Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 4
zai kwanta ba." Inna Laure ce ta sake binta ta riketa tana fadin "Haba Sadiya ina yi miki magana kina sake zabura? Banda abinki duk wanda ya zagi uwar wani ai tasa ya zaga, daga gani ai kinsan babu tarbiyya, wuce mu tafi daki." Ba ta ko musa ba ta tabi bayanta suka nufi dakin Sadiya. Ba ta bari sun shiga ba ta biyo bayansu da muciya a hannu tana faman huci tana fadin "Aikin banza, har Kura ce zata ce da Kare maye? Za a samo mai tarbiyyar dai a cikin mu. A fusace Sadiya ta juyo tana fadin "Inna kina jinta fa abin da take gaya miki, don Allah ki barni nai mata jini da majina a jikinta kinga sai ta shiga taita yinta." 1.07 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CЕ Da sauri Innar tata ta sake riko hannunta tana fadin "Na dai gaya miki ki shige muje ďaki ko?" Ran Sadiya a 6ace domin ba haka ta so ba. Za ta mazgawa Lami rodin dake hannunta da sauri Lami ta kaucewa Rodin dan haka bai sameta ba sai kawai ya yi tsalle ya tadda Mero ya sameta gefen jikinta. a Da sauri ta kalli inda rodin ya sameta, a fusace ta ce, "Wallahi ba zan yarda ba, haka kawai ni ba da ni ake fada ba a nemi a cutar dani?" da sauri ta nufi inda Sadiya ke tsaye, itama Lami ta nufeta gami da damko wuyanta, nan take kokawa ta ta kufce a tsakaninsu su duka ukun. Da kyar Inna Laure ta kwato Sadiya daga' hannunsu, tana faman janta 108 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE tana dagewa sabida taurin kai, duk kuwa da har su biyu suka hadar mata. A fusace Inna Laure ke fadin "Yanzu Sadiya abin da na gaya miki ba zakiji ba kenan? To'shikenan bari na yi tafiyata tunda ban isa na fadi ki ji ba." Lami cikin huci da mai da numfashii ta ce, "kyaleta mana in ba tsoro ba walląhi muyi mata wanka da jini in yaso yau duk mu kwana a bayan kanta." Meroviceta amshe da fadin "Ganemin hanya yar uwa wallahi ni yanzu zan iya kaiwa dare ina wannan fadan kuma ban gaji ba, ke idan ma kwana za ayi ana yi Bissimillah dan halak ka fasa." Ran Sadiyayya cika da daci sakamakon maganganun da suke gaya mata dan haka ta hau kokarin kwace 109 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE rikon da Innar ta yi mata tana fadin "Don Allah Inna bari na nunawa wadannan Kananan 'yan iskan basu isa komi ba a gurina." Ita kuwa Innar bata saurareta ba, illa janta da take kara yi har suka isa kofar dakinta tana fadin "Ba komi muje cikin dakin ai da sauran lokaci da kwanaki a duniya, kada ki damu in sun san wata ai basu san wata ba. Da haka har suka shige cikin dakin suka barsu suna faman hayaniyarsu. Bayan sun shiga dakin ne Inna ta hau azalzalarta da ta sallameta ta tafi don kar azo a tadda ana fada ace ita ce, ta haddasa. Da sauri ta dauko kudi ta mika mata, ta kirga, sannan ta dago ta kalli 'yar cike da tuhuma "Ya na ga haka 110 ALAWIYYA WADA ISA 'YAR ALJANNA CE kuma Sadiya? Kin sani fa na riga na yi lissafin abin da zamuyi da kudinnan. Sadiya ta kalleta kawai tana fadin: "To Inna abin da na samu kenan, dama yanzu niyyata naje dakinsa na samo miki wasu, shine wannan "yar bakin ciki ta hanani shiga dakin." Da sauri ta mike ta saka kudin cikin riga tana fadin "Ba komi Sadiya bari na tafi ke dai ki kara hi,ma kuma ki daina bari ana fada dake domin garin neman gira sai azo ana rasa ido." Tana kammala fadin haka ta fice da sauri ba tare da kowa ya a cikinsu ya ga: fitarta ba, domin da suka gaji da maganganunsu babu wanda ya tanka musu, sai kowacce ta nufi shashenta iАg 111 **** ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE Tafe yake a kan titin wanda ke kunshe da motoci a gefe sun cunkushe titin, haka Alhaji Sadik ya dinga ratsa motocin cikin kunar rai da tashin hankali, sambatu yake yi amma shi kansa in akace ya maimaita abin da yake fadi ba zai iya ba. Bai san inda ya dosa ba, shi dai kawai yana tafiya ne, tun yana ratsa cikin gari har yaje ya riski daji, ga kuma wani gudu da yake yi ba na wasa ba, yana cikin gudun ne sitiyari ya kwace masa ya je ya doki Bishiya kansa ya bugu, nan take ya suma. A kan hanyarsa ta zuwa kauyensu ne ya kula da wata mota a lalace daga gani hatsari ne ya sameta musamman yanda ta bugi bishiyar nan gabanta ya yi kwatsa-kwatsa. 112 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNACEA T6 Hardzai wuce sai wata zuciyarstay gargadeshi da cewar bai halatta gareshi ya wuce wannan gurin bai je ya dubaikos) akwai wani mahalukida cikin motar nan basg don hakayav samu nguri yamajiyels motarsa ya gangara inda, motar takesd aikuwa yana isa ya leka Motar sai gas mutum/a sume jini ya wanke masa fuska, nan ntakes yarhau kokarin ceto rayuwar Alhaji Sadik. EN sb nids ub sb usyd ism Sai da ya /kwantars dashioa bayänA motarsa sannan ya rufe motar ya shiğa ya tayare yanjuya kan Motar zuwasAsibitid yaria naddu'ar Allahyasvbawazwannansa mutumins lafiya,ryasas yanandairsauranls numfashi. nitidiaA SBaiv bar Asibitin banesaig da ya tabbatar an bawa Alhaji Sadik duk watas kulawa da ta dace a bashi.cHar ya farfadole daga suman da ya yi amma kumä yasgig 113 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE gaba da bacci yana fidda numfashi kamar na kowa sakamakon ruwan allurai da akai ta bashi. Sai da ya tambayi likita lokacin da ake sanya ran zai ya farkawa daga baccin, ya gaya masa sannan ya juya ya tafi. Gida ya koma ya sanar da Mama sannan ya umarceta da ta shirya abinci mai kyau da duk abin da za a bukata a Asibitin domin ya kaiwa Alhaji Sadik. Haka kuwa aka yi, duk abin da za a bukata ta hada masa, sai da ya fuskanci sauran kusan awa guda daga lokacin da aka bashi sannan ya kama hanyar tafiya Asibitin. A gabansa Alhaji Sadik ya farka amma zafin buguwa da ke kansa ta hana shi yin kwakkwaran motsi, magana ma ta gagara illa kallo kawai da idanuwa, don 114 ALAWIYYA WADA ISA. YAR ALJANNA CE haka basu iya cewa komi ba,, illa kallon kallo da suke yi, sai Alhaji Aliyu ne ke ce sannu, shi kuma ya amsa da kansa wanda shi kansa baya iya bude shi sosai. Da ya fuskanci Alhaji na jin jiki sai ya kira Likita ya shawarceshi da ya yi masa allurar bacci, ko ya samu saukin jin zogin ciwon, haka kuwa aka yi sai da ya tabbatar bacci ya dauke shi sannan ya kyaleshi ya tafi daga asibitin tare da nema alfarmar a dinga kula da shi kafin ya dawo. Kwanansa üku a Asibitin ya samu sauki sakamakon kulawa ta musamman da yake samu, har ana iya yin hira mai tsawo da shi, sannan yana iya tashi ya je har badaki ba tare da an kai shi ba. Ranar da ya cika kwana hudu ne Alhaji Aliyu ya shiga Asibitin. Zaune ya taddashi bisa kan gadon ga goshinsa 115 ALAWIYYA WADA ISA 'YAR ALJANNA CE daure da bandeji, ya saki dariyar jindadi yana fadin "Masha Allahu, Alhaji naji dadin ganinka a yau domin sauki ya sake samuwa kwarai. Ya isa ya zauna kusa da shi yana dubansa cike da jin dadi. Alhaji Sadik ya maida masa da martanin murmushinsa sannan yace masa "Alhaji ina godiya matuka, Allah ya saka maka da alkairi, ka taimaki rayuwata ka cetoni daga halaka domin ba don Allah ya kawoka ba zan iya mutuwa, Allah ya saka maka da Aljannar firdausi. Alhaji ya sake fadada murmushinsa ya ce masa "Ai ba komi Alhaji wanda ya taimaki wani shima Allah zai taimakeshi, ni kaina ina cike da farin ciki sakamakon samun saukinka, sai dai abin da yafi damuna bai wuce rashin sanin inda Iyalinka suke ba ballantana na sanar da 116 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CЕ su halin da kake ciki, kuma su san inda kake su zo su gana da kai." Bai iya ce masa komi ba illa hawaye da ya fara kara kaina a fuskarsa, hankalin Alhajji Aliyu ya yi matukar tashi nan take ya hau fadin "Subhanallah Alhaji ya kake hawaye? Me ke faruwa? Ko suma iyalin naka sun shiga halin da ka shiga ne? kake tunanin su? Hankalina ya tashi matuka, domin kukan babban mutum bashi da kyau." A hankali ya girgiza kai yana fadin "Ko daya Alhaji ban rasa kowa daga Iyalina ba, sai dai babban rashi na zama lafiya da kwanciyar hankali da nayi a cikin gidana, gidan ya zama tamkar sansanin yaki, babu wata rana ko wani lokaci da zan iya warewa nace ana zaune lafiya a gidana, hatta ranar da wannan tsautsayin zai sameni ina bacci da safe 117 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNAА СЕ nake mafarkin gidana na ci da wuta, jama'a sun taru suna zuba ruwa amma kamar suna kara mata fetur, kowa ya kasa kasheta." Ya ja dogon numfashi gami da goge hawayen da ke zubo masa. Alamun damuwa ya bayyana a idon Alhaji Aliyu cike da kulawa yace masa "Assha, Alhaji lallai kana cikin musiba da tashin hankali, rashin samun kwanciyar hankali daga Iyali illa ce babba ga namiji domin hatta tattalin arzikinsa karyewa yake yi, Alhaji ya aka yi haka ta faru?" Alhajin ya dago kansa ya dubi Alhaji Aliyu sannan yace masa "Wato Alhaji lamarin ya samo asali ne tun daga farkon neman aurena, wani abin ya faru a idona wani abin kuma labari ne aka bani." 118 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE LABARIN ALHAJI SADIK Tsaye suke a jikin motarsa shi da babban amininsa Auwalu suna hirar yaushe gamo kasancewar Alhaji Sadik din ya yi tafiya ta tsawon wata guda. Fuskokinsu cike da fara'a, Auwalu ne ke zolayar Sadik din da fadin "Wato Alhaji wannan kasuwancin na fita China dinnan ya karbeka matuka, sai. wani kyalli kake kana sheki daga ganinka nera ta riga ta zauna, ka shiga sahun matasan miloniyoyi, mu kuwa ka barmu muna ta bin Inuwa har sai dare ya yi sannan mu nemi makwanci. Sadik ya yi dariya cike da farin ciki ya ce masa "Gaskiya dai Alhamdulillahi sai godiyar Ubangiji kam, an samu rufin asiri." 119 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ 1 'a ar ak ge haj Ss wal abt rzil ih Alh All farl ido bal Auwalu ya dubeshi da alamuu tambaya a fuskarsa ya ce masa "Rufin asiri kawai? Ai wannan ya wuce a tsaya a rufin asiri, har da arziki ka duba fa kaga abin da ka mallaka a lokaci daya, ya kamata in an kai matsayi a yarda an kai." Sadik ya yi dariya yace "Gaskiya ne to Allah ya wadata mu gaba daya ya bamu yanda zamu iya." Auwalu ya amshe da "Amin" sannan ya dora da fadin "Yanzu abin da ya rage maka kawai ka samo abokiyar zama sai komai ya kammala cika." Sadik ya kalleshi cikin mamaki yace masa "Kai ma ka bi layi kenan, kullum zancen Hajiya kwaya daya ya 2, kamata nayi aure. Auwalu ya yi murmushi yace masa "To ai abin da ya kamace ka kenan, shekarunka sun kai kuma halinka ya kai 120 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE ka rike mace ko guda ce ma ballanta daya." Da sauri Sadik ya bude baki yana fadin "Ko guda nawa? Na samu na aura, dayar ma ai abin ba akudi yake ba? Auwalu ya yi dariya sannan yace "Abokina ka tsorata kenan, to yanzu me ka shirya akan maganar auren?" Sadik ya gyara tsayuwarsa sannan yace " Ni ban shirya komi ba wallahi, shirina abin da na mallaka a hannuna wanda ni aka ce ga auren to zan kashe su ba tare da jin komi ba." Auwalu ya yi dariya sannan yace "Kana nufin ko yarinyar da zaka aura baka tana da ba?" ya sake yin dariya yace masa "A ina fa na tanada? Ni fa babu abin da ke gabana illa neman kudi, ina ma na samu damar da har zan zauna na 121 F ALAWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE kalli mace balle har na tantance wacce ta dace dani?" Auwalu ya kwashe da dariya har da hka kafa sannan yace masa "Gaskiya abokina baka da dama to banda abinka zaka auri kudi ne?" Sadik yakatseshi da fadin ga mutumina yanzu dai ka bar wannan maganar in dai kanada wata da kake ganin ta dace dani mai dan dama-dama kawai ka hadani da ita, in naga ta yi mini sai kawai mu daidaita." Auwalu ya ce masa "To banda abinka ka taba ganin wani ya zabawa wani mata?" Sadik yace "Ai ba kaine zaka zaba mini ba, kai mai samowa ne idan ka samu sai ka kaini mu gana idan tai min shikenan in Allah ya yi sai kaga ta zama matata ko?" 122 ALAWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE Auwalu ya amsa da cewa "Gaskiya ne abokina ai kuwa akwai wata yarinya da nake gani zaku dace domin yarinyar matar manya ce irinku don komi ya ji."" Da sauri Sadik ya tambayeshi "Allah Abokina?" Auwalu ya yi dariya ya nufi kunnensa ya yi masa rada, gaba daya suka yi dariya suka tafa, sannan suka nufi cikin motar suka shiga, Sadik ya tada motar suka bar gurin. To sun sanya lokaci zuwa gurin wannan yarinya da Auwalu ya kwadaitawa Sadik ita, don haka suka yi sallama da juna suka yi alkawarin sai wannan rana za su sake haduwa. A kofar gidansu ya saukeshi ya yi masa ihsani da ya saba kana ya ja motarsa ya nufi inda ya yi niyyar zuwa. 123 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE **** Yammaci ne mai cike da ni'ima wanda ke ba da iska mai sanyi da ratsa jiki. A kofar gidansu Auwalun ya tsaya ko fitowa daga motar bai yi ba, hatta 'yan majalisarsu ma hannu kawai ya daga musu, da sauri Auwalun ya bude ya shiga shi kuma ya ja motar suka kama hanya. A kofar gidansu yarinyar suka tsaya da motar, Auwalu ne ya fara fitowa shi kuma sai da ya kashe motar sannan ya fito ya zo kusa da Auwalun suka jeru jikin motar suna kallon kofar gidansu yarinyar. Suna nan a tsaye wani yaro yazo zai wuce, Auwalu ya yi sauri ya tsaida shi ya aika shi domin ya kirawo musu ita. Bayan 'yan mintuna kalilan yaron ya fito ya sake nufo inda suke yace musu "Wai ance tana zuwa" da sauri Auiwalun ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СЕ ya ce masa "Yauwa yaro mun gode kaji, ya sanya hannu a aljihunsa ya dauko Naira dari ya mikawa yaron yana fadin "To ga wannan ka kaiwa Mamanka ka ji dan albarka." Cike da murna ya amsa yana duba kudin sabuwa ce kal, yana fadin "Nagode Allah ya saka da alheri." Sannan ya falla da gudu ya nufi gida. Dai dai lokacin da Mero take fitowa daga gidan tana takawa a hankali, ta yi kwalliya daidai gwargwado. Kai tsaye inda suke tsaye ta nufo tana isowa gurinsu ta dan risina sannan ta יי ce, "Barkanku da zuwa.' Cike da fara'a Auwalu ya amshe da Maryama, Maryama, barkanki da yamma gamu yau a gidanku ba zato ko?" 125 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ Murmushi kawai ta yi shi kuwa gogan idanuwansa na kanta yanayi mata kallon nazari. Auwalu ne yaci gaba da fadin "Maryam na san zaki yi mamakin ganin mu a daidai wannan lokaci, to kamar yanda kika sani ni Jakadan alheri ne, ga abokina nan dan uwana kuma aminina na kawo miki dafatan zaki karbeshi hannuwa bibbiyu." Da sauri ta daga idanuwanta ta kalli Sadik, nan take suka yi ido hudu, murmushi ya sakar mata, ita kuwa kunyace ta kamata ta yi saurin sunkuyar da kanta,shi kuwa gogan sam idonsa ko motsawa bai yi ba domin shi kansa ya tabbatar da cewa Maryam din tasa ta yi. Auwalu ne ya ya fito shi da hannu cike da zolaya yafe fadin "To kai Abokina na gama nawa aikin bari na ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE zagaya baya na barku ku tattauna don kar naji sirrinku." Dariya ya sakar masa gami da harara yace masa "To dama ya za'ayi mu bari ka ji sirrin mu ka kwantar da hankalinka tunda na san inda take ai ba sai ana wani labe labe ba sanda zanzo ma kana ina." Aljihunsa ya sanya hannu ya dauko kudi masu yawa ya mikawa Mero ya ce mata "Ki rike wannan kinga yanzu magariba ta kusa, idan Allah ya kaimu gobe da dare zan dawo Insha Allahu." Da sauri ta gyada kai alamun ba za ta karba ba, Auwalu ne ya tirsasata ta karba, sannan suka yi sallama da juna ta juya ta nufi gida su kuma suka tashi motarsu, a soro ta labe tana lekensu sai da ta daina ganin motar sannan ta shiga gida. 127 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE Shi kuwa Auwalu zolayar Sadik ya hàu yi yana fadin "Abokina gaskiya kai mishan ne, kai fa kace mini baka iya ko kallon mata, ka sanyani nemo maka mata amma yanzu daga ganin 'yar mutane ka rude ko maganar arziki ka kasa yi, har da wani cewa gobe da daddare zaka koma." Sadik ya kwashe da dariya yace masa "Haba Abokina kai dai tunda ka cika aikinka ai shi kenan, yarinyar ce ai ta yi, shi yasa ka ga na kasa ce mata komi kallonta kawai nake yi don ma talauci ya yai mata cikar tana jikuwa, da kudi zata zama babbar yarinya." Dariya Auwalu ya sake yi yace "Ai mu zama damu yana da amfani matuka domin idanuwanmu suna zagayawa ko ina a cikin garin nan lungu da sako." Ya ci gaba da zolayarsa. 128 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE "Abokina kawai ka ce ciniki ya fada." Auwalu ya fadi yana dariya. Sadik ya yi saurin amshewa "Mai kyau ma, ai kawai sai shirin aure, kana ganin yarinya ta hada komi da komi babu makusa, ai yanzu ina sauke ka gida na nufa na sanar da su labari mai dadi, musamman Hajiya." Da haka sukaci gaba da tattaunawa har ya isa gidansu Auwalu ya saukeshi ya karawa Motarsa wuta ya nufi hanyar gidan Hajiya kai tsaye. Anan zan dakata a cikin littafi na daya sai mu nemi littafi na biyu domin jin yadda zata kaya. Taku har kullum, mai debe muku kewa Alawiyya Wada Isa. 129 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 2 Π TALLA! TALLA!! TALLA!! "Abban Ilham yau ina zuwa ne da sanyin safiya haka.?" Ya dubi Agogon Bangon dake dakin tara da 'yan mintuna. "Me ki ka ga ni.?" Shi ma ya tambaye ta. "Na ga ne ka ci ado kamar wadda za ka fita wani taro na musamman." "An ce ba kullum ake kwana a gado ba, kuma haka ne wadannan masana fadin magana sun fadi gaskiya, yau kai ne a can وو gobe kai ne a nan. 1 130 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE Ta bishi da kallon mamaki domin amsar tasa bata fuskanci ainihin abin da take son ji ba." "Uhm sai an karya min harshe kuma, ni dai tambaya na yi amsa nake bukata kawai ina zuwa yau da safe.?" "Neman aiki.?" Ta jima ta na kallon sa da mutukar mamaki. "Neman Aiki.?" Ta fada da mamakinta.?" "Zan je neman aiki ne saboda al'amura sun fara yawa, duniya ta na da girma, haka hanyoyin samu na da fadi, babu mamaki idan can ta ki ka koma can, fadi ta shi dai dama bawa bai isa ya ce yafi karfin 131 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE yi ba, in har ina busar numfashi. Zan je ko Allah zai sa a dacс." יי "Me ne ka rasa.?" "Me ne na samu.?" Ya dawo mata da tambayar ta kai tsaye. Ita kuma ta saka masa ido cikin mutukar mamakin kalamansa." "Ban samu komai ba, Hafsa ídan ki ka auna cewar idan Allah ya ba mu aron rai gobe ba irin yau ba ce jibi ba rin gobe bace haka gata citta, don haka ya zama dole na shiga duniyar neman abin rufin asiri abubuwa sun cunkushewa rayuwa ta, na ga alamar baki san da haka ba." 132 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ Ta mike daga in da take ta dawo kusa da shi "Mai yasa kake yanke kauna da daukaka ta." Ya zuba mata ido kafin ya ce komai sannan ya gyara murya ya cc, "Daukaka lokaci ne da ita, ki na nan za ta zo ta turmeshi. ki, kuma kada ki manta ba a rayuwa a dakushe." "Kamar yaya.?" "Da ni na ke shuhura, yanzu kuma ke ce, gobe ba fa ba ke bace, to ya za mu yi da wannan rayuwa, lokacin da duniya take yi da kai, lokacin jama'a ke yi da kai. In kin ji an ce duniya. To ba duniyar ba ce jama'ar cikinta ne. Ranar da jama'ar suka koma kan wata, kaka ke nan.?" 133 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE "Amma dai ka san duk lalacewar dan zaki yafi karfin kadangare, ko da a ce ban da wani abu da zan tabuka mahaifina mai kudi ne, ba kuma zai hanani duk abin da nake bukata ba." Ya dora hannuwansa a kai, daga bisa ni wani murmushi ya kubuce masa "Da a сe zan fadi na mutu. Wannan shi ne abu mafi soyuwa a cikin zuciyar iyayen ki, ni kuwa don me zai sa na zauna ina barautar abin da za su ba ni, wadanda ko kauna ta a raye ba sa su. Hafsa ki rike daukakar ki, ni ma zan je na nemi abin da zai rufamin asiri, daga rana irin ta yau na rabu da harkar rubutu, har Abada kuma ina mai nadamar kasancewa ta marubuci. 134 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE Tirkashi, in ba ka yi ba ni guri. Wani Kasaitaccen labari, mai sa ka zubar kwalla, mai fauke da wata sha'umar soyayya, wannan labarin ya kasaitu ya samu ingancin aiki, sabon salo a cikin rubuce rubucen zamani, ka da ka saki a baka labarin wannan Kasaitaccen littafi mai suna. BA ALJANNA BACE. Matashiyar marubuciyar nan 'yar uwa ga Hadiza Adam shi shitu wato Rabi'atu wacce ta rubuto littafaina kamar haka BAKIN JINI NА. TAKAICINA FARIN CIKINA. MURAIDIN RAINA DAN KUKA, 135 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE ki d k ALKIBLATA NI CE NA DACE ZANEN DUTSE TA KARA YUNKURAWA TA KAWO SABON LABARI MAI SUNA ...BA ALJANNA BACE, KI NEMI NAKI A KASUWA DA ZARAR YA FITO. Kada ku manta da sunan BA ALJANNA BACE S a 136 Littartafan marubucivar:. SHARRIN ZUCIYA ..RABIN JIKI GUGUWAR ZAMANI RUWANIDO DUNIYAR MAKARANTA CE YAR ALJANNA CЕ YarAjanna Ce ALAWIYYA WADA ISAH BUGAWA DA YADAWA: Printing & Publishing by: SARAUTA PUBLISHERS A 08034255307 Cover Graphics Anka-Graphics Fagge 07030319787 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 4 of 4