bayani don kar ki ganni shiru amma hakan
bai yiwu ba don ina cikin inuwa ma fama da kan Kn
nawa nake yi balle kuma ace na fita cikin rana saj,
in ji kamar wuta aka dora min akan. Don Allah ki
yi hakurin wahalarwar daRre na yi miki tun da ga shi 2.
na saki kin taso kin zo har wannan lungun namu
mai matsatsi da yawan kwatause sos) sna nТ
Ta ce "Kai daina fadin haka don Allah yanzu
ka je asibitinc?ded su ni owst gy ៩៦ ទចននិនយ
Ya girgiza kai ya ce A'a ban je ba amma
Ummana ta yi min jike-jiken wasu saiwoyi suK ALSАВП CE
nake sha kuma ina jin dadin su don na dan jiі
dadi" for evabad evilslead rinsg sasi gix
Ta ce "To Allah ya kara maka lafiyaa En esnision
Ya ce "To na gode Nana na gode, kwarai da
kulaward da ki, ka nuna min na gode Allah KO. 2
Ubangiji ya saka miki da-alherHM" 5 sA ILUS2 SD
***
43
POKS KE ME KOMI IS THIRAT
Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodang!
Tun daga wannan ranar kullum Nana za ta sa
a kawo mishi abin karyawa da safe abincin rana
da kuma na darc ba ta dai sake zuwa gidan don
duba shi ba, to amma kowane lokaci tana cikin yi
mishi aike har dai ya samu lafiya ya fara fitowa.
Tun daga ranar da ya soma zuwa kofar
gidansu Nana ya aika ya kirata ta fito bai sake
komawa bakin hanyar da yake zama ya zauna ba,
kullum ya kan je gidan su Nana ne da yamma ta
fito su sha hirarsu sai dai kuma babu zancen sosai
ya cikin hirar tasu mafi yawancin kalamanshi
sukan tafi ne ga yin godiya ga karancin da ya се
wai Nana ta yi mishi.
Tun Nana tana sauraronshi har dai ta gaji ta ce
ita kam ta rufe wannan zancen tsakaninsu in da
maganar da ya kawo in kuma babu to sai ya yi
murmushi ya ce "To ai shi kenan Nana yanda duk
ki ka ce a yi ai hakan za a yi amma in ban da haka
i da ba zan gaji da gaya miki wannan alherin ki ba
kin taba ganin tsaleliyar budurwa kamarki tana
sauraron gurgu?"
Nana ta yi tsaki ta ce "Kai kuwa Nura me ya
sa ka ke yin haka ne shi gurgu ba mutum ba ne?
Da sauri ya ce "Mutum ne ma cikakke amma ai
irinku ne kawai suke kallonmu a haka."
44
Da kamar wuya. HafsatC. Sodangi
da Ta çev"To ni dai a kashe irinm wannanji
maganar a tsakaninmu on baki. dama kuma na riga
na Ya ce "Nima na bári ba zan sake yi ba tundaa kin ce ba kya so."ki ke mikewa cskin sauri ki tafi Soyayya ce mai karfi ta kullu a tsakanin Nura
da Nana duk da dai ba furtata ba illa dai dukkan
alamominta sun bayyana haka nan su da suke jin
abin a jikinsu suna ji babu abin da Nana ke son jin
ya fito daga bakin Nura illa gaskiyar abinda ta sana
shi ne a tsakaninsu don ta samu damar yiwa
yayarta bayani a kan shi ta ji abinda za ta ce,
amma shi ya ki kullum sai dai ya turo kekenashi
ya zo ya yi hirarshi ya kama hanya ya tafi wani
lokaci ma ko da ya san ba ta nan a gidan zai turo
keken nashi ya zo kofar gidan ya kira su Rahma
da Kannenta su zo su yi hira ya kuma ba su
cakulct da sauran tsaraba yara su karba suna
murna shi kuma ya tura kekan shi ya tafi.a Kalaa"
Hankalin Nana ya kai matuka wajen tashi
akan dabi'un Nura na kin furta soyayyarshi gareta
ko kuwa yana nufin ya ce shi bai san halin da
suke ciki ba ne? Ko kuwa jira yake yi sai ita ta yi
mishi nuni kan hakan, ta jinjina hakan cikin
zuciyarta ta ce kai ita kam ba za ta iya ba don ita
kam a wurinta ba ta taba daukar wayewar kan
45
Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodang!
'yan matan yanzu dake cewa samari suna sonsu a
matsayin wayewa ba don haka ba za ta iya ba, in
shi bai ga dacewa ya yi magana ba to shi kenan su
yi ta zama a haka ai kowa yana jin jiki.
Shi kuwa Nura yana kwance a dan tsukakken
dakinshi da bai ko isarshi mike kafa sosai saboda
tsawonshi cikin dare ne amma idonshi biyu ya
kasa yin barci saboda tsananin tunani, lokaci ya yi
da ya kamata ya furtawa yarinyar nan gaskiyar
lamarinshi tun da dai zuwa yanzu ya tabbatar
alamomin da yake gani a tare da ita na so ne
abinda wani sashin na zuciyar ke gaya mishi
kenan, yayin da daya 6angaren na zuciyarshi ke
mishi kashedin maza ka je ka wargaza 'yar alakar
da ku ka soma samu garin saurinka da бабare,
yanzu haka wannan sakin fuskar da take maka na
tausayi ne bisa halin da ta ganka a ciki kana furta
wata kalma mai kama da soyayya a gareta
al'amarin naku ya watse gaba daya, shiru ya yi
yana kallon saman dakin duk da bai iya hango
komai saboda tsananin duhun dake ciki rayuwa
yake tunawa da yanda al'amura ke juyawa suna
canzawa a kowane lokaci, ya lumshe idanuwanshi
a hankali cikin tunanin al'amuranshi da yake gani
tamkar a mafarki yake.
46
***
Da kamur wuya.... Hafsat C. Sodangi
Nana tana gida a yau kasancewar ranar ta Lahadi ce tun safc take tare da Antinta a kicin
suna faman shirya abinda karyawa kasancewar
maigidan ya dawo daga tafiya ga kuma baki da ke
ta faman shiga da fita sai wajen karfe goma Nana
ta kammala ta shiga bandaki ta yi wanka ta fito ta
shirya tsaf, bayan ta gama shafe-shafenta ta yi
shiri cikin wata atamfa da ta yi matukar dacewa
da ita ta shigo falon Antinta ta sameta ta nemi
wuri ta zauna tana tambayarta.
"Za ki karya yanzu ne?"
Cikin sauri Hajiya Salma ta ce mata
"Karyawa kai Nana kalli agogo fa wajen sha daya
ne yanzu."
Nana ta tashi ta fita ta je ya kawo musu suka
zauna suna karyawa cikin mu'amala mai dadi da
kauna mai yawa.
Hajiya Salma ta kalli Nana ta ce mata "Ina
ganin fa kamar nan ba da daďewa ba Alhaji zai yi
aurenki don na ji ya fara yin maganar."
Nana ta dago ido ta kalleta cikin nutsuwa ba
tare da ta nuna damuwa game da maganartata ba,
cikin shagwaba ta ce mata "To na kawo saurayi
ne Anti da za a fara zancen aurena?"
47
Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi
Hajiya Salma ta yi murmushi "Shi kam Alhaji
ko ki kawo saurayi ko kar ki kawo ina ruwanshi,
tun da shi dama ina ganin kamar yana da wanda
yake son baki."
Gaban Nana ya yanke ya fadi ya ke son ba ní
fa ki ka ce?" Ta yi tambayar .cikin nuna alamar
tashin hankali.
Hajiya Salma ta yi maza ta tsuke fuka ta ce
"Bai isa ya yi hakan ba ne?"
Nana ta sunkuyar da kai cikin sanyin jiki da
sanyin murya ta ce "Ya isa Anti." Ta mike za ta
fita, ta ce mata "Dawo ki zo ki zauna ki gaya min
mene ne?"
Nana ta dawo ta zauna tana sauraron 'yar
uwar tata kan ta ce komai aka shigo aka yi
sallama, Nana ta amsa yaron da ya yi sallamar ya
ce "Wai Nana ta zo in ji Nura." Ta сe "To gaya mishi ina zuwa."
Ya juya ya tafi, ita kuwa Hajiya Salma ta zuba mata ido cikin nutsuwa a hankali ta bude
baki ta ce mata "Ni me ke tsakaninki da wannan
mutumin ne?"
Nana ta yi shiru cikin tunanin abinda za ta се
mata sai ta ji ta ce "Ina fata dai ba shi ki ke shirin
kawowa gidan nan ba? Don na lura da irin zaburar
48
Da kumar wuya.... tafsat C. Sodangi
da ki ka yi da na ce miki ina ganin kamar Alhaji
yana da wanda yake son baki, dama kuma na riga
na lura da ke duk lokacin da aka ce yana kiranki a
waje zumbur ki ke mikewa cikin sauri ki tafi sabanin su Musa da in sun zo sai an yi kamar anan yi da ke kafin ki fita."
yi
Nana ta yi shiru ta sunkuyar da kanta kasa ta
shiru tana sauraron yayar tata dake ta faman
tashin hankali sai da ta gaji ta yi shiru don kanta
sannan ne Nana ta mike tsaye ta nufi kofar gida,
Nura yana zaune cikin kcken shi yana sauraron
fitowarta.
"Barka da fitowa, ranki ya dade." Ya fadi
cikin murmushi da murnar ganinta. Ta amsa mishi
sai dai bata maida mishi murmushin ba kamar
yanda ta saba abinda ya sanya gabanshi faduwa,
in ce ko dai lafiya Nana?"
Ta dan kalleshi a hankali ta ce "Lafiya kalau."
Ya ce "Haba Nana ai ba haka na sanki ba, ba
haka na saba ganinki ba taimakeni ni dai ki gaya
min in dai wani laifi na yi don in yi sauri in ba ki
hakuri." Ta dan saki fuska cikin kokarin da take
yi na ganin ta nuna mishi babu damuwa, ta ce "To
ni laifin me za ka yi min?"
Ya ce "Haba Nana in ki ka fadi haka ai sai in
49
Da kumat w Hasged
ga kamar ban isa in yr muki lartin ba ne
Та се "Ba haka ba ne ot dat kawat ba ka mun
komai na laifi ba ne sht ya sa na gaya maka haka "
Ya.ce "To at shi kenan ba na javayya da ke
tunda kin ce ban yi mikı komar ba na yarda ban yr
miki ba, amma duk da haka ma rokonki gafara m
har abinda ya sosa mikı ran ya shafeni"
Ta dan yi murmushi kawai ta yi shiru suka
dan shiga hira sai dai ta kasa sakin jikinta su yı
hirar sosai kamar yanda suke, haka Nura ya gajı
duk kokarinshi na ganin ya rabata da damuwarta.
hakan bai yiwu ba.
***
Washegari a makaraula suna zaune a dakin
karatu suna nazarin littattafansu saboda gab suke
da soma jarrabawar su
Kwatam sai ga wani yaron ajinsu Ans ya
shigo ya ja ya tsaya a kansu yana murmushi
"Nana wurinki fa na zo."
Ba tare da ta daga ido ta kalleshi ba ta ce
'AGani ai Allah ya sa lafiya, ya ya."
"A'a lafiya Kalan zuwa dai na yi in rokeki
wata alfarma."
Ta bar abinda take vi ta dago tana kallonshi
ya sake wani mumushn kafin ya sassauta
50
Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodang! muryarshi ya ce mata "Kin san yau sha hudu ne ga watan biyu, wato ranar valentine tun safe nakc nemanki don in rokeki tunda yau ranar masoуа сс kin kuma sani dama ni masoyinki ne ke ce dai kawai ba ki bani hadin kai ba, amma tunda yau rana ce ta musammán ki bani hadin kai mu raya ranar ta zamo mai tarihi da ba za mu manta da ita ba, kamar yanda ni kullum ki ke cikin raina ba zan taba mantawa da ke ba." Ya zuba mata ido
cikin sauraro don ganin irin lalataccen kallon da ta ke mishi, ya dan saki wani murmushi na sakarci tare da tsaki "Ni ke Nana kamar ba 'yar jami'a ba." Ya sake kallonta ya ga ko inda yake ba ta kallo balle ta saurareshi, sai Zuwairiyya ce ma ta ce mishi.
"Ai sai ku je ku yi ta yi duk wata eda da ba ta ku ba ba ku san asalinta ba suma ma yin nata ba su san dalilinsu na yinta ba amma kun ara kun yafa, wai ku ga wayayyu 'yan boko tö yana da kyau ku rinka tunaw ada cewar ku Musulmi ne." "Ai kuma shi kenan tunda ke ma kin min fuck-up"Ya jiuya ya fita ya bar su suka ci gaba da abinda suke yi bayan sun tashi daga makaranta ne, suna dawowa gida Nana ta ke baiwa Zuwairiyya labarin abin da ya faru. 51
Du kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi
Cikin sanyin jiki Zuwairiyya ta ke ee mata
"To ki dai sani cewa, mijin Anti tamkar uba yakс
a wurinki, don kuwa babu abin da bai yi miki ba
cikin abubuwan da uba ke yiwa 'yar shi."
***
Kwana da kwanaki Nana tana gida cikin
matsanancin hali da damuwa saboda rashin sanin
halin da take ciki ga dai maganar da Antinta ta yi
mata wanda tun daga ranar ba ta sake ce ata
komai ba, ga shi kuma wani dalilin da ba ta sani
ba ya sanya Nura ya dauke kafa ya daina zuwa
gidansu ya koma zaman kan hanyar da dama can
yake yi sai in ta zo wucewa ya fan rusuna yana
daga kan keken guragun ya ce mata "Barka da
fitowa ranki ya dade a dawo lafiya."
Abin da yake matuka bata takaici da kona
mata rai me ta yi mishi ya ke mata irin wannan
cin zarafin? Ko kuwa dai wani ne ya yi mishi
wani abu a kanta ba ta gaya mishi ba, ko kuwa dai
haka ya yi sha'awar yi mata don ra'ayin shi na
kanshi wadannan sune tambayoyin dake kai kawo
cikin zuciyarta.
A wannan lokacin ne ta gane tsananin
shakuwar da suka yi kafin dauke kafar da ya yi
don kuwa ba karamar wahala take yi ba, ta rasa
52
7
Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi
inda za ta yi ta san me ke faruwa, wata zuciyar
tana raya mata ta samu Antinta ta ji inda wani abu
ta san ba za ta kasa sani ba. Kuma wata kila in ta
yi sa'a ma sai ta ji duk wani abin da ake ciki.
Da daddare ta samu Antin nata a dakinta cikin
shirin kwanciya ta nemi wuri ta zauna yayin da Hajiya Salma ta maida al'amarinta garcta in ji ko
dai lafiya na ganki yanzu ba ki kwanta ba bayan kin wuni kina wahalar makaranta?
Nana ta ce ba komai Anti lafiya kalau, so dai
kawai na ke yi Anti da in sani ko an yi wani abu
ne?"
"Wani abu kamar ya ya?" Hajiya Salma ta
zuba mata ido. Nana ta dan sunkuyar da kanta
Kasa ta ce "A'a gani dai kawai na yi Nura ya daina
zuwa kofar gidan nan ban kuma san abinda ya sa
hakan ba."
Hajiya Salma ta zuba mkata ido cikin nutsuwa
ta ce mata "Ni na sa aka hana shi saboda na gane
hikimarshi na zuwan da yake yi din bai wuce ya
yaudarcki ba, ya sa ki bijirewa iyayenki, tun da
shi ban ga alamar ya tsaya matsayinshi ba."
Nana ta dan kalleta a hankali ta ce
"Matsayinshi kamar ya ya Anti?"
Cikin takaici ta ce mata "Ba kin ce mun gurgu
53
ba ne?"
Da kamar жига.. Нafsat (. Sodang
Та се "Е,."
Ta ce "To shisshige mikin me ya ke yi kullum
sai ya je ya yi bararshi ba zai ajiye 'yan kudinshi
ya samu na cin abinci ba shi da tsohuwar shi sai
ya je ya sayowa yara kayan ciye-ciye masu tsadar
gaske ya kawo musu wane irin gurgu ne wannan
da-budadden ido haka? To ba na so bana so maza
ki fita hanyar shi, tun ba mu kai ga samun bacin
rai ba, su kansu su Rahma in aka ce musu gashi
nan yana kiransu sun rinka tsalle kenan suna
murnar zuwanshi wato shi kuma tashi hikimar
kenan ya saye zuciyarki, ta alawar da yaek baiwa
'ya'yanki to na ki."
Nana ta dan yi shiru zuwa can sai ta се
"Amma fa Anti shi Nura wannan mutumin ni ban
taba ganinshi yana karbar sadaka ba ba na zaton
yana bara, ni ban ma taba ganin wani ya zo wuce
wa ya mika mishi wani abu ba, iyaka dai in ji
suna gaisawa da jama'a."
Ta ce "Ba ya bara me ye sana'arshi?"
Nana ta ce 'Nima ban sani ba."
Ta ja tsaki ta ce "Ahau to ai gara ki yarda
yana barar akan ki ce ba ki san abinda yake yi ba,
tun da dai ga shi yana kashe kudi ko jiya fa ga
54
Da kamar wuya... Hafsat C. Sodangi
abubuwan da ya baiwa wani dan almajiri ya
kawowa su Rahma, can na kwace na ajiyc in
kuma bai bari ba da kaina zan je in samu ita
Umma Talatun in ja mata kunne danta ya fita
hanyarki, tun muna shaida juna da ita cikin
mutunci."
Ta dan yi tunani kadan zuwa can ta ce "Ni
Umma Talatu ma fa ban santa da wani da ba nata
na cikinta don bana zaton ta taba haihuwa na dai
santa da yaya me yayumen 'ya'yan jama'a to zan
gaya mata kul ta fita hanyata, tun rai bai kai ga
baci ba, ko kuwa kin ga rashin kyautawa na ne
don na lura tunda na fara magana ki ke kallona?"
Cikin nutsuwa Nana ta ce "A'a."
Ta ce "Yauwa ai kema kin san ba zai yiwu
ace kin auri gurgu ba ko? In ban da rigimama irin
ta shi ina zai kai tsaleliyar budurwa kamar ki?"
Nana ta tashi ta fita ta koma dakinta ta kwanta
cikin takaici da 6acin ran abinda Antinta ta sa aka
yi wa Nura, duk da ba ta shirya yin jayayya da
mijin yarta akan wanda aka cc mata zai bata ba ko
da kuwa wane ne abinda Antin nata ta yi ya yi
matukar 6ata mata rai kuma in da za ta samu
damar zabar wa kanta miji to da gurgun ta zaba ta
bar masu Kafafuwan. 55
Du kumar wuya.. Hafsat C. Sodangi
Gari na waye ba ta ma tsaya yin atkin komar
ba don kar Nura ya kai ga fitowa kan hanyar da
yake zama ya zauna. Ta yafa hijabinta ta yi maza
ta kana hanya ta nufi gidan nasu kai tsayc ta
shige cikin zauren nasu ta yi sallama a bakin kofar
dakin shi daga ciki ya amsa ya kuma ba ta izinin.
shigowa, a hankali cikin sanyin jiki da nutsuwa ta
shiga yana kwance kan 'yar shimfidarshi ya
kudunduna cikin lallausan bargonshi ga wani
kamshi mai ni'ima da ya gauraye dakin yana
ganinta ya yi maza ya tashi zaune, yana kallonta
cikin nutsuwa sosai Nana ta kawar da fuskarta
daga kallon da ya ke yi mata yayin da zuciyar ta
ke tunanin mutum mai tsabta da son jin dadi dubi
halin da ya ke ciki amma komai nashi tsab komai
nashi mai kyau, ga shi kyakkyawa in ban da
lalurar gurguntaka da yake ciki ai kuwa da babu
wata uwa da za ta ganshi ba ta yiwa diyarta
sha'awar aure shi ba.
"Nana in ce ko dai lafiya?" Ya yi tambayar
bayan ya gama nazarinta, ta sunkuyar da kanta
kasa cikin rawar murya ta ce mishi "Na zo ne in
ba ka hakurin abinda Antina ta sa aka yi maka."
Da sauri ya kalleta ya ce "Antinki kuma Nana
me za ta min da har za ki zo kina bani hakuri a
56
Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi
kanshi? Ai ni ba ta min komai ba"
Nana ta daga ido ta kallesh ta cc "Ba ta ma
komai ba ka daina zuwa gidatanu? Ko kuwa
kawai ka yi hakan ne don kana bukatar bata min
rai?"
Da sauri ya ce "Haba Nana me zai sa ni kuwa
in bata miki rai, to a kan wane dalili zan yi haka?
Menene jin dadina idan na bata miki? Ai ni
tunanina da burina bai wuce ace na samu damar
da zan faranta miki rai ba in kyautata miki in
sanyaki farin ciki, in ga murmushi ya bayyana a
fuskarki."
Та се "То in haka ne menene ya sa ka daina
zuwa gidanmu sai ka zauna a hanya idan na zo
wucewa ka ce min Malama barka da dawowa irin
gaisuwar da ka ke min a lokacin da ba ka sanni
ba."
Ya ce "E, Nana gaskiyar magana ita ce an
hana ni zuwa gidanku bisa kashedi mai tsanani
ban yarda Anti ce ta bayar da wannan umarnin ba
kuma ba zan yarda wani ya ce min ita ce ba don
haka kema kar ki yarda ace miki ita ce, babu
mamaki nema ake a hadamu da ita. To amma ya
zama dole in kiyaye zuwa gidan saboda tsoron
abin da zai shafi lafiyata, tuni kuwa kin ga duk
57
Da kamar wuya.... Hafsut (. Sodangi
abin da zai shafi lafiyata ai dole in tsorata da shi
tun yanzu ma ya ya? Ballc ace wani abu ya sake
samuna shi ya sa na koma zaman kan hanya in da
zan rinka ganinki tunda Allah ya jarrabi zuciyata
da son ganinki. Kwana faya in ban ganki ba sai in
.rasa nutsuwata in kasa fahimtar al'amurana in rasa
inda zan tsoma raina, in ji dadi. To ni kuma ga
yanda nake yanda duk na kai da sonki dole ne in
hakura in danne zuciyata in ja bakina in yi shiru
tunda a ina ki ka taba ganin an baiwa gurgu
tsaleliyar budurwa kamar ki? Don haka ni ban ga
laifin masu yi min kashedi a kanki ba, son ki suke
yi sun kuma ga ba ki dace da ni ba, don kuwa
dama ai kin san an ce wai da kamar wuya,
gurguwa da auren nesa. To nima na yarda da
kamar wuya gurgu da auren tsaleliyar budurwa..."
Umma Talatu ta tsaya a bakin kofa tana
tambayar "Kai da waye kake magana Nura?"
Da sauri ya ce mata "Umma Nana ce ta shigo
yanzu, dama zan ce mata ta shigo ta gaisheki."
Da sauri Umma Talatu ta ce "A'a ba na so ban
ce ta shigo gaisheni ba bana bukata kai dai da
yake baka da zuciya to ka je ka yi ta yi tunda an
cc ka fita hanyarta in kuwa ba haka ba a karasaka
amma ta zo yanzu ka tasata a gaba tana maka
58
Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi
iyayi me za ta gaya maka? Mc za ta gaya maka da
za ka tsaya kana sauraronta? In dai ba nema ka ke yi sai ka ja mana abinda zai damemu ba?"
Cikin nutsuwa ya ce mata "Ki yi hakuri
Umma? Ba laifin Nana ba nc ita ma ba ta ji dadin abinda ya faru ba, ai tun da ma ta zo har gida
Umma ina ganin babu wani zargi a kanta."
Та се "Кai tafi can don Allah kai kana da ma
ai ba zaka ga laifinta ba tun da idonka ya riga ya rufe a kanta in babu ruwanta ai da ruwan 'yar uwarta tunda ita ce ta turo a yi maka kashedin, ko
yanzu ma ni ban yarda da ita ba watakila wani abin aka hado har da ita ya sa ta yi sammako ta zo
mana gida ka ga in sun turo wani yanzu ya zo ya duba sai ya zo ya sameta su sami damar yi mana cin zarafi, tun da mu ba masu shi ba ne, ka san su
mutane yanzu in mutum ba wani abu ne da shi ba, to ba komai ba ne, wasu ma kallonshi suke yi tamkar shi din ba cikakken mutum ba ne, don haka ta tashi ta fita."
Da sauri Nura ya ce mata "Yi hakuri Umma,
ai ke ba mai dabi'ar wulakanta bakonki ba ce ita
Nana ai baukwarki ce ki yi hakuri."
Umma Talatu ta juya ta koma cikin gida ta bar su nan tana barin wurin Nura yà shiga baiwa
59
Da kamar wuya... Hafsat C. Sodangi
Nana hakuri, "Ki yi hakuri Nana ta Umma wai
babu dama wani ya yi min wani abu komai
Kankantarshi sai ta ce dole sai ta ji zafinshi. Ki yi
hakuri don Allah kin ji."
Nana ta sunkuyar da kanta kasa ta yi kokarin
boyc fuskarta daga hawayen dake zuba saboda
tausayi, "To wai in mutum yana da wata matsalar
rayuwa shi kenan komai kyan halinshi da dabi'ar
shi wai shi din kuma shi kenan ba zai mallaki
abinda yake so ba?" A hankali ta mike ta sake
gyara hijabinta ta ce mishi "Zan tafi."
Ya ce "To Nana na gode, Allah ya saka miki
da alheri don Allah. ki yi hakuri kan abin da
Ummana ta yi ba ta yi miki hakan don kiyayya ba
"
ne."
Nana ta ce "Ba komai ta juya ta fita daga
dakin sai dai maimakon ta yi waje sai ta shiga
cikin gidan Umma Talatu tana tsakar gida tana
faman shura furar sayarwar ta, ta amsa sallamar
Nana cikin fara'a tamkar ba ita ce ta gama balbala
masifar nan ba dazu-dazun nan, Nana ta nemi
wuri ta tsugunna don ta gaisheta Umma ta yi
maza ta tkatseta ta hanyar mikewa ta nufi dakinta
tana fadin shigo mana shigo daga ciki."
Ba ta yi musu ba ta bi bayanta dakin nata dan
60
Da kamar weya.., Hafsat C. Sodang! tsaf yake an maleleshi da kafet ga kuma kusurunta guda biyu manya ga kayan mutanta daga waje ba za ka taba zaton haka dakin tsohuwar ya ke ba. Nana ta zauna a kasa duk da umarnin da tsohuwar ta bata na ta hau kujera ta zauna cikin ladabi ta gaisheta, itama kuma ta amsa cikin sakin fuska da walwala har tana tambayarta ya ya
mutanen gidan naku?"
Ta ce mata "Lafiyarsu kalau."
Ta mike da nufin tafiya "Baba Talatu ta yi
maza ta mike ta je ta shura mata fura katon
mulmule ta nade a takara ta sanya a leda ta miko
mata ta ce "Ta kaiwa Antinta hannu biyu Nana ta
sa ta karbi furar cikin yanayin godiya da
girmamawa, ta juya ta fita a kofar gida ta tarar da
Nura yana zaune kan keken guragun shi ta nuna
mishi furar da Umma Talatu ta bata ya yi
murmushi ya ce "Ina ruwan Umma."
Ya sake kallonta cikin murmushi ya ce "Kin
ga in ban dda akan keken guragu nake ai da sai
kawai in mike in taka miki, to babu hali."
Nana ta kalleshi ta ce "Ba ka dai yi niyya ba
kawai tunda ai kana tura keken naka ka je ko ina."
Nura ya ce "A'a Nana ba zan rinka bin ki da
wannan keken ba a rinka kallonki ana nuna wa
61
Da kamar wuya.... Hafsat C. Sodangi
ana ccwa wancan yarinyar saurayin ta gurgu ne
bayan kuma ba hakan ba ne."
Ta ce "Kai ne ka ke ganin kamar hakan
matsala ne ni a wurina ba komai ba ne tunda na
san kowane mutum da darajar da Allah ya yi
mishi."
Ya girgiza kai a hankali nuna alamar hakan
ne, ta ci gaba da tafiyarta yayin da shi kuma ya ci
gaba da bin ta da kallo.
a
***
Nana tana isa gida ta tarar da Antinta a fusacе
dalilin neman ta da ta yi ta rasata a cikin