Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 5
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels SIRRINZUCI SA'ADATU SAMINU KANKIA (Mrs. Sani Abbas) Hakkin Mallaka (m) Sa'adatu Saminu Kankia Copy right (c) Sa'adatu Saminu Kankia An rubuta a shekara ta: 2008 GODIYA TA MUSAMMAN Ga daukacin masoyana, makaranta littattafaina, fatan alkairi a gare ku baki daya, ina godiya, akan addu'ar da kuke yi mani da fatan alkairi, Allah (S.W.Т) ya bani ikon ci gaba da yi maku yarda kuke so, kuci gaba da yi mani addu'a, shi ne fatana. Ina alfahari daku koda yaushe. 2 SIRRIN ZUCI - 2 Z uciyarta cike da sake-sake na tunanin Likitan da labarin da ya bata, sai ta rinka jin tausayinshi, ta yi sallama ta shiga, daga murmushi, ta raba su zata wuce cikin daki. Daddy ya dago kao yana kallonta, ya ce "Zo nan Naja'atu." Ta tsaya cak tana kallonshi, to bata yi musu ba sai ta koma ta tsaya kusa da kujera, yayin da shi kuma ya dan hada rai ya ce, "Zo zauna, ki fadi mani abin da ya ce maku." Mummy dake zaune gefe daya tana kallon su, ta kasa daurewa cike da mamaki ta kalle shi ta ce "Wace irin tambaya ce haka Daddy, kanka daya? Ina ruwanka da zaka ce sai ta fadi maka abin da ya fadi mata sai kace karamar yarinya.?" Ya kara daure fuska ya ce, "Amma Mummy yaya za'ayi daga zuwan mutum a yarda dashi ba'a tsaya wani bincike ba." Mummy ta yi dariya, ta cе "To ai dama shi aure ya gaji haka, kana ina mace auren mutumin da ba ma jinsu daya ba, bata son shi ba balle in da ya fito, in dai soyayya ta hada su ya aure ta a zauna lafiya har da zuri'a balle ni banga laifin wannan Likitan ba, Musulmi ne kuma bahaushe irin mu rashin saninshi kuma ai ba matsala ba ce duka yaushe suka hadu? Ka bari tafiya ta yi tafiya mana kana nan zaya kawo 'yan'uwanshi, kuma ka ji duk iya abin da kake so ka ji a akan shi."Ya ce, "Ni Mummy kin kasa fahimta ta ne, rayuwa ta canza, yanzu dole ne sai an sanya ido fa." Ta yi murmushi ta ce, "Idan dai 3 bayanin da na yi maka bai gamsar da kai ba, to ba zani taba fahimtarka ba, sai dai abin da nake so ka fahimta shi ne, babu dalilin da zaya sanya ka zuba ma yarinya ido alhalin kai babu wanda ya zuba maka, ko kuwa shi kenan ta ci gaba da zama kenan ba zata samu miji ta yi aure ba, saboda wani ra'ayinka can daban, ko kwanaki da kaga na zuba maka ido ka kawo wannan yaron da ya fara zuwa wajentga, don nima ban yarda da take-taken shi ba ne, amma wannan na fadi maka babu ruwanka ka rabu da ita, ai ta mallaki hankalinta, kuma tasan abin da yake daidai da ita, sai ka bari idan ta yi abun magana sannan kayi, amma ni bani son tsangwama irin haka." Sallamar maigadi ta katse Hajiya, yayin da ya shigo da iyayen kaya cikin ledoji ya aje ya ce, in ji wannan bakon da yazo na Naja'atu ne." Daddy ya kara hade rai, yayin da idanuwanshi suka kada suka yi jajir, sai huci yake yi, ya wurga ma Naja'atun harara, bai yi magana ba, ya jefa remote din dake hannunshi bisa kujera ya mike ya nufi daki. Hajiya ta yi dariya cikin zuciyarta ta ce, "Kayi ka gama, ka dawo bisa hanya." Ta juya tana kallon Naja'atu da ke tsaye cikin damuwa, ba ta ji dadin abin da Hajiya ta yi ma Daddyn ba, duk sai ya bata tausayi, kai sai ta rinka ganin laifin kantga, da ta sani bata fita ba, bata son ganin bacin ranshi. Hajiya ta ce, "Zo kwashi kayanki rabu da shi kinatsu ki kwantar da hankalinki ku fahimci juna, idan Allah ya kaddara shi ne mijinki zani yi murna." 4 Jikinta ya yi sanyi, ta duka ta kwashi ledar kayan ciye-ciycn ta kai kicin, sannan ta debi na kayan shafa ta nufi daki, hirar ranar ta ruguje gashi Daddy ya yi fushi, gaba ki daya sai ta ji ta tsani kayan, kai shi kanshi Likitan ji take yi zata iya rabuwa da shi tunda Daddy ba ya so. Dare ya fara mikawa tana kwance kan gado, sai juyi take yi, kalaman Likitan suka rinka dawo mata cikin kai daya bayan daya, ta gamsu da abin da ya fadi mata, kuma ga alama manufarshi akanta alkairi ce, irin mijin da take mafarkin samu kenan, watau zasu fahimci juna su gini zuri'arsu bisa tsarin kansu, to amma da ta tuna Daddy da yanayin da ya shiga, sai ta ji damuwarta ta karu, har ta rinka jin ta rabu da Likitan kawai shi yafi. Daddy shu'umin mutum ne, ya iya birkicewa, ita kuma da zaran taga ya canza, shi kenan sai hankalinta ya tashi. Har kuka ta yi damuwa ta yi mata yawa, ta lalubo wayarta ta bude da nufin ta kira shi ta ba shi hakuri, amma sai ta kasa, tana gudun kada ya fadi mata bakar magana, balle yana cikin fushi, da wuya ya dauki wayar, ta maidata ta aje gefen filo, ba'a jima ba, ta ji kira ya shigo jikinta na rawa ta tashi zaune ta dauki wayar, sai taga sunan Daddy zuciyarta ta rinka dakan uku-uku, kamar kada ta dauka, sai taga rashin daukar ma wani laifin zaya janyò mata, kara ta dauka ta ji meye ra'ayinshi, idan ya ce ta rabu da Likitan shi kenan sai ta ba shi izinin ya sallame shi ba tare da Mummy ta sani ba. Ta bude wayar ta manna a kunne. Muryarshi a 5 dusashe alamar har yanzu bai warware ba, ya ce "kema bake yi barcin ba? Ta amsa mashi "Eh." Ya ce, "Me zaya hana ki barci Naja'atu.?" Ta runtse ido tana jin zuciyarta na yi mata wani irin tukuki, a hankali ta ce, "Babu komi ina shirin yi yanzu." Sai ya yi shiru kamar ya aje, ta dan saurara ta ji shiru, ta ce "Daddy ka aje ne.?" Ya ce, "Ina saurarenki, kin gane ko, kiyi hakuri kan abin da na yi maki dazu, naga daga ke har Mummy ranku ya baci, ni kuma akwai abin da na duba ne shi yasa na yi maki magana, amma tunda Mummy ta ce in rabu dake shi kenan." Ta ce, "Daddy fushi kayi kenan.?" Ya ce, "Ko daya, na yi tunani ne sai naga abin da Mummyn ta fada gaskiya ne don haka ina yi maki fatan alkairi." Ta saukar da ajiyar zuciya, hankalinta ya kwanta ta ce, "Daddy na gode." Ya ce, "Kada ki samu damuwa, kwanta kiyi bacci, Allah ya ba mu alkairi." Ya rufe wayar, itama ta tsaya tana kallon wayar sai tayi murmushi ta rufe baki daya ta jefa karkashin filonta. ko ba komi ta samu natsuwa, don haka cikin kwanciyar hankali ta yi barcinta. Washe gari bata fita da wuri ba, har Daddy ya fita ofis don haka ta kara samun natsuwa. Da yamma ne suka yi bako gidan kanin mahaifin su Daddy, Alhaji Isa, yazo kan maganar da suka yi da Hajiya ta waya kan zuwa neman auren Daddy gidan su Farida. Har zuwa lokacin Daddy yana ofis bai dawo ba, Hajiya ta fito suka zauna falo, ana gaisawa sannan ta kira Naja'atu taje ta kawo mashi kemu da ruwa, ta gaidashi to sai ta komi kicin suna aiki tare da mick. Mummy ta ce, "Yau da nayi niyyar fita in same ka, saboda mutanen nan tunda suka aiko ba'a tura masu da wani bayani ba, sun ji shiru, kada su dauka ana wasa da maganar ne, don haka na ce kara mu zauna asan meye abin yi". Alhaji Isa ya gyara zama ya ce, "Haka nc, rannan mun yi magana da shi Daddy din kuma ya sanar dani cewa, ita dai wannan yariyar yake so, to gobe nake sanya ran zuwa tare da wani abokina, a tsaida magana shi kenan". Hajiya ta ce, "Haka dai ya kamata ayi, ni kaina nafi samun kwanciyar hankali." Daddy ya bude kofa ya shigo, ganin Baban nasu ya sanya ya saki fuska yana dariya, ya iso ya zauna yana gaida shi. Alhajin ya ce, "Yaya ofis din yau?. Ya ce, "Alhamdulillahi komi lafiya." Ya ce "Ya yi kyau, dama yanzu magana muke yi akanka, dangane da maganar nan dai, ka dai amince ita ka ke so ko.?" Ya dubi Mummy sai ya yi murmushi, Alhaji ya ce "Magana zaka yi kada sai mun kashe magana kazo da wata kuma." Ya shafa kanshi yana dariya ya ce, "Babu damuwa, ku ci gaba kawai nan din dai na tsaya." Alhaji ya dubi Hajiya ya ce, "To kin ji, don haka goben insha Allahu zani je, sai kayi kokari ka sanar da su, su san da zuwanmu, duk abin da muka yi zani biyo in sanar da ku." Hajiya ta ce, "Shi kenan Allah ya tabbatar mana da alkairi." Alhajin ya mike yana shirin tafiya, Daddy ya bi bayan shi suka fita, yayin da ita kuma ta tashi ta koma 7 cikin daki. Yana tarc da Alhajin har ya tafi, sannan ya dawo cikin gida, cikin falo ya hadu da Naja'atun ta fito daga kicin zata nufi daki, duk maganganun da ake yi tana jinsu tsab cikin kunnenta, yau kam ta ida tabbatarwa Daddy ba ya ra'ayinta. Zuciyarta ta kare sosai, ta dauke kai kamar bata ganshi ba, shima kallonta yake yi yana lura da yanayinta tana shirin murda Kofa ya kirata Naja'atu sai ta tsaya cak ba tare da ta juyo ba, ya cc, "Yau kuma ko sannu da zuwan ba zani samu ba.?" Shiru ta yi ba ta ce mashi komi ba, ya ce, "To zo ki kawo mani abinci yunwa nake ji." Ba ta yi musu ba ta nufi teburin cin abinci, yayin da shima ya wuce cikin dakinshi, har ta gama zuba mashi abincin yana ciki bai fito ba, don haka ta sanya wani filet din ta rufe mashi tana shirin tafiya sai gashi ya fito har ya canza kaya ya ce, "Sorry na barki kina jira ko.?" Muje ki kai mani cikin falo." Ta dauko ta bi bayanshi zuwa cikin falon, sai ta ajc kan tabur, sannan ta janyo shi gabanshi, ta koma ta bude firij ta fiddo lemuna kwali da robar rujwa ta aje kan faranti ta hado da kofi, ta kawo ta aje mashi yana kallonta ya ce. "Sannu na gode." Sai ta dan saki fuska tana kokarin boye damuwarta. Ba ta zauna ba ta juya zata tafi, ya ce "Zo zauna mu yi hira mana, wai saurin me kike yi haka.?" Ta dube shi tsab cikin ido, yayin da shima ya zuba mata nashi, zuciyarta ta yi sanyi, sai ta yi murmushi ta dawo ta zauna, tana kallo yayin da shi kuma ya fara cin abincin yana nazarinta yanzu tausayinta yake ji, saboda iya nazarin da ya yi mata ya 8 fahimci tsananin kaunar da take yi mashi, to shi kanshi ya rasa abin da yake damunshi dangane da ita, kai matsayin da komi yake yi tana cikin zuciyarshi, yarda yake jinta a ranshi yanzu nema take yi ta take Farida, abun har tsoro yake ba shi, musamman ganin yarda abubuwan da suke ta kara tsananta ko daren jiya sai da ya yi mafarki da ita, abun ya tsaya mashi cikin rai, ya yi imanin matsawar bai dauki mataki ba, al'amarin zaya iya canzawa, don haka ne ya amince da auren Faridar, me yiwuwa idan yaga an tsaida lokacin aurensu zaya yi kokari ya cire Naja'atun a ranshi, baya son ita Farida ta zarge shi da cin amanarta, tunda har magana ta kai gaban iyaye, dole ne da itan za'ayi. Ya dan lumshe ido, sannan a hankali ya sauke kwayar idonshi akan Naja'atun, cikin sa'a itama ta kalle shi, sai suka yi murmushi ya ce, "Naja'atu matar Likita, gashi kina tsoron allura, idan kuka yi aure yaya kenan.?" Itama ta taya shi dariyar, tunda ta lura hirar yake ji, ta ce, "Ai in dai yana sona ba zaya yi mani allura ba." Ya zuba mata ido ya ce "ko.?" Ta cе, "Sosai ma, ba ka gani ba, ko da bani da lafiyar da nace bani son allurar kyale ni ya yi bai yi mani ba." Ya jinjina kai ya ce, "Na yarda meye sunanshi.?" ta ce, "Sai ka saya." Ya ce, "Kenan dai kina sonshi.?" Ta yi murmushi ta ce, "Idan ban so shi ba in so wa? Ina laifin wanda yazo ya ce yana sonka." Ya ce, "Babu tunda kema kina so." Ta yi dariya ta ce "wa ya fadi maka.?" Ya ce, "Ai ba sai an fadi mani ba, alamunki kadai sun isa su sa in sani, jiba dazu ba, fushi kike yi, amma yanzu daga fara maganar shi kin saki kina dariya kamar ba ke ba."Ta sunne kai tana murmushin mugunta, ta lura dai kishin Likitan nan yake yi, ta ce, "Yanzu kai don Allah idan aka yi maka maganar Farida yaya ka ke ji.?" Ya zuba mata ido yana tuhumarta, sai ta yi murmushi ta ce, "Ni ban ce ina son Doctor Khalid ba, sai dai yana daya daga cikin mutane masu muhimmanci a rayuwata, saboda ya so ni a zuciyarshi, kuma ya fito ya sanar da ni, kaga wannan shi ne dmauwa, ko da wasa idan mutum ya furta yana sona, wallahi zani dauke shi da muhimmanci." Ya ce "Ashe nima yanzu idan na ce ina sonki, za ki bani irin wannan muhimmancin.?" Ta girgiza kai, ta ce, "Ba ka fahimce ni ba, kai son da zaka yi mani so ne na zumunci da kuma matsayin da muke a yanzu, don haka ko baka fito fili ka sanar dani ba, na sani kana sona, kuma ina na sanyaka cikin mutanen da nake kauna kamar son da nake yi ma 'yan'uwana da muka fito ciki daya. Kaga irin wannan muhimmancin daban yake da irin wanda zani ba shi, saboda shi ba jinina ba ne, amma kauna ta sanya yazo in da nake, har ya nuna sha'awar muyi zama dashi na rayuwa, gama nashi muhimmancin da ban ne saboda ya shafi wani bangare na zamantakewa daban, kamar yarda zaka auro Farida ne, kaga can take waje daben ba jininka ba ce, amma so da kauna ya sanya kayi sha'awar zama da ita na rayuwa, kuma zaka bata muhimmanci daban da na sauran mutanen 10 da ka ke zaune tare da su tsawon lokaci." Ya jinjina kai ya ce, "Na fahimce ki, sai dai kin san cewa nima zani iya cewa ina sonki, kuma ki bani wancan matsayin da kike magana.?" Ta yi murmushi ta ce "Da kamar wuya Daddy, tunda zuciyarka wani ruhin take so daban." Ya saukar da ajiyar zuciya, ya ce, "Amma kinsan ni mijin mace hudu ne.?" Ta dube shi da sauri, shima ita yake kallo, a hankali ta sauke kwayar idonta tana kada kai ya ce, "Ko kina ganin haka ba za ta yiwu ba.?" ta ce, "Zata iya yiwuwa, amma akan wata." Ya ce, "Me zaya hana ke.?" Ta yi murmushi ta ce "Mu bar maganar nan Daddy, yanzu fa aka gama magana kan aurenka." Ya cem "To shi ne me? Namiji nake fa.?" Sai ta yi murmushi ta tashi ta bashi waje taga yana neman kauce hanya, anya kan Daddy daya? Yanda yake doki kan Farida ace har ya fara magana kan wata? Ko da yake ita kanta tasan zolayarta kawia yake yi, amma a cikin zuciyarta ji take yi, idan har zaya yi mata hakan ta ji dadi. Da dare ta yi zamanta cikin daki bata fito ba, saboda Daddy na gidan, bata son ganinshi balle ya fama mata gyambon da ke cikin zuciyarta, ta lura nema yake yi ya yi mata yawo da hankali. Da safe ma har ya fita tana cikin daki bata fito ba, da rana ne Alhaji Isa yazo wa Mummy da labari mai dadi, cewa yaje ya gana da mahaifin Farida, kuma sun yi murna da hakan, don haka sun bada izinin akai kayan sanya rana, da na neman aure baki daya." Mummy ta yi murna kwarai, 11 ita kanta idan taga Daddyn ya yi aure hankalinta zaya fikwanciya, soyayya idan ta yi tsawo matsala take ko kuma su janyo masu abin magana a gari. Bayan Alhaji Isan ya tafi, ta yi shiri ita da aja'atu suka tafi kasuwa, duk wani abin da za'a nema cikin kayan baiko sai da suka sawo shi, har Naja'atun tarinka jin haushin Mummyn ita ma ta cika zakwadi kan auren. Ba su dawo gida ba sai yamma likis, loka cin Daddy ya dawo gida, har ya sake shiri zaya fita, cidn falo suka hadu da shi, Naja'atu ta dauke kanta tana rike da jikkar Mummy, ta shiga daki ta aje mata samman ta fito ta wuce su Mummy na yi mashi bayanin salfon da Alhaji yazo dashi da kuma ita matakin da ta dauka, sai yayi murmushi kawai ya yi mata sallama ya fice wajen Farida zaya je. Tafiya a tsanake bisa titi har ya isa gidansu, maigadi ya bude mashi ya shiga, iyayen duka sun fita don haka cikin falo ta shiga dashi. Hankalinta ya kiyanta, murna fal da cikintga Daddy ya zama nata, ya irra zaune cikin falon yayin da ita kuma take ta zurga zurgar hada mashi abin motsa baki, sai da ta kimtsa komi sannan tazo ta zauna, sanye take da wando na jin ruwan bula, ya matse ta dam, ya fiddo surar jikinta kar kalmar daya da lissafi, haka ma rigar ta tsuke ta ta dda sassan wuyanta waya, har kana gano kirjinta, sai ya dan lumshe ido har kullum yana da takaicin irin, suturun da Farida ke amfani da su akasin Naja'atu da koda yaushe take yin cikakkar shiga ta mutumci, irin tamu ta Hausawa. 12 Ya dago yana kallonta sai ta lumshe ido tana murmushi ta ce, "My man yaya ka ke.?" Ya dan saki fuska ya ce, "lafiya lau Farida, ya jin dadi.?" Ta kara fadada murmushinta, ta ce, "Lallai kam ina cikin shi yau kasan wani abu.?" ya ce, sai kin fada." Та се, "Allah duk da kkake cewa zaka aure ni, zaka aure ni, wallahi jinka kawai nake yi gani nake yi kamar kana shafa mani mai ne, ashe dai da gaske mafarkina zaya zama gaskiya.?" Ya yi murmushi ya ce, "Har yanzu kin kasa fahimtata Farida, ni magana daya nake yi, bani son wani ya saba mani alkawari, kamar yarda bani son in saba ma wani idan zaki tuna tun ba ki mallaki hankalin kanki ba, ba ki ma san meye son ba, ni na yi maki alkawarin cewa zamu yi aure, to meye dalilin da zaya sanya yanzu da rana tsaka in saba alkawarin? Alhalin ba ki ce baki sona ba.?" Ta yi murmushi ta ce "Haka ne kuma na gode, ka nuna mani cewa kana da alkawari, ba kamar, yarda wasu mazan suke ba." Ya ce "Ke da Mummy ban san wanda ya fi wani zumudin abun nan ba, yanzu itama ta dawo daga kasuwa ita da Naja'atu, wai sunje sayayyar kayan baiko." Farida ta yi dariya ta ce, "Naja'atun tana nan bata tafi ba kenan.?" Ya yi murmushi ya ce, "Tana nan, dama an fadi maki tafiya zata yi ne? ta dan tabe baki ya ce "Wai ke don Allah mcye dalilin da ya sanya ki ka tsani Naja'atu alhalin ita kuma koda yaushe tana karfafa mani guiwa akan in soki, da wuya muyi hira da ita bata yi mani maganarki ba." 13 A Don da nan Farida ta canza fuska, ta ce "Ni ba wai damuna ta yi ba ne, abu guda nake dubawa yarinyar tana da kyau, gashi kuna zaune wuri daya sai na rinka ganin kamar yau da gobe idan kuna tare zata iya janye mani kai ka koma wajenta." Daddy ya rinka Kyalkyatar dariya, ya ce "Ashe ba ki yarda da kanki ba kenan.? Та сe, "Bа haka ba ne, halinku nake ji Daddy, idan ku ka ga jar fata balle wadda take kwaskwas irin Naja'atun, ba wuya kun canza." ya ce, "Amma ka da ki manta in da na yi zama can ma ne ke da jajayen na usuli." Ta jinjina kai ta ce, "Share wadannan ai su ba jinsika ba ne, amma ita wannan da bambance, tare ka ke da ita koda yaushe, cikin zaman da kuke yi zaka iya ganin wani abu wajenta da zaya iya daukar hankalinka. Ba zani 6oye maka ba, wallahi tunda nake ban taba jin kishin wata diya mace ba irin Naja'atun, har barci take hana ni, kai wani lokacin ma cikin mafarki ganinta nake yi muna fada saboda kai." Daddy don dariya har da hawaye, ta ce, "Kana daukar maganata wasa, Allah kuwa abin da ke cikin zuciyata ne na fadi maka, don haka ko lokacin bukin nan na gaya ma Mama a sanya lokaci kadan, idan muna tare zani fi samun kwanciyar hankali." Daddy ya ce, "To wai menene kike gudu.?" Ta ce "Tsoro na guda kada ka ce zaka so yarinyar don gaskiya muddun ka ce zaka so ta, ba karamin rikici rayuwata zata shiga ba." Daddy ya yi tsuru yana saurarenta, saboda yanzu haka yarda yake jin Naja'atun cikin zuciyarshi, abun har ya fara bashi tsoro, idan ta fahimci haka yaya zata 14 yi kenan.?" Wannan wani sirri ne da ya bar ma zuciyarshi. Hirarsu mai dadi cikin tsananin nuna kulawa ga junansu, hakan ya sanya Daddyn ya dauki lokaci sosai tare da ita, har Mama ta dawo. Suka kara tattauna maganar da ita, an fara kiran sallar magaruba, Farida ta yi mashi rakiya har bakin motarshi, kamar yarda ya saba, sai da ya zauna sannan ya fiddo mata ledar da ya yi mata tsaraba, ya bata ta yi godiya, suka yi sallama ta shiga gida cike da zumudı yayin da shi kuma yaja motar ya fita, kan hanya ya tsaya masallaci ya yi sallah, bai koma gida ba ya wuce asibiti duba mahaifiyar wani abokinshi da suke aiki tare, ba ya da aboki kamar Aliyu, sun damu da juna. Shi Aliyu asalin mutumin Funtuwa ne, jininsu yazo daya suna tafiyar da harkokinsu tare to mahaifiyarshi ce bata jin dadi aka kwantar da ita, jiya yau wajen aiki yake fadi mashi. Da ya shiga cikin asibitin ta waya ya kirawo Aliyu sai gashi ya fito sannan suka shiga tare, ya jima tare da su da aka yi kiran Sallah suka fito suka yi sallah masallacin dake bakin get din, sannan suka koma ciki. Aliyu ya ji dadi kwarai musamman ganin yarda Daddy wanda ya fi kira da ainihin sunanshi Saddig, ya nuna damuwarshi akan abin da ya dame shi ga uwar hidimar da ya yi masu, haka nan ya jima tare da shi sannan ya yi masu sallama suka fito har wajen mota, ya nufo gida. To kuma nan gida daidai lokacin Dr. Khalid ya 15 isa gidan Ibrahim na waje lokacin da ya iso, don haka shi ya tarbe shi suka gaisa ya tambaye shi "Naja'atu na nan kuwa.?" Ya ce, "Eh tana nan." Ya ce to ka fadi mata ta yi bako". Ibrahim ya yi murmushi ya ce, "Ва damuwa, ka shigo ciki kawai." Ya yi murmushi ya сe, "Ba komi nan ma ya isa, shiga ka yi mata magana." To bai yi musu ba, ya shiga cikin falon in da Naja'atu ke zaune tare da Hajiya suna kallon wani film da ake nunawa a tashar Nollywood, ya dauki hankalinta sosai bata ji shigowar Ibrahim ba, sai dai ta ji maganarshi in da ya ce, "Anty Naja'atu, kina da bako.?" Ta zuba mashi ido a razane, ta ce "Ni?

Chapter 1 of 5