Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 4
mara fara'a haka nan bai cika sakin fuska ga na kasa da shi ba, ke ni wani lokaci ma ban cika son ganinshi a gidanmu ba, saboda zuwan na shi ya kan takura ni. "Ina ajin karshe na secondary school shi kuma ya tafi bautar kasa lokacin nan kuwa na zama budurwa, tafiyarshi babu dadewa muka zana jarrabawar fita daga secondary school na kuma yi sa'a sakamako ya yi kyau har ina cikin murnar zan 23 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sødangi samu wucewa jami'a don karo ilimi na. Kwatsam ranar wata Juma'a ba zan taba mantawa ba Babana ya shigo gida cikin fara'a yana kwalawa Innata kira, Ramatu! Ramatu!! kina ina ne? Inna ta fito da dankwalinta rike a hannu tana kokarin daurawa sannu da zuwa Malam, har ka dawo ko kuma ba ka je kasuwar ba ne? Baba ya yi murmushi ai ban sami zuwa kasuwa ba, gidan yaya na je muka yi hirarmu saboda dama kin san aikenshi biyu yana nemana kin ji wai dama aiken saboda yaran nan ne wai yana so zai hada Umaru da Zuwaira, na ce ko in ban da yaya wannan ai ba sai an yi sharawa da ni ba, Inna ta ce haka ne Allah dai ya tabbatar mana da alheri ni kam ina dakina hankalina ya kai matuka wajen tashi ji nake kamar in tsoma baki cikin maganar ta su, in shaida musu cewar bana sonshi sanin halin Baba da na yi ya sanya na ja bakina na yi shiru na hakura na koma bakin gadona, na zauna ina sauraron irin bugawar da kaina ya ke yi a dalilin kalaman da na ji mahaifina yana fada, ban san sanda hrawaye suka soma zubowa daga idanuna ba. Umma ta shigo ta sameni cikin wannan hali ta tsaya tana tambayata menene ya sameki? Na cc 24 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi mata babu komai Umma: Ta tsaya tana kallona, babu komai kamar ya ya? Kina kuka kina fadin babu komai, na cc ba kuka ba ne wani abu ne ya fada min a idona, ta ce to madalla ta juya ta fita, ta barni ina share hawayena. Abu biyu ya fi kona min rai gashi dai za a haďani da mutumin da ba na so ga shi kuma karatuna zai katse. "Kin san na fada miki halin danginmu musamman irin matsayin da baban Umar ya ke dashi a cikin dangi don haka maganar ma in ce ban yarda ba ko in nuna bijirewata bai taso ba, zan bata goma ne kawai daya bata gyaru ba, don na san babu mai goyon baya na sai dai kawai in tada hankalin iyayena, ran nan kwana na yi idona biyu saboda tsananin tunani, da asubar fari na fito na yi alwala na koma dakina na yi sallah na koma kan gadona na kwanta a raina ina fatan Allah ya kawo wani dalili da zai sa a fasa wannan auren. Gari ya gama wayewa na fito na gama 'yan ayyukana dana saba na koma dakina na kwanta ba tare da na saurari wani abin karyawa ba, sai wajen azahar na fito na yi alwala na yi sallah nja je na yi wanka na shirya na roki Umma ta barni na je gidan wani aminiyata Nadiya. Umma ta kalleni ta cc dama kin nutsu kin san abin da duk za ki yi ba 25 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi za ki wuce abinda aka shiryo miki ba. "Ban yi magana ba na juya na koma dakina na zauna zuciyata kuwa sai sakc-sake ta ke yi kan abinda ya kamata in yi, kwana biyu bayan nan Umar ya zo gidanmu sai da ya gama duk abinda zai yi sannan ya shigo wurina ya zauna muka gaisa a yanayin da muka saba kullun bai sakc ce mun komai ba ya tashi ya yi tafiyarshi, hakan da ya yi mun ya kara sani na tsaneshi, na jí babu abin da nake so irin in sameshi in gaggaya mishi maganganu marasa dadi, ko zan ji sanyi cikin zuciyata. Dare na yi na kira layinshi a wayata bayan na boye lambata yana dauka na ce mishi ya ya Umar ni ce. Ya ce na ganeki menene? Na ce bugowa na yi in rokeka ka yi min wata alfarma, ya ce kamar wacce iri kenan? Ban 6oye mishi ba na gaya mishi gaskiya ni ina da wanda nake so, nan take ya katse layin bai sake sauraron maganar ba ban kuma san yanda aka yi ba sai dai kawai na ji maganar ta watsu a cikin dangin, dangi sai dai kuma hakan bai hana yin aurenmu ba an yi shagalin biki ni da Umar aka kuma kawoni gidanshi, sai dai kuma ina tabbatar miki tun daga ranar da aka kawoni gidan har yau din nan bai 26 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi taba daga ido ya kalleni da wata manufaba ballc wata mu'amala ta hadamu tun ban damu da hakan ba har na shiga damuwa, har na zo a yau na hakura ke dai bar shi duk abinda na ce ina so zai yi min dana bukaci shiga makarannta ya samar min haka nan hidimomina kullum bai gajiya dasu amma iyaka kenan." Nana ta zuba mata ido cikin nutsuwa ta ce "Ke Zuwairiyya to duk wannan kyallin da ki ke yi na mene ne?" Ta yi murmushi ta ce "Nana kenan kyallin hakurino da muguwar kaddara." Nana sake yin wata ajiyar zuciya mai karfi ta ce "Amma ai gara ki je gida ki sanar da iyayenku, don su san halin zaman da ku ke ciki." Тa сe "To akan me zan yi hakan? Mu dai yi ta zaman a haka har mu ga iya inda abin zai tsaya." *** Kan hanyar Nana ta dawowa gida ta sake ganinshi zaune kan keken nashi na guragu, tun daga nesa ta hangi kyakkyawar fuskarshi mai cike da fara'a da walwalar da ta zamo ta halittace, Allah da iko yake wannan kyakkyawan saurayi kome me sanadin gurguntakarshi oho? Kusan kullum anan wurin take ganin shi tun daga ranar 27 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi da ta soma ganin shi kuwa zuwa yau din nan babu wata rana da ta biyo ta nan bata sameshi zaune anan wurin ba sai dai kuma ba ta ga kamar bara yake yi ba, don ba ta ga alamar hakan a tare da shi ba. Nana ta iso wurin cikin yanayinta na nutsuwa da kamun kai, "Malama barka da dawowa." Ba tare da ta yi zaton jin gaisuwar ba ta amsa tare da waiwaye kadan don ganin mai gaisuwar, idanuwansu suka hadu yayin da ta yi maza ta kawar da kanta ta ci gaba da tafiya, cikin zuciyarta kuwa tunani take yi, rayuwa da wuya take shi kuma wannan ko me ye sanadin wannan gurguntaka na shi? Tun da ita dai bata ga alamar Kafafuwan nashi a shanye suke ba, yau da gobe kullum ta zo wucewa zasu gaisa dashi tun yana fadin Malama barka da dawowa, har suka zamo rige-rigen gaida juna suke yi a hankali kuma shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu, ta yanda ko Nana ba za ta makaranta ba zata san abinda ya biyo da ita ta zo ta nan layin suka gaisa ta koma gida. Daga baya har ta zama ko wani abu aka yi a gida ta ji dandanonshi ya yi mata dadi, za ta ce wa yayarta Hajiya Salama a zuba mata a kwano ta je ta kai mishi, tun tana zubawa ba tare da nuna 28 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi son sanin wanda ake kai wa ba har dai ran nan ta bukaci sani, Nana ta yi mata iyakacin bayanin da za ta yi mata sai dai ba ta ganc mutumin da akc gaya mmatan ba, ni fa ban san wani gurgu anan wurin ba, watakila dai daidaitar lokacin zuwanki yake yi ya fito." Fadın hakan da Hajiya Salma ta yi ya sa Nana ta sa ido kan mutumin da suke gaisawar kullum wanda ko sunanshi ba ta sani ba, sa idon da ta yi kuwa ya sa ta gane gaskiyar 'yar uwartata, ba kowane lokaci ake samunshi ba zaune a wurin ba. Sai dai kuma ai bai yiwuwa ace mutum ko wane lokaci yana zaune a wuri daya baya motsawa dole yana da wasu al'amura da zai yi na hidimomin rayuwa, ita kam ba kamar yayar ta ba da take cewa mata kila ita kadai ke ganinshi ko kuma don ita yake fitowa ya zo nan wurin ya zauna. Sabo ne mai karfi ya shiga tsakaninsu tuni har zuciyarta ta soma raya mata in da zai daure ya bude baki ya ce yana sonta ita kam da shi ta aura, don ya fiye mata duk samarin nata da take dasu kwanciya cikin ranta, sai dai yayarta anya Hajiya zata yarda ace gurgu ta aura, ace gurgu ne mijinta, ita kam ko a jikinta, abinda ta sani kawai shi ne tana son shi za kuma ta iya aurenshi ta bar masu 29 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi Kafafu biyu. Sun dauki lokaci mał tsawo cikin, wanan hali kafin ran nan Nana ta dawo daidai lokacm da ta saba biyowa, ganewar da ta fi yana da lokacin fitowar shi nan wurin ya sanya bata yarda ta tsaya ta bata lokaci bayan tashinsu baa dawo ba, don kar ya yi ta zaman jiran dawowar ta Kamar kullum yau ma ta biyo cikin sauri ta ke tafiya doh ta san ta dan yi latti kadan a dalilin wahalar & motocin haya suke yi hankalinta bai kai gane baya wurin ba sai da ta iso saboda tafiyarta take yi ba tare da tana kalle-kalle ba, sai da ta iso gab da wurin lokacin ne ta daga ido ta kalli wurin babu shi babu keken guragun nashi cikin kaduwa ta ja ta tsaya, ina ya tafi ko dai ya ga na yi lattia zuwa ne ya tafi tun ban zo ba? Tambayoyin da suka zo cikin zuciyarta kenan, ta yi waiwayen da za ta yi ko za ta hango wani wanda za ta iya tämbaya wani abu game da shi babu to in ta ga wani ma me za ta cc musu wa za ta ce tana nema? Tun da ko sunanshi ba ta sani ba, balle sunan unguwarsu, a hankali cikin sanyin jiki da rashin jin dadi ta wuce nufi gida da niyyar an jima ta sake fitowa don ta gani ko ya canza lokacin fitowa ne. ta A gida hankalinta bai kwanta ba sallah kawai 30 Ракаркt wte Sehag ta yi ba ta ma duba inda abincinake ba, balle ia je ta kan shi tana idar da sallah ta je ta yi wanka. ta fito tana shafa mai cikin sauri da sauri Hajiya Salma ta ke kwala mata kira. "Latiya Nana ba ta zo ta dauki-abincinta ba?" Tana daga cikin dakinta ta ce. "Ban jin ci ne yanzu." Ta fito tsakar gida rike da gyalenta a hannunta cikin shirin fita, Hajiya Salma ta daure fuska "Mc ki ke nufi? Ina za ki yanzu daga dawowarki bayan ko abinci ba ki ci ba." Ta ce "Nan za ni yanzu zan dawo." Hajiya Salma ta ce "Ai ko kofar gida ba za ki leka ba sai kin nemi abinda ki ka ci tunda tun safe ba kya gida yanzu kuma kin dawo daga zuwanki za ki sake fita saboda ba ki damu da yunwar cikinki ba." Nana ta dawo cikin sauri ta shirya abinda za ta ci ta yi maza ta gama ta fita don ganin ko mutumin da take nufin ya fito, ta sake isowa wurin babu shi babu dalilinshi ta juyo ta dawo gida hankalinta da zuciyarta babu nutsuwa sosai. Washegari tana shüri tana kallon agogon Kosa Kwarai lokcin fitarta va yi in ban da tana tsoron kar ta vi samnakon fitowa ta samu bai fito 31 Da kamar wnya... Hafsat C. Sodangi ba da tuni ta yi sallama da yayar tata ta fito ta daďe da kammala shirinta tana jiran lokaci ya cika gani take tamkar agogon bai tafiya daidai Da kyar ta samu lokaci ya cika ta fauko jakarta ta fito ta yi sallama da Hajiya Salma ta fito zuciyarta cike da fatan ta sameshi zaune kan keken guragun nashi, tun daga nesa ta gane babu shi a dalilin daga ido da ta yi ta kallo wajen gabanta ya yanke ya fadi, kar dai ya canza wani wurin zaman ne? Wani ne ya yi mishi laifi ko kuwa dai dama shi haka dabi'arshi ta ke? In ya zauna anan ya kwana biyu gobe kuma sai ya canza ya koma wani wurin, tun da ai ita da kanta ta sani shi din bai wani dade yana zama a wurin ba, to kuwa in zai canza wuri me zai sa ba zai gaya mata ba? Tunda dai ya san akwai mutunci mai Karfi a tsakanin su. A makaranta tun daga zuwanta Zuwairiyya ta kalleta ta ce "Yau kuma me ya faru na ga kamar ba kya cikin nutsuwar ki? Kwanakin baya dai kin dan wartsake, amma yau kam abin ya dawo don da ganinki na san ba kya cikin nutsuwar ki." Nana ta zuba mata ido tana kallonta, jimawa kadan ta nisa ta ce mata ko aikin dana tfi gida dashi jiya ban samu na yi ba. 32 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi Zuwairiyya ta sake kallonta ta cc "To wai mc ya sameki ne?" Ba ta boye mata ba, ta bata dukkanin labarin dake tsakaninta da mutumin, to ko dai bai da lafiya ne Nana? Gabanta ya yanke ya fadi jin maganar Zuwairiyya ba ta kawo haka ba cikin rainta, in har ta shi zai yi ai ya kamata ace ya yi sallama Zuwairiyya ta ci gaba da bayani. Nana ta zaro ido tana kallonta cikin fargaba da faduwar gaba, ta yi kuskure da ba ta yi wannan tunanin ba wanda kuma shi ne farkon abin da ya dace ya zo cikin zuciyarta da ba ta ganshi ba a wurin, ji ta tamkar za ta tashi ta koma gida a wannan lokacin sai dai kuma yin hakan bai da wani tasiri sosai za ta fi son ta tashi a daidai lokacin da ya ke fitowa don ta gani za ta sameshi ko ba za ta sameshi ba, in dai a yanzu ma ba ta sameshi ba to ta tabbatar kenan babu lafiya, ya zama dole ta dauki matakin neman inda yake don ta san halin da yake ciki. *** Yana kwance a dakin zaure cikin matsanancin hali a dalilin tsananin ciwon kan da yake ciki, sai dai kuma ba halin rashin lafiyar dake damunshi ba ne matsalar da ta fi damunshi, halin da yarinyar za 33 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi ta kasance a dalilin rashin ganinshi na kwana biyu da yarinyar ba ta yi ba, shi ne babbar damuwarshi. Tsohuwar da take kula da shi ta yi sallama a hankali ta shigo dakin bayan ta ji ya amsa mata sallamar ta ta ta Karasa wurin shimfidar ta shi tana tabashi don jin yanayin dumin jikin nashi, sannu Nura ya ya jikin naka? Cikin sanyin murya ya amsa da sauki Umma. Ta sa hannu ta bude kwanon dake ajiye kusa da shi ta mayar da murfin kwanon ta rufe, ta maida hankalinta a gareshi yanzu nan kunun ma ba ka sba ba Nura? Ace sai ka kauraccwa cin komai kamar wani dan yaro? А ina ka ga ana kin cin abinci don ana rashin lafiya? Ai ko ba dadi sai ka ci ko kadan ne don maganin da ka ke sha ya yi amfani. Ta shi ka ga ni maza sha kunun nan ko kadan ne ga maganin ka ka sha, Nura ya mkie ya zauna a tsakiyar katifar tashi da kyar ya ke iya bude ido saboda tsananin ciwon kan dake damunshi. "Umma ban san sunan yarinyar ba ne dana aika an nemi gidansu, an gaya mata kar ta ga ba ta ganina a wurin da ta saba ganina bani da lafiya nc." Umma Talatu ta yamutsa fuska "Kai rabani da zancen wata yarinya kana fama da kanka kana 34 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi zancen wata can da ba ta dammu da kai ba, in ta damu da kai ka kwana biyu ba ta ganka ba ita ba za ta nemi inda kake ba ta ga halin da ka ke ciki?" Cikin sauri ya ce "A'a Umma ai yarinyar mai mutunci ce, ba ki ga yanda take amsa gaisuwata ba, abincin nan da wani lokaci nake dawowa dashi ai ita take kawo min, ina ganin inda ta san ba ni dá lafiya da za ta nemeni ta ga halin da nake ciki." Umma Talatu ta miko mishi kwanon sha ta ce "Maza karbi ka sha." Bai yi musu ba, ya sa hannu biyu ya karba cikin ladabi da nuna girmamawa ya kai bakinshi ya sha daidai gwargwado sannan ya maida kwanon ya ajiye, ya ce "Alhamdulillahi bayan ya share bakinshi, to ungo maganin ka sha." Ta miko mishi kofin ruwa, ya sha ya gyara kwanciyar shi tare da gyara rufuwarshi. *** Hankalin Nana ya kai matuka wa wajen tashi kasancewarta yau ma ba ta sameshi wurin zaman nashi ba, gashi kuma Zuwairiyya ta ce mata bai zamo lallai ace canza wuri ya yi ba watakila lalurar rashin lafiya ce ta hanashi fitowa. Wai me ya samu Nana ne, ni fa ba na son ace mutum yana cikin wani hali amma ba zai fada a sani a yi mishi maganin damuwarshi ba, sai dai ya yi ta wani 35 Da kamat wuya... Hafsat C Sodangi kumburc-kumbure, Ilajiya Salma kenan lokacin da al'amarin na Nana ya soma wuce saninta. "Za ki gaya mini ne abinda ya dameki ko kin fi so sai Alhaji ya shigo na gaya mishi." cika ta dauko Rahma tana daga gefe ta yi maza ta ce "Umma ai dazu da na ga Antin tana kuka naKall tambaycta abinda yake mata ciwo ta ce mun wai kanta ne."ijn daed ien Nana ta gallawa yarinyar harara yayin da Hajiya Salma ke fadin kuka Nana? Kina cikin halin da damuwa ke sanyaki zubar da hawaye amma ni 'yar uwarki ba za ki gaya min ba? Laifin mc na yi miki da za ki dauki wannan matakin a kaina ko kin taba kawo min damuwarki ne ban yi wani abu a kanta ba?" Cikin sauri Nana ta ce "A'a Anti ba fa haka ba ne ni bani da wata damuwa ni dai mutumin nan ne dana gaya miki rashin ganinshi yake hanani jin dadi sai ma ganin kamar wani abu ne ya sameshi, don ina ganin kamar haka kawai ba zai daina fitowa wajen ba." Hajiya Salma ta zuba mata ido cikin damuwa, "Ni fa har yanzu ban gane wannan mutumin da ki ke fada ba, kuma 'yan samarin da suke shigowa gidan nan da na yi musu magana a kan shi sun cc 36 Dä kamar wuya.. Hafsat C. Sodang! ba su gane shi ba, kar dai fa dama ke kadai ki ke ganin shi in kuwa haka ne kin san ba na kirki ba ne?" Nana ta yi maza ta ce "Haba Anti wannan mutumin bai yi kama da wanda zai iya cutar da dan Adam ba, na san shi din mutum ne kamar kowa illa iyaka dai yana da lalurar kafa tun da da keken guragu ya ke amfani wannan kuwa bai canza mishi komai ba daga kyakkyawar halittar shi." Hajiya Salma ta ce "To ki dai yi a hankali, ki dan yi bincinke kadan ta nan inda ki ka saba ganinshi ko ba ki san sunanshi ba in dai da gaske ne yana zama a wurin kamar yanda ki ka fada ai ba za a rasa wanda zai gane kwatancenshi ba da za ki yi ba, don kin san halin da yake ciki hankalinki ya kwanta, ina dai ce ba wani abu ne a tsakaninku ba?" Ta yi maza ta ce "A'a babu komai." Ta се "Shirya ki rike Rahma ku je ta yi mikį rakiya ku dan yi binciken kadan a kanshi kar ku yarda ku yi nisa." Ta ce "To ba zamu yi ba." *** Tsayuwarta a wurin ta kai kusan minti uku 37 Da kanyaWepaHalsat Sedangl kafjg U fuhitu da a ta lambaya ta yi tambayniwajgngau, uku ba ta, samu wanda ya ce ya gancshi ba, duk da su din ga dukkan alamu sumamezaa unguwar ne. Blankalinta Ya soma Jashi, Jashi, isoro soro ma ya somare kamatkar daifa zancen Antinta ya zama gaskiya ila kadaj ke ganinshi, ta yi kamar ta juya ta nufi gida sai,kurum ta i kai ko dama hakan ne ba mai cutarwa ba ne aa gareta ya kamata ta nemeshi ta ji menene dalilin da da yake fitowa tany ganinshi yanzu kuma ta daina bayan ya riga ya sa sun gaba ita da shi? Ci gaba da nema da ta yi shi ns dalilin da ya sanya ta yi nasarar gano inda gidan Basu yake cikin wani lungu, tana, tsaye a kofar zaurgn, gidan nasu mai tsananin duhu saboda tsukewar shi, tana tana nazarin nazarin zauren kafin ta shiga cikinshisaboda bata jya hango112.00 komai daga nan inda take tsaye, yaron da ya rakotan ya sake ce mata in dai ani saurayi mai yawo a a keken gidansu, idan ma ya guragyike nema to nan ne gidan nuna miki, wani gida ba wannan ba akan shi ne nasu to karya ya yi miki don na ga alamar wumin dan ashana ne, kullum ka ganshi da nkakkun kaya kuma yana fama da kanshi çikin uragi amma sai ka ga ya fito daa safeafe yanа 38 Γε Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi rabawa masu kafa biyu sadaka bayan shima wurin bara yake wuni. Nana ta tura kai zuwa cikin zauren saboda bata jin dadin bayanin da yaron ke mata in kin shiga ciki ki ce ina babar Nura? Sunan Mamanshi kenan yaron ya sake mata bayani duk da ba neman hakan ta yi ba. Suna shiga cikin zauren Rahma ta buga tuntube da wani katon turmi dake kafe a gefe, a firgice ta kwallara kara da sauri Umma Talatu ta fito daga dakin cikin zauren tana fadin "Subhanallahi, wacece wannan? Kin yi tuntube ne da turmin nan ko?" Cikin ladabi Nana ta soma gaisheta, cikin ladabi ita kuma tana amsawa, tare da nuna kulawarta ga 'yar karamar yarinyar, to ki yi hakuri mana ya ya budurwa kamar ki kuma da raki? Yi hakuri, yi hakuri, sa hannu biyu ki share hawayen naki, kar Malam dina ya fito ya ga hawayen naki, ya ce baya auren saboda baya son raguwar mace, hannu biyu Rahma ta saka tana share hawayenta, yayin da Nana ke ta faman murmushin al'amarin nasu. "In ce ko ku baki ne?" Ta yi tambayar bayan ta maida hankalinta wurin Nana. Nana ta ce "A'a 39 Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi anan unguwar muke ta can sama kadan wajcn gidan Alhaji Sani." Tsohuwar ta ce "To, to to na ji wa ku ke nema?" Nana ta ce mata "Babar Nura nake nema." Та се "То ai ni ce babar Nura, sai dai kuma ba ki sanni ba nima kuma ban gane ki ba." Nana ta ce "E wani mutum nake nema ta shiga siffanta mata shi sai da ta yi shiru sannan ta ce "To ai ina jin dai Nuran kenan ki ke nama ko kuwa shima ba ki san sunan nashi ba ne?" Nana ta yi murmushi ta ce "E." "To in ce ko dai lafiya?" Nana ta sake cewa "E, zuwa dai na yi in ji ko lafiya ba na ganinshi a wurin zamanshi shi ne na ce bari in tambaya saboda jiki da jin dadi ya kama." ২ Umma Talatu ta ce "Ai kuwa Nura yana nan kwance kwana ukun nan duka jikin nashi babu dadi, shiga nan bayan ki yana ciki ku gaisa." Ta waiwaya ta kalli kofar ta ce "A'a ba ma sai na shiga ba a dai gaya mishi ina gaisheshi Ubangiji Allah ya ba shi lafiya." Umma Talatu ta ce "To me kenan kuma aka yi kin zo har gida amma ba za ki shiga ki ga jikin 40 Da kamor wuya.... Hafsat C. Sodangi na shi ba? Ai ko daga tsayc ne kya shiga ku gaisa." Ba ta yi musu ba saboda ganin girman shekarunta, a bakin kofar ta yi sa!lama daga ciki ta ji an amsa sallamar tata don haka a hankali ta tura kofar ta shiga dakin wanda shima duhun cikin shi bai barin a fahimci abinda ke cikinshi cikin gaggawa sai da suka zauna kan wata tabarma dake shimfide cikin dakin na dan wani lokaci kafin ita da Rahma su ka fahimci abinda ke cikin dakin a dalilin sabawar da idanuwansu suka yi da yanayin hasken dakin, daga katifar da yake kwance akai sai ko keken shi na guragu dake ajiye a gefe, cikin sauri ta juyo gareshi bayan ta dan juya idanuwan ta zuwa kallon yanayin dakin, idanuwansu suka hadu cikin nutsuwa da jin kunya ta tambayeshi ya ya jikin naka?" Da kyar ya iya bude baki ya amsa mata da sauki saboda tsananin farin cikin da ya samu kanshi a ciki ya sakarwa Rahma murmushi tamkar ba rashin lafiya yake yi ba "Yan mata ya sunanki?" Rahma ta bude baki a hankali ta ce mishi "Sunana Rahma." Ya ce "A'a suna mai dadi Baba ya zabar miki 41 Da kamar wuya.... Hafsat C. Nodang! in ce ko dai yana sonki da yawa ne?" Rahma ta gyada kai nuna alamar lallai baban nata yana sonta, ya sake wani murmushin to matso daga nan mu dan yi hira mana Ba ta yi gardama ba, ta je kusa da shimfidar tashi ta zauna, yana dan wasa da 'yan yaisunta yana kuma fakon Nana yana satar kallon ta sai ya ce "Ni Rahma ya sunan Antin naki ne?" Ba tare da ta dan yi jim ba ta bude baki ta ce mishi "Sunanta Nana." Ya yi murmushi ya ce "Nana Asma'u ko Nana Aisha ko Nana Fatima?" Rahma ta ce "NIma ban sani ba." Ya kalli Nana ya ce "Don Allah Nana taimaka min cikin aljihun kekenan nan nawa akwai cakulet dan mikowa Rahma." Cikin sauri da nutsuwa ta mike ta nufi kan keken nashi ta sa hannu a aljihun keken kamar yanda ya gaya mata ta jisu da yawa a ciki, ta debo kwaya uku cakulet ce masu tsadar gaske zuciyarta ta raya mata ta mika mishi. "Haba debo mata da yawa mana wannan me zai mata." Ya fada yana mai kallon fuskar Rahma. Ta sake karo mata sannan ta koma wurin zamanta ta zauna. "Sai ki ka ga bana fitowa." A hankali ta cе 42 Da kamar waya, Masat C Sadang mishi e, dama na ce watakila ba ka dda lafiya ne?" а лсс "ВBari kawai gNanawaniiiy sb matsanancin ciwon kai ne nake fama da shi in yaub tashi sai an yi ta dora min kankara a kaina sabodaitr tsananin ciwo, na so kwarai a ce na yi jarumtakar da na fita na je can wurin in jira zuwanki in yi miki

Chapter 2 of 4