Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
ta tashi zata tafi, dan haka Mummy ta fita yi mata rakiya, yayin da shi kuma ya zauna a gajiye, yunwa da gajiya na cin shi. Sai ya laluba wayar shi yana neman layin Naja'atu ta fito ta bashi abin shi. Mummy ta shigo ta zauna, ta ce "Sai yanzu?" Ya lumshe ido cike da gajiya ya ce 'Wallahi kuwa, motoci sunyi yawa a wajan wankin, duk can na 6ata lokaci na." 47 Layin Naja'atu da yake nema shine bai shiga ba, ya sakc kira a karo na biyu, nan ma shiru. Dan haka ya rufe wayar yana kallon Mummy ya ce "Wai yaran nan basu gidan ne?" Mummy ta ce "Wai sun je saloon nc, daga can zasu biya gidan A'isha su karbo mani sako, hala abinci zata zo ta baka?' Ta tsare shi da idanuwa. Sai yayi murmushi yana shafar kai. Ta се "Nema dai kake kai maida mani diya 'yar aikin ka ko?" Yayi dariya ya ce "A'a Mummy ba haka banc." Та сe "To fadi mani menene? Dama akwai maganar da nake son yi da kai, kada ka 6oye mani, ka fadi mani gaskiya, me ke faruwa tsakanin ki da Naja'atu?" Shima ya zuba mata ido yana murmushi, to amma shi baiga dalilin da zaya sanya ya tsaya wani boye-boye ba, ya jinjina kai ya ce "Mummy idan zaki tuna kwanakin baya kin taßa yi magana kan cea ko zani nemi Naja'atu ne?" Ta ce "Uhm." Ya се "То gaskiya Mummy son ta nake yi, kuma auren ta zani yi." Dariya ta kusa kubce mata, saboda yanayin da yake maganar, amma ta dake ta ce "Ita Faridar kayi yaya da ita, gashi ka ce kai mijin mace daya ne?" Yayi murmushi ya ce "Wannan ta wuce, maganar gaskiya nifa da gaske nake." Ta ce "Naji da gaske kake, na ce ita Farida fa?" Ya cc "Maganar ta tana nan, idan na aure ta daga baya zani auri Naja'atu, kuma munyi wannan maganar da ita ta amincе." Та се "Ita Naja'atun ta yarda ta zauna jiran ka sai ka auri wata sannan daga baya ka aure ta?" Ya ce "Eh Mummy." 48 Ta jinjina kai ta ce "To ni ban amince ba, kuma ina son ka rabu da yarinyar mutane, kada ka yaudare la, ka barta tayi auren ta." Daddy ya girgiza kai, ya се "Allah kuwa Mummy da gaske nake, babu yaaudara tsakani na da Naja'atu har abada." Ta daure fuska ta cc "Watau so kake yi ka watsa mani kasa a ido ko?" Ya ce "Mummy kamar yaya?" Ta cc "To ni dai nasan matsawar Farida taji zaka auri Naja'atu bayan auren ta, ba zata yarda ba, ita kuma wannan ka zo ka rabata da mai sonta, a zo abu yha ki yin dadi, wa kunya zata karem mawa?" Ya saukar da ajiyar zuciya yana kallon ta. Yaа се "Mummy nifa mijin mace hudu ne, kiyi hakuri ki yarda da maganar nan, Allah kuwa babu yaudara ko makamancin haka a ciki, idan kika ce dole in rabu da Naja'atu kin dora mani aiki babba, saboda ban san yanda zanyi da kaunar ta ba, ni kaina ban san lokacin da kaunar ta ta dasu cikin zuciya ta ba, kiyi hakuri Mummy." Та се "То amma Daddy kai ka baribida baya, sai da nayi maa magana kan yarinyar nan, ka ce ba haka ba, sai yanzu da abubuwa suka rikice sannan zaka bullo da wata magana, to ni dai na fada maka bani so, ka rabu da ita ta ta samu miji tayi aurenta, an fada maka tara mata sauki ne?" Ya karkace kai da sigar lallashi, ya ce "Mummy na sani ba sauki bane, sai dai ban san yanda zani yi da kaunar ta ba, ki ci gaba da yi mana addu'a, insha Allahu komi zaya warware." Babu 49 yanda za tayi dole ta rabu dashi. Sai dai har cikin ranta ba'a son ranta ba. Amma da daddare mai wanki ya shigo da kayan guga na Hajiya, Naja'atu ta karba ta shigar mata dasu, Hajiyar na zaune ta gama sallar isha'i tana lazumi. Tayi sallama ta shiga da kayan, sannan ta bude dirowa tas hirya mata su. Tana shirin fitowa ta daga kai tana kallon ta, ta ce "Zo nan Naja'atu, zauna magana zanyi dake." Taji zuciyar ta na bugawa da sauri, duk sai ta tsorata, jikin ta babu karfi ta zauna tana kallon Mummy, yayinda ita kuma ta ida shafa addu'a. Sannan ta juyo tana fuskantar ta, tare da "Wata tambaya nake son yi maki, kuma tsakanin ki da Allah kada ki 6oye mani ki fadi mani gaskiya. Me ke tsakanin ki da Daddy?" Da farko tambayar ta bata tsoro har ta rasa abin da zata ce, to sai dai kuma da matsayin Mummy a gare ta ya wuce ta boye mata wani abu, don haka ta sarda kai tana wasa da zoben azurfa dake manne a hannun ta. Ta ce "Sona yake yi." Mummy ta jinjina kai ta ce "Kuma kema kina son shi?" A hankali ta daga mata kai. Mummy tayi murmushi ta ce "Hakan ba laifi bane, sai dai baki yi mani wayau ba Naja'atu, keda saurayi yana son ki, kuma daidai gwargwado yana da na kanshi, ga ilimi yana dashi, sai ki tsaya kina jiran Daddy, dake shirin auren wata?" Ta ce "Mummy nima ya ce aurena za yayi." Tayi murmushi ta ce "Na sani, amma ba wai bani sonki da Daddy bane, kinga ni na haife shi, kuma 50 bry sonanhi, fetoj soo dilk albeshkoyavanicikimefalayi imanavktn albei asparsebodai dari hisa dari namaprekiakan rcn Farida lo ammahze podusan Ji kin shiga wanihali pnawyyasi babana in pata kuma hada zaya su, ta sonkle yan s cikin kwanakin iya.aurcen ta kısamu ya hada ku biyu, tunda namyi yake, saı nutsuwa da Dr Khalid vana samun dai ifa kanta can bangaren yarınyar zata. yarda ayi mata sosai sa kişhiya dake yan watanhi ta yin auren su? Ko l a VA i kamar deZe ki haka idan kika tsaya ya tafi ganm Hniixei bayaninda balainkishi sakiyihm ajayki mashirafatata Kllanidi.daga togaata kataadamla badayr, skineawsanyahafeukiinujim zukiaciygabawda Mmamiya taa yraşinshekargakian jirarashi?" amma ya tabbataramata tdiii cowalkaddabbasanabultwaruwda MsmanAllaHudemaskinn aesho tahdaivana klavida Kanarahar mpted Tewavir shi ta keiy muddinnla rabu shiga damu Ratten Bridatashi grdall Ran ER THE P eaniy cikin halin dae ma funda fatan Mummy alkairi. ta kawo hujjojin ta tasan dole ne tayi bıyayya Zainaq ta fito suka ci gaba da hrar gare ta, tunda tasan ba zata cuce ta. ba, ko kuma ta Su. cuci Den danta, haka gaskiya-ta Hauva ta koma cikin daki ta basu tada, saf ta rinka jin, tausayın W Har suka game hirar su Daddy bai dawo ba, hakarMRaw ury shaihinarau, feredaRaiwaPbani sonki da Daddy bane Naja'taingdba halia hangehniwkir dokakadHa mtsDdalyubagannykanikakayaudawouyalngmehiihgn Najayithakası yayfama baridmakaakiakuinazhaizbya otbin bauvkamsakgidsuromvoná magánernagudäishaие 63 ce maganar Farida tana nan, daga baya ne zaya aure ki, shi kuwa Khalid jira yake yi kowane lokaci kice kin shirya ya aure ki, to sai ki tsaya jiran wanda shi kanshi baisan tsawon lokacin da abun zaya dauka ba? Kilama daga baya ya zo ya ce ya fasa." Naja'atu ta dago kai tana kallon ta, ta ce "Kwarai kuwa kadan kenan daga halayyar maza." Sai taji tsoro, ta saukar da ajiyar zuciya, ta ce "Shi kenan Mummy na fahimta, zaniyi kokari in rabu dashi." Tayi murmushi ta ce "Yauwa, sai ki kwantar da hankalin ki, ki tsaya kan Khalid ku fahimci juna, insha Allahu zaki ga hasken abun." Ta jinjina kai sai ta sanya hannu ta goge fuskarta. Mummy ta sallame ta ta taso ta fita. Da wuri taje ta kwanta, sabi da bata son su zauna hira Daddy ya tsare ta, don haka ta shiga daki tayi kwanciyar ta, zuciyar ta cike da tunani iri-iri, ta kulla wannan ta kwance, bata san yanda zata yi ta raba zuciyar ta da kaunar Daddy ba, ko da can da bai fito ya ce yana sonta ba, ta kasa hakura dashi, balle kuma yanzu da ya hure mata kunne da kalamanshi na soyayya masu dadi, bata ki ace koda yaushe tana tare dashi ba yana jifarta da mayatgaccen kallon shi, yana tsananin yin tasiri a kanta. To sai dai tasan dole ne tabi umarnin Mummy, bata son ta saba mata. Hawaye ta rinka yi sosai, tun tana kukan zuci har ta kai ya fara fita, saukin ta daya da yake ita kadai ce cikin daki, sai tayi mai isarta, a karshe ta hakure ta barma Allah komi. Zainab ta shigo cikin dakin tana 52 kallon ta, amma ita Naja'atu sai ta lumshe ido kamar tana barci, dan haka tayi tsammanin tayi barcin, ta juya tasanar da Daddy ccwa barci take yi, dama shine ya turo ta kiran Naja'atun yaji ta shiru, kuma ya kira layin ta shima a rufe. Da ta kuma ta sanar dashi ya zuba mata ido cike da damuwa, ya ce "Kin tabbata lafiyar ta lau kuwa?" Zainab tayi murmushi ta ce "Allah kuwa lafiyar ta lau, ta ce mani barci take ji zata kwanta da wuri." Ya jinjina kai bai sake magana ba. Ba'a jima ba aka kira wayar Zainab din, ta dauka ta duba sai taga Dr Khalid ne, tayi murmushi ta amsa mashi da sallama. Ya ce "Zainab me ke damun Naja'atu ne, ina ta kiran layin ta tun dazu na gaza samu?" Tayi murmushi ta ce "Lafiya lau, ta kwanta ne da wuri, ina jin layin a rufe yake." Ya ce "To ki bata wayar ina son in ji muryar ta atleas in samu peace of mind." Ta kyalkyale da dariya, ta ce "Yes sir." Sai ta tashi ta nufi dakin, tà shiga ta dan bubbuga Naja'atun, ta dago kai tana kallon ta. Ta ce "Dr ne ya a waya duk kin rikita shi, kin kama waya kin rufe." Ta amshi wayar, tayi mashi sallama. Zainab ta fice tana yi mata dariya. Yayin da ita kuma ta tashi zaune tana gaida shi, yanzu kam dole shi zata rike tunda tasan ba zata samu Daddy ba. Ya saukar da ajiyar zuciya, ya ce "Naja'atu me yasa kike son wahalar dani ne? Kin san tsawon lokacin dana dauka ina neman layinki ban samu ba? Gashi na kwanta amma na gaza samun barci saboda banji muryar ki ba." Ta ce "Kayi hakuri don Allah, kaina ne yake yi 53 mani ciwo nasha magana na kwanta." Ya cc "Ayya sorry nayi tsammanin baki da loakaci na ne, in ce abun har ya kaimu ga haka? Banda sauye-sauyen da nake fuskanta daga gare ki ace har an fara rufe mani waya, wai dan Allah Naja'atu me yake faruwa ne?" Ta kwantar da murya ta ce "Allah kuwa babu komi." Ya ce "To amma yanda kike sakin jiki dani kwanakin baya yanzu bani samun shi, wani laifi nayi?" Ta ce "Ai baka laifi waje na, balle kuma iya sani na babu wani abu." Ya ce "Na amince dake, gobe insha Allahu zan dawo, zan zo muyi wata shawara mai muhimmanci." Та се "To Allah ya kawo ka lafiya, na gode Allah ya bamu alheri." Yayi murmushi ya ce "Na gode Naja'atu, kinga irin abubuwan da kika saba mani dasu, shi yasa duk dare idan banji muryar ki ba ba zani iya runtsawa ba, yanzu haka barcin nake ji, amma rashin jinki ya sanya na kasa barci." Та се "To ka kwanta kayi barcin ka, sweet dreams." Sai ta rufe wayar tana murmushi. Dagowar da zata yi sai taga Daddy tsaye a kanta ya zuba hannuwa cikin aljihu, fuskar shi a daure yana kallon ta. Duk sai ta tsorata, ta aje wayar gefe daya tare da sarda kanta. Tsahon lokaci sukayi shiru, sannan ya saukar da ajiyar zuciya, ya ce "Kinyi daidai." Bai sake magana ba ya juya ya fice. Hankalin ta ya kara tashi, sai ta koma ta kwanta, bata san yanda zatayi ba, domin ko ta fito ta bishi, sai taga yanda ranshi ya baci idan ta haye mashi wulakanta ta za yayi, dan haka ta rabu dashi din ya fiye mata sauki, 54 kada ta kara ma kanta wani zafin, ko da yake ko ta tashi ta bashi hakuri tasan dai dole rabuwar za suyi, dan haka hakurin da zata je ta bashi ma ba za yayi wani tasiri ba. Da kyar ta samu ta runtsa, hankalin ta ya tashi sosai, tunda Allah ya halicceta bata taba shiga mayuwacin hali ba irin haka, sai taji gabaki daya ta tsani zaman ta Abujar, idan gidan su ne ba zata fuskanci matsaloli irin haka ba, sai ta rinka ganin laifin Daddy, ita dai iya tunanin ta bata yi mashi laifin komi ba, bai san cewa ita ta fishi damuwa ba, shine za yayi fushi da ita. Da safe ma har rana tayi sosai tana cikin daki bata fito ba, tana ta shirya kayan su na sanyawa. Zainab ta shigo tana harararta, ta ce "Ki tashi ki fita kiyi ma Daddy hidimomin shi, kin shagwaba shi komi sai kinyi mashi, yanzu tunda na fita baibar ni na huta ba, sai ya ce inyi wancan da na gama kuma ya се wannan." Naja'atu ta kalle ta tana murmushi, ta ce "To ai kin samu lada ko?" Ta ce "Wace lada? Tunda duk abin da nake yi bai san inayi ba, komi nayi sai ya ce baiyi mashi ba." Naja'atu tayi murmushi kawai. Sai ta taso ta fito, can ta hango shi bisa teburin cin abinci yana kalace, bata yi mashi magana ba, ta shiga dakin Mummy ta gaida ta, sannan ta fito ta nufi inda yake. Ko kallon ta baiyi ba har ta isa, ta dan dafa kujera ta ce "Ina kwana?" Ya zuba mata ido yana kallon ta fuskar shi babu walwala. Sannan ya amsa kamar dole, sai tgaji zuciyar ta ta dan taßu, ta tsani a 55 dauri mata fuska, musamman nashi da yafi komi saurin tayar mata da hankali, amma da yake ta saba da halinshi bai iya fushi ba, baya iya boye damuwar shi. Sai ta sassauta tana kallon shi, ta ce "Daddy fushi kake yi har yanzu?" Ya jefe ta da muguwar harara, ya mike a fusace ya nufi dakin shi. Naja'atu tgayi tsaye sororo tana mamakin fushin Daddy, sai ta jinjina kai ta koma cikin falo ta zauna. Bai jima ba ya fito, daidai nan aka kira wayar shi ya tsaya yana magana. Farida ce akan wayar. Naja'atu ta zuba mashi ido cike da tsana, tana jin matsanancin kishi a zuciyar ta. Ya ce "Kiyi kokari ki shirya zani fito yanzu muje, ina son in dwo gida da wuri." Naja'atu ta runtse ido kamar za ta fasa kuka, tana jin shi ya zo ya rabata ya fice, sai ta bishi da ido har ya fita, sannan ta jinjina kai. To amma sai zuciyar ta tayi sanyi sam bata damu da abin da yayi ba, tasan dai dole rabuwa za suyi, kuma ko kwanciya zata rinkayi Kasa yana taka ta sai ya shiga wannan damuwar, don haka ta kudurfe zuba mashi ido kawai ba zata sake shiga harkarshi ba balle yayi mata wulakanci, matsalar Daddy kenan bai iya bacin rai ba. Har yamma bai dawo gidan ba, sai taji dadin haka, kara shi da kanshi ya juya mata baya sai su rabu cikin ruwan sanyi. Da maraice ita Zainab suka fita zuwa gidan Aunty A'isha, daga can zasu shiga super market suyi saye-sayen kayan amfani a gidan. Da suka isa gidan Aunty A'isha ta rinka kyalkyar dariya, ta ce "Dama yanzu nake shirin tura direba ya dauko 56 mani ke Naja'atu, Daddy bai jima da barin gidan nan ya kawo mani karar ki." Sai taji zuciyar ta tana bugawa, ta tsani ko sunan Dadday taji an ambata, so take yi da karfin tsiya ya yakuce shi. Zainab tayi dariya ta ce "Ai dama zuba mata ido nayi tun jiya na lura babu jituwa tsakanin su, amma ta rinka kokarin 6oye mani, Naja'atu kin cika zurfin ciki." Naja'atu tayi murmushi kawai. Suka zauna A'isha ta umarci Zainab ta shiga kicin ta ida hada mata girkin da ta keyi, yayin da ta zuba ma Naja'atu ido ta ce "Daddy ya kawo mani karar ki cewa kin canja mashi, yanzu ko magana baki son yi mashi, kuma baiyi maki laifin komi ba." Naja'atu tayi murmushi ta ce "Aunty A'isha rabu da Daddy rigimar shi tayi yawa, matsalar shi daya ce ya cika zafin kishi da saurin fushi, ni banga laifin da nayi mashi ba, ina cikin daki Zainab ta kai mani waya ta Dr ne ya kira, ina magana dashi ban sani ba ashe ya shigo cikin dakin, da na gama magana ne na ganshi, sai cewa yayi na kyauta ya juya ya fita, tun daga nan ya dauki fushi dani ko da na gaidashi da safe da kyar ya amsa mani, da nayi mashi tambaya sai kawai ya tashi yayi tafiyar shi cikin dakin shi, kuma ina zaune ya zo ya rabani ya fita ko kallona baiyi ba, to yaya yake so inyi?" A'isha tayi murmushi ta ce "Nasan halin Daddy da saurin fushi, don haka sai kin rika yin hakuri, sai abu na biyu, ya ce baya son yaga kina kula Dr Khalid, ranshi 6aci yake yi, to sai dai da kaina na bashi amsa. Gaskiya banji dadin yanda kika yi saurin amsa 57 maganar Daddy ba, ke kiyi tunani mana, idan dai sonki yake ya donmi ba zaya hakura da auren Faridan ba, tunda ai ba daura masa aure akayi ba, don ya raina ki sai ya ce ki jira sai ya auri wata sannan ke ya aure ki, ke kuma har kin yarda da haka, sai kace shine autan maza. Me Daddy ke dashi wanda Dr baya dashi da har zaki yarda da wannan rainin wayau? To sai dai na gaya mashi idan dai ke yake so to ya tsaya a kanki, idan kau ya ce sai ya auri Farida to wallahi ba sonki yake yi ba sai kiyi ta kanki." Naja'atu ta jinjina kai ta ce "Na ruga na fidda maganar Daddy a raina, kamar yadda kika fada mani haka Mummy ta fada mani, kuma na yarda, don haka sai ku tayani da addu'a Allah yayi mani zabi mafi alkairi." A'isha ta ce "Insha Allahu, kuma sai ki kama kanki ko auren zaki yi zaya fi ganin ki da mutunci, amma matsawar ya fahimci cewa kina son shi sosai, da kuwa ya rinka wahalar dake kenan, matsala ce babba mace ta nuna ma namiji matsanancin so, har kara ki bari nashi yafi naki." Naja'atu ta jinjina kai ta amince da abin da suka fadi mata. Dr Khalid ya kira ta ta waya, sai ta tashi ta fita, sannan ta amsa mashi. Ya sanar da ita ya iso lafiya, don haka zuwa dare yana nan fitowa. Ta ce "To Allah ya kawo ka lafiya." Ya ce "Me kika tanadar mani?" Sai tayi murmushi ta ce "Sai ka iso dai." Su kayi sallama ta dawo ciki. Zainab nayi mata tsegumin ta cika jin kunya. 58 Basu dade ba suka fito suka yima Mummy saye- sayen ta, suka koma gida. Motar Daddy na nan, amma da suka shiga ciki basu ganshi ba, don haka Naja'atu taji dadi, hakan yafi mata sauki, kara ta rinka nesa- nesa dashi. Da Dr Khalid ya iso ta fita ta same shi zaune waje, da fara'ar shi ya tarbeta, sai taji duk wata damuwarta ta yaye Khalid abin so ne ga duk wata macen da ta san ciwon kanta, haka nan daga ita har yaransu zasu samu kyakkyawar kulawa, sai ta rinka gode ma Allah cikin zuciyar ta da yayi mata baiwa da samun masoyi kamar shi. Kamar kullum, hirar su cikin nutsuwa da ma'ana, sai da ya tattara hankalinta gare shi sannan ya fuskanci ta sosai, ya ce "Maganar da nace maki ina so muyi, ko kin manta?" Tayi murmushi ta ce "Tana raina, naji baka ce komi bane shi yasa na kyale ka." Yayi murmushi ya ce "Dadina dake kenan kin cika jan aji." Ta ce "Babu zancen jan aji anan, kaifa kace zaka zo muyi wata magana, to kuma ka zo baka ce mani komi ba, sai in tambaya? Tunda ban san abin da zaka ce mani ba, na sani ko cewa zakayi-zakayi aure." Yayi dariya yana kallon ta, ya ce "Aure da wa Naja'atu?" Ta ce "Na sani ko kana da wata budurwa a Kano." Khalid ya rinka dariya, ya ce "Ban taba sanin kina da kishi ba Naja'atu sai yau, in banda abinki ina naga wata budurwa? Ke kadai ce kwallin kwal, kuma baki da kishiya." Dadi ya rufe Naja'atu. Ta ce "Cika baki dai, kada fa na shiga da wata daya ace mani za'a 59 cika alkawarin da akayi ma wata?" Ya zuba mata ido ya cc "Idan haka ta faru yaya zaki yi?" Ta daga sama tana tunani, sannan a hankali ta zuba mashi ido, ta се "Allah kuwa ba zani zauna ba gidanmu zani koma." Ya ce "Ni kuma ba zani iya hakura dake ba, kinga kau zancen inyi maki irin abin da zuciyar ki bata so bai tasò ba, bari kiji in gaya maki, ni ra'ayina daban yake dana sauran maza, Allah bai zuba mani jarabar dake din nan ba zaki isheni ba, da har zani tara mata da yawa, burina kawai mu fahimci juna, ta yanda zamu ba 'ya'yanmu tarbiya mai kyau, su tashi cikin rayuwa mai albarka, bawai in tara mata ba suyi ta haihuwar 'ya'yan, ta yanda ba zani iya sauke nauyin su da Allah (S.W.T) ya dora mani ba, a karshe ma su dawo suna tsine mani." Naja'atu ta jinjina kai tana murmushi, sai taji ya burge ta, ko ba komi ya nuna yana da zurfin tunani, ita kanta tana yin wannan tunanin akan Daddy da yake neman hadasu su biyu ita da Farida, alahalin shi kanshi shekarun shi ba wasu bane, a ganin ta bai isa hada mata biyu ba ya rike, to sai dai kaunar shi data dauka ta dasa ma zuciyar ta ita ke wahalar da ita, ta yanda bata ganin aibunshi ko kuma hangen abin da zaya faru matsawar zata same shi. Khalid ya gyara zama yana kallon ta, ya ce "Mu koma kan tushen maganar mu, shawara ce za muyi, kuma ina son ki taimaka mani don muga komi ya tafi yanda nake sonshi. Watau kwanakin baya gwamnati ta dauki likitoçi hamsin cikin fadin kasar nan, inda ta 60 tura su kasashen waje su kayi kwas akan 6angarori da dama, yanda idan suka dawo zasu ci gaba da taimaka ma al'umar kasar ta yanda za'a samu saukin kashe kudi wajan fidda marasa lafiya waje, kinga wannan ba karamin ci gaba bane, to yanzu ma kashi na biyu za'a fidda, kuma ina sanya ran cewa ina cikin wadanda za'a tura, sai dai kwas din duka na wata tara ne, kuma gaskiya da ci gaba ne sosai, don haka nake son muyi magana ta fahimta dangane da lamarin mu." Naja'atu ta jinjina kai ta ce "Gaskiya ci gaba ne sosai, Allah ya tabbatar da alkairi." Ya zuba mata ido ya ce "To yanzu yaya kike ganin za'ayi?" Tayi murmushi ta ce "Kai wane tsari kayi?" Ya ce "Abin da na kasa shiryawa kenan, don bukatar ki ina bukatar ki kusa dani, ko da yaushe, to sai dai idan nace muyi aure kafin mu tafíi, ko na tafi hankali na ba zaya kwanta ba, saboda kinga halin da nake ciki, iyayena sun rasu balle in ce in barki hannun su, idan kuma na tafi na barki abubuwa zasu rinka wahala, kuma gaskiya ni ina da tsananin kishi, ba zani iya barin amanar ki hannun wani aboki na ba, mutane basu da tabbas yanzu, duk wanda kace zaka bashi kayan ka, to nema yake yaga bayan ka, don haka kikaga ban taba kawo wani aboki na wajan ki ba, yanzu ma kenan balle kuma munyi aure kina matsayin matata, ba 61 zani iya barin ki hannun wani wanda ba jinina ba, kinga nan ma akwai matsala. Haka nan ina shakkun in tafi in barki ba muyi aure ba, kina ganin za'a barki har zuwa lokacin da zani dawo, to kuma ke zaki iya jira ne?" Ya ci gaba da kallon ta yana son yaji abin da zata fada. To ita kanta bata san abin da zata ce ba, sai dai hujjoji da ya kawo suma abin dubawa ne. Ta jinjina kai ta ce "Shi kenan zanyi kokari inga na jira, kaima fa ka rike alkawari?" Yayi murmushi ya ce "Ni ke nafi ji Naja'atu, insha Allahu zaki same ni mai alkawari." Ta ce "Sannan ina son ka samu lokaci muje Katsina kayi magana baki da baki da Baba, idan ya amince shi kenan, saboda yana yawan yi mani maganar aure." Ya jinjina kai ya ce "Nima dama nayi tunanin yin hakan, don haka kada ki samu damuwa idan komi ya kankaman zani fidda lokaci sai kiyi mani jagora." Tayi murmushi ta ta yanda ta tsara shi. Da zaya tafi ya fiddo mata tsarabar Kani, tayi godiya, su kayi sallama ya tafi. To kuma bayan kwana biyu da yin maganar, yana ofis ya kirata yana yi mata albishir din magana ta tabbata, ta taya shi murna da fatan alkairi. Yanzu kam hankalin ta ya karkata ga Khalid, saboda har yanzu Daddy fushi yake yi da ita, ko zama gidan baya yi, idanma yana gidan 62 baya zama falo, ko da yaushe yana cikin dakin shi, kwata-kwata ta daina ganin sakin fuskar shi, to itama sai taja jikinta, idan ma taga lokacin fitowar shi tayi sai ta tashi tabar falon, ko hanya bata hada su, ta tabbar baya ra'ayinta, don haka cikin kwanakin ta samu nutsuwa da Dr Khalid, yana samun kanta sosai, sai ya rinka jin kamar bazaya iya tafiya ya barta ba. Da yamma da izo ciki ta shiga dashi, yayi ma Hajiya bayani da bakin shi. Tayi murna, sannan atayi mashi fatan alkairi. Ya gabatar mata da bukatar shi cewa ayi hakuri, auran su sai ya dawo. Mummy ta jinjina maganar a ranta, amma ya tabbatar mata da cewa kada ta samu damuwa, insha Allahu zata same shi mai rikon alkawari, kuma ya sanar da ita cewa "Yana so suje har can Katsina gidan su Naja'atun yayi magana baki da baki da iyayen ta." To sai ta amince tayi mashi fatan alkairi. Zainab ta fito suka ci gaba da hirar su. Don haka Hajiya ta koma cikin daki ta basu waje. Har suka game hirar su Daddy bai dawo ba, hakan yayi mata dadi, don haka suka sake suka sha hirarsu tare da Zainab. Zainab ta rinka saha'war soyayyarsu, cikin nutsuwa

Chapter 4 of 5