Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 4
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels Sarauta Publishers Yar Aljanna CeALAWIYYA WADA ISAH ALAWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE HAKKIN MALLAKA ALAWIYYA WADA ISA SHEKARAR BUGU 2014 GODIYA Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga tsarkakakken sarki mai kowa mai komai. Tsira da amincin su tabbata ga shugaban halitta Annabin karshe Annabi Muhammad (S.A.W). JINJINA Gareka balarabe kurmi mai littafi kasuwar kurmi (BUGAWA A COMPUTER) SARAUTA 08034255307 (BUGAWA DA YADAWA) NAJIB SARAUTA 08034255307 yar Aljanna anna ce ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE dalibai. arfajiyar Jami'ar Abubakar FTafawa Balcwa da ke garin Bauchi, ta cika makil da Yawanci masu masu burin barin Jami'a a washe gari domin kammala karatunsu na Digiri da suka yi a wannan makaranta. Sanyayyar la'asar ce mai kunshe da ni'ima wacce ke bayar da iska mai dadi da sanyaya zuciya, bishiyoyi sai rangaji suke, da alamar suma suna ta ya dalibai murna ne. "Da alama yanayin ya yi musu da di domin suna ci gaba da gabatar da sabgoginsu cikin nishadi. Daga masu daukar hotuna, sai masu shirye-shiryen dansewa da za suyi da daddare, wato sand up party domin bankwana da junansu. 3 ALAWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE "Can gaban mass communication department kuwa wasu 'yan mata ne zaune cike da nishadi, da alama suma masu tafiya goben ne. suna ta faman zabga musų kamar zasu tsaga gurin, da ma su wadan nan 'yan mata ya zame musu tamkar al'ada, idan har za su hadu to aikinsu baya wuce suyi ta musu, har ma sauran dalibai 'yan uwansu sun rada musu suna Argument group. Wanda bai sansu ba sai ya dauka fada suke yi, amma ina tuni sun riga sun fahimci junansu, har su gama musun su ta shi ko harara bata wanzuwa a tsakaninsu. "Yau din ma dai aikin nasu suke yi da suka saba, musu ne ya karke a tsakaninsu, sannan kuma kowacce na tsaye akan ra'ayinta tana kare kanta. Ta tsuniyar gizo dai bata wuce koki, domin wadan nan 'yan matan babu ALAWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE abin da suke tattaunawa akai illa batun aurensu. Wanda ya kasance shine agendarsu ta gaba bayan sun kammala karatunsu. Tafe take tana takawa dai dai kamar ba zata taka kasa ba, cike da nutsuwa take tafiyarta. Riga da siket ne a jikinta da su ka yi mata kyau suka bi tsarin jikinta. Sai kuma karamin mayafi da ta yane kanta das hi, bayan ta kuma jelar gashinta da ta tufke ya fado bisa gadon bayanta. Hankalinta na kan 'yan uwanta 'yan Argument group. Ta kagu ta same su ta ji abin da ya saka wannan fitaccen musun da kowa ya yi shuru yake sauraronsu domin ita ma ta samu damar sanya musu albarka a wajen fadin na ta albarkacin bakin. Ko kuma layin da alama ita ma yanayin yana yi mata dadi, shi yasa take 5 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNACE takawa sannu a hankali tana jin ita ma tana rangaji kamar yanda bishiyun daji ke yi. Musun na su da alama ya dauki zafi domin har ta iso gurin ba su Ankara ba, sai da tattaba kawunansu tukunnan suka Ankara da ita, Hanan kenan. Cikin yauki take fadin "to sarakunan musu, ana sana'ar ne? Me ya tufke musun naku haka har baku san na iso gareku ba, sarakan hayaniya." Dukkansu su ka yi dariya gami da cewa "zauna 'yar uwa ki ji kan topic din da muke tattaunawa ke ma ki dora naki ra'ayin sai muga wanda zai יי yi nasara." Ta samu guri ta zauna tana sauraron yanda bayanin kowa yake kasancewa. 6 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE Nafisa ce ta fara fadin "Aure fa Sunnah ce ta Annabi Muhammad (S.A.W) wanda kuma muka wayi gari muka tsinci Iyayenmu da Kakanninmu a ciki, sannan kuma karshen maganar mu ma karan kanmu shine duk wani dan adam da ya samu ba ta hanyar aure ba ya shiga uku da musiba da bakin cikin rayuwa da rashin kyawun asali. "Dan haka dole ne na zama mai son aure da kaunarsa har ma da muradin yinsa." buWannan shine dalilin da yasa na dagen wajenganin na kammala karatuna akan kari domin na cikawa mahaifana burinsu, shima kuma ya cika mini nawa burin na auren abin sona Muhammad, domin kuwa tuni 7 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE muka matsu da juna har ma muka kosa." Fauziyya ta amshe da sauri ta ce, "abin da ki ka fada Nafisa haka ne." Amina ni zumudin da kike yi shine yake bani mamaki, idan kuma zumudi akan aure ne ina matukar mamaki, yanzu dan Allah ni ban isheku misali ba?" Kuna fa gani ko waya mu ka yi Bello ta wadatar da mu, idan kuka kula ma yana kwana biyu bai shigo ba, ni kuma bana damuwa. Wani sa'ilin ma har na fi Kaunar Yayana ma akansa. Kuma kamar yanda kuke zümudin auren nan da soyayya haka muma muka yi, amman abin da nake so ku gane 99 "dokin na lokaci daya ne." Da kunyi auren kun kusanta da juna shi kenan zaku samu gamsuwar da ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE S dokin zai tafi, saura kauna da shakuwa ita ce ma zata yi aiki. "Ni kam dagewata akan karatuna bai wuce na kammala na samu sakamo mai kyau domin na samu damar wucewa Masters dina kai tsaye, sirrin yin hakan a gurina shine ya zama ina da zazzurfin ilmi da duk wata mace da Bello zai yi gangancin aurowa, kafin ta kamo ni sai ta ci kwa-kwa kuma tana kokarin kamoni ni na sake yi mata nisa." Amina ta yi saurin amshewa da cewa kun ji ko, ke ma dai duk kaucewar ki auren na ki kike kokarin kasawa domin so kike kifi duk wata mace da zata wayi gari ta ganta a gidan mijinki haskawa da kuma matsayi. Mu kuwa tunda ba taba yin auren muka yi ba ai dole ne mu zo muji yanda yake. 9 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СЕ Ke kuwa kin riga kinyi kin san ko ma menene a cikinsa, shi ya sa ki ke ganin bekon mu don muna zumudin yinsa, kuma ke ma din idan aka yi bibiya kan ra'ayinki za a ga cewa kuskure ki ke so ki yi masa da dagiya don ki sake samun jin dadin rayuwar zaman auren naki, kuma ki kare kimarki da Yaranki 29 duk dai ta gidan auren."" "Hanan ta yi murmushi cike da yauki tana kallonsu daya bayan daya, yanda kowa ke tsaye kan ra'ayinsa babu sassauci shine abin da yafi birgeta da su. Ta faďada murmushinta sannan ta ce, musu "duk ku tsaya ku saurara da wannan musun naku, kun san ni mamakin da kuke bani baya wuce kullum zancen aure da Samari. Kun ganni nan babu abin da ya dameni da wani saurayi 10 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE ko alkawarin auren wani, dan haka nake rayuwata hankalina kwance. Na sani aure lokaci ne, idan lokacin ya zo kuwa babu tsimi balle dabara, dan haka ni bana soyayya, don bana san matsala a rayuwata, shirin dagewata a karatuna kuwa bai wuce na cikawa Babana burinsa ba akan nasihar da yake yi mini a kullum yana nunamin cewa ilmi security ne ga rayuwar diya mace, domin yakan zame mata jagora a rayuwarta duka, ko ta gidan Iyayenta ko kuma ta gidan aurenta, kai duk ma inda ta tsinci kanta a rayuwa. Don haka ni ina ganin nawa ra'ayin shine daidai da rayuwata." Haka nan suka ci gaba da musayar ra'ayi a tsakaninsu har suka koma dakinsu basu daina ba, sai da suka kusa raba dare sannan kowacce ta yi shirin kwanciya cike da kewa dan jimamin 11 ALAWIYYA WADA ISA- YAR ALJANNA CE washegari za su rabu da juna kowa ya kama hanyarsa ta komawa gidan mahaifansa. "Haka kuwa aka yi, domin gari na wayewa kowacce ta fito da kayanta suka hade guri daya suna jiran azo daukarsu, babu abin da sukeyi sai jaddada rikon amana da zumunci mai dorewa a tsakaninsu tunda ga whatsapp ga facebook chat sannan ga Istagram kuma zamu dinga musayar hotunan juna kunga musu bai kare ba kenan. A hankali aka kwashe su daya bayan daya, yau 'yan Argument sun kare babu group dinsu kowa ya nufi muhallinsa cike da kewar juna, da zumudin riskar iyayensu da 'yan uwansu. 12 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE Tun a hanya take yiwa Dadynta waya tana sanar masa cewar sun kusa karasowa, shi kuwa Dadyn ya kasa zaune balle tsaye saboda dokin zuwan 'yar lelensa. Tamkar ta balle murfin motar ta fito tun bata yi parking ba haka ta ji saboda ganin Dadynta a farfajiyar gidan a tsaye yana jiran zuwanta. Da sauri ta bude kofar ta fito da gudu ta nufeshi, jikinsa ta fada tana hawayen farin ciki, shima sahafata kawai yakeyi yana fadin "Alhamdulillah," ina godewa Allah da ya nufa kika kammala karatunki, yau burina ya cika a kanki Allah ya bada sakamako mai kyau. "Amin Daddy" ta amsa masa a daidai lokacin da ta baro jikin Dadyn take gaisawa da sauran mutanen gidan da suka 13 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE fito domin tarar ta, kasancewa Hanan din 'yar gidance. Soyayyar tata ta samo asaline da soyayyar da mahaifinta Alhaji hafiz ke yiwa mahaifiyarta Binta, duk da cewa ba sa tare da ita amman kaddarar rabon haihuwa a wani gida ta hadasu, zumunci kuma kullum karuwa yake yi a tsakaninsu. Kwananta biyu da dawowa tana ta shan gata da lele daga kowa na gidansu musamman Dadynta. Ranar da ta cika kwana na biyu ne ta sanar da Dadynta, tana so ta je gurin Mamanta domin ta ganta. A zahiri Dadyn nata bai so tafiyarta ba domin shima har yau dokin ganin Hanan yake yi amma dole ne ya hakura ya barta ta je, domin yanda yake son ya kasance tare da ita mahaifiyar ta ta ma za 14 2 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE taso hakan, dan hakama ya amince mata tare da yi mata addu'ar Allah ya tsare masa ita. Da yammaci su ka yi sallama Direba ya tafi kaita. **** SILAR KOMAI A babban falon gidan ta sameta zaune tare da 'yan kannenta suna kallo. A guje suka taro ta suka runngumeta suna fadin "Aunty oyoyo". a Farin ciki da murna suka cikata domin tana kaunar 'yan kannen nata, ta dinga shafa su tana sake ji kaunar sun karuwa cikin ranta. Ita kuwa Maman tasu kallonsu kawai take yi tana jiin wani irin dadi cikin ranta, kaunar 'ya'yan nata na Kara ratsa ruhinta. 15 ALAWIYYALWADAISAYAR ALJANNA CLA sismsunaimasalesanjikinitasta isalini des mahaifiyar dtába takebstastedurkusab tasi gaishetscike ta girmamawa, ital maicikem da farin ciki take amsawansmutadoni Bauchi saukar yaushe dafatan kunzo **** lafiya?" Ta amsa da "lafiya kalau Mama sannan ta samu urtalzdundle Suka ci gaba hirar yaushe gamo. Bayan ta hutomeztastireslkayamastarshigadkitchen domini alywmahaifyand tata aikinrabinciss dareve stor Bue st onst salue sing Karfe takwas nodarer ramar sunsi kammalasdua komuin scha itiuneira falo sura.kalloniashal Dadi korea, It Mob s ni Maingidai panyi sailama arthingprib Yaran suka shirdahudtosunalii нasas barka idavzuwä, shyaiyamstgowsyarzauriask yana wasarda yaramsmwsk sins nilio ibeb SIMILINI SIST SISA 16 21 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE Cikc da ladabi ta ce masa "Baba barka da dawowa. Da sauri ya dago idona su ka yi ido biyu da Hanan yд fCua murmushinsa yana fadinAa Hanan saukar yaushe?" Itama cike da fara'a ta ce, "yau امام nazo Baba. Ta gaishe shi cike da ladabi shima ya amsa da fara'a. ya maida kallonsa ga Mamarsu yace “Ashe yau munada babbar bakuwa a gidannan, da latan dai anyi mata kyakkyawar tarba? Wani sanyi ta ji a ranta domin tana jin dadin yanda yake nuna Kaunarsa ga diyar tata, kamar shine ya haifeta. Cike da jindadi ta ce "mun bata tuwo taci." Su ka yi dariya gaba dayansu. Suka ci gaba da tattaunawa kan karatunta, ya tayata murna day a ji cewar ta kammala karatunta, haka suka ci gaba da hira cikin nishadi da kaunar junansu. 17 ALAWIYYA WADA IBA- 'YAR ALJANNA CE Ai dauki tsawon lokaci da shigowa gidan ba akan şanar da shi cewar ana sallama das hi a waje, kai tsaye yace a cewa bakon ya shigo domin yasan ko wanene, daman yasan da zuwansa, don haka Mamansu ta mike kuma ta umarci yaran da su tashi su koma karamin falo su bar musu nan. Bayan 'yan mintina ne suna zaune a karamin falon suna kallo, Hanan ta jiyo Karar wayarta ana kiranta. Ta duba ko ina bala ganta ba sai ta dinga jiyo sautin kiran wayar da ga babban falon da suka baro, don haka ta nufi falon kai tsaye cikin hanzari domin ta dauko wayar tata. Cike da nutsuwa ta shiga falon ta tsaya bakin kofa ta yi sallama, sai da suka amsa sannan ta shiga cike da ladabi ta durkusa, Baba ne yace mata "Yauwa Manan kin bar wayarki rana Kara, dama 18 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE yanzu nake shirin na miko miki. Ta yi murmushi kanta a kasa ta amshi wayar sannan ta gaishe da bakon, kana ta mike tana fadin "dan karta dameku da kara shiyasa na taso na dauka, tan agama fadin haka ta fice." Tuni ya zurfafa cikin tunanita domin ta yi matukar birgeshi tun daga ladabinta da nutsuwarta, ballantana kuma kyawun surarta duk da dai Hijabi take amma fuskarta kadai ta dauki hankalinsa. Tuni jikinsa ya mutu, komai ya tsaya masa cak, nan take ya mata da duk abin da ya kawo shi ya tsallaka wata duniyar. Da kyar Alhaji ya dawo da shi daga zurfin tunanin da ya afka, cike da zolaya domin tuni ya riga ya dagoshi. A daddafe suka kammala maganar da 19 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СЕ sukeyi. Da sauri ya shigar masa da maganar Hanan, da tambayar sa ya fara. "Alhaji dama kana da Yarinya kamar wannan ban taba ganinta ba?" Gata nan kuwa ka ganta?" amma ba anan gidannan take dab a, domin lokacin ina Asibinta ne, tinnan duk dan da ka Haifa agidannan ka je da shi gurina, kuma na tabbata da tana gidan nan da kaje daa ita." Alhaji Aliyu ya yi dariya "Ai lookacin tana makaranta ne, yau dinnan ta zo ta dawo daga Unibersity ta can Bauchi ta kammala Karatun Digirin ta akan Islamic studies." 7 Alhaji Sadik cike da mamaki ya zaro idanuwa, "Digree Alhaji? Kuma a fannin ilmin addinin musulinci? Amma Alhaji ka rufeni matuka domin kai ne fa da kanka ka bani shawara na nemi irin 20 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE wannan yarinyar na aura domin na samu maslahar gidana, gata kuma a gidanka amma baka sanar dáni ba?" Alhaji Aliyu ya yi dariya yace masa "Kaima kasan zance kake yi, Alhaji ya ya za'ayi na baka wannan galleliyar diyar tawa alhalin ka tsufa, ko ka manta matanka guda uku ne ga kuma 'ya'ya, cike da zolaya yake maganar. Shima cikin fara'a da kwantar da kai ya amsa masa "ai ba anan take ba Alhaji Sadik, abin ai dacewa ne ba a saurayi ko babba take ba, kuma Alhaji kamar yanda na gaya maka aure shigar sauri ya yi mini, duka ban wuce shekara arba'in ba a duniya. A wannan zamanin kuwa ka san akan samu saurayin da bai yi aure ba wanda ya fini shekaru." Alhaji ya fadada murmushinsa ya ce, masa "Nima ina zolayarka ne, ai shi 21 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA CE aure lamari ne na Allah don haka kada ka damu zamu tattauna kan maganar ka insha'Allah kuma zakaji duk yanda ake ciki." Dai dai nan su ka yi sallama ya raka shi har waje suna tattaunawa kan maganar Hanan, har sai da ya shiga motarsa ya ja sannan suka rabu. Karfe sha daya na dare suna shirin kwanciya ne Alhaji ya sanar da Mama duk yanda su ka yi da Sadik kan maganar Hanan, sannan ta umarci maigidan nata da ya samu lokaci ya sanar da mahaifin Hanan din. Ya ji dadin hakan matuka, shima albarkar ya sanyawa al'amarin sannan ya kwanta domin rintsawa. Ita kuwa Mama ko da ta kwanta baccin kinz uwa ya 'yi domin tunaninta gaba daya ya kare a kan yan da Hanan zata amince da wannan 22 ALAWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE maganar, domin ta san kowacece diyar tata. Yau kwanaki uku kenan da yin maganar Alhaji Sadik da Hanan, abin yana damun Maman matuka cikin ranta, domin ta rasa ta ina zata 6ullowa Hanan domin ta sanar da ita halin da ake ciki. Shi kuma Alhaji Sadik ya dami Alhaji Aliyu da maganar, don kusan kullum sai ya kirashi a waya ya fi a kirga akan maganar. Hakori dai yake ta ba shi tare da tabbacin za a duba yiwuwar maganar. Ranar da aka cika sati ne Mama ta yi kundunbala ta nufi dakin da Hanan take. Kwance bisa gado ta taddata ta yi nisa cikin chatting da 'yan Argument 23 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СЕ group. Dan haka bata so koda sakan daya ta dauke idonta daga kan wayar ballantana kuma ta ajiyeta, domin tuni musun nasu ya dauki zafi. Yau kuma suna tattaunawa ne akan amfanin auren mace mai ilimi. Dole ba dan taso bat a dakata ta ajiye wayar tata domin amsa sallamar Maman nata, domin ta kula a fuskar Maman sam babu wasa a tattare da ita. A kujerar dake gefen gadon ta zauna ta kira sunanta cikin tausasawa "Hanan ina so ki saurareni ki bani hankalinki, kinga dai yanzu ke ba yarinya ba ce, tuni kin mallaki hankalin kanki, kuma kinyi ilimi mai zurfi ta kowanne bangare, kin kuma san abin da Allah ya hukunta akan duk dan adam din da ya zama baligi mace ko namiji, kinfi kowa sanin cewa aure shine daraja da martabar 24 ALAWYYAWADA ISA. YARALJANNA CE diyadmavé şduma kinssan dai mune mukad zamorsitaroziwankis duniya don haka ba.b zamu thbh/yi miki abin da zai cutar da ke ba. DITI ISUS FTICKS idsInar sosnasbsanars da ke cewa waimd mutumin da ya zo gurin Alhaji rariarndaskika zöji har kika shiga dauko 2 wayarki. BdShine yd zoclyanad sohkib dab aurevlsm яр эллslsd sb ida eb snct6} sb iKufin ta kammala ta katseta ta Zaros? idorigamis da bude bakista dafe kirjintai cikesda mamaki ta kalli mahaifiyar ta tan amma.kuma sai ta kasa furta komisnsi i Uwar ta karanci me ke zuciyartas domhaka ta tare ta da cewa "Na san dama zaiskib yi mamakinsewannan Maganasb domin násan ke a tunaninki idan zabiakas baki to saurayi zaki so mai kananan shekaru, sai dai ina so ki gane cewa shi aure zabin Allah ake nema ba na mutum 252S ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ ba, ba kuma son ranka kake zaba ba, abin da yafi muhimmanci a aure shine ka nemi zabin Ubangiji to sai kaga Allah ya haneka dana sani. Kuma ni abin da yasa na karbі maganar ba wani tantama sabida Alhaji Sadik mutum ne mai kirki da karamci, duk da dai basu dade da Alhaji ba amma a tattare da shi da halayyarsa ba makusa sai alheri don haka nake shawartarki da ki yiwa kanki fada kiyi nazari akan abin, mu ba zmu yi miki dole ba, ki yi tunani ki tattauna da zuciyarki, sannan yace yana nan zuwa ku gaisa. Tana kaiwa nan ta tashi ta fice daga dakin bata tsaya ta saurari abin da diyar ta ta za'ta ce ba domin ta san ma ba zata ce din ba. 26 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE take yi bisa gadonta amma bacci ya ki daukarta, sai da ta kusa raba dare a haka sannan barci barawo ya yi awon gaba da ita. **** Washegari haka ta wuni ba wani ishasshen kuzari a jikinta. Maman tata ta fahimci halin da ta shiga don haka ta kyaleta take ta gudanar da harkokinta gabanta. Girki ma ita ce, ta yi abin ta domin Hanan din ta koma tamkar wata marar lafiya. A wannan yanayin ta wuni har zuwa dare. Tana zaune a dakinta ta yi zurfi cikin tunani Maman nata ta daga labulen dakin ta ce, mata " kina da baki a falo:" Bata tsaya ta ko da kalli fuskarta ta juya ta ficce.. 28 ALAWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE Gabanta ya fadi ras, ta mike da sauri a rude ta fara zagaye a dakin nata, sannan daga bisani ta dangane da gaban Mudubin dake dakin, ta kalli kanta sana da kasa. Doguwar rig ace a jikinta ta atamfa super Yaluwa, dinkin ya amshi jikinta ya yi mata das, daga kasa an buda rigar komai na jikinta kalar Yalo ne, babu dankwali a kanta don haka a sanyaye ta dauko wani dan karamin Hijabi mai tạf da nayafi ta saka ta zagayo da mayafin ta gyara shi yai mata das, tamkar Wata Balarabiya, babu wata kwalliya a fuskarta amman kuma da yake ta saba kwalliyar sam babu muni a fuskar ta ta. Da sallama ta shiga. A rude ya dago ya kalleta su ka yi ido hudu. Nan take ta tafi da imaninsa domin ta yi masa matuka, kamshin turarenta 29 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СE Different Women wanda ya kama jikinta ya doki hancinsa. Hankalinsa ya tattara a kan kallonta ji yake kamar ya hadiyeta don so. Cikin nutsuwa ta sanu guri ta zauna cike da ladabi ta gaisheshi da muryarta mai kasha masa jiki, ya amsa a tausashe idanuwansa na kanta har wannan lokacin. Shiru ya dan ziyarcesu na dan wani lokaci sannan ya fara da yi mata Magana da cewa "Malama Hanan ya gida ya karatu?" kanta na sunkuye ta amsa da"Alhamdulillah." A yanda take amsa masa babu yabo babu fallasa, bai damu ba domin shi mutum ne mai hakuri da saurarawa, don haka kawai yaci gaba da yi mata Magana. "Na sani kin samu labarin komai nawa daga mahaifanki, to daman a zo ne don mu ga juna kuma mu samu fahimtar 30 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CЕ juna, ya yi ajiyar zuciya gami da tattara muryarsa sannan yaci gaba da fadin "Hanan hakika tun ranar da na ganki naji kin kwanta mini a raina, komi naki ya birgeni musamman iliminki da kuma nutsuwarki gami da tarbiyya da kika samu daga Iyayenki, ba sai na gaya miki ba, kin san wasa ba zai kawo ni gurinki ba dan haka ina mai tabbatar miki da cewa ina kaunarki matuka, kuma aure ne ya kawo ni ba maganar wasa ba, fatana shine na samu wani bigire a cikin zuciyar ki wanda zai zamo muhallin soyayya' ne ka dai, hakika idan na samu hakan to zan kasance mai matukar farin ciki a cikin rayuwata sannan kuma mai matukar sa'a da dacewa. Akwai alamun maganganunsa sun ratşa zuciyarta, tausayinsa ya kwarara cikin zuciyarta ganin yanda ya nuna 31 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAK ALJANNA CE Kaunarsa Karara gareta sai dai ita kam har yanzu ba zata iya tantancewa shin tana son sa ne ko a'a, duk kuwa da cewa a zuciyarta ta tabbatar Alhajin ya yi yanda mace ke bukatar namiji domin sam ba shi da wata makusa a tare dashi. Tsayayyen namiji ne dogo kuma mai matsakaicin fadi fadi ba mai kiba ba, fari ne tas mai madaidaiciyar fuska cikakkiya, yana da kwarjini da cikar kammala gami da zafi, tsayin fuskarsa ya dace da zubin da jikinsa. Yana da manyan idanuwa da kuma dogon hanci hade da kyakkyawan baki, yana da yalwataccen gashin kai da na gira, ga sajensa ya kwanta lub-lub akan fuskarsa wanda ya kara masa kyau, dan gayu ne na ajin karshe domin duk shigar da zai yi tun dag asana har kasa kala daya ne hatta gilashin idonsa kalar 32 ALAWIYYA WADA 1SA- ‘YAR ALJANNA E kayansa ne, gashi wayayye irin namijin da ake ya yi. Da ganinsa kudi sun ratsa shi, ba kudin na sa ba, duk da ta fusknaci bai yi wani zurfin karatun boko ba, da alama dai yafi zurfi ga bangaren kasuwanci amma kuma gogewa da wayewarsa tafi ta wanda ya yi Digiri. Maganarsa ce ta. katse mata tunaninta cikin dadin muryarsa yace mata "Hanan zan koma ina ganin ya kamata na kyaleki, ki samu dammar yin nazari don ki fiddoo da hukunci kyakkyawa wanda nake fatan zamanto alkhairi a gurin mu duka." Tamkar kurma haka ta zamo a gaban Alhaji Sadk sai kace ba itace a cikin Argument group ba. Rafar 'yan dari biyar ya ajiye mata a gabanta sannan ya umarceta da ta ba shi 33 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA СЕ karasa, daman na kira ne nace miki sai da safe." Ta gyada kai cikin ranta ta ce, "amma zumudinka ya yi yawa." Can ta amsa masa da cewa "to shikenan mu kwana lafiya." Da sauri ya amsa "Nagode Asuba ta gari." Wani irin yanayi ya ji ya ratsashi, ya bi wayar da kallo tamkar Hanan din yake kallo a jikin hoton wayar. Cike da dumbin tunaninta ya isa cikin gidansa, haka ya raba dare yana suranta Hanan cikin idanuwan zuçiyarsa. Muryarta na yi masa amsa kuwa a kunnuwansa, har 6arawon dare yazo ya sace shi ba tare da ya yi shawara dashi ba. Ita kwa Hanan mamajin irin zumudin da Alhajin ke yi a kanta takeyi, ko dai ba komi tana son namiji mai sonta da nuna kulawa a gareta, kuma mai 36 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СЕ lokacinta, ta wannan bangaren dai Alhaji Sadik babu makusa. **** Washe gari da safe ta shirya tsaf cikin wasu English wears Riga da wando jeans sunyi matukar yi mata kyau sai kuma ta dora After dress baka a kansu. Kai tsaye teburin cin abinci ta nufa inda ta iske Iyayen nata suna karyawa. Cike da ladabi ta

Chapter 1 of 4