Reading RASHIN GODIYA by HAYATU BABA ZUBAIRU Chapter 1 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Downloaded From https://tknovels.com.ng Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Arewa hausa novels
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup and cooking)

WHATSAPP NO:
+2347039625239
RASHIN GODIYA
RASHIN GODIYA ✂ 1
BISMILLAHIR RAHMANIR
RAHIM
Rana ta take sosai duk wanda ka gani a cikinta
dole ce ta fito dashi daga gida. Tana zaune a
bayan bus ita kadai kamar mayya saboda babu
mai zama kusa da ita...karnin da take yi yasa
ake gudunta. Daidai asibitin tace da kwandastan
akwai na nan. Bai ji abinda tace ba saboda
karar horn daga motocin da ke sintiri akan titin.
Ai kuwa mutanen ciki kamar hadin baki suka
fara cewa akwai na nan, kai baka ji ne ana yi
maka magana akwai mai sauka. Kusan duk
mutanen bus din fitowa suka yi suka bata hanya
ta wuce. Wata dattijuwa ta rike hanci...wai!
yarinya a rinka wanka don Allah. Kwandasta
yayi dariya ai irin matan nan masu gayu da
kazanta suna da yawa. Amma dai gaskiya
yanmata idan kika dore a haka sai dai kiji ana
biki a makota amma ba naki ba. Aishatu bata ce
komai ba har aka bata canjinta tayi gaba.
Wani daci ne ya tokare mata wuya ta kasa
hadiyar yawu saboda radadin da zuciyarta ke yi
mata. Inda sabo ya kamata ta saba da kyamar
da mutane ke yi mata a dalilin ciwon da take
fama dashi. Hawaye ne suka sauko mata tayi
saurin gogewa da kasan hijab dinta sannan ta
karasa gate din asibitin. AMC....Assalam
Medical Centre. Tabbas shine asibitin da Anti
Lawisa ta kwatanta mata. Daga kanta tayi tana
karewa ginin kallo, a rayuwarta tana son gida
mai kyau, ba don lalura ce ta kawota ba da ta
bawa idanunta hakkinsu.
Tana shiga ciki reception ta wuce ta tarar da
mata biyu tsaye. Sallama tayi musu suka amsa
tare. Daya daga cikinsu ta kalli dayar, ke
Jummai warin me nake ji haka, ko jiya a nan
kika bar flask din abincinki ne? Bana son
wulakanci ta bata amsa a harzuke, kila ma
shegen cover shoe dinki ne da baya samun iska.
Ta kalli Aishatu ke baki ji karnin bane don
Allah? Ai gara wari akan wannan silent bala'in.
Ita dai Aishatu bata ce komai ba don tasan ita
ke fitar da wannan abin kyamar. Likita zaki gani
ne taji an tambayeta. Eh ta amsa amma ina
neman wata nurse ne Risikat. To wanne zaki
fara? Likitan ko Sis Risikat din. Daga baya
Aishatu taji ance gani meye ake kiran sunana.
Hmmmm kai Jummai yau anyi shara kuwa? An
fitar da bola da wanke toilets? Wurin nan has a
terrible odour. Aishatu suka nuna mata, ga
wadda take nemanki. Risikat na matsowa ta
tabbatar daga ina warin yake sai tayi shiru don
a matsayinta na maaikaciyar lafiya bai kamata
tasa mara lafiya yaji ba dadi ba. Haka ta daure
ta matso kusa da Aishatu, gani how can I help
you?
Dan murmushi tayi tace Anti Lawisa ce ta turo
ni. Tuni Risikat ta washe baki Ahh kece yar
yayarta ko? Ai ta fada min zaki zo. Kinyi saa Dr
Rano bai dade da zuwa ba. Sai dai zaki sami
layi ta fada tana nuna matan dake zazzaune a
wurin da aka yi domin zamansu suna shan sanyi
AC. Ina fata dai akwai kudi ko. Zaki bude file ki
biya consultation fee. Nawa ne ta tambaya tana
kokarin bude jaka. Jummai tace dubu biyu kudin
file sai dubu da dari biyar na ganin likita.
Sai da ta gama biyan kudin Risikat tace ta
zauna zaa kira ta. Idan tana bukatar wani abu
tayi mata magana. Kinsan farkon zuwana
unguwar mu Lawisa ta taimake ni sosai. Bana
manta alheri so feel free to ask idan kina son
wani abu. Godiya tayi mata sannan ta kara
shafa yar jakarta ta tabbatar kudinta yana nan.
Sai da babanta ya sayar da tumaki hudu aka
bata kudin don ance mata irin lalurarta tana cin
kudi sosai.
Kusan mintuna talatin tana zaune saura su biyu
a wurin taji ance Aishatu Yusuf. Gabanta ne yayi
mugun faduwa ta mike kamar an tsikareta.
Yanzu ta yaya zata yiwa likita bayanin ciwonta.
Gaba daya ta rude don saboda irin wannan
kunyar ta kasa fadawa kowa tana da ciwo har
sai da ya bayyana kansa.
RASHIN GODIYA ✂2
Sallama tayi tare da kwankwasa kofa taji muryar
namiji ya amsa daga ciki. Hantar cikinta ta sake
kadawa da ta shiga taga mutumin ba wanni
babba bane. Sai da Aishatu ta kwashi rabin
minti a tsaye...malama ki karaso mana akwai
taji ya fada yana danne dannen computer.
Aishatu ta karaso gaban table din ta zauna kan
kujera. Zumbur Dr Rano ya mike yana
kallonta...sorry wani wari nake ji,ina zuwa.
Karkashin kujerarsa ya duba da bayan labule.
Har wurin gadon da marasa lafiya ke kwanciya
ya duba su duk sai da ya leka yana yi yana dan
kallonta. Ko dai tusa tayi masa ne tana shigowa
ya tambayi kansa. Ganin irin kallon da yake
mata yasa ta galla masa harara. Ya dan shafa
kansa yana dawowa wurin zamansa tare da
karfafa zarginsa na cewa iska ta sakar masa
mai wari.
Yana zama ya jawo file din gabansa, Aishatu
Ja'afar ko. Kai ta gyada masa kawai. Ya dauko
biro ya dora kan wata takarda. Aishatu
shekarunki nawa?
Ashirin da hudu.
Kina da aure ne?
Eh...har ya rubuta tayi saurin cewa a'a.
Cikin rashin fahimta ya kalleta. Bangane ba?
Tace wata bakwai kenan da rabuwarmu da
mijin.
Sai da Dr Rano ya gama rubuta bayanan da
yake da bukata ya ce to me ya sameki?
Kasa dago kai Aishatu tayi tana wasa da wani
zobe a hannunta tace kuraje ne suka fito min
suna yin ruwa sannan ina fitar da wani ruwa.
Ganin daga nan bata da niyar kara yin wani
bayani ga lokaci yana tafiya yasa ya danna wani
abu a jikin bango. Ba jimawa wata nurse ta
shigo. Gani doctor. Ya tashi daga kan kujerar sa,
zan duba patient dinnan ne idan kuma kina wani
aikin ki kira wata tazo muyi tare.
A bisa tsarin asibitin idan lalura ta bukaci likita
namiji zai duba mace a jikinta sai ya kira nurse
mace ta tsaya a wurin saboda kare mutumcin
su.
Gadon nurse din ta nuna mata, taso ki kwanta.
Aishatu ta dan zare ido a ina? Dama dai Anti
Lawisa ta fada mata da wuya idan ba sai likita
ya duba wurin da kansa ba. Shiyasa ma ta jima
da ciwon bata yi yunkurin zuwa asibiti ba.
Daga dan guntun bayaninta Dr Rano ya dan
gane inda ta dosa. Nurse tana rike da file din ya
cigaba da yiwa Aishatu tambayoyi game da
abinda idanunsa suka gani a jikinta. Haba dole
yaji wari mana. Ita kanta nurse din don bai
kamata ta nuna kyamar patient bane amma sai
da ta kawar da kanta gefe.
Dr Rano yace Aishatu tun yaushe kika fara
ciwon nan?
Wata shida kenan ta amsa daga kwance.
Muryarta har rawa take tana magana. Yana
kallo ta share hawayen da suka dade cikin
idonta tana hanasu sauka.
Tijjani ya cuceta tunda a dalilinsa yau ita ce
kwance ana kare mata kallo cike da kyankyami.
Dr Rano ya katse mata tunani...banda kurajen
da discharge akwai wurin da ke miki ciwo ne?
Eh marata tana ciwo kuma idan zanyi fitsari da
zafi wani lokacin ta amsa idanunta a rufe jin an
tura mata wani dogon abu. Bata san nurse din
ce ma a kanta ba ba likitan ba. Nurse din tana
gamawa tace da Aishatu ta tashi an gama. Dr
Rano yace ki kai sample din lab ga request form
dinta ki hada dashi.
Wani rubutun yayi sannan ya bata takardar da
zata kai wurin ba da magani. Ga wadan nan ki
fara sha kafin ayi test din. Ki dawo nan da
kwana uku.
Har ta tashi yace Aishatu ki dena sakaci da
lafiyarki kinji ko? Rashin zuwanki asibiti da wuri
yasa ciwon ya kamaki haka, banda haka da tuni
kin manta dashi.
Dan murmushi tayi nagode doctor. Zan kiyaye in
sha Allah.
Aishatu na rufe kofa ya dauki wayarsa wadda ta
jima tana vibrating lokacin da yake duba
Aishatu...sunan Fadila ya gani ta kira sau goma
sha hudu. Allah gani gareKa yace don yau kam
gidansa bazai masa dadi ba.
RASHIN GODIYA ✂ 3
Shopping yaje yayi mata na tarkacen kayan
kwadayi kala kala duk na toshiyar baki. Idan da
kayan zaki zaifi jindadin bata hakuri.
Har ya shiga gidan bai ganta ba, yaransa biyu
Aliya da Aliyu kadai ya gani suna wasa tare da
mai aiki. Da murna suka tare shi ya basu tasu
tsarabar...Aliya ina Mamanki? Tana daki ta
amsa masa tana barewa kaninta sweet.
Da sanda ya shiga kamar barawo ya tarar da ita
a kwance tana kuka. Motsi kadan yasa ta juyo
tana kallonsa idanunta jazur sun kankance. Fitar
min daga daki munafuki.
Zai yi magana ta hana shi ta hanyar daga masa
hannu...wallahi nayi regretting aurenka
Huzaifa...ka cuce ni.
A kan gado ya ajiye jakarsa da white coat
sannan ya zauna. Yau kuma me nayi Fadila?
Meyasa kike son tadawa kanki hankali a banza?
Kin san yanayin aikina tun kafin ki aure ni amma
ke kullum zuciyarki bata kitsa miki komai sai
zargi. Ta ce to ka rasa abinda zaka zama sai
likitan mata sai kace wani namamajo. Indai ba
tsabar son mata ba meye na specializing akan
cututtukansu eyye?
Ledojin da ya shigo dasu ya tura mata. Fadila
kiyi hakuri don Allah. Ban taba tunanin cin
amanarki ba. Lokacin da kika kira ni dazu ina
duba patient ne. Kinga its against dokar asibiti
ace kana duba mara lafiya kana waya. Ledojin
da ya ajiye ta janyo tana lekawa daya bayan
daya...to ai kaine Huzaifa sai ka rinka kula duk
wata mace nurse ko patient. Ta dan gutsiri
chocolate kaga ai dole na rinka zarginka. Amma
komai ya wuce.
Ajiyar zuciya yayi ya tashi zai shiga wanka.
Fadila ta bishi har kofar toilet din...Abban Aliya
don Allah kada kaci amanata. Ina tsananin
sonka shiyasa nake kishinka da yawa. Gefen
fuskarta ya shafa tare da daga mata
gira..soyayyar da kike min ce ta hana ki ce min
sannu da zuwa dana dawo? Sunkuyar da kanta
tayi kasa kayi hakuri bazan sake ba. Yanzu ma
sharrin shaidan ne. Yayi murmushi haka kika iya
ai.
Aishatu kuwa bayan ta karbi magangunanta gida
ta tafi. Mamanta Hassana ta gani tare da wasu
mata biyu sun zo taya awakin da suka yi mata
saura. Da faraa ta shiga gidan ta gaishe su. Sun
gama daidaitawa akan dubu shahudu zasu sayi
guda hudu. A dole Mama ta amince suka bata
kudin suka kada awakin. Duk abinda suke yi
Aishatu tana gefe tana kallonsu tana share
kwalla. Suna fita tace Mama meyasa kika sayar
dasu. Su kadai suka rage fa. Hassana ta yi dan
murmushi to Shatu idan bamu yi miki ba waye
zaiyi miki? Duk halin da kika tsinci kanki
qaddara ce amma laifinmu ni da Babanku.
Saboda haka ni dai ina sake baki hakuri ki yafe
mana kada mu hadu da fushin Allah. Shatu tace
ni ki dena cewa na yafe muku. Kamar yadda
kika fada qaddara ce kawai.
To naji yanzu ya kuka yi a asibitin? Kinga likitan
da Lawisa ta ke fada. Eh Aishatu ta amsa
sannan ta bata labarin yadda suka yi.
Kwana biyu da fara shan magungunan da Dr
Rano ya rubuta mata taga kurajen sun fara
motsewa da kansu. Hakan yasa kaikayin ya fara
raguwa. Babanta Mal Sa'id Jaafar yana ta
fafutukar wani abokinsa ya biyashi bashin da
yake binsa abin yaci tura. Dan pansho din da
ake bashi ma na tsohon malamin makaranta
wata na uku kenan shiru. Duk ya damu saboda
kanwar matar sa Lawisa ta fada masa ciwo irin
na Shatu yana bukatar kudi. Shi kuwa tunda
shine yayi silar kamuwarta da ciwon dole yayi
iya yinsa don yaga ta sami lafiya. Mashin dinsa
ya bugar ya bata wani abin abu a cikin kudin,
sauran kuma ya ajiye saboda bukatun gida.
Bayan kwana uku ta shirya ta koma asibitin.
RASHIN GODIYA ✂ 4
Aishatu sammako tayi saboda kada ta tarar da
layi,amma duk da haka akwai wurin mutum
takwas a gabanta. Hira suke yi abinsu ita kuwa
seat din layin karshe taje ta zauna saboda kada
a fara gudunta yadda aka saba. Tana nan zaune
tana duba wani littafin addu'o'i daga Quran da
Sunnah wata mace da a kalla zata bata shekaru
goma tazo ta zauna kusa da ita. Kayan jikinta
ma abin kallo ne. Kana ganinta kasan akwai
wadata. Aishatu na ganin haka ta tashi tsam ta
koma wata kujerar nesa da matar. Ga
mamakinta sai taga ta taso tazo kusa da ita ta
zauna. Aishatu ta sake mikewa sai matar tace
haba yar uwa me nayi kike guduna haka. A dan
kunyace tace yi hakuri ba gudunki nake ba. Baki
ji wari ba da kika zauna kusa dani? Yar dariya
matar tayi har hakorin makkanta ya
bayyana...kinga yi zamanki nima irin lalurar dake
tare dake gareni. Aishatu ta dan gyara zama wa
ya fada miki? Risikat matar ta nuna mata. Cewa
tayi mu zauna tare tunda duk Dr Rano zamu
gani. Aishatu tace au..amma ke banji kina wari
ba.
Dariya matar ta zake yi. Ni sunana Sauda ke
fa? Sunana Aishatu
Sannu Aishatu. Kin dade da ciwon ne? Kafin ta
bata amsa nurse tace Aishatu Sa'id.
Tashi tayi ta tafi room 3 inda Dr Rano yake.
Bayan ya amsa sallamarta a bakin kofa ta tsaya
taki karasowa. Fuskarsa ba faraa sosai
sakamakon fadan da sukayi da Fadila kafin ya
fito.
Ganin da yayi ma Aishatu kamar a tsorace take
da dashi yasa ya dan saki fuska. Zo ki zauna, ya
dan kalli file din Aishatu ko? ya jikin?
Da sauki Alhamdulillah.
Kina ganin canji da kika fara shan magani?
Eh ina gani
Yayi Bismillah kamar yadda ya saba idan zai
fara duba mara lafiya ya dauko result din test
din da aka yi mata. Kinga infection kika samu
wanda yake barazanar taba miki mahaifa
sakamakon rashin zuwan ki asibiti da wuri.
Mahaifa likita ta fada a dan tsorace, yanzu
bazan haihu ba?
No ba haka nake nufi ba, da kinzo da wuri dai
bazai kai haka ba.
Wasu magungunan ya rubuta mata sannan yace
ina bukatar duk panties dinki ki zubar dasu. Ki
sayi sababbi kamar shida. Su ma zaki rinka
wankesu da ruwan zafi da dettol.
Sai kuma ki rinka amfani da pad saboda
discharge din. Kiyi amfani da atleast hudu
kullum. Ki yawaita tsarki da ruwan dumi ko da
bakiyi abinda ke bukatar hakan ba.
Kanta a kasa saboda kunya ya dan rage murya
kina jina kuwa Aisha? Tana dago kai suka hada
ido.
A daidai lokacin aka banko kofa da karfi sai da
suka mike gabadayansu.
Fadila ce ta shigo a harzuke da wata farar shirt
a hannunta...Huzaifa meye wannan? Ta nuna
wani jan shati a jikin rigar. Janbakin wace
shegiyar ne haka? Da so kayi ka rufe ni ko, to
Allah Ya kamaka. Ina hada kayan wanki
naganta. Wallahi idan baka nuna min yar iskar
da take neman hanani zaman lafiya ba sai na
tara maka jama'a.
Aishatu sai ta kalleshi ta kalli matar. Idanunsa
sunyi jawur ya rike karfen kujera da
hannuwansa. Da gani kasan daurewa yake kada
ya karasa gabanta ya shaketa.
A hankali yake magana yanzu Fadila da izinin
wa kika fito? Kuma wurin aikina ne kika ga ya
dace muyi wannan zancen. zata sake magana
ya kama hanunta ya kalli Aishatu idan zaki iya
ki dawo karfe biyar, sai in ganki a lokacin. Ya ja
hannun matarsa suka fita.
RASHIN GODIYA ✂5
Aishatu ta dade a tsaye tana mamakin wannan
al'amari da ta gani, wannan matarsa ce ko
budurwa? Nurses din da suka ga fitowar Dr
Rano suka sami abin gulma. Ba karon farko ba
kenan da Fadila ke zuwa. Ita dai Aishatu fitowa
tayi a sanyaye ta koma wurin zamanta ta zauna.
Shaf ta manta da Sauda sai da tace mata har
kin gama? Tace a'a likitan ya fita ne amma yace
zuwa karfe biyar zai dawo.
Sauda ta tashi to ai gara mu tafi gida. Yanzu fa
sha biyu da kwata ai kinga akwai zama. Aishatu
ta gama yanke shawarar zama a asibitin don
kudin hannunta take tsoron yiwa gibi kada ta
kasa siyan magani. Sauda ta dan tafa hannu
tunanin me kike yi ne? Tashi mu tafi mana.
Uhmm ba komai ki tafi kawai ni zan jira har
biyar din.
Sauda tace ko gidanki da nisa ne? Eh Aishatu ta
amsa ta dan gyara zama. Kudin da zata kashe
daga yan kaba zuwa gwammaja gidansu ai ba
kadan bane. Gara kawai ta jira ta gama
gabadaya.
Sauda tana ta kallon yadda Aishatu ke zama
lost in her thoughts tace kinga layi biyu zaki
wuce tsakanin asibitib nan da gidana. So ki zo
muje ko don yin sallah. Da farko Aishatu taki
yarda sai da Sauda tayi ta roko da magiya.
Wata farar benz taga Sauda ta nufa. Suna shiga
ta kunna AC din motar ta ja suka tafi. Basuyi
tafiya mai nisa ba suka je gidan Sauda. A ranta
Aishatu tace tsabar gata yar wannan tafiyar ma
sai an shiga mota. Wani dattijo ya taso ya bude
musu gate, Sauda cikin ladabi ta gaishe shi
sannan ta shiga tayi parking din motarta.
Yara biyu ne duk yan mata wanda babbar bata
wuce shekaru goma ba suka taho wurinta da
gudu suna mata sannu da zuwa. A tare suka
durkusa suka gaishe da Aishatu ta tambayesu
sunayensu. Babbar tace sunana Sajida wannan
kuma ta nuna kanwar sunanta Islam. Wadda aka
kira Islam ta suma kuka Umma kinga ta fadi
suna na bata jira na fada ba ko. Aishatu ta
durkusa a gabanta tana rarrashinta ni banji me
ta fada ba ma. Islam tayi wa Sajida gwalo Allah
Ya kara bata ma ji ba. Sajida tace Umma kin
ganta ko. Anti sunana Aisha amma Islam
Ummana take kira na. Aishatu tayi murmushi
ashe ma sunanmu daya. Islam sai murna ta rike
hannun Aishatu. Sauda tace to kaji ya isa haka
fadan kun tsare min bakuwa a waje.
Falon gidan Sauda ma abin kallo ne ga Aishatu.
Bayan sunyi sallah Sauda ta kawo musu abinci.
Da kyar Aishatu taci kadan saboda ta kasa sakin
jiki da Sauda. Suna gamawa Sauda tace naga
baki kira mijinki kin sanar dashi ba kada yaji
shiru. Aishatu ta dauko yar motsatstiyar wayarta
da tasha salatif, batir din wayar ma ana ganinsa
don bata da cover din baya. Mama ta kira ta
sanar da ita. A dan zaman da suka yi Aishatu
ta fahimci Sauda tana da kirki shiyasa ta dan
saki jiki da ita. Sauda tace mijinki yana karbar
treatment kuwa? Don idan ke kadai ke shan
magani indai yana da infection bazaku warke ba.
Aishatu ta ce auren ya mutu.
Ba dai dalilin ciwon ba ko. Allah sarki. Kinga ni
na kawo mana ciwon nan gida gashi watan mu
na uku kenan da fara neman magani kuma
Alhamdulillah sauki ya fara samuwa. Musamman
bayan mun fara ganin Dr Rano.
Aishatu tace ai naga kamar yasan abinda yake
yi. Nima kwana na uku da fara zuwa amma
kinga kaikayin ma ya ragu sosai.
Haka suka zauna suna ta hira. Har Sauda ta
bata labarin yadda ta sami ciwon ta. Wato
Aishatu duk macen da bata da godiyar Allah
komai kudi komai rashi to tana tare da matsala
babba a rayuwa. Ni kinga Baban Sajida babu irin
abinda baya min na jindadin rayuwa. Duk kasar
da yaje saboda yanayin aikinsa sai ya yi min
tsarabar sutura mai yawa. Allah Ya hada ni da
wata makociya mai rokon tsiya. Itama fa mijinta
nada rufin asiri amma roko tamkar a jininta
yake. Kuma aron na kaya ne. Daga hijab zuwa
mayafi ta fara. Kafin na ankara mun fara
exchanging kaya. Ta karbi nawa taje taro nima
na karbi nata. Duk abinda akeyi maigidan bai
sani ba. Sai wata rana naje gidan zamu biki tare
na fara period duk na baci. Kawai ta dauko min
pant a cikin kayanta ni kuma ganin mun zama
daya kawai na saka. Wallahi Aishatu sai da
baban Sajida yayi kusan wata uku baya fita
saboda irin kurajen da muka rinka yi. Ga wani
ruwa mai wari...nayi kuka nayi dana sani sosai,
baki ga yadda na rinka bashi hakuri ba don na
zata saki na zaiyi wallahi. Kinga sai ya gaggauta
gama gininsa muka dawo nan don ya raba mu.
Shiyasa yanzu ladabin da nake masa ko kadan
nasan banyi rabinsa ba ma da.
Aishatu ta jinjina labarin tace amma Anti Sauda
gara ke sau dubu akai na. Ni da kika ganni
namiji duk kyansa akai kasuwa. Sauda tayi
dariya haba kanwata ayi haka kuwa...Aishatu
tace ai anyi ma.
Labarin Aishatu Sa'id Jaafar
RASHIN GODIYA ✂6
Iyayen Aishatu duk yan garin Getso ne a jahar
kano. Babanta Mal Sa'id yayi karatu har NCE
yayi. Bayan ya gama ya sami aikin koyarwa a
makarantar gwamnati sannan ya auri Hassana
mahaifiyarsu. A Gwammaja ya ke zaune tare da
iyalinsa Allah Ya azurta su da 'ya'ya hudu.
Aishatu ce babba sai kannenta maza uku Sadiq,
Nurain da autansu Mahmoud. Iyayensu suna
zamansu lafiya. Hassana tana kiwon awaki da
tumaki sannan tana sayar da zobo.
A haka yaransu suka yi karatu. Aishatu tana aji
biyar a secondary school ta hadu da Fahad sun
tare da iyayensa a kusa da gidansu. Tun da ya
ganta yake sonta idan yayi mata magana ko
kallo bai isheta ba saboda tana ganinsa da su
Garzali daya daga cikin fitinannun unguwar.
Babban burinta a rayuwa ta zama lawyer.
Lokacin tafiya teaching practice Fahad ya
nemi makarantar su Aishatu. Nan fa yan mata
da yawa suka nuna mishi so saboda dan gayu
ne na ajin karshe. Kullum kayan jikinsa sai kaga
karin guga ya saka turare yana baza kamshi.
Lifan dinsa kuwa kafin a tashi sai yasa maigadi
ya kara wanke masa shi. Duk abinda yake yi
don Aishatu tayi noticing dinsa ne, ita kuwa ko a
jikinta. Karshe ma tunda ya rinka nunawa kamar
kanwarsa ce ita tunda su makota ne sai ta biye
masa. Duk yarinyar dake sonsa sai ta rinka
kamun kafa da Aishatu.
Duk hanyar da Fahad zai bi don ya sami kan
Aishatu yayi amma abin ya faskara. Karshe
Fahad dai mahaifinsa yasa yaje gidansu Aishatu
nema masa aurenta. Mal Sa'id ya yaba da
karamci irin na gidansu Fahad da yadda suka
fara tuntubarsa kafin ma yayi magana da
yarinyar. Wannan dalilin yasa ya yi alqawarin
bawa Fahad auren Aishatu bayan ta gama
WAEC. Amma da sharadin zata cigaba da karatu
bayan anyi auren.
Tunda Babanta ya sanar dasu Mama ke ta
murna. Ko ba komai yaron yana da nutsuwa a
ganinsu. Duk kawaici irin na Aishatu sai da ta
nuna bata so har ta sanar da iyayenta irin
abokansa na unguwar. iyayenta suka ki yarda da
maganarta, a ganinsu samun dan mutumci
kamar Fahad a irin wannan zamanin sai an tona.
A haka Fahad ya rinka bibiyar Aishatu da dukkan
kyautatawa tana wulakanta shi son rai. Idan
yazo sai Mama ta fattattake take fita.
Wata rana yana mata hira a soron gidansu ta
hade fuska. Ita ko kadan bata son Fahad, taki
jinin namiji mai ji da kansa kawai don yana da
kyau. Wannan kuwa halin Fahad, suna zaune sai
juya wayarsa yake yi. Sabuwar model ce don sai
da ya sayar da tv din dakinsa ya cika ya saya.
Duk yadda yaso ta nuna tayi noticing wayar ma
taki. Can yar karamar wayarta tayi ringing taga
sunan dan wan babanta Kamal. Da sauri ta
dauka harda kara kashe murya don Fahad yaji
haushi. Nan ta rinka magana cikin jan hankali
har Kamal sai da yayi mamaki. Kusan minti
ashirin yana son ajiyewa tana sake jan hirar.
Iyakar kulewa Fahad yayi don shi mutum ne mai
tsananin kishin abinda yake so.
Tana gama wayar ta dan kalle shi ni zan shiga
gida sai da safe.
Tasss taji ya dauke ta da mari, ni zaki yiwa
wulakanci Aisha? Don kinci saa nace ina sonki.
Duk masifar da yake mata bata fahimta saboda
yadda marin ya shigeta. Hawaye ne kawai yake
wanke mata fuska. A zuciyarta ta kudire bazata
taba yarda ta aure shi ba.
RASHIN GODIYA ✂ 7
Ihunta yasa Mama ta fito soron da gudu.
Aishatu me ya faru? Ta kalli Fahad ..me ya
sameta Fahad. Aishatu zata yi magana ya
durkusa har kasa gaban Mama sai ga hawaye a
idanunsa kamar famfo, Mama cewa tayi ko zan
mutu na dawo bazata aureni ba. Nace ta manta
iyayenmu sun riga sun shiga maganar. Shine ta
soma kuka ita da ta aure ni gara ta mutu. Ran
Mama yayi matukar baci tunda tasan dama
Aishatun ba son Fahad take ba.ta dubi yarta da
ta rike kumatu kin kyauta Aishatu tunda ke kike
da iko akan ki ba mu ba. Bari babanki ya dawo
zan sanar dashi gara ayiwa tufkar hanci mara
kunyar banza.
Wallahi Mama sharri yake min. Mari na yayi
Wani marin taji daga mahaifinta da ya shigo
gidan a lokacin kuma duk yaji abinda suka ce.
Wato ke ban isa da ke ba ko. Da ina miki kallon
saliha ki rinka mikil mikil da ido kamar
mutuniyar kirki.
Fahad ya durkusa a gaban Mal Sa'id yana bashi
hakuri. Baba ni na janye gara a bari ta zabi
wanda take so. Baba yace ai bazaayi haka ba
Fahad, ka turo min Alhajin gobe muyi magana
asa lokacin biki. Sai nayi maganin wannan
rashin kunyar taki.
Mama tace kayi min daidai, suka shige gida
suka bar Aishatu da baki a bude. Fahad ya yi
mata wani kallon banza..kadan ma kika gani
Aisha. Ni din nan nafi karfin mace ta wulakanta
ni. Macen ma irinki wadda bata gama wayewa
ba. Yana gama magana ya fice abinsa.
Daren ranar Aishatu tasha kuka. Mama na jinta
duk tausayinta ya kamata amma ta share.
Yarinya alkhairi na bin ta tana sa kafa tana
shurewa. In ba haka ba meye aibun Fahad.
Iyaye maza sun hadu an tsayar da biki wata
biyu. Hakan yayi daidai da gama jarabawar
qualifying da Aishatu zata yi. Ba karamin tashin
hankali ta shiga ba jin cewa ko SS3 baza tayi
ba. Wan babanta ba yadda baiyi ba amma Mal
Sa'id yaki hakura. Tun wan nasa Alh Dalhatu
yana fada har ya koma nasiha saboda yasan
kafiya irin ta kaninsa. Suna zaune a dakin
mahaifiyarsu a Getso, Alh Dalhatu yace wai
Sa'idu shin yaron nan ko iyayensa sun maka
wani abu ne da ka kafe sai ka bashi 'ya.
Gwaggo Juma tace banda lalacewa ma ai dan
uwanka ya dace ya bada ita ba kai ba. Baba
gyara zama ni dai kuyi hakuri amma yarinya
karama bata isa na rinka sa'insa da ita akan
maganar aure ba. Jiya fa a gabana ta kare
masa tanadi da yazo. Har tana cewa shi makiri
ne. Yaya kaji fa, dama ya fada min a makaranta
ake hure mata kunne. Shiyasa nake son cireta
kowa ya huta. Duk shawarar da aka bawa Baba
sai ya kawo uzurinsa. Dole suka kyale shi da
matarsa suka rinka shirye shiryensu na biki.
Lokacin kamar yasan Aishatu gudunsa take ya
rinka sauri. Ranar larabar da suka gama
jarabawa akayi kamunta. Kawayenta sunyi
mamaki sosai don babu wanda ta fadawa.
Mamakinsu

Please Login or Register in order to submit comment