Ya yi murmushi ya ce,
"Doctor ne, na ce ya shigo ciki, ya ce a'a." Kunya ce
ko mi, duk sai ta ji ta takura gashi Mummy na wajen,
don haka ta kasa ce mashi komi.
Mummy ta yi murmushi ta ce, "Wai ke Naja'atu
wace iri ce? Idan ba ki sake a gidan nan ba, sai
yaushe? Tashi ki shigo dashi don mi za ki rinka aje
mutum waje? Wannan ba kima ba ne." Jikinta ya yi
sanyi, ta mike ta shiga cikin daki, ta dauko mayafi ta
fita zuwa wajen. Yana tsaye jingine da mota, rike da
waya yana magana, don haka da ta isa sai ta tsaya
gefe guda minti daya ya yi sallama ya rufe wayar
yana kallonta, sai suke yi murmushi ba ki daya ya се,
"Naja'atu yaya gari.?" Ta ce, "Alhamdulillahi, ka yini
lafiya.?" Ya yi murmushi yana kallonta ya ce, "Lafiya
lau sai alkairi." ta ce "ka shigo daga ciki." Ya ce, "Tun
yanzu Naja'atu.?" Ta yi murmushi ta ce, "To meye?
Mummy da kanta ta ce ace ka shigo."
16
Ya yi murmushi gaskiya ya ji dadi har cikin ranshi, alamun samun nasara kenan." Don haka ta shiga gtaba yana biye da ita har cikin falon, yau kuma
ya yi shiga sosai, ta boyel fari sol, yana daukar ido, shigar ta sauka kasa sosai, da hula kube, ya yi kyau daidai gwargwado ba ya da makusa don haka itama
Mummy ta yaba dashi, suka gaisa cikin mutunci,
sannan ta tashi ta koma cikin daki, ba'a jima ba ki kira
Naja'atu ta shiga, ta ce "Ki shiga kicin ki samo mashi
abin da zaya ci." Ta yi murmushi ta fito ta bashi hakuri, sannan ta shiga kicin cin ta yi tsaye tana
tunanin me zata ba shi, sai ta bude firij ta fiddo lemun
kwali ta aza kan faranti da kofi ta bude wani bokiti ta
debo cake din da suka yi ranar demick ta zuba a filed
ta hada ta dauko ta fito.
Yana zaune hankali kwance ta yi sallama ta aje gabanshi bisa tebir, ya zuba mata ido a hankali ya ce
"Na gode." Ta yi murmushi ta duka tana fasa lemun,
ta zuba mashi a kofi sannan ta koma ta zauna ya dube
ta farin ciki cike da zuciyarshi, ya ce "To ai ni Naja'atu duk kin rikita ni, na ma rasa ta ina zani fara."
Та се, "Me aka yi.?" Ya jinjina kai ya ce, "Meye ma ba'ayi ba, kin karrama ni da yawa na ji dadi kuma na
gode Allah yasa tafiya ta yi tsawo." Ta ji nauyinshi
tana murmushi ya dauki lemun yana kurba a hankali,
sai ya rike kofin ya kirata. "Naja'atu." Ta dago kai
tana kallonshi, ya ce "Kina ganin kin amince dani in ci gaba da zuwa.?" Ta yi shiru, ya ce "Magana za ki yi, ni dai Allah yasan manufata akanki, fatana Allah
17
S
ya hada kanmu in ga mun zama mata da miji, muna
raya sunnar Manzon Allah, don haka ki saki jiki muyi
magana ta fahimta, kada ki ji shakkun komi ki fito fili
ki fadi mani abin da ke cikin ranki, ni kam na gamsu
dake kuma nasan nayi zae mai kyau, ban sani ba ko
ke kina da wani ra'ayin daban."
Ta yi murmushi ta ce, "Haka ne, sai dai kamar
yarda na fadi maka ina son mu samu lokaci mu
fahimci juna, kafin maganar aure ta shigo, kasan komi
a hankali yafi." Ya ce, "Haka ne, yanzi kina jin in ci
gaba da zuwa ko kuwa so kike yi in daga maki har sai
kin gama nazarin.?" Ya tsare ta da ido, sai taji
nauyinshi, ya cika saurin karya mata zuciya, ta yi
murmushi ta ce, "Babu damuwa, zaka iya zuwa."
Daidai lokacin Daddy ya kunno kai cikin falon,
bai lura da abin da ke faruwa ba, sai da yazo tsakiyar
falon, sannan yaga Dr. Khalid, bai san dalili ba, sai ya
ji wani irin faduwar gaba da tsananin kishi. Dr. Khalid
ya mike da sakin fuska ya mika mashi hannu suka
gaisa haka nan ba don Daddyn yaso ba, cikin hikima
ya yi satar kallon Naja'atun ya sakar mata wata
muguwar harara, sai tasha jinin jikinta, bai ce mata
komi ba, ya raba su ya shigc dakinshi, sai ta saukar da
ajiyar zuciya, tana kallon Dr. Khalid shima kallonta
yake yi bai ji dadin yarda ya karbe shi ba, ya koma ya
zauna yayin da wajen ya dan dauki shiru, sai ya yi
gyaran murya ya kirata "Naja'atu." Ta zuba mashi ido
ya ce "Kiyi hakuri da ni kada ki yi tsammanin ina
neman takura maki, ki fadi mani yaya kikc da wannan
18
mutumin.?"
Ta yi murmushi ta ce "Daddy dan gidan nan ne." Ya ce, "Kc fa.?" Ta zuba mashi ido, ta ce "Ni ce bare
a gidan, mahaifiyata ce 'yar'uwar Mummy, don haka
ta dauko ni ina zaune tare da ita asalinmu 'yan Katsina ne, kamar yarda ka sanar dani mahaifanka Talakawa
ne, to nima haka nawa suke, mahaifina Masinja ne, sai
dai ni ban sha wahalar rayuwa ba, saboda daidai gwargwado mahaifinmu tsaye yake kanmu, koda
yaushe, don haka ba zani ce rayuwa ta yi mani wahala ba, yanzu haka ina da takardun shaidar kammala
karatuna na NCE, nice babba a gidanmu, haka sauran 'yan'uwana ma suna nasu karatun, cikin wannan
yanayin ne Mummy ta roki alfarma aka bata ni ina
zaune tare da ita, saboda cikin 'ya'yanta mata Zainab
ce ta rage bata yi aure ba, tana karatu a A.B.U Zaria.
Kuma gaskiya ina jin dadin zamana tare dasu tana da
fahimta kamar yarda ka gani."
Yayi dariya yana jinjina kai, ya ce "Lallai kam
na gani kuma na yaba, haka nan naji dadi kwarai, da
ya kasance matsayinmu daya, a kalla zaki ga kima ta
haka nima za ni ga taki saboda wani lokaci da kaina nake tunanin "Anya ban kai kaina inda Allah bai kaini ba, karfina kasancewata dan talakawa." Ta yi murmushi ta ce "To ai ni ma 'yar talaka wance kamar ka, kuma kana manta wani abu, yanzu fa babu matsiyaci sai wanda baya da ilimi, baya da zuciyar
nema, kai kau gashi daidai gwargwado kana da na rufin asiri, kuma tsaye ka ke koda yaushe kana neman
19
na kanka, kaga wannan shi ne arzuki."
Ya yi dariya, ya gamsu da bayaninta, sai ya ji ta
kara shiga ranshi, yarinyar tasan ciwon kanta, kuma
tana da hankali sosai, irin matar da yake nema kenan,
Allah ya amshi addu'arshi, ya hada shi da ita, sai ya
fara addu'a akan Allah ya ida mashi nufin shi.
Ya gyara zama yana fuskantar ta, ya ce, "Sai abu
na biyu, tsakaninki da Allah kada ki 6oye mani komi,
shin kin taba soyayya.?" Naja'atu ta dube shi tar cikin
ido, tambayar ta dan yi mata nauyi, sai dai ya daure ta
da igiya, kuma ma ai fahimtar juna suke so suyi, don
haka ta saki jiki dashi sosai, tana kallonshi ta ce "me
ye soyayya.?" Ya yi dariya ya ce, "Kada ki maida
kanki Karamar yarinya Naja'atu, a tunanina yanzu ko
yarinya 'yar Primary aka yi ma wannan tambayar zata
iya bada amsa kai tsaye." Ta yi murmushi ta ce "Na
sani, sai dai kasan kowa da irin tashi fahimtar? Ya ce
"To ina saurarenki ke yaya ki ka fahimci kalmar.?" Ta
ce, "Yarda na dauki soyayya, shi ne ka so wanda-yake
sonka, ya kasance ku duka kuna son juna." Ya jinjina
kai ya ce "Haka ne." Ta girgiza kai ta ce "To gaskiya
in dai wannan ce soyayya zani iya ce maka ban taba
yinta ba." Ya ce "Na yarda dake sai abu na uku, ina
son ki fadi mani gaskiya tsakaninki da Allah, koda
wasa Daddy bai taba gaya maki yana sonki ba."
Ta yi murmushi ta ce "Ka damu da maganar
Daddy, to gaskiya bai taba cewa yana sona ba, idan
ma ba ka sani ba mun dade bamu shiri dashi, babu
zancen soyayya tsakanina dashi, sai na zumunci,
20
kuma bani tsammanin idan har zata faru, saboda yau din nan sai da muka fita kasuwa muka yo sayayyar kayan baiko na aurenshi ina tsammanin nan da kwana biyu za'a sanya lokacin bukinsu, kaga kenan babu
komi, sai dai za ni so ka sanar da ni dalilin da ya
sanya kayi mani wannan tambayar? Dr. Khalid ya yi murmushi ya ce "Ba za ki fahimce ni ba, amma tunda
kin ce ga matsayin da ake, na gamsu." Ya zuba mata ido, suka yi murmushi ba ki daya. Mamakin kanta
take yi, yarda mutumin yake neman canza mata ra'ayi
lokaci daya, koda yake idan ma bata soshi ba, wa zata
so? Daddy ne yanzu ya fi karfinta dole ne ta cire
zuciyarta akanshi, amma Daddy? Sai ta girgiza kai
"Da kamar wuya."
Cikin hikima Dr. Khalid ya rinka kokarin janyo
hankalin ta gare shi, kuma ya ji dadin yarda ta bashi
hadin kai sosai, suka yi hira ta fahimta, hakan yaja
suka dauki lokacin mai tsawo da su kansu suka yi
mamaki. Yana shirin tafiya, ta je kwankwasa kofar Mummy ta sanar da ita za ya tafi. Don haka
Mummynta fito, suka yi sallama, ya ji dadi kwarai
suka fito tare da Naja'atun ta yi mashi rakiya har
wajen motarshi sai da ya zauna ciki, sannan ya dube ta
ya ce "Kiyi mani wata alfarma guda.?" Ta zuba mashi
ido tana jiran taji abin da zaya fada, ya ce "Lambar
wayarki nake so ki bani ina jin dadin sauraron muryarki kinga ko banzo ba, zani iyab kiranki mu
gaisa. Ta yi mumushi ta yi tsammanin wani abun ne
can daban zaya tambaya, sai ita fadi mashi ya saka a
21ΟΓ
ا
Naarshh Aansaka ya Sat, kara,lavA MAXADAANtinkdkbiytn
gade eni bThinoukd NinaallamaBјA
Wufinta, ta lura dai kishin Likitan nan yake yi, ta cе,
"YanXMnidapi ,erawaleikýn falak Mmamyna
Faa saiaVikmurmuslnita ydan jin nauyia Mu
BiajaaB iGr isata zanaa kaisa4layiinatass9a"Uaakanirki
AANMARGIN, deriva Mummyya samaraa maganga kradakt,ridanha,kiaafo rtani hsamaaa kidadh ya
Pista" Sehata sdaga memalkai,zMumikta i "a
saskivanaiew" naa yaba Aledabanshazdoahaka ki
kwader ida hansalinki kw fabimoniunaridantAlah ya
nufa mjigkgnakinimere eurn gin radanuani dasuka
son cawonakansu, Rahama neekuma aakidjalfabatirda
hakaaydon haka kicire komi kbkahialkibladai
Ki maki bayaninkanshi ko"kana sona, kuma ina na
sanyakajaias batafrre dnatakorRáda eabata labarda
dakraytmer denitavdangenqnda raguwenshifaMuraa
itinearein ancllabbae vabbalarirmananda
iba shi, saboda shi ba jinina ba ne, amma kauna ta
sanyaDeally ya fito daga joikinadakinshtaakowkallonsu
Paini da Manufa tabusingain abinaiiyourag ta
ban mekaboazarinshi fi yeantegarosai. zkanmakewa dabawnshihaByatdinke ma kowarhaidhanaac
takeavafkidalblak ibalgindaka a caоуь Каа
baSan ba kiabkawndazsbigatahiaginyhiwaukansá
zake Bathirac hedellunmbanaialfahatiudanirinuvadA
22 10
mata
Mummy take janta jikinta, ko mahaifiyarta bata yi irin haka don haka kullum rana suke Kara shakuwa, tana son matar har cikin ranta, tana bata hakkinta, da 'yancin kanta, da wuya Mummy ta yi mata abin da zaya 6ata mata rai, ko wani abu ta yi ba
daidai ba, cikin lallashi zata nuna mata kuskurenta,
kuma ta sanya ta ta gyara to itama ko da yaushe cikin taka tsan-tsan take, bata son ta kuskuro ta, duk lokacin
da ta yi waya da su Inna, suna kara gargadinta akan ta
iya kanta, ta tsaya matsayinta, kada ta kuskura su ji
wani abu marar kyau ya taso daga gare ta.
Dare yaja sosai, suna ta hirarsu, karfe sha daya
ta shiga daki ta yi shirin kwanciya, sai ta janyo
wayarta zata rufe, nan taga miscall goma na bakuwar
lamba, babu shakka lambar Dr. Khalid ce, bata ji dadi
ba, zaya yi tsammanin ko ta ki dauka ne. Ta dauka ta
yi serving din lambar, bata kai ga rufewa ba, sai ga
kiranshi ya sake shiga, ta yi murmushi ta dauka,
muryarta kasa-kasa ta amsa mashi da sallama, ya ce "Naja'atu kina so ki rinka wahalar dani ko.?" Та се,
"Kayi hakujri, ina falo tare da Mummy muna hira,
yanzu na shiga zani kwanta, naga miscall din ka har guda goma." Ya ce, "To kuma ba za ki kirani ba.?" Ta yi murmushi ta ce "Ka yi hakuri na amsa laifina." Ya
saukar da ajiyar zuciya, ya ce, "Shi kenan kin fi karfin komi a wajena, amma hankalina har ya tashi, naga lafiya lau muka rabu, yanzu kuma ina ta kira anki daukar wayata."
Ta ce, "To na ce ka yi hakuri, Allah kuwa
23
gaskiya na fadi maka, ba ni cikin daki ne." Ya ce "Na
yarda, dama na kira ne in ce maki Good night, in
kuige ji sassanyar muryarki nasan za ni samu barci
mai dadi." Naja'atu ta yi shiru tana jinshi, duk sai ya
dora mata nauyi bata saba da irin wadannan kalaman
ba, ya ce "Kin yi shiru ba ki ce komi ba." Ta cе, "То
me zani ce maka? Ka sanya na ji nauyin ka ma." Ya
ce, "To gaskiya ki daina, Naja'atu kalmar so ce fa ta
hada mu, wata rana ma tare zamu zauna mu zama
hanta da jini, idan ba mu fahimci juna ba tun yanzu
can gaba zaman ba zaya yi mana dadi ba, don haka ki
saki jiki dani, ina son mu samu shakuwa tsakaninmu
ta haka ne za ki fahimce ni da halayyata, haka nima
zani san me kike so da kuma abin da ba ki so." Tа се
"Shi kenan, Allah ya bamu iko." Ya yi murmushi ya
ce "To na gode, kwanta kiyi barci, Allah ya bamu
alkairi." Ya rufe.
Naja'atu ta zuba ma wayar ido, sai ta yi
murmushi ta rufe ta aje ta gefe guda ta kwanta tana
karanto addu'o'i, data natsu sai ta rinka gani fuskar Dr.
Khalid yana yi mata murmushi. Ta lumshe ido tana
tariyo kalamance "Simple man yana da saukin kai da
dadin zama, tana sha'awar halayyarshi. Amma kuma
da ta tunu Daddy, sai ta ji gabanta yana faduwa, bata
san abin da ta yi mashi ba, yake yi mata fushi, koda
yake ba ya rasa nasaba da ganin Dr. Khalid, ta rasa
abin da yake damunshi ya tsani Dr. Khalid, ko
maganarshi aka yi idan yana wuri sai yasha mur baya
cewa komi.
24
Mamaki yake bata sosai, ita bata ga dalilin nuna kishi akanta ba, tunda baya sonta, hasali ma ga wadda yake so yana shirin aurenta, to so yake yi yaga ta
zauna tana wahala a kanshi alhalin shi bai damu da ita
ba, baya sonta? Insha Allahu zata yi iya bakin kokarinta taga ta cire shi, daga ranta. Ta ci gaba da
tunaninta, a hankali ta dan ja tsoki, sharrin zuciya kenan, idan ta tashi kamuwa da son abu, bata sauraren
mai ita, idan bacin haka ita kanta tasan Daddy ba
ajinta ba ne yanzu ne ta gane kuskuren da ta yi, da ta
dasa ma kanta kaunarshi, kila saboda haka ne yake
neman ya rinka juya ta. Mamakin kanta take yi da har
ta fada cikin irin wannan makauniyar soyayyar ta son
maso wani.
Da wannan tunanin barci ya dauke ta har cikin
mafarki ta rinka ganin mutanen biyu, kowa yana fadi
mata asirin zuciyarshi. To na Dr. Khalid dai tasna
gaskiya ne, amma na Daddy, sharrin zuciya ne bata
tsammanin har abada zaya iya fitowa ya ce yana
sonta. Sai ta rinka jin tausayin kanta.
Washe gari ba ta tashi da wuri ba, don haka har
Daddyn ya fita ofis, basu hadu ba. Sai da yamma da
ya shigo suna zaune falo tare da Ibrahim suka yi mashi sannu da zuwa, ko kallon sashin da suke ba yi ba, ya raba su ya wuce zuwa dakinshi. Ibrahim ya
juyo yana kallonta, cike da mamaki ya ce, "Wai me ke damun man din nan ne? Tun safe yake fushi, yau bai jira ya sauke ni, makaranta ba sai dai direba ya kaini." Naja'atu ta yi murmushi ta ce "Me yiwuwa ofis ne aka
25
Sata mashi rai ko." Ya ce "To amma Anty Naja ina
laifin mu da abun zaya shafc mu.?"
Naja'atu ta yi murmushi ta ce, "Kasan kowa da
irin halayyarshi." Ya cc, "To Allah ya kyauta." Та се
"Amin." Suka ci gaba da hirar su, ya dauki tsawon
lokaci cikin dakin, sannan ya fito. Kai tsaye ya nufi
kicin ya fito rike da kwalin lemu da kofi, ya zauna
yana cin abinci shi sai dai fuskarshi a daure, Naja'atu
ta rinka nazarinshi tana mamaki ita bata ga dalilin
wannan fushin ba, duk ya takura kanshi kuma ta yi
imanin ita abun ya shafa. lya tunanin da ta yi bata ga
laifin da ta yi mashi ba, idan ba shigowa da Dr. Khalid
ba, wannan kuma ba laifinta ba ne, Mummy ce ta ce
ya shigo, don haka sun fi kusa "To waj ma menene
dalilinshi na neman takura mata.?"
Da ya karc cin abincin ya shiga cikin daki bai
dade ba ya fito ya fice daga gidan baki daya. Abu
kamar wasa cikin kwanaki biyu Naja'atu ta gaya kan
Daddy, bata fahimci in da ya dosa ba fushi yake yi
sosai, tsakaninshi da ita sai harara yana magana da
kowa a gidan, amma ban da ita idan ta gaida shi baya
amsa ba, ko hira suke yi da Mummy idan ta fito sai ya
daure fuska baya kara yin magana. Tun tana kokarin
danne wa har takai abun ya zauna mata cikin rai, ita
kanta takura sosai, bata sake wa hankalinta ya tashi
matuka gabaki daya sai ta fara tsanar zama gida kara
ta yi tafiyarta ta huta, zata samu lokaci ta yi ma
Mummy magana ta shirya mata tafiya.
Ranar Asabar aka kai kayan baiko gidan su
26
Farida, kannen Mummy su biyù suka zo daga Katsina, da kanwar Babansu dake zaune Kaduna, sai matar Alhaji Isa, da Anty A'isha, sai sauran kawayen Mummy da abokan arzuki, sune suka hadu suka kai kayan. Lallai Mummy tayi hidima Farida mamaki ta
rinka yi abun na manya ne, sun dauke shi da girma
lallai kam Daddy ba ajinta ba ne, saboda a bangaren
su Faridar ma sunyi hidima sosai, tayi imanin idan ita
ce zaya aura ba za'a yi masu irin yarda taga an yi ba.
Sai tasha jinin jikinta. Mummy da kanta ta debi
lokacin bikin wata biyu masu zuwa, kowa ya yi na'am
da hakan, ana ta sanya albarka.
Yinin ranar bata ga angon ba, bata damu da son
ganinshi ba kuma. Washegari da wuri ta tashi ta yi
wankin underwears cikin kewaye, sannan ta shiga
goge-goge cikin dakin, ta 6ata lokaci sosai karfe tara
ta gyara komi fes, sai ta fito don ta samu abin da zata
sanya ma cikinta, yunwa take ji daren jiya bata ci
abincin ba haka nan ta kwanta. Gidan shiru kamar
babu kowa, Mummy bata tashi ba saboda bata ji
motsinsu ba, haka nan bakinsu ma, Ibrahim kuma
tasan ya tafi lesson sai ita kadai ke hidimominta, ta shiga kicin tana ta harare-hararen abin da zata ci.
Babu komi sai sauran abinci, ita kuma kunyar girka
wani abu takc yi, sai ta jawo filas ta hada tea mai
kauri ta tsaya nan tana sha.
Hankalinta ya yi nisa bata ga shigowarshi ba, sai
da ta daga kai sannan ta ganshi tsaye jikin kofa, ya
rungume hannayenshi akan kirji yana jifarta da
27
3
mayataccen kallonshi da take dauka harara ce sai ta
dan ji tsoro yayin da shi kuma ya ida shigowa ciki
sosai, sai ta yi amfani da wannan damar zata fice,
yasha gabanta da sauri a tsorace taja da baya tana
kallonshi fuskarta babu walwala, ya ce "Naja'atu kina
ganina shi ne ba za ki gaishe ni ba?" Ta sarda kai
kamar ba da ita yake ba, ya ci gaba da kallonta ya сe
"Da ke nake magana fa?" Zuciya tazo mata iya wuya,
ta ce "To me kake so in ce maka Daddy? Idan ma na
gaishe ka ba amsawa kake yi ba, ka tsiri fushi da ni."
Ya yi murmushi ya dafa firij ya ce "Yanzu laifina kike
gani kenan?" Ta ce "Dole in ga laifinka mana, idan
wani abu na yi make ka fito ka fadi mani mana, sai in
baka hakuri, amma ban san laifina ba, ka tsanani. Idan
na gaida ka baka amsawa, ba ka zama in da nake kayi
hakuri insha Allahu na kusa tafiya in bar maka gidan
baki daya".
Zuciyarta ta kare, hawaye cike da idonta, ta sake
raba shi zata wuce, ya ki bata hanya, ya tsaya kawai
yana kallonta, sai ta bashi tausayi, shi kanshi ba zaya
iya cewa ga takamaimai abin da ta yi mashi ba, illa
dai kawai yasan ya ji zafin zuwan da ya yi ya same ta
da Likitan nan har cikin falo. A hankali ya saukar da
ajiyar zuciya, ya ce, "Amma Naja'atu ni nafi ganin
laifinki." Ta ce "Da na yi maka me?" Ya ce, "Uhm,
kin san munyi magana da ke baki-da-baki na ce zani
kawo maki saurayin da ya dace dake har nan gida
ko?" Ta ce "Ni kuma nace maka ban yarda ba, kuma
bani so". Ya ce "Kenan shi ne dalilin da ya sanya kika
28
kawo wannan guy din har cikin gida ko?" Ta ce "K.e
da kaga laifina kan shigowar Dr. Khalid cikin gida, Mummy ce da kanta, ta aika ta ce ya shigo, don haka
bani na shigo da shi ba."
Ya ce "To amma tun farko me yasa kika tsaya
kika saurare shi". Zuciya ta kara cika ta, bata ga
dalilin wannan iko da yake neman yi mata ba, ta cce
"Amma kasan cewa I'am matured enough, da ya kama
ta in zabi abin da yake daidai dani ko?" Ya jinjina kai,
ya ce "Haka ne, kenan shi yasa da na bata raina akan
abin da kika yi, kema sai kika dauki fushin dani." Ya
girgiza kai ta ce "Ni ban yi fushi da kai ba Daddy,
kaine kake yin fushinka, naga idan nace zani ci gaba
da kula ka, sai ka wulakanta ni a banza don haka naja
jikina".
Ya ci gaba da kallonta yana mamakin bakin
yarinyar, ya ce "To ni dai na fadi maki ba fushi nayi
dake ba, na fadi maki ne don ki gane kuskurenki". Ta
ce "Ni fa Daddy idan zaka maida jikina kunnuwa, ba
zani yarda nayi maka laifi ba, Daddy kayi mani adalci
mana, kowane dan Adam yana da ra'ayin kanshi a
rayuwa, don mi zaka tursasa ni akan abin da zuciyata
take so". Ya zuba mata ido ya ce "Kenan kina so ki
fadi mani cewa kina son Dr. Khalid?" Ta ji nauyinshi
sai ta sarda kai ta ci gaba da juya shayin da cokali, ya
ce "ki fadi mani in ji da bakin ki". Sai ta saukar da
ajiyar zuciya, ta ce, "Daddy mu bar maganar nan, duk
abin da zani fadi maka, ba zaka fahimce ni ba, amma
ni na sani kai ba zaka iya yin abin da kake son ni in yi
29
3
ba." Ya ce "Ban fahimce ka ba.?" Ta ce "Nasan kana
son Farida ko ba haka ba.?" Ya jinjina kai yana
kallonta, ta ce "A matsayin da kuke yanzu, yaya zaka
ji idan tashi daya Mummy ta ce ka rabu da ita?"
A hankali ya yi murmushi ya ce, "Shi kenan na
fahimce ki, komi ya wuce, amma duk lokacin da na
samu dama, ina son mu zauna mu yi wata magana ta
fahimta tsakanin mu". Ta jinjina kai ta ce "Ва
damuwa". Ya ce, "To nima hada mani tea din, yunwar
nima ta fiddo ni, duk kin sa Pressure ta yi mani yawa
yunwa tana neman kamani". Ta yi murmushi kawai, ta
daha mashi tea din ya karba yana sha, ita kuma ta yi
sauri ta ida shanye nata, ta aje kofin, ta fice. Da ta
shiga daki ta koma ta kwanta, tana tunanin rigamar
Daddy sai abin ya rinka sanyata dariya, zuciyarta tayi
sanyi.
To yinin ranar lafiya lau suka yini, amma da
daddare da Dr. Khalid yazo, Mummy na cikin daki,
haka nan shima Daddy ba ya gida, don haka bata
shigo dashi ba, nan waje suka zauna suna hirarsu, ya
ce "Jiya kunsha hidima, yaushe ne lokacin bikin?" Ta
ce, "Nan da wata biyu". Ya yi murmushi ya ce, "Ya ji
dadi, nima da za ki amince mani da an hada har da
namu anyi baki daya". Naja'atu ta dube shi, sai tayi
murmushi tana girgiza kai, a cikin zuciyarta ta shiga
tunanin, "ita dai tasan tana ra'ayin Dr. Khalid, tana
sha'awar ta zauna tare da shi suna hira, yana sanya
zuciyarta cikin nishadi tare da debe mata kewar
abubuwa da yawa, amma bata taba jinshi a cikin
30
1
zuciyarta ba, balle har ta yi tunanin yin aure dashi, matsalarta kenan ta dasa ma zuciyarta kaunar Daddy
ta yarda ita kanta tasan tana cutuwa, saboda son maso
wani take yi, kuma ta cire tunanin zata same shi,
amma duk irin yarda taso taga ta rabu da kaunarshi
abun ya faskara, wannan wani sirri zuciyarta ne da
take ganin ita kadai ya shafa, babu mai iya yi mata
maganinshi sai Allah".
Ta saukar da ajiyar zuciya tana kallon Dr. Khalid
shima ita yake kallo, sai ta yi murmushi ta ce "kana
daukar aure abu mai sauki alhalin ba saukin ne dashi
ba." Ya ce "Meye wuyar shi Naja'atu? Nayi
tsammanin abin da ake so shine ya zamto ma'aurata
suna son juna." Ta ce "Akwai wannan, sai dai
fahimtar juna tana gaba da komi a cikin lamarin aure,
dukkan yanda zamu so junan mu, matsalar akace babu
fahimta, to zaman ba za ya dore ba, don haka nake
son mubi komi a hankali, ko shi Daddy da kaga za
yayi aure, tare yake da yarinyar, ance tun tana karama
sun jima suna son juna, akalla ya fahimce ta, itama
haka, to mu fa, duk yaushe ne muka hadu?"
Yayi murmushi ya ce "Na fbahimta malama,
idam kina jawabi sai ka ce 'yar jarida, ince kina
karatun littafi ko?" Tayi murmushi ta ce "Ina tabawa,
amma masu ma'ana, wadanda nasan zasu amfaneni ba
wadanda zasu 6ata mani lokaci ba." Ya ce "Yana da
kyau, kuma na gamsu da jawabin ki, na yarda da ke,
Allag ya shige mana gaba." Tayi murmushi da amsa
mashi da "Amin." Kadan kenan daga irin halayen shi
31
da take so, bai cikia jan abu ba, yana da saukin kai da
saurin fahimta, cikin nutsuwa suke hirar su. Karfe tara
da rabi yayi mata sallama zaya tafi, sai ga Daddy ya
dawo, ya shigo da motar ya ajeta can nesa dasu bai zo
inda suke ba, sai dai ya daga masu hannu ya shiga
gida. Naja'atu bata ji dadin abin da yayi ba, to sai ta
lura shi Dr Khalid bai damu ba, yayi matga sallama
yaja mota ya fita.
Da ta shiga cikin gida, ranta ya dan