Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 4
abin da ke baki gane ba shine ba duka aka taru ka daya ba, dole komi lalacewa akwai nagari, kuma idan kana addu'a kana mika zabi na alkairi ga Allah sai kiga yayi maka zabi na alkairi, ga shi kuma muna zaune kin samo na gari ko?" ya fada tare da zolaya. Kunyar Dady ce ta kamata dan haka ta sunne kai ta tashi ta fita da gudu tana dariya. 71 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE Shi kuwa Dady dadi ne ya kama shi da murna, domin kullum addu'arsa kenan Allah ya nuna masa auren diyar ta sa don har ma ya fara fidda rai da batun auren ta domin halayyar da take nunawa kan maganar mijin aure abin yana bashi tsoro domin har ya fara tunanin ko ba lafiya take ba. **** Abu kamar wasa karamar magana ta zama babba, maganar auren Hanan da Alhaji Sadik ta kankama domin tuni Baba Malam ya kirawo Sadik ya tabbatar masa da cewar ya kamata ya turo magabatansa kan maganar. Hakan ba karamin dadi ya yi wa Alhaji Sadik ba, don haka bai yi kasa a gwiwa ba ya hado komai na aure ya sanya ranar kawowa. 72 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE Sati biyu aka sanya za a kawo komi na auren, don haka Alhaji Bashir ya sanar da shi, ya yi murna matuka, amma da yaji cewar mutumin yana da uku ita ce ta hudu nan da nan ransa ya baci, ya dubi Alhaji hafiz ransa a bace ya ce masa "Yanzu kai Hafiz ya za'ayi ace Yarinya kamar Hanan a aura mata mutum mai mata uku, ai an kware ta saboda Allah menene gaggawar sai anyi mata aure a bari mana har Allah ya bata saurayi dai dai ita sai a aura mata." Alhaji Hafiz ya nisa sannan yace "Tabbas abin da Yayan nasa ya fadi gaskiya ne to amma ya zai yi da hukuncin da Ubangiji ya zartąarai ba tsumi babu dabara. Ya fuskanci Yayan nasa sosai yace masa "Ka kwantar da hankalinka Yaya, abin da duk ka fadi gaskiya ne amma al 73 ALAWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE ta yi auren kudi Allah ya sauwake wai kuma ita ce ta hado abin da zaben nata ya zabo mata kenan? Ita dai kam biris ta yi da zantukan mutane ta kankame Ubangijinta domin dai ita kam ta san tafi karfin ta yi auren kudi domin kowa yasan cikin kudi ta taso gaba da baya. BIKIN AURE Shagalin bikin auren Alhaji Sadik da Hanan ya kankama, duka bangaren biyun komi ya kankama, saura sati biyu duka-duka a fara shagalin dumu-dumu. Iyayen Hanan kam bakinsu har kunne domin ganin Allah ya kawo musu lokacin auren diyar tasu, Gangaren Mamanta kuwa abin ba'a cewa komai, domin yanda take cikin farin ciki tamkar 75 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE ita kadai ta fi kowa kaunar Hanan din, ballantana kuma Alhaji Aliyu wanda ya zamo shine silar komi. Sai dare ta samu damar, kuma da ta online kai tsaye Group Argument na whatsapp ta nufa, said a ta kammala karanta sakonnin da suka wuce ta sannan ta fara tura musu da tsarin ranakun aurenta, daga kasa kuma ta ce, tana gayyatar kowa da kowa, wanda bai samu dama ya yi mata addu'ar fatan alkairi. Nan da nan ta fara samun amsoshi na karyatawa musamman Fauziyya da Nafisa domin su sun hakkake cewar zolayarsu kawai take yi amma ba wani batun aure tare da ita a kwanan nan. Fauziyyar ce ta fara aiko mata da amsar cewa "haba mai tsoron aure, mu zaki zolaya? karfa ki manta mun san ko 76 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE ke wacece a bangaren maganar aure don haka babu wabi kife mu da zaki yi.” Tana kammala karantawa dariya ta subuce mata har tana shirin fadowa daga kan gadon da take a kwance dan dariya, bata kammala dariyar ta ta ba, wani sakon ya shigo. Nafisa ce ta aiko da cewar "Hahah! Hanan kenan kice yau Allah ya kawo mu lokacin da kike jin sha'awar aure a kanki, tunda har kike karyar fadin ranar aurenki, a hankali wata rana sai kiga har kin samu nutsuwa a 6angaren auren har kin aiko mana da takardar gayyata ta gaske ba ta zolaya ba, kinga sai muzo mu sha bikin gaske ba na tatsuniya ba." Dariya ce ta sake cin karfinta, ba ta iya cewa komi ba, wani sakon ya sake shigowa. 77 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СЕ Amina ce ta ke ce mata "Na fuskanci inda kika nufa Hanan, ba wani kike zolaya ba illa mu masu zumudin komawa gida muyi aure, kinji munyi shiru ba muce ga ranar auren ba ko? Shine kika biyo ya wata hanyar don ki zolaye mu, to kisha kuruminki nan ba da dadewa ba zaki ji kiranmu sai ki shiga Jaka ki taho biki, kinga daga ranar shegantakar da kike yi mana ta kare, ke kuwa ki yi ta zama a gida ki zama daddawar daka." "Kun fi kowa sanin cewa ni Hanan ba halina ba ne zolaya, sannan ban iya karya ba ko da wasa, kun san idan ba da gaske nake ba babu yanda za ayi na shirga karya na sanar daku, kunga ko wannan kadai ya isheku ishara ku gane cewar shi aure fa lokaci ne, da sonka da kinka da zumudinka da kuma ko in kula 78 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE dinka babu ruwan Allah, wallahil azim kun san idan na rantse da Allah a kan karya na san makoma ta, to wallahul azim aure zanyi, kuma yanda na turo muku tsarin komai haka abin yake, afuwarku kawai zan nema na rashin sanar daku da banyi da wuri ba, wallahi nima haka nan auren ya zo mini ba shiri, shiyasa ban samu damar sanar da kowa ba, sai yanzu da abubuwa suka saukaka, ina zuba idanuwana a bisa hanya sai na ganku." Halin da suka shiga na mamaki ne ya sanya suka kasa ce mata komi, illa yi mata addu'ar fatan alkairi kadai. Ranar Alhamis ita ce ta kama ranar kamu dan haka tun kafin ranar aka shiga hidimar gyaran jikin amarya, ana gyaraya ana kuma tsumata ga turaruka da akeyi don haka duk inda ta gilma wani kamshi 79 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE ne ke fita daga jikinta mai dadi da daukar hankali, jikinta kuwa sai wani sheki yake yi da silbi, ga wani taushi tamkar jikin Jaririya. Biki kam ya kayatar, guri guda aka tanada dan yin kamu sannan da aka gama kamun kuma aka yi gadar kauyawa, abin ya kayatar matuka, 'yan Argument ne Amarori domin sune a kan gaba a komai. Kyawun da amarya ta yi kuwa fassara shi a nan kauyanci ne. Washegari kuma dinner aka shirya lafiyayya wacce ta amsa sunanta, duk wani abokin arziki ya halatta ya kuma taya ango da amarya murna. Ana kammala dinner ne kuma aka dawo da amarya gida ta shirya domin kaita dakinta Tamkar a mafarki take kallon alamarin wai ita ce yau za a kaita gidan 80 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE aure, haka ta dinga shiryawa tana cike da mamakin hukuncin da Allah ya kaddara bisa kanta. Daddynta ya yi mata nasiha matuka akwaialamun kuma duk abin da ya gaya mata ya shiga cikin kunnenta matuka, da kuka suka rabu da Daddy, yana sanya mata albarka da yi mata fatan alkairi, kai tsaye gidan mahaifiyarta aka zarce da ita,ida da Baba Aliyu suka hadu suka yi mata nasiha, nan ma dai da kukan suka rabu, sai gidan Baba Alhaji kuma, duk da dai yana zolayarta amma ya gaya abubuwa masu matukar fa'ida da idan ta rike za suyi mata jangora zuwa ga kyakkyawar rayuwa da cimma nasara a cikin rayuwar aurenta. Cikin nasara sa sa'a ta shiga gidan mijinta, sashen nata kam ya tsaru tamkar Aljannar Duniya, babu ce kawai babu a 81 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CЕ sashen, komi ka kalla na waje ne babu wani abu dan gida Nigeria, Hanan kenan 'yar gata. A babban falon gidan suka taddasu wanda zai sadaka da sashen kowa a gidan har da na mai gidan. Bayan sun gaisa ne suka damka amanar Hanan a hannunsu. Uwargida wacce dama ita ce ta amshi dariyarsu tun farko ita ce, ta sake yin murmushi ta ce,"Ai ba komi da ai duk na kowa ne, wannan ai 'yar uwace a gurin mu, insha Allahu zamu riketa da amana da gaskiya Allah ya bamu zama lafiya ya kawar mana sherrin shedan-a tsakaninmu." Gaba daya suka amsa da Amin. Ana shirin yin addu'a ne Lami wacce ke cika tana batsewa, cike da tsiwa ta ce, "A'a Maman Nabila gara kawai ki fito ki 82 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE fadi gaskiya kishiya fa ba 'yar uwa ba ce, in ke kin amsa to ni dai gaskiya ban amsa ba don amana wahala gareta." Ta juya ta kalli Sadiya ta ce mata "ko kuwa 'yar uwa, ki ya kika ce? Ko kema kin bi sahu?" Sadiya ta yatsine fuska ta ce, "ai kema kin san tankawa ma yabawa ce, ina ni ina amsar amanar kishiya, gidan miji ne gashi nan aure ta zo yi kamar yanda mu ma shi muke zaune muke yi don haka ta share guri itama ta zauna kowa ya taka irin rawarsa a kalla." Gaba daya gurin suka cika da mamakin abin da ya fito daga bakunansu don haka ba shiri suka dauki amarya zuwa sashenta jiki a sabule kowa na fadin albarkacin bakinsa, suna kuma kara yiwa Hanan nasiha akan hakuri da taka tsantsan a zaman takewarsu. 83 ALAWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA CE Bayan dan lokaci 'yan kai amarya suka watse, sai 'yan Argument aka bari suma sun jira ne a sayi baki sannan su koma gida, suna cikin jimamin abin da kishiyoyin suka yi matane sakon ango ya shigo wayarta ta buda da sauri ta hau karantawa. "Amarya ki kara hakuri gani nan zuwa gareki, zuciyata cike take da zumudin riskarki, idanuwana cike suke da dokin ganinki cikin siffar amarci, ki وو shirya gani nan zuwa. Nafisa ce ta karbe wayar ta karanto musu abin da ya aiko, tana kammalawa suka saki ihu da tafi suna fadin "kai wannan ango naki Hanan gwanin iya soyayya ne, kinga yanda yake tattalinki tamkar wani kwai! Dole 84 ALAWIYYA WADA ISA. 'YAR ALJANNA СЕ kishiyoyinki su yi kishinki, ai kin amshe zuciyar mai gidan gaba daya." Cike da zumudi Alhaji ya shigo ciki, farar shadda kal Getzner, Babbar riga aka yi masa da 'yar ciki da wando da bakin zare aka yi dinkin jikin shaddar don haka hattta agogon hannunsa baki ya sanya, ya yi matukar kyau da daukar hankali. Abokansa ke biye da shi dauke da 'yar karamar akwati cike da kayan siyen baki. Fara'arsa taki karewa, idanuwansa kuwa na kan gimbiyar tasa. Allah -Allah yake a kammala siyen bakin ya sallami kowa a barshi daga shi sai amaryarsa, don haka ya dinga jin komi a takaice, ba dadewa suka kammala suka yi sallama dasu suka barsu suna zolayarsu. 85 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE Dakin amarya ya rage daga ita sai angonta, ya bi ko ina da kallo shirin dakin ya matukar birgeshi ya sanyawa' aurensu albarka sannan ya umarce ta da su tafi sashensa, ba tare da gardama ba ta mike ta bi bayansa har zuwa sashen nasa. Yanda ta ga tsarin 6angaren nasa ya matukar kayatar da ita, bata taba zaton Sadik arzikinsa ya kai haka ba, sai a yau da ta zo muhallinsa, gaskiya gidansa ya tsaru, gida ne na babban maikudi ba dan karami ba. Kai tsaye ya umarceta da dauro alwala, shima ya yiwo ya fito daga bedroom din sanye da doguwar riga sassauka, ya yi mata jagora zuwa bedroom dinsa sannan suka tada sallah 85 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE raka'a biyu daga koyarwar Annabi (S.A.W) don neman tabarrakin auren. Bayan sun kammala ne ya kama kanta yayi addu'a, sannan ya janyo Kazar day a zo da ita ya bude yah au bata tana ci shima yana ci, tana matukar daukar hankalinsa. Sai da ta koshi don kanta sannan ya umarceta da ta cire kayan jikinta masu nauyi sannan ya dauko mata masu sauki ya bata ta amsa ta hau cirewa cike da kunya. Abin da ya faru a wannan dare dai mai matukar girman gaske ne, Alhaji Sadik ya yi farin ciki matuka domin ya samu matarsa cikakkiya kuma kamilal mace, wannan ba karamin kara mata daraja yayi a idanuwansa ba. 87 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA СЕTА Washe gari ruwan dumi ya cikal mata kwamin wanka domin(vgasa) jikinta sosai, ta ko ji dadin hakan matuka. λυλε καυμε Tsaf ta fito cikin wata doguwar rigar shadda kalar purple wacce aka yisd wa aikin duwatsu daga Dubai,uyarı amsheta matuka ta kara wani kyau da sheki ga kamshi na tashi mai daukar hankali. Bisa abin sallah ya taddatarı bayan ta ida tana zaune bisa kai batar ko motsa ba, shima yayi kyau cikinio farar shadda doguwar riga da wando sai sheki yake yi. ment isri isb dibse isilA Ya sakar mata murmushin farinb ciki da tsantsar kauna, da siririyar muryarta mai dauke hankalinsa sta amsa masa martanin murmushin dabi 88 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE cewa "Barka da safiya Alhaji." Ya sake fadada murmushinsa yace mata "Barkanmu dai Hanan ya bakunta?" Murmushi kawai ta yi bata iya amsa masa kanta na sunkuye, ya sake sakin murmushi cike da jin dadi yace "Hanan kina burgeni matuka, kunyarki na matukar kayatar dani domin kara miki ado take yi." Ya ajiye mata plate dauke da farfesun kaza da kuma shayi a kofi mai dumi ya ce mata "Ga shayi nan na hado miki ga kuma farfesun Kazan an ki daure ki cinye duka sai ki sha wannan دو maganin." Ya mika mata Brustan da Ampeclos, sannan ya mike gami da fadin وو" Ina zuwa. A hankali ta dinga kurbar shayin zuciyarta na dawo mata da abin da ya faru gareta daren jiya, cikin ranta take 89 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE fadin "Lallai ta dace da miji, tabbas Alhaji ya san ta kan soyayya, ya iya tatti da kulawa da tausayawa, ashe aka soyayya take dadi?" Da ace ta san haka rayuwar aure take da dadi da tun asali bata dinga gudun auren ba. Da wannan tunanin ta kammala karya kumallo, a daidai lokacin Alhaji ya turo kofa ya shigo da sallama, suka yi ido hudu suka yi murmushi, Alhajin yace "Ince ko dai kin cinye tas kin sidi kwanon?" cike da zolaya yake fadin hakan. Ta sake yin murmushi ta ce masa "A'a na dai ci abin da ya sauwaka. Ya sake fadada murmushinsa yace mata "Hana zan fa yi miki dura idan baki cinye ba" kanta na sunkuye bata iya ce masa komai ba, dai dai kunnenta ya N 90 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE matso ya saita bakinsa cikin taushin murya yace mata "Hanan ina matukar kaunarki, kina daukar hankalina kina sanyani nishadi kin tafi da imanina gaba daya, anya kuwa zaki barni na dinga tafiya nemo mana na tuwo kuwa Hanan?" Maganganun nasa sun matukar birgeta sun ratsa kwanyar ta, ji take yi tamkar ita kadai ce tafi kowacce mace sa'a a duniya. Haka suka 6ata lokaci suna nunawa juna kauna, har said a baki 'yan uwan Hanan suka fara zuwa, sannan yayi Karfin halim barin sashen nata ba don ransa na so ba. ASALIN ALHAJI SADIK To kamar yanda muka ji daga bakin Baba Malam, Alhaji Ahmad maikamshi shine Kakan Alhaji Sadik wanda ya haifi mahaifinsa mai suna Alhaji Muhammad. 91 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE Alhaji Muhammad sanannen dan kasuwa ne wanda kasuwancinsa ya bunkasa ba a cikin gida Nigeria kadai ya tsaya ba hard a kasashen waje, Babbar sana'arsa ita ce, safarar turare daga kasashen waje zuwa gida Nigeria, wannan sana'a tasa ta bunkasa matuka domin ya kasance babu inda ake zuwa neman turare kowanne irin nau'I sai gurinsa tun daga kan diloli har masu karamin jari. Alhaji Muhaimınad ya kasance shine babban da agurin Aihaji Ahmad wanda matarsa uwargidansa ta Haifa masa, don haka ya dorashi akan komi na sana'arsa har ta kai ta kawo ma duk kasar da zai fita das hi yake fita, domin so yake yi ya bude ido da kasuwancin sosai idan girmaya-zo masa shi kuma sai ya huta. Shekarar Alhaji Muhammad talatin da biyar a duniya aka aura masa wata 92 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE 'yar uwarsa ta nesa mai suna Sauda, suna nan zaune cikin rufin asiri, Allah ya azurtasu da samun da namiji wansa suka sanyawa suna Sadik. Kasancewarsa babban Jika yasha gata matuka a gurin Kakansa Alhaji Ahmad, domin bai bar mahaifinsa ya yi komai na haihuwarsa ba, haka kuma ya ci gaba da hidima dashi har sai da Allah ya karbi rayuwarsa. Shekarar Sadik bakwai a duniya Allah ya kawo wani mummunan al'amari na hadarin jirgin sama wanda ya hada da Alhaji Ahamad da babban dansa Muhammad a kan hanyarsu ta zuwa india daga nan zasu wuce France domin shigo da turaruka. Ba karamin tashin hankali suka shiga sakamakon wannan mummunan 93 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE rashi da ya samesu, wanda ya haddasa Kakar Sadik da mahaifiyarsa yin takaba. Sun samu shekaru cikin wannan jimamin sannan daga bisani suka dangana, an raba gado kowa ya samu abin da ya samu, Kakar Sadik bata bari gadonsa yaje hannun ko da mahaifiyarsa ba, said a Allah ya say a isa shekarun hankali sannan ta danka masa dukiyarsa, ba a dade ba itama ta ce, ga garinku nan. Ya ji mutuwar Kakarsa domin ya shaku da ita, wannan yasa dole ya dawo hannun Mahaifiyarsa gaba daya ba don ya so ba, domin mahaifiyar tasa tuni ta yi aure har ma ta haifi diya mace. Haka suka ci gaba da rayuwa, shi kuma ya durfafi kasuwanci ba kama hannun yari músamman da ake ya gaji dukiya mai tarin yawa, don haka ita ya juya ya fara neman arziki. 94 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE Allah ya sanya masa albarka a kasuwancin domin yana faraway ya dinga samun alkairi mai dinbin yawa. Bayan shekaru sunyi ni sa mijin Babar tasu yayi wata rashin lafiya kwanza takwas a asibiti yace ga garinku nan, wannan ya tilastawa Sadik daukar nauyin komi na mahaifiyarsa da na kanwarsa, wannan ya sanya yana matukar ji da mahaifiyar tasa sam baya son abin da zai 6ata mata ko kaďan. TUSHEN KOMІ Kwance yake a katafaren gidansa wanda za a iya cewa na mashahurin mai kudi ne, dakin da yake kwance ciki ya wadatu da kayan more rayuwa ga wadataccen sanyin A.C a dakin, gaba raba ce kawai take sauka ta ko ina, ga kamshi ya wadata cikin dakin, cikin baccin nasa ne mai cike da rudani yake 95 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE ganin gidansa naci da wuta sosai, yana tsaye kofar gidan cike da jimami da tashin hankali ya kasa aiwatar da komi, sai makwaftansa ne ke yin iya kokarinsu wajen kasha wutar, amma kuma idan suka zuba ruwa tamkar fetur suka zuba nata sai kara tsiri takeyi. Motsi yake yi bisa gadonsa sakamakon wannan mummunan mafarki da yake yi, sau biyu yayi juyi sannan ya farka firgigit tamkar wanda aka tsikara!. Sai me? Hayaniya ya jiyo a bakin kofar dakinsa, ya saurara yana jin abin da yake faruwa. Muryar Lami ya jiyo a sama cikin fada da hakikancewa tana fadin "Wallahi Sadiya duk nacin ki baki isa ki shigo mini dakin miji ranar girkina ba." A daya bangaren kuma ya jiyo Sadiya na masa mata da fadin "ban fahimce ki ba me kike nufi ba Lami, ni da ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE dakin mijina kice ban isa na shiga ba? Kika san uzirina da ke tafe dani gurinsa?" Lami ta yi shewa gamida tafa hannu "Uzuri? Allah yasa kece tattabara karewar aure wallahi ba zaki shiga ba, domin kuwa yau ikona ne sai ki bari sai ranar girkinki sannan kya gaya mmasa ko ma menene amma banda yau din. Ran Sadiya ya yi matukar 6aci takai makura a fusata don haka kai tsaye ta nufeta tana shirin tureta tana fadin "To wallahi baki isa na uban kuturu ma ya yi kadan balle na makaho, kai tsaye ta dauko wuyanta suka fara kokawa." Mero c eta nufo su. da sauri sakamakon hayaniyarsu da ta jiyo tana fadin "kai kai kai, wai mi ke faruwa ne? nake ta jin hayaniya haka taki ta kare?" Sadiya da ke rike da wuyan Lami ta waigo ga Mero tana fadin "Wai 97 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE wannan 'yar rainin wayon ce take neman shiga dakin mijina bayan bata san uzurin da zai kai ni gurinsa ba" Da sauri Lami ta amshe da hannunta na, tokare a jikin kofa tana girgiza cike da tsiwa "Wallahi babu mai shiga yau sai dai ayi 'yar rotse-rotse a gidannan akan na daba dama shigar min don kuwa nima ba a barina na shigarwa kowa ehe." Mero ta maida kallonta ga Sadiya ta ce, mata "A gaskiya Sadiya ba kiyi gaskiya ba, ko nice b azan yarda a shigar min, haka kawai da sassafen nan mijinka yana bacci ko tashi bai yi ba azo a shigar maka gurinsa ai dda matsala, ki bari dai ya fito sai ki sameshi a waje ki gaya masa ko menene. Bin bayan da Mero ta yi shi ya kara mata karfin gwiwa don haka ta sake ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE kwabe baki ta saki tsaki sannan ta ce, a ki kyaleta mana karta bari ya fito, ke wallahi idan na ga dama ma ko a wajen b azan bari ta ganshi ba sai dai ta kirashi waya." a Ran Sadiya ya kara baci cike da mamaki ta kalli Mero ta ce, "Af kema mara mata baya kika yi? Lallai munafuncin gidannan kullum karuwa yake yi." Ta girgiza kai sannan ta ce, "Yanzu kuwa za ta ji a jikinta." Da sauri ta sake damkota suka kama kokowa. Merro kuwa sai ta koma gefe tana kallonsu tana fadin "Babu wacce zata hana, idan kukaji ciwo a jikinu zaku daina ne, don nima ba wuce ku yi min na yi ba, kuma ko na hanaku ba zaku hanu ba." Basu Ankara ba suka ga Alhaji Sadik tsaye a gabansu, ransa ya dugun 99 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNА СЕ zuma, cikin karaji da tashin hankali yake Magana. "To sarakan bala'i da masifa sarakunan tashin hankali, dan masifa da sassafen nan kun hanani na huta, yan zunnan a cikin baccina nake mafarki ana gobara a gidana, ana ta zuba ruwa amman wutar taki mutuwa, ashe bala'I da masifarku ake nuna mini wacce kowa ya kasa maganceta, yanzu ku ko kunya ba kwaji a dinga jiyo masifar ku a makwabta?" Zasu yi sauri su saki juna a tsorace su koma su tsaya kai a sunkuye da alamun rashin gaskiya tattare da su. Mero ce ta yi tsagal ta ce, "Allah ya sa dai ni babu ruwana, ni ma zuwa nayi na rabasu, naga abin ya fi karfina, wai akan shigowa dakinka ne suke wannan tashin hankalin وو da sassafen nan....... 100 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA Е Da sauri ya katseta a fusace cikin daga murya "Rufe mini baki dalla, har akwai wata abar yabo a cikin ku wacce za a ce gara ita?" Ya maida kallonsa ga Lami da Sadiya sannan yah au yi musu gargadi da fadin " Ku kuma sarakan rashin mutunci, shine don ku tozarta ni kuke min masifa haka da sassafe akan shiga dakina kawai, to daga yau duk ku ukun bana bukatar ganinku a dakina, kuma ko abinci kuka yi ku cinye abin ku ku da 'ya'yanku ni bana bukata." A tsorace Lami ta bude baki za ta yi Magana ya yi saurin gwaleta da fadin "Rufe mini baki, bana bukatar maganar kowa daga cikin ku, ku bace min dagani yan zunnan shashashai kawai." Dukkansu jikinsu ya yi sanyi gwiwoyinsu sam babu kwari suka juya 101 ALAWIYYA WADA ISA-'YAR ALJANNA CE sim-sim suka nufi waje, shi kuwa Alhaji cikin dakinsa ya koma yana faman huci tamkar zaki. Haka zai zi ya wucesu a tsakar gida cike da dacin rai hannunsa rike da mukullin mota fuskarsa sam babu sauran annuri, idanuwansa tuni sun kada sunyi jawur, kai tsaye wajen motarsa ya nufa ya tadata a fusace ya fice da gudu. Ita kuwa Lami tamkar dama jira take ya fita ai kuwa sai ta nufi kofar dakin Sadiya wacce ta nufi sashenta tuntuni, ta tsaya a kofar sashen nata ta rike kugu tana fadin " Ina kike munafuka kin shige daki kina dariyar farin ciki ko? Burinki ya cika kin tarwatsa min kwanaki na d azan yi da mijina, dama abin da kike wa bakin ciki da kishi kenan, to wallahi ina tabbatar miki da cewar bashi kia 6 102 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE dauka don lowa yaci tuwo dani wallahi miya yasha mai barkono ma kuwa." Da sauri Sadiya ta bude kofa ta fito tana huci, ta galla mata harara sannan ta amsa mata da cewa "Ke Lami ki dubeni da kyau, kin san baki isa nayi maki kyashin akan miji ba, domin banga abin da zan yiwa kishin ba a tare da ke." Ran Lami ya kara baci, ta yi dariyar bacin rai da mugunta sannan ta ce, "Shiyasa naga kina bakin ciki da ranar kwanana har kina kasa bacci, da sassafe kina shigo mana, wa ya sani ma ko har laße kike yi mana?" Sadiya ta kara fusata ta damko wuyan Lami sannan ta ce, "Yanzu kuwa za kici na Jaki." Dukkansu zasu fara kokowa kowacce na kokarin huce haushinta jikin 'yar uwarta. Mero dake shara a tsakar gida ta jiyo su ta nufosu 103 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CЕ hannunta rike da tsintsiya tana fadin "Af ke Lami baki san Sadiya tana yi miki labe ba? Ai kullum in kina girki a tafe take kwana, ta je ta labe ta dawo ta shiga daki, haka take fama har gari yaw aye, abin da tyasa bana gaya miki sabida bai shafeni ba kar ace na hada fada. Da kyar ta kwato kanta daga hannun Sadiya ta nufi inda Muciya take ta dauko ta nnufo Sadiya da ita gadan gadan tana huci tana fadin. "Wallahi tunda kika: tarwatsa min farin ciki na yau sai na tattaka ki." Da sauri Sadiya ta dauko Rodi ta nufo Lami itama tana fadin "Kafin ki illatani ke, ni bara na fara illataki mu zuba dan halak ka fasa..." Sallamar Inna Laure ce ta katse ta, tana ganinsu da makamai a hannu, ta nufi Sadiya a rude ta kwace Rodin tana fadin 104 ALAWIYYA WADA ISA- ‘YAR ALJANNA CE "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un, Sadiya me ya kai ki ga aikata haka? Ai wannan ba shine makaminki ba sam bai dace dake ba, fada da kokawa ai ba naki ba ne Sadiya." A fusace Sadiya ta ce, "Inna wannan 'yar rainin hankalin ce da sassafen nan take neman bala'I dani ta dagulamin lissafi." Lami ta kalleta shekeke cike da tsiwa ta ce, "Ga rainin hankali nan a tare dake, da sassafe an zo mana gida ko karyawa ba mu yi ba. Sai yanzu na sake tantance inda kika koyi zuwa dakin mijin mutum da sassafe ashe iyalan sammako ne ban sani ba." Da sauri Mero ta amshe "Kamar kin shiga zuciyata cam abin da nake so na ce kenan, bamu isa mu sake a cikin gidanmu ba sai a doka mana uban sammako haka." 105 ALAWIYYA WADA ISA- 'YAR ALJANNA CE Lami ta harareta ta gefen ido gamida kwabe baki tana nunata da muciyar dake hannunta "Dallacan rufe mini baki, ca na yi maki'ina neman mai tare mini zaki wani sako mini bakinki, ki kalleni da kyau babu wanda nake shayi a gidannan warki nake daidai kugun kowa don haka ki kama bakinki, tunda ba dole akeyi ba, tun dazu sai wani shisshigewa kike yi kina so ki ce zaki tare mini. Ta saki wani wawan tsaki. Ita kuwa Mero tsayawa kawai ta yi tana kallonta, ta tabe baki ta girgiza kai sannan ta koma gefe tana kallonsu. Itama dai Inna Laure mamakin ne ya cikata kallonsu kawai take yi domin bata san me zata ce ba. Sadiya ce ta fizge hannunta da ga hannun Inna a fusace ta nufi Lami tana fadin "Mahaifiyar tawa kike gayawa 106 ALAWIYYA WADA ISA. ‘YAR ALJANNA СЕ haka? Yau idan banga jini ya yi miki ado a jikinki ba hankalina ba

Chapter 3 of 4