Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 4
gidan ba tare da ta nemi izinin ta wajen fitar ba. "Ina ki ka je Nana?" Ba tare da da ta kalleta ba ta ce mata gidan su Nura. "Gidansu Nura?" Hajiya Salma ta tambaye ta cikin hanzari da kuma zare ido saboda mamakin amsar da ta ba ta, Nana ta juya za ta nufi dakinta, Hajiya Salma ta sake daka mata tsawa ta kirata, ta nufi dakinta, itama ta bi bayanta zuwa dakin nan ta da duruksa a Kasa, Nana ni ki ke baiwa amsa kan ki tsaye ba ki damu da ko raina zai baci ba." Nana ta soma kuka, kuka mai tsanani tsawon lokaci Hajiya Salma tana kallonta cikin mamakin dalilin kukan nata, sai da ta yi ya isheta ta yi shiru 62 Da kamar wuya.... Hufsut C. Sodangi ta mike za ta fita sai ta ce mata "A'a ai babu inda za ki sai kin gaya min abinda na yi miki da ya saki wannan kuka da ki ka yi wanda da ganinshi an san bakin ciki ne ya sa kika yi shi." Shiru Nana ta yi ba ta tamka mata ba, tsawon lokaci tuni ta na mata fada har ta koma rarrashinta Nana ta bude baki a hankali ta ce mata babu komai Innarmu kawai na tuna, tana fadin hakan wasu hawayen suka sake zubo mata ta ci gaba da wani sabon kukan, jikin Hajiya Salma ya yi matukar yin sanyi ta kalli 'yar kanwar tata ta ce mata "Nana menene damuwarki? Wannan kukan da ki ka yi da alamar akwai 6acin rai mai tsannai a dade ina bata miki rai ba ki gaya min ba. In kuma ki ka yi min haka ba ki min adalci ba don kuwa a zaman da na yi dake na jawoki a jikina ta yanda za ki maidani tamkar mahaifiya ki saki jikinki dani ki sani cewar baki da wata wacce ta fi ni tunda mun riga mun rasa mahaifiyarmu ni din mamadinta nake a wurinki don kuwa danma Hausawa suna cewa wai babban ya uwa ce, wato ba ki daukeni a haka ba." Nana nta kara sunkuyar da kanta kasa cikin rawar murya, ta ce mata "Haka ki ke a wurina Anti." 63 Da kamar waya.... Hafsat C. Sodangh Hajiya Salma ta gyara zama ta ce "Ko haka nake Nana akwai wani abinda na gane ba k gamsu da adalcina a kanshi ba don haka ina so ki gaya min shi in gyara." Ai tsawon zamana dake ban taba ganin kin yi kuka na tambaycki dalilin kukan ki ka ce min Inna ki ka tima na sai yau, na kuntata miki da yawa, a d'an tsakanin nan ko?" DA sauri Nana ta ce "A'a ba ki taba kuntata min ba ni dai kawai..." Ta sunkuyar da kanta kasa ta yi shiru. "Yi magana mana ki gaya min abinda ke ranki." Hajiya Salma ta bata umarni. Nana nta ci gaba da yin shiru. "To kina dai so kenan sai raina ya baci ina ganin dama bukatarki kenan, ta ce "A'a to in ba haka ba ne gaya min." A hankali cikin sanyin murya ta ce mata ni dai kawai Anti da na so ne ki yi min nima irin yanda Innar mu ta yi miki. Hajiya Salma ta zuba mata ido tana kallonta jimawa kadan ta ce mata "To Nana tunda abinda ki ke so kenan in kyaleki ki auri Nura ko?" Nana ta sunkuyar da kanta kasa, ta yi shiru "To ai kin gani in na yi magana sai ki yi sauri ko kuwa akwai wani wanda ki ke sone bayan Nuran? 64 Da kanar waya.... Hafsat C. Sodangi Cikin sauri ta ce mata a'a Hajiya Salma ta ce to in dai maganar Nura ce, zan iya barinki ki aurcshi Nana tunda abinda da ki ke so in yi kenan, to amma fa ki sani Inna ta goyi bayana ne na auri mutumin da bai da wata matsala in ba ta abin hannu ba, ke kuwa kin fini sanin irin mutumin da ki ke son aura. Kina ganin nan gaba in kin yi hankali ba za ki zargeni kan barinki da na yi ki ka yi hakan ba? Nana ta če "A'a ba zan taba zargin ki ba, sai dai kullum in kara daukanki a matsayin mai tausayi da kyautatawa ga komai karamai gana kasa da ke don kuwa na yi imani kina tsaye wajen ganin na samu alheri in har wani abu sabanin haka ya faru dani to ba zan taba zarginki ba don kuwa na san in na yi miki haka ban yi miki adalci ba, tsawon zamana dake alherinki na sani ban tabа ganin wani abu sabanin hakan ba, don kullum abin da ki ke nufi dani kenan in kuwa na ga wani abu saba wa haka to ba daga gareki ba ne, Hajiya Salma ta kalleta yayin da ta ke jero mata dadadan kalamai da take ganin zasu kara sanyaya mata zuciya game da al'amarinta, ta ce "To ai shi kenan Nana ni madadin Inna ce a wurinki ina kuma fata in ci gaba da zame miki hakan a kowane lokaci ban ki Nura don komai ba sai don ganin rashin 65 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi dacewarshi dake don kawa kin cancanci samun kowane irin miji d azai kula dake ba wanda zai zamo ke ce mai zuwa kina kula da shi ko dawainiya da shi ba, amma tunda ba ki fahimce ni ba har kina ganin tamkar rashin mahaifiya ne ya saki rasa abinda ki ke so, to na daina daga yau zan sakar miki marra zan tayaki son abinda ki ke so zan kuma yiwa Alhaji bayanin yanda muka yi dake don ya sani. Na kuma san shi al'amarinshi mai sauki ne kwarai in dai a kanki ne ko da ya sa rana ki k ace ba kya son wanda zai ba ki zai iya fasawa, balle bai riga ya furta ba, don haka daga yau kar ki sake damun kanki har ki shiga cikin damuwa don kuwa ni da shi dukanmu masu tausayin ki ne ba masu nufin kuntata miki ba, don haka ki saki ranki ina miki addu'a tare da kyakkyawan fata na wannan zabi naki ya zamo miki alheri." Nana ta sunkuyar da kai kasa cikin hawaye saboda farin cikin da ya kamata babu abinda ya fi tsaya mata a rai irin tausayin Antin nata da ta rinka zarginta cikin ranta cewar tana kin Nura ne don kawai ta ga shi ba mai wani abu bane ga shi kuma gurgu, ita kuma tana sha'awar ta auri mai abin duniya, a yanzu ta gane abinda duk Antinta 66 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi take yi tana yi ne don amfaninta ita kanta ba don bin son zuciyarta ba. Tun daga wannan lokaci da ta yi mata wannan bayani sai ta sakarwa Nana mara kan takura mata da take yi da kuma yawan yi mata magana kan samarin dake zuwa wurin ta,.tana kin fita a yanzu tana ji tana gani za a yi sallama da Nana ta ce ba za ta ba, ba za ta daga ido ta kalleta ba, balle ta tambayi dalili, sai dai ma da ta ga kwana da kwanaki tun maganar da suka yi da ita ba ta ji an ce Nuran ya zo ba, shi ne ta ce mata "To wai ke yaya ne? In an zo an yi sallama dda ke ki ce ba za ki ba, shi kuma wanda ki ke so din ban ga yana zuwa ba, ko kuwa ya yi fushi ne ya ce tunda dama Antinki ta koreshi to shi kenan ya hakura." Nana ta yi murmushi ta ce "To menene in ya yi hakan? Da sauri Hajiya Salma ta ce "A'a ai sai in tura mishi jama'a su je su ba shi hakuri." Nana ta kyakyale da dariya ta ce "Tafdijan." *** Nura yana zaune kan keken guragunshi kan hanyar da ya ke daidaita yana zama don ya rinka ganin Nana suna gaisawa, sai rarraba ido ya ke yi yana tunanin wai ko da ya ga ta biyo ta wata 'hanya cikin hanyoyin da yake zaunc a tsakiyarsu, 67 Da kamur wuya.... Hafsat C. Sodangi cikin zuciyarshi kuwa lissafin rabonshi da ganinta yake'yi, to ko lafiya? Wannan ita ce tambayar da ya kasa amsawa, kanshi gaba daya ta dauke kafa ta daina biyowa ta wannan hanyar hatta yaran gidan su da yake gani yake samu yana tambayarsu lafiyarta suma ya dana ganin su to ko dai bata da lafiya ne? Ko kuwa Antinta ta dauki wani tsattsauran mataki a kanta? Ya tuna rabonshi da ganinta tun daga lokacin da ta je gidansu ne Umma Talatu ta bata fura gaban shi ya yanke ya fadi, daya tuna irin kashedi mai tsanani da Antinta ta tura aka yi mishi, to ko dai ranar ta gane ta je wurinshi ne ta dauki wani mataki mai tsanani a kanta? In kuwa haka ne ya zama dole ya nemi labarinta koma ya je har gidan don neman sanin halin da take ciki. Bai damu ba in ya so in Antin ta ji labari ta cika alkawarin da ta yi na Karasa mishi 'yan kafafuwan nashi, inma da wani tanadi da ta yi mishi wanda ya wuce haka duk ta aiwatar a kanshi in dai bayan ya san halin da Nana take ciki ne, to ya yarda don kuwa ya fiye msihi sauki akan ya yi ta zama ba tare da ya ji wani labari game da ita ba na dalilin da ya sa da baya ganinta. Ci gaba da zama a wurin ya yi har lokacin tasowarta a makaranta ta yi bai ga ta zo ta wuce 68 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi ba, a hankali cikin sanyin jiki ya tura kckenshi wasu yara da ya riga ya yi sabo da su a wurin suna tayashi suna kuma yi mishi hira har suka isa kofar gidan su Nana, suna tsaye a wurin suna tunanin yanda zasu fitowa lamarin shi da yaran don kuwa wancan korar da aka yi mishi ma yana tare da yaran aka koreshi mu koma ne daga can lungunmu koma ne daga can lungu mu boyeka sai mu dawo mu m shiga gidan mu tambaya ina ta ke? In san gaya mana shi kenan sai mu zo mu gaya maka in kuwa sun ganemu sun biyomu sai kawai mu fito da gudu ma zo mu turaka da gudu mu fice musu daga cikin layinsu in kuma muka riga muka bar layinsu ai shi kenan me suka isa su mana ai kaima kana da sojojin ka Nura ya kalli yaran cikin murmushi ya ce "Ina sojojin nawa suke?" Da sauri suka ce mishi gamu in sauranmu suka ji labari, suka fito ai ba zasu iya damu ba." Nura ya yi murmushi ya ce "Ai ba zan so ace mun yi hakan da su ba, yanzu dai kawai kai Babawo kai ka tsaya daga zaure kai Bala sai ka yi sallama ka shiga ciki ka tambaya, Nana tana nan?" Bala ya ce "A'a ni ba sai ya bini ba zan je ni 69 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangı kadai, Babawo a wurinka in kun ga na fito da gudu sai ya turaka da gudu kawai ku bar wurin." Suna cikin haka sai ga Nana ta bullo ta wata sabuwar hanya da ta koma bi cikin wani lungu da sauri Babawo ya ce "Yauwa ga ta can ma." Tun kafin ya gama rufe bakinshi ya ji umarnin da za a bashi ya ruga da gudu ya karasa gareta cikin haki ya ke mata magana, ta juyo a hankali ta kalleshi ya nuna mata Nura zaune cikin keken guragunshi, ta ja ta tsaya ta ce "To gaya mishi ya zo nan mana gani ina tsaye." Babawo ya kalleta ya ce "An fa ce in muka kara takowa kofar gidan nan komai ya samemu mu muka ja." Та се "Ва ga abin da na ce ba? Ba zani can inda ku ka tsaya ba ku karaso nan." Ya juya da gudu ya koma, suka karaso tare. Nana ta zuba ido tana kallon yanda yaran ke turoshi kan keken cikin raha da farin ciki, kome yake gaya musu oho? Sai kyalkyalewa da dariya suke yi, a dan zaman da Nura ya yi a wurin gaba daya yaran unguwar ya sayesu, a yanzu yana fitowa wurin za su zo su kewayeshi su zauna su yi ta hira, maimakon da dashi kadai Nana take wucewa suka iso wurinta yaran suka saki kcken 70 Da kamar wuya.... lafsat C. Sodangi nashi suka koma gefe suna hidimarsu suka ba su baya ya zubawa ido yana kallonta cikin nutsuwa don tabbatar da yanayin ta. "In ce ko dai lafiyarki kalau Nana? Nana da kwanaki ban ganki ba hankalina ya tashi na ce ko ba ki da lafiya ne, ko kuma wani abin ne ya faru a cikin gidan da ya hanaki fitowa?" Ta ce "A'a daina biyowa ta can kawai na yi." Ya dan turo keken nashi ya matso kusa da ita "Haba Nana me ya sa ki ka mun haka kin yi min rowar wadannan kyakkyawan idanuwan naki masu kama da an diga musu ruwan zaiba, kin kuwa sani sarai in ban gansu ba hankalina baya kwanciya." Ta ce "Yanzu ba ka gansu ba?" Ya ce "E amma ai sai da na zo nan kin ga kuma karya dokar da aka sanya mun na yi wanda bai dace ba kullum mutum ya kan yi kokarin bin umarnin na gaba da shi ne don ya samu ko zai yi dace ya gama lafiya." Ta се "Haka ne to yanzu ni zan shiga gida ya yi maza ya ce "To Nana sai yaushe? Sai yaushe zan sake ganinki." Ta ce "Duk lokacin da ka ke son gattirna kana iya zuwa kofar gidanmu kamar yanda yanzu ka zo 71 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi ta wuce ta shiga ta barshi anan yana bin ta da kallo, da sauri su Babawo suka iso suna tambayarshi ya ya dai Mai nasara ta bata maka ne? A koya mata darasi? Nura ya dora hannu a baki cikin nuna girman maganar da suka yin yа се "Har da ita sai ku iya bata mata a kaina? Da saurinsu suka ce to in ta bata maka mu meye gaminmu da ita da ba zamu rama wa maigidanmu ba?" Nura ya ce "To ai ita wannan da ku ke gani zamanta nake yi akan kujerar nan in ban da saboda da ita da ba kuma ganni anan ba don haka a tayani girmamata." Gaba daya suka hada baki suka ce "Yanda ka ce haka za a yi." Suka kama hannun keken suka shiga turawa, suka maidashi gida har yamma Nura yana tunanin abinda Nana ta yi mishi na tafiya da ta yi ta barshi ba tare da ta tsaya ta saurareshi ba, ya yi kamar ya danne ya hakura sai kuma ya ji ba zai iya ba ai zamanta yake yi a garin in ba ta harkarshi ta daina sonshi to ya canza wurin mana don haka nan take ya yanke shawarar komawa gidan nasu tunda ta ce duk lokacin da yake son ganinta ya je can in ma gatse take yi to shi kam a kanta bai san gatse ba, bari ya je ya gani. 72 Du kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi Lunguna ya bi a hankali yana tura kekenshi don kar yaran unguwar su ganshi su bashi shi kaďai yake son tafiya, yana isa kofar gidan ya ga Rahma tana fitowa daga ciki da gudu ta karaso wajenshi cikin murna ya ya Nura ina ka je?" "Ban je ko ina ba Rahma." Yana bata amsar yana kokarin debo mata cakulet daga aljihun keken nashi ya miko mata hannayenshi biyu a cike, tana murna ta karba da gudu kuma ta koma cikin gida don ta shaida wa Nana isowarshi jimawa kadan sai gata ta fito wai ka shigo Nura ya zuba mata ido cikin shakku in shigo Rahma? Ya yi murmushi koma dai ki sake jiwowa da kyau, kafin Rahma ta amsa umarnin da ya bata sai gashi an leko an ce mishi wai ka shigo daga nan." Ya yi kamar yanda aka gaya mishi yana shiga dakin wanda dama don baki aka tanadeshi Rahma ta bi bayanshi tana mishi hira, Nana ta shigo dakin dauke da kayan ciye-ciye iri-iri ta ajiye mishi yanda zai rinka jin dadin cі. Nana ta koma kan wata kujera ta zauna ya zuba mata ido cikin mamaki "Nana ya ya aka yi wannan abin mamakin ya auku?" Ta yi murmushi ta ce "Ikon Allah kenan." Ta ja bakinta ta yi shiru ya ce "To in kin amince da 73 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi wannan nasarar da muka samu Nana to in je in gayawa Ummana mana don a shirya turo magabata na?" Ta ce "In ka yi hakan ma daidai ne." Ya ce mana "Nana ni kuwa me zan ce miki a rayuwa? Kin soni so na hakika kin soni duk da lalurar da nake tare da ita, ni kuwa in Allah ya yarda zan nuna miki halaccina." *** Cikin sati biyu kawai sai magana ta yi karfi tsakanin Nura da Nana har mijin Umma Talatu da aminanshi sun zo wurin Alhaji Sani kan maganar ta su, ya kuma amince ya sanya musu rana inda ya gargadesu da bai son komai na hidimar al'ada da a ka san ana yi in banda sadaki shima ya yankeshi a matsayin Naira dubu biyar, kayan aure ma ya ce a barshi, in ta je dakinta a yi mata ya yi wannan karancine bisa dalilin sanin da ya yi mijin Umma Talatu, Malam Mudi ba wani abu ne da shi ba, don haka ya ga tunda ita Nana ita ta zabi dansu a haka to ya kamata komai a yi musu shi bisa adalci. Shi kuwa Nura bai yiwuwa a tsaya kwatanta farin cikinshi a yanzu kusan ko wane lokaci yana gidansu Nana suna hira shi da Hajiya Salma kuwa 74 Da kamar wuya.....Hafsat C. Sodang! sun yi matukar sabawa ta maidashi tamkar kaninta duk lokacin da ya tura keken guragunshi ya shiga cikin gidan don gaisheta in ya juya ya fita sai ta bi shi da kallo cikin zuciyarta tana fadin iko sai Allah mutum har mutum komai nashi gwanin kyau an yi mishi Tubarkallah sai dai kuma babu kafa, ko haka aka haifeshi ko kuwa da girmanshi lalurar ta sameshi, oho. Daga dukkan kallon da take mishi dai ta kasa gano ta inda ya yi mata alama da gurguntaka a jikin nashi haka nan in banda Malam Mudi da Umma Talatu ne suka tsaya suke gabatar da komai na hidimar auren nashi to da bata yarda da cewar su din yana da gami da su ba don kuwa ba ta ga ta inda ya dauko su ba. Kwanaki suna ta matsowa shirye-shirye sun yi karfi sosai kusan duk wani abinda ake bukata na shirin auren ya kammala babu abinda Alhaji Sani da Hajiya Salma ba su tanadar mata ba sun iyakar yinsu don su nuna mata irin gatan da take dashi, don ma suna yi suna tunanin irin gidan da zata zauna a cikin komai-da Nana kc bukata na shirin baki Antinta ta bata don kar ta je tana neman wani abu a wurin angon ba tunda an san baidashi daga shi har iyayen nashi. 75 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi Nura yana zaune kan keken guragunshi a dakin da ya saba sauka a yanzu gidan su Nana abincin "da Hajiya Salma ta aiko a kawo mishi ya ke ci yana kuma sauraron shigowar Nana, jimawa can ta shiga cikin kwalliya sosai, sannan da zuwa .ya daga ido ya kalleta cikin murmushí ni in ce ko har kin soma cin kwalliyar bikin ne? Ta tayashi murmushin ta ce "Da aka yi me?" Ya ce "To gani na yi Nana sai wani kara kyalli ki ke yi kina kara washewa, gashi kullum na ganki cikin wata sabuwar kwalliyar zan gan ki." Nana ta yi murmushi ta sunkuyar da kanta kasa cikin nuna alamar jin kunya." Sun dan zauna shiru saboda kunyar shi da take ji sai ya kawar da zancen da cewa "To ni Nana kullum ina tambayarki shirye-shiryenki na biki don in ga abinda zan iya tanadar miki amma kin ki yin magana, ko kuwa ba za ki yi komai ba ne?" Ta ce "Walima kawai zan yi." Ya ce "Ai dama ita ce muhimmiya sauran duka ai kwaikwayon dabi'un turawa ne, wanda bai da wani amfani." Та се "Нaka ne." 76 1 1 a Da kamar wuya... Hafsat C. Sodangi Ya ce "To amiha ita ma walimar ai da gindinta take zaune don haka nake so in san abinda zan samar miki na yin walimar ko?" Ta girgiza kai nuna alamar "A'a." Ta ce "Anti ta riga ta gama komai ta kuma yi min kashedin kar in ce zan dora maka wani nauyi don haka bana bukatar komai." Ya ce "To Allah ya sakawa Anti da alheri Nana." Nana ta ce "Amin." 東車車 Ranar daurin auren ta kasance ta Asabar cc saboda aminan Alhaji Sani da ya gayyata yakc kuma sa ran zuwansu. Tun kwana uku kafin ranar kuwa gida ya cika makil da jama'a 'yan uwa da abokan arziki na nesa da na kusa sun hallara, ranar daurin auren da misalin karfe goma sha biyu daidai aka daura auren wanda ya samu halartar mutane, dabandaban na nesa dana kusa wadanda aka yi zato dama wadanda ba a yi ba da daddare aka kai amarya dakinta a gidan Umma Talatu wanda ko kayan jeren bai dauka ba saboda kankantarshi sai katifa kawai aka jefar musu a kasa aka dai kawatashi da labulaye sai ko kafct. LL Da kamar wuya... Hafsat C. Sodangi Umma Talatu ta yi hidimar biki fiye da duk yanda aka zata abinci dana sha babu kama hannun yaro, duk nau'in da ka ke so akwai tun daga na gargajiya dana zamani. Hidima dai gwanin sha'awa sai kwalliyarta take yi ta shiga wannan ta fita ta shiga wancan, kuma masu tsadar gaskc kowa sai kallonta yake yi yana mamakin al'amarinta ita da mijinta. Ranar budar kai tun da yamma Umma Talatu ta sallami kawaye ta shaida musu cewar kowacce ta nufi gidansu tunda an yi biki an gama ta kuma basu abinda suka nema na sallama babu maganar jiran sayen baki, don angon ba mai irin wannan hidimar bane tun da ma shi ba wasu abokai ne dashi ba, da zasu rakoshi. Sukan kawaye tun da an basu abinda suka nema ko a jikinsu, suka yi sallama suka tafi suna murna cikin zuciyarsu suna cewa iko sai Allah Nana nta auri dan gurgu amma hidimar bikinta komai tubarkallah. Gaba daya 'yan biki sun watse an bar Umma Talatu daga ita sai amarya wacce ke zaune a dakinta cikin shirin taryen angonta. Idar da sallar isha't kawai ta yi ko gama jan carbinta ba ta yi ba ta ji sallamarshi a bakin kofar 78 dakinta. Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi Sai da ta shafa Fatiha sannan ta amsa sallamar, ta shiga kokarin yin kaye-kayen abinda take ganin yana bukatar kawarwa don ta samar mishi inda zai ajiye keken shi na guragu, ya sake yin sallama ta amsa tare da ba shi izinin shigowa, ya tura kai ya shiga cikin dakin. Nana dake tsaye a gefe tana jiran shigowar shi don ta taimaka mishi fitowa daga cikin kenan nashi ta ja baya cikin sauri saboda razana da ta yi a dalilin ganin angon nata tsaye kyam akan kafafunshi. Nura ya sakar mata wani lallausan murmushi ya ce Nana amaryar gurgu. Mu hadu a littafi na biyu don jin ci gaban labarin. Taku Hajiya Hafsat C. Sodangi. 79 Da kumar wuya.... Hafsut C. Sodangi 80 AKARA CITY OKSHOP 08027014161 Tsarin Bango: ANKA- GRAPHICS FAGGE 07030319787 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 4 of 4