Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 4
gaishesu, suma cikin fara'a suka amsa mata. Alhaji Aliyu ne ke tambayar ta "Hanan ince ko kin karya?" cike da ladabi ta amsa masa "Baba na karya tun dazu, dama ina sone na je gidan Baba Alhaji domin yana ta mita wai har yanzu banje na gaisheshi ya ganni ba." 37 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE Ya fadada fara'arsa ya ce mata "Gaskiya ya dace kije Hanan tunda duk kinga Iyayenki shima datijo ai sai kije ki bashi nasa hakkin." Ta mike tana fadin "To Baba nagoe sai na dawo kenan." Baban ya amsa da cewa "Si kin dawo Hanan Allah kiyaye ki gaishe da Baban, idan zaki dade sai Direba ya dawo inyaso sai ki sanar da shi sanda zaki dawo sai ya koma ya daukoki." A risine ta amsa da cewar "To Baba nagode." Sannan ta juya ga Maman tata "Mama na tafi." Ta dago ta dubeta fuskarta cike da walwala ta ce mata "Allah ya tsare, ki gaishe da kowa." Ta amsa da "Amin." Ta juya ta fita. Unguwar Dukawa suka nufa gidan Kakanta, sunci sa'a yau babu cunkoson abin hawa a titi don haka ba dadewa suka 38 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CЕ isa kofar gidan Direba ya tsaya ta fito da sauri ta nufi cikin gidan cike da zumudi, sannu a hankali ta dinga wuce manyan sorayen gidan tana gaisawa da masu zama a soron har sai da ta isa cikin gidan ta riski Kakanninta mata kowacce a dakinta, sunyi barkwanci yadda suka saba da hirar yaushe gamo, sannan ta nufi sashen kakan nata. Dan farin Dattijo ne, mai alamun shekaru da yawa fuskarsa da kansa cunkushe da furfura yana zaune bisa buzu hannunsa rike da carbi yana lazimi, ga littafan ilimi nan kewaye das hi, haka duk kewayen dakin gaba daya littafai ne na ilimin addini, a hankali ta isa inda yake ta zauna kusa dashi tana jira ya kammala. Sai da ya hada laziminsa ya daga hannu itama ta daga ya yi addu'a suka shafa a tare sannan ya juyo gareta, 39 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE fara'arsa ta fadada domin yana matukar kaunar jikar tasa ya ce mata cikin zolaya "A a bakuwar garin masa yaua gari inji maki bako? Ai ni nayi fishi dake sai yau kika ga dammar zuwa ki gaisheni? Ta yi dariya sannan ta ce, masa "Haba dan tsoho mai ran karfe ka taба jin inda miji ya yi fishi da matarsa, ai mu auranmu auren zobe ne ba rabuwa, kai min afuwa kasan ina ta Iyayena ne kafin na zo ga 'yan karo, na tsayane na kwashi albarkar rayayyu kafin nazo ga wanda ko yau ko gobe za a iya fasa kukan mutuwarsa." Ya saki murmushi wanda ya kawata fuskarsa sannan ya ce "Amma wannan yarinyar kin iya shakiuiyanci, to ai ba wanda ya san gawar fari sai Allah, niď in da kike gani sai Allah ya barni ya 40 ALAWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE dauke miki lyayen naki sai kuma kice da Allah me?" Cikin barkwanci ta ce, "Ai bani da ja akan maganarka domin kai ai ran karfe gareka don haka don kowa ya mutu ya barka ba mamaki kaga sai kai mana jiran duniyar." Dariya ta subuce masa ya ce "Kai Hanan baki da dama, ina nan kin banni da kewa wai sai dai na jiki ta waya? To yaya 'yan samarin naki abokan nawa mai tsoron aure ko dai har yanzu ni kika mannewa wannan farar furfurar tawa tana birgeki kо? To tunda yanzu kin kammala karatun naki sai a zo a daura auren zobe, na san ko ban bayar da sadaki ba babu komai, in kuma kin matsadubu daya ai ta isheki, ke sai n agama kamar kin yi tsada a dubu dayan nan. 41 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE Harararsa ta yi a wasance ta cc, "Allah ya yi mini tsari da auren tsoho kamar kai, ka hadani da wadannan tsofaffin matan naka da ko tafiya da kafafuwansu basa iya yi, har dama dama ma kai ka dan fisu kwari kaima din kadan....." Karar wayarta cc, ta katse mata hirar tad ago ta duba don tag a ko wanene "shinc dai" ta fadi cikin ranta, sannan ta daga wayar. Cikin tausasa murya ya ce mata "Hanan ya kike?" cikin sanyin jiki ta amsa masa "lafiya kalau nake." Ya danyi jim sannan ya ce "Dama naje gidanku ne yanzu don na ganki sai aka ce ai kin taho gidan Kakanki, shine na sa aka kwatanto mini inda yake gidan ba 6oyayye bane وو ban sha wahala ba na samu. 42 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CЕ Mamaki ya cikata ta dan yi jum, cikin ranta take fadin "Wannan wacce irin bibiya ce wannan mutumun yake yi mini ne?" Shiru din da ya yi ne ya sanya ya sake cewa "Hello Hanan ba kya jina?" A kasalance ta masa da cewa "To yanzu kana kofar gida kenan?" "Da sauri ya amsa "Eh, hakane. Ta kwabe baki sannan ta amsa masa "To ba 99 matsala gani nan zuwa. Tun da ta fito take sakawa tana tufewa cikin ranta har sai da tai so kofar gida ta fito waje. Jingine a jikin motarsa ta hango shi, cikin shigar wani Yadi dan ubansu na manyan mutane, kalar ruwan kasa ne anyi masa dinkin boda ya yi matukar yi masa kyau, kamar kullum komai nasa ruwan kasa ne, har gilashin idonsa, 43 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ hannunsa rungume a kirjinsa sai daukar idon duk wanda ya ratsa ta gurin yake yi. Ya sakar mata murmushi a yayin da su ka yi ido hudu da shi, ita kanta ya birgeta matuka domin ko ba komai tana so taga mutum wayayye kuma dan gayu. Cike da nutsuwa da takun ta dai dai ta iske shi a in da yake tsaye. Shi kuwa idonsa na bisa kanta yana faman aikin nasa, ji yake kamar ya dauke ta su tafi a yau, amma ina ya san ba hali. Dan haka ya maida hankali ga tsantsar kallonta kana ya fara da cewa. "Sarauniyar mata kinyi kyau fa, kin 92 zama tauraruwa a cikin taurarin duniya.' Wani dadi taji cikin ranta domin tana son namiji mai yabawa mace, ga dukkan alamu dai Alhaji Sadik yana neman hade duk halayen da Hanan ke so daga namiji. 44 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE こ Kanta a sunkuye idanuwanta na kallon kasa saboda kallonta da yake yi ta ce masa "Nagode fa." Ya gyara tsayuwarsa sannan yace "Hanan gaskiya ke 'yar gata ce, yau kuna nan gobe kuna can, kina jin dadinki, inama so na da kaunata ne suka samu wannan gatan cikin zuciyarki, da na kasance namijin da yafi kowanne sa'a a rayuwa, da na zamo dan gatan da babu kamarsa. Hanan ina dai miko sakon kokon barata gareki a ko yaushe, har gobe ina nan ina dakon irin sakamakon da kokon nawa zai barato mani, Allah ya say a kandamo mini babban Alkairi wanda zai zamo haske a rayuwarmu gaba dayanta. Tuni kalamansa suka fara kasha mata jiki, taushin muryarsa kamar bat a namiji ba, da maganganunsa masu ratsa 45 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE zuciya sun shige ta sosai, tabbas namijin da ya iya soyayya yana matukar birgeta. Ba ta iya ce masa komai ba illa "Ya kamata muje ka gaishe da Baba Malam ko?" Hakan ya yi matukar yi masa dadi cikin ransa, domin ya san da ba amshe shi ba ko gaisuwarsa ba za a amsa ba balle har a shigar dashi gurin wanda yake Uban kowa cikin zuri'ar, don haka babu ko ja ya bi bayanta suka tafi. Farin cikinsa ya fadada day a gansu sun shigo gaba daya, da sauri ya mike yana yi wa Alhaji Sadik barka da zuwa. Da sauri ya zube a gabansa yana gaisheshi, cikin fara'a da murna ya ce, "Af kace kai ka ji tsoro ka ba da kai, baka san ni ma dan takara ba ne, ka ke durkusa mini?" Suka yi dariya gaba dayansu sannan suka zauna suka gaisa. Cikin 46 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE zuciyar Baba Malam fadı yake "Allah yasa dai yarinyar nan ta amince da mutumin nan domin ga dukkan alamu ya yi kamannin kammala da kyakkyawan asali, amma in ba a yi sa'a ba Hanan sai ta gujeshi. Hanan din ya kalla ya ce mata "Ai sai kije ki samo masa lemo da dan ruwa ko?" ta mike ba tare da ta ce, komi bat a fita. Baba Malam ya maida hankalinsa ga Alhaji Sadik yace masa "kai yaro daga ina kake ne kuma menene sana'arka? Alhaji Sadik ya gyara zama gami da fadada murmushinsa domin tambayar ta yi masa dadi, cike da ladabi ya ce masa "Sunana Alhaji Sadik, mahaifina kuma sunansa Alhaji Muhammad dan gidan Alhaji Ahmad mai kamshi...... ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE Da sauri ya katseshi da fadin "A a Ahmad mai kamshin dai nawa na unguwar Dala cikin Makwalla? Ko kuma ne mai irin wannan sunan?" Da sauri Sadik ya amshe cike da jin adi "shine dai, Alhaji ai babu wani mai wannan sunan a nan nahiyar sais hi." Alhaji Sadik ya fadi cike da zumudin ganin wata hanya mai kama da samun nasara ta samu. Baba Malam ya sake duban Sadika karo na barkatai fuskarsa cike da alamun tausayawa yace,"Yaro ashe kai jikana ne ban sani ba, Allah ya jikan Ahmad aminina ne tun muna kananan yara tare muka yi karatun allo mu ka yi sauka, kai tare ma aka sha mu, duk wani wasa na kuriciya irinsu langa da tamaula, da duk wani kiriniya ta kuruciya tare muka yi da Ahmadu, abin day a faru amintarmu ta A 48 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE fara sanyi bai wuce harkokin kasuwancin mu da ya banbanta ba, domin shi Ahmadu yana shigo da turare kowanne irin nau'i shine sana'arsa, dan haka ba kasafai ya fiye zama a Nigeria ba, ni kuwa da yake Malanta ita ce, gadon Iyayena don haka sai ya zama kasuwancin nawa na cikin gida nake yi, sai dai na tura a shigo mini da atanfofi da shaddodi a sai da saboda ko yaushe ina tare da mahaifina ina daukar ilimi, dan haka sai mu kan dade bamu gana da juna ba. To ka san idan sana'a ta banbanta to ba kasafai mu'amala ke dorewa ba, gashi a lokacin babu hanyoyin sadarwa kamar yanzu, don haka muka nisanci juna kwarai sai ya zamana sai sanda Allah ya so haduwarmu sai kaga mun hadu a wani guri, da haka dai har girma 49 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA СЕ 1 ya fara cimmana Iyayenmu da suka rasu muka yi 'ya'ya nauyi yah an kanmu sosai ban Ankara ba sai kawai naji hatsarin jirgi ana lissafa wadan da su sai naji har da Ahmadu na wa da dansa, ranar da na ji tashin hankali wanda ya kasa gushe mini cikin raina. Yana zuwa nan ya fara shesshekar kuka, Alhaji Sadik ya yi sauri ya share kwallar da ke zubo masa, sannan yace "Baba sai hakuri don Allah kada ka yi kuka, in ka yi kuka mu kuma mmuyi me?" Da haka ya rarrashe shi ya hadiye kukan da ya zo masa, Alhaji Sadik ya ce masa "Baba ai shi wannan dan nasa shine mahaifina, ni kadai ya Haifa a lokacin da yake da shine yake taimaka masa wajen kasuwancin dan haka ya zama tare suke zuwa ko ina don ya fahimci harkar shi 50 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE kuma ya zauna a gida ya huta mahaifin nawa ya zama shine ke yin komi, to da yake kana taka ne Allah na tasa sai duk suka cimma ajali a lokaci daya." "Allahu akbar, Allah ya ji kansu, nayi rashin aboki na kuruciya, amma kuma yau na yi farin ciki matuka da na sake yin tozali da irin tsatson Ahmadu, Allah ya yi muku albarka, Allah ya tsara mana alkairi a cikin wannan lamari." Da sauri ya amsa da "Amin Baba." Tuni zuciyarsa ta cika da farin'ciki domin da alamun jiyo kamshin Hanan zata iya zama mallakinsa. Da sallama ta shigo hannunta dauke da lemon Izotik da robar ruwa faro a kan faranti sai kuma kofin sha a gefe, a gabansa ta ajiye masa sannan ta koma kusa da Kakan nata ta zauna. 51 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CЕ Ya dubeta da kulawa yace mata "Ke Hanan bayan duniya kika tafi kawo lemon ne?" Ta yi murmushi ta gyada kai ta ce, masa "Wadannan tsofaffin matan naka kasan ba gani suke yi ba sosai ba, wai su ba su ma san lemon ya kare ba, sai da na duba ko ina ban samu ba, sannan na aika aka siyo shi yasa kaga na dade." Ya yi murmushi yace mata "Af haka kikace da su? Zaku hadu ne ai, ni ma ban san ya kare din ba dake ni ba son zakin nake yi ba dama don baki ake ajiyewa. Ya yi murmushi domin yanda suke yi da Kakan nata yana birgeshi, bai damu bay a bude da kansa ya tsiyaya a kofi ya sha domin ya san har yanzu Hanan bat agama sakin jiki da shi ba, balle hart a tsaya zuba masa lemon. 52 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ Yana kammala shan wanda ya zuba ya mike yana fadin "To Baba ni zan koma." Baban ya amshe da sauri "To Saddiku Allah ya yi maka albarka nagode matuka." Nera dubu ashirin ya ajiye masa a gabansa da wani tirare mai kyau yacе "Baba wannan kaci goro." Bai kara tsayawa bay a fice. Hanan bata iya ce masa komai ba illa biyo shi da ta yi a ranta tana jaddada kyautatawarsa a gareta, lallai ya fara kamo tasharta domin tana matukar son a kular mata da dan tsohon nan domin shi ma ya kula da ita a rayuwarsa. Ba su yi wata doguwar tsayuwa ba, godiya kawai ta yi masa, ta kuma isar masa da godiyar Baba Malam sannan suka yi sallama tajuya ta kooma cikin gidan, shi kuwa bai tafi ba har sai da ya 53 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE daina ganinta sannan ya ja motarsa ya wuce zuciyarsa cike da shauki da murnar alamun samun nasara. Baba Malam ne ya dubeta, duba na nutsuwa da babu wasa a cikinsa, ita kanta ta karanci cewar ba was an don haka dolente ta shiga nutsuwarta ta tattara masa hankalinta guri guda. Baba Malam ya fara da cę mata "Hanan ina mai baki shawara sannan ina umartarki da ki yarda da batun Yaroon nan ki aureshi ba don komi ba sai don ya cancanta, ina so na nusar da ke cewar "auren mutumin da ya mallaki hankalin kansa ba daidai yake da na yaro karami ba, kina dai kallon yanda zamani ya zama samarin nan sai fama akeyi da su, a kan su rike matan nasu da gaskiya amma ina da anyi aure haihuwa daya biyu sai saki, shi kuwa Babba ya san darajar iyalinsa da 54 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СЕ darajar rikon aurensa don haka za ki ga ya jure ya hakura da duk wani abu da zai faru, da wuya ki ji an rabu sai dai wata kaddara ta Ubangiji. Dan haka ni dai ina rokon ki arzikin da ki daure ki amince da shi, gashi kyakkyawa yaro, gashi da karamci da girmama na gaba, ke hasalima Kakansa da ya haifi ubansa aminina ne tun tale-tale." Dariya kawai ta yi cike da zolaya ta ce masa "To waye yace maka bana sonsa?" shima dariyar ya yi yace mata "A haf! Hanan har sai angaya min, ni da na. san halayyarki sai kace wata mai aljanu, ko aljanu ne dake ne yanzu na yi miki rukiyyar ko kya dawo hayyacinki ki yi aure. Bata ce masa komai ba illa mikewa da ta yi tana dariya tana fadin "Bari ka ga 55 ALAWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA СЕ na zo na koma gida saboda ina so na je gidan Daddy, kullum sai ya yi mini waya yana tambayara yaushe zan dawo." Murmushi ya yi yace nata "Ai duk wani goce godenki na gano inda kika dosa, ni nasan aid a wuya na fada maki abu ki ki yin aiki da abin, don haka ni zan tattauna da Dadyn naki a kan maganar Insha'Allahu, ki gaishe mini da kowa nagode, Allah ya maki albarka." Ta amsa da "Amin" Sannan ta dauko goronta da turarenta ba ka'ida da take kawo masa ta bashi ya karba yana sanya mata albarka suka yi sallama ta tafi, dama tuni ta kira direba a waya yana waje yana jirsnts don haka sai ya dauketa suka tafi gida. 56 **** ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE Alhaji Sadik kam ya riga ya rikice akan soyayyar Hanan domin a ganinsa Hanan dince kadai zata iya magance masa matsalarsa da ke addabarsa a cikin gidansa. Tafe yake a mota yana shirin komawa gidansa bayan wuni da ya yi yana hidimomin neman kudinsa, iskar da ke busawa a wannan dare ta yi masa dadi matuka domin tana kunshe da tarin ni'ima a cikinta, mutane na ta gudanar da harkokinsu cikin nishadi saboda dadin da yanayin yayi musu. Yana ta kallon yanda mutane ke harkokinsu amma a badini tunani ne iriiri cunkushe cikin zuciyarsa. Cikin ransa ne yake fadin "Ina ma Hanan ta zamo mallakinsa a wanna rana da yanayinta yake matukar birge kowa, lallai kam yanayin ya dace da masoya, sai 57 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE dai kash tashin hankalinsa baii wuce halin da zai tadda gidan nasa ba domin ya sani babu wani sauyi cikin al'amarin gidan sai ma dai abin da ya karu, nan take nishadin da yake tare da shi ya sauya zuwa takaici da tarin nadama a haka har ya isa gidan. sbKamar yanda ya saba sai da yayi hon dinsa na ka'ida sannan kowa ya san ya dawo, Yaransa suka fito suka yi masa barka da zuwa, sannan kowa ya nufi daakinsa shi kuma kai tsaye dama dakinsa ya wuce. Saida ya kammala komi na bangaran wanka. Cin abinci da sauran duk abin da ya dace yayi sannan ya kwanta bisa doguwar kujera yana kallon tashar Al-jazecra har bacci yafara daukarsa sai kawai ya farka firgigit dab tunanin Hanan dinsa, dama tuni ya bawa 58 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE matansa hutun zuwa dakinsa a matsayin horo bisa wani laifi da suka yi masa, dan haka sai kawai ya tsinci kansa da son ya ji muryarta ko ya kara samun saukin abin da ke ransa. Ringing uku ta daga wayar, cikin tattausar muryarta ta amsa "Hello Alhaji baka yi bacci ba cikin wannan daren?" Wani sanyi yaji cikin rana,. Can kasan makoshinsa ya amsa "Ina ni ina samun damar bacci Hanan bayan sonki da tsananin Kaunarki sin hana ruhina da gangar jikina sakat, idan har banji ki ba bana iya aiwatar da komi a rayuwata." Ta yi wani sassaukan murmushi da alamun kalaman nasa sun ratsata, sannan ta ce, masa "To ni dai kar ka hadani da matana domin magidanci kamar kai a dai dai wannan loakci ya dace a ce yana tare da matarsa. 59 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE Shi kansa ya san hakan ya dacc, amma sai dai shi kuma bai dace ba da haka sai ya wayance yace mata "Hanan ba zan kira ki ina tare da Matata ba domin idan nayi hakan ya zama cin fuska, matata ta kammala duk abin da zata yi mini, ta je sashenta ta duba Yaranta kuma sai can dare zata dawi shine nayi amfani da wannan damar na kiraki don na rage kewarki." Cikin nutsuwa ta tausasawa suka dinga musayar zantukan soayya musamman bangaran Alhaji Sadik wanda yake jin Hanan din a can cikin ransa da ruhinsa, duk da dai har yanzu bata saki jikinta yanda ya dace ca amma shi kansa ya san an samu ci gaba a tafiyar tasu sosai. 60 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE Sai da dare ya raba sannan Hanan ta fara Hamma sannan Alhaji ya yi sallama da ita ya kashe wayarsa. Kwanan Hanan biyar a gidan Mamanta ta yi sallama da su da nufin ta komawa gidansu domin Dadyn nata ya damu da ta zo ya ganta. Suma su Alhaji Aliyu da kannenta har ma da Maman nata basu so tafiyar tata ba domin suna jin dadin zama da ita. sai dai dole suka hakura suka yi sallama da ita sai dai ta basu tabbacin cewar ba zata dade ba zata dawo. Haka nan suka tsattsaya a farfajiyar gidan suna yi mata sallama har sai da motar ra fice daga gidan, 'yan kannen nata har da hawaye suka koma cikin gida rayuwarsu sam babu dadi. Shi kuwa Alhaji Hafiz wannan rana sai ta kasance masa ranar farin ciki a 61 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE gareshi domin dawowar Hanan cikin gidansa, ranar wuni ya yi a gida suna shan hirarsu da diyar tasa, hatta abinci tare suka ci dai da dare ya yi sannan ta yi wa Dadyn nata sallama ta nufi dakinta domin runtsawa, ita kanta rayuwar tana yi mara dadi domin tana da cikakken gata ta kowanne bangare. Kwananta daya a gidansu Alhaji Sadik ya bayyana a can, karfe biyar na la'asariya ya yi parking da motarsa a kofar gidansu, ya fito ya jingina a jikin motarsa kamar yanda ya saba, yayi amfani da wayarsa domin sanar da ita cewar ya iso. Bata dauki tsayin lokaci ba ta fito sanye da doguwar riga 'yar saudiyya kalar kofi, ta yi mata kyau matuka, shi ma din sut ne a jikinsa kofi kala sunyi matukar amsarshi sosai. 62 ALAWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE sw Cikin takunta na nutsuwa ta iso gareshi fuskarta cike da murmushi ta yi masa sallama sannan ta yi masa barka da zuwa, idanuwansa sun kasa dauke kansa daga barin kallonta, cike da nishadi yace mata "Lallai akwai alamu zuciyoyinmu sun fara zamowa daya domin gashinan mún sanya kaya kala daya ba tare da kowa ya san dan uwansa zai sanya ba." Ya fadi yana ci gaba da kallonta, kallon da tun yana damunta har ma ta saki jikinta da shi, izuwa yanzu domin ba zai taba iya dainawa ba. ST Murmushi kawai ta yi wanda ke kara kawata fuskarta ta ce masa "Lallai kam akwai alamun faruwar hakan." Amsar tata ta yi masa dadi, don haka ya sake gyara tsayuwarsa ya zuba mata idanuwańsa, komi nata birgeshi suke yi matuka.nit nadd 63 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE Basu dauki tsayin lokaci ba a waje ta yi masa iso zuwa babban falon gidan na su, suka zauna bisa lintsima lintsima kujerun da ke cikin falon, suna fuskantar junansu. Har izuwa wannan lokacin Sadik ya kasa dauke idonsa daga kallon Hanan, ita kuwa kanta na sunkuye sai jefi jefi take daga idonta suyi ido hudu da Alhaji, duk sanda hakan ta faru kuwa, wani irin yanayi take tsintar kanta a ciki, izuwa yanzu kam ta fara samun nuutsuwar zuciyarta a kan Alhaji Sadik domin duk wasu halaye da ake son Namiji dasu yana da su, a bangaren halittarsa kuwa dama sam babu makusa ballantana kuma bangaren mu'amala, uwa uba kuma kyautatawarsa da yake yi mata ba tare da nuna gazawarsa ba. Ya kara tattara hankalinsa guri guda yana duban Hanan din da kulawa, 64 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ can kasan makworonsa ya kira sunanta "Hanan ina so a yau na san halin da nake ciki a game da ke, har izuwa yanzu fa ban fuskanci wata kalma kwaya daya wacce zata tabbatar mini da kina sona da aure ta fito daga bakin ki ba, Hanan kin sani ina kaunar mallakarki a matsayin matar aurena ta sunnah, kinga ni ba yaro bane da zan yi ta zuwa gurinki babu wata kwakkwarar magana tsakaninmu ba kimata ba се. Ina neman alfarmarki a yau daki sanar dani matsayina a cikin ranki, idan har banyi miki bane ki sanar dani, sai na hakura na mika lamarina gurin Allah, na san ba zi wofintar da ni ba." Yana kaiwa nan ya dakata jikinsa a sanyaye, tamlar wanda aka zarewa laka. Itama dai Hanan. din tuni an kwashe lakar jikinta domin da zaka daga 65 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE danyatsanta daya a wannan lokacin komawa zai yi dan kansa sabida tsabar rashin kuzari, maganganunsa sunyi mata fata-fata. A cikin ranta take fadin "Lallai Alhaji Sadik sjine namiji wanda ya dace a so shi so mai inganci, shine kuma namijin da ya cancanci ya kasanco abekin zamantakewar aure na har abada lallai tabbas ya cancanta kamannir halayensa sun done, halayyarsa ta zame masa ado, juriyarsa kuwa ta ame jagora zuwa nasararsa da kalamansa kuwa ya zame masa tauraro mai kyalkyali akan fuskarsa, tabbas idan nace bana son Alhaji Sadik to na yi wa Ubangijina butulci domin shine ya zabo mini shi ya hadani da shi, idan ma na guje shi to ban san irin wanda zan ci karo da shi a gaba ba...." 66 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE Gyaran muryar Alhaji Sadik ce ta katse mata dogon tunaninta, bayan da shiru ya ziyarci dakin na tsayin lokaci, har yanzu Hanan ke nake saurare shin kina ganin kin amince na ci gaba da zuwa gurinki kuma na saka dan ba akan maganar aurenmu ko kuwa na dakata?" Kanta sunkuye ta masa masa "Ва komi Alhaji ka ci gaba akan niyyarka, Allah yasa mu dade ya sanya mana alkairi da abin da yafi alkairi a rayuwarmu." Wani irin sanyi yaji cikin ransa ya tsirga masa, ya rasa wanne irin yanayi yake ciki dadi, murna ko farin ciki, ya daga hannunsa yana godiya ga Allah, sannan daga bisani ya juya ga Hanan din yana fadin "Hanan nagode da kyautar soyayyarki gareni nagode da samarwa kaunata gurbi a cikin zuciyarki, nagode 67 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE da amincewarki dani a matsayin abokin rayuwarki, bani da abin da zance sai dai na yi godiya ga Ubangijina domin shine silar komi, sannan kuma a yi mana kyakkyawan fatan alkairi a rayuwarmu baki daya." Bata dago kanta ba, illa murmushi da ta yi ta amsa da "Amin." Zumudi ya hana shi ci gaba da zama domin gani yake gara kawai yaje ya fara shirin duk abin da ya dace ya yi akan batun aurensu. Ya ajiye mata kudi yanda ya saba, sannan ya yi mata sallama, cike da nishadi ya tafi yana fadin sąi sunyi waya. **** Tana kammala cin abincin dare, kai tsaye falon mahaifin nata ta nufa kamar 68 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ yanda ta saba a kullum don ma yau bata son cin abinci tare da shi da nan zata je suci. Da sallama ta shiga ta iske shi zaune bisa kujera idanunsa sanye da medical Glass, hannunsa rike da jaridar Daily trust yana karantawa, yana jin sallamarta ya ajiye Jaridar a gefe ya amsa mata, sannan ya tattara hankalinsa gareta gaba daya. Gabansa ta je ta zauna ta ce, masa Dadday sannu da hutawa da kuma יי karatun news paper." Ya yi murmushi ya ce mata "Sannu dai Hanan, na kuwa ji dadin ganinki yanzu domin dama ko baki zo ba zan sanya a kirawo mini ke idan na kammala, na zauna. Gaba daya ankalinta ya koma gareshi cike da zakuwa ta ce, masa 69 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE "lafiya Daddy?" me ya faru? Ko wani laifin nayi maka ne? Ya yi murmushi ya cewa Hanan din kwantar da hankalinki diyata ,ba ki yi mini laifin komai ba, Baba Malam ne ya sanar da ni cewa akwai wani Yaro jikan amininsa da yake zúwa wajenki kuma ya yaba da komi na mutumin, shine yace na sameki na tambaye ki shin ko kin amince da maganarsa? Ta yi dariya ta sunkuyar da kai kasa amma ba ta ce, masa komi ba. Shima dariyar ya yi yace "Lallai wannan wanne mai sa'a ne haka Allah ya kawo shi, har kika amsa maganarsa kai tsaye ba tare da wahala ba?" Ta ďago ta dubeshi fuskarta cike da fara'a ta ce, masa "Daddy ni fa wallahi baku fahimce ni ba, ba fa wai ina gudun 70 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE aure bane, A'a halayyar mazan ce ta fita a raina shi yasa na kasa saurarar kowa na kwammace na bawa karatuna muhimmanci, domin yanda nake ganin jawarawa barkatai a gari, abin ba a cewa komi. Daddy ya yi dariya ya ce "Hanan kenan kinyi tunani mai kyau, amma kuma kuntatacce domin

Chapter 2 of 4