi auren Lumshmaira amma taki amin **ABDUL’AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** cewa musu saboda da wani sharadi da gindaya wanda kuma ya gagari kowa, Shi dai wannan wannan sharadin kuwa shi ne bazata auri kowa ba face jarumi da yayi gagarumar jarumtakar da tafi ta sarki, kowa ya sani cewa Sarki ya taba kasha 'yanfashi sama da mutun dubu uku shi kadai saman ya kasha gawurtaccen zakin day a addabi mutane adajin farauta da hannu bad a makami ba A halin yanzu akwai wadansu dazuzzuka guda biyu a yamma da birnin Baitul Harwal. Daji na farko ana kiransa da suna Sinil maut. Tun zamanin kakan sarki wato fiye da shekaru saba'in baya fatake da mafarauta basa iya wucewa ta cikin dajin Sirril maut domin akwai wata tsohowar macijiya da ta zama kangarau kuma gagarau acikin wani kogi dake tsakiyar dajin ana kiranta da suna Barukul karsum, mahalfin Sarki Abu Zaiyan ma kafin ya rasu sai ya gargade shi akan cewa kada yace zai shiga dajin siril maut yace zai yaki da macijiya Burukul karsum domin itace sanadin ajalin kakansa na uku kuma shima dafin tane ajikinsawanda ya sahi kwanciya cuta ta tsawan shekaru bakwai, azamaninsa ne yasa malamai **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- sukayi istahara suka gano cewar baza ataba samun nasarar kasha wannan macijiya Burukul kursun ba sai ashekarar da aka zubar da jini mai yawan gaske a nahiyar gaba daya irin jnin dab a ataba zubar wa ba. Lashmaira ta sanar da cewa idan ba askashe macijiya Burukul kursum to ta hakura da yin aure har abada kuma wanda ya kasha macijiyar shine zai zamo mijinta kodai kuwayafi kowa tsufa talauci da muni a nahiyar. Dallinta nayi wannan furci shine itama macijiyar ce sanadiyar ajalin mahalfinta. Mahalfn Sarki Lashmaira yakasance gawurtaceen Sadauki harma yafi Sarki Abu zaiyan Jarumtaka kuma uwarsu daya ubansu daya, ranar ada ka haifi lushmaira ranace wadda baza ataba mancewa da ita ba a birnin Baitul hairal domin ranar ce akayi asarar dubban rayuka sakamakon shirin maciya Burukul Karsum, Wata Asabar ce ayammacin sakaliya mutane nata hidimominsu kamar yadda aka saba kawai sai aka ga wani abu mai tsananin tsawu da kauri mara misiltuwa yafaso Katanga birnin ya Zuro kansa ya kama yiwa mutane dauki dai dai yana ci, sai dai ka ga ana gatsa dan adam **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** tamkar ansa addda an daddatsashi, jini kuwa yarinka fallatsa da malala, sai da abin ya fara had'ye mutane saman aka gane cewka macijiya ce Nan fa gari ya hautsine mutane suka kama guje guje da iface iface nan da nan labara ya riski sarki Abu zaiyan a wannan lokaci kuma mahafin Lashmaira yana can Karshen gari, inda matarsa ke nagudaacikin gonarsa inda yake noma, wata kuyangarsa nayi mata Ungozoma. Asannan mahalfin Lashmaira na kofar bukkar da matarsa take nagudar yana tai kawo cikin zakuwa kuma yana ta addu’ar Allah yas sauketa lafiya. Lokacin da labari ya riski Abu zaiyana cewar gafa wannan muguwar macijiyar ta shgo gari ta fara mummunar barna sai hankalinsa ya tashi saboda yasan sharrinta kuma ya sami cikakken labarinta awajen mahalfinsa wanda ya gargadeshi akan kada ya kuskura yayi gaba da gaba da ita. Nan take Sarki yasa aka tara dakaru majiya karfi yace suje su yaketa saman kuma ya tara malaman garn suka dukufa suna neman **ABDUL'AZIZ SANI M/GINI** --- **TURBAR GASKIYA** nauke daga uban giji ta fuskar rukonsa dan ya magance musu ita. Byan Sarki Abu zaiyan y agama wannan shiri sai shima yayi shigar yaki yahau kan dokinsa ya zaburshi da gudu izuwa can bayan

Chapter 1 of 4