Reading RASHIN GODIYA by HAYATU BABA ZUBAIRU Chapter 2 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya karu da suka ga Uncle Fahad ta
aura. Daga masu tayata murna sai yan hassada.
Kyakkyawan mutum kamarsa ya kare da
Aishatu. Ba wai bata da kyau ba amma kyale
kyalen rayuwa basu dameta ba. Ranar asabar
aka daura aure da yamma aka kaita dakin
mijinta.
RASHIN GODIYA ✂ 8
Aishatu zaune gaban kakarta Gwaggo Juma, tayi
kuka har ta gaji. G.Juma ta kawar da kanta gefe
ta share yar kwallar da ta taho mata. Ba don
Aishatu yarinya ce mai kyaun hali ba da ba zata
damu ba saboda irin abinda Baba yayi musu na
nuna musu iyakarsu akan yarsa. Kiyi hakuri
Aishatun Nabiyy, wadda kika gaji sunanta uwa
ce ga dukkan mumini kuma duniya ta shaida
mace ce ta kwarai. Aishatu cikin kuka tace ni
Gwaggo Allah idan aka kaini guduwa zanyi.
Kowa yaki ganewa amma Fahad mugu ne ga iya
sharri. G. Juma ta rufe mata baki da hannunta
wanda yasha jan lalle gabadayansa, kul kike irin
wadannan maganganun. Ya riga ya zama
mijinki. Kuma idan har na isa dake zaki yi
amfani da shawarar da zan baki. Ki rike Allah ki
tsayar da gaskiya a dukkan lamuranki. Kiji tsoron
Allah kada ki tarwatsa rayuwarki kawai don ba
kya son mijin da Allah Ya rubuta zaki aura. Duk
matan da suke guduwa ko kashe miji saboda
kiyaya wallahi komai dadewa sai sunyi dana
sani. Ki auri mijin da ba kya so ma ai jarabawa
ce. Idan kika yi hakuri kuma kika dage da
kyawawan halaye sai kiga Allah Ya daidaita ku.
Idan ko har babu alkhairi a auren to da sannu
Allah zai warware shi Ya baki rabonki. Duk
abinda hakuri bai baki ba to rashinsa ma bazai
baki ba. Ni so nake ko bayan babu ke idan ana
kwatancenki ace ke mace ce mai biyayya ga
Allah. Shiyasa kika bi mijinki sau da kafa.
Aishatu ta dago kanta ta kalli fuskar kakarta
nagode Gwaggo. In Sha Allah zanyi amfani da
shawararki. G. Juma da sauran yan uwansu
suka tashi suka tafi dama motocin kawo amarya
suka biyo.
Fahad da kansa ya shigo gidan ya tarar da yan
kawayenta uku da basu tafi ba yace su fito kada
su rasa mota. Daya daga cikinsu tace haba
ango ai baka sallame mu ba. Dari biyu ya zaro
daga aljihunsa ya mika mata, gashi nan ku shiga
mota. Allah Ya bamu alkhairi. Ganin yadda ya
hade fuska babu wadda ta sake magana suka
da uko jakunkunan su suka fice.
Duk muguwar niyar Aishatu na cusguna masa
shawarar G. Juma tasa ta watsar. Shiyasa da
ya shigo dakin da sallama ta amsa masa fuska a
sake. Wuri ya samu ya ajiye ledar hannunsa.
Kaza ce guda daya gasashshiya sai juice mai
sanyi. Kitchen ya tafi ya dauko plate ya zuba
kazar gaba daya ya dan barbada yaji a kai ya
fara ci ko kallon Aishatu bai yi ba. Ba dai tace
bata son shi ba. Zata gane bata da wayo don
yana da mugun riko. Gidan da suke sama da
kasa ne da babansu yake ginawa yaransa. Kasa
yayansa ne Khalid da matarsa Maryam da
yaransu biyu. Saboda riko irin na Fahad ya dena
kula wan nasa saboda ya hanashi aron mota.
Aishatu tana ta kallon ikon Allah sai da Fahad
ya cinye naman gaba daya ya shanye juice
dinsa. Dama karamin kwali ne daidai shan
mutum daya. Yana gamawa ya shiga toilet yayi
wanka ya fito ya nemi wuri ya kwanta. Da tana
sonsa ba karamin haushi zata ji ba amma yanzu
dariya ya bata. Tana nan zaune taga da gaske
dai bazai kula ta ba sai ta tashi ta dauki wata
doguwar riga da hijab ta shiga toilet ta canja
kaya. Da hijab din ta fito a jikinta ya dan tabe
baki meye kike ta wani rufe jiki kamar abin
arziki ne a ciki. Ita dai bata ce komai ba ta
shimfida abin sallah ta tayar. Kafin ta idar yayi
nisa a baccinsa. Itama tana idarwa bacci ya
dauketa akan abin sallar.
Mafarki takeyi wai kunama ta harbi babban dan
yatsanta na kafa wani irin zafi har tsakar kanta.
Tayi saurin bude ido da salati ta ga Fahad tsaye
a kanta yasa kafa ya take mata dan yatsan
kafa. Tayi saurin janye kafar lafiya Fahad taka ni
fa kake yi. Karfe nawa yanzu kina kwance kina
baccin asara. Ba sallah ba girki bare na ganki
kinyi wanka. Tayi sauri ta tashi tana shafa dan
yatsanta. Kayi hakuri in sha Allah bazan sake
ba. Ki wuce akwai dankali da kwai ki soya kuma
kada ki bata lokaci don yunwa nake ji.
Sallah kawai Aishatu tayi ta shiga kitchen din.
Dankali ta gani dan kadan an zube a kasa sai
kwai gudu biyu a cikin farar leda da bread.
Zama tayi ta kirga dankalin, guda ashirin ne cif.
Ikon Allah lallai Fahad mutumcinsa ragagge
ne...sai tayi saurin rufe bakinta da hannunta
Astagfirullah...lallai Fahad mutumin kirki ne.
Ta soya dankali da yayi kukut a plate da kwai
guda biyu ta hada da bread din duk ta dora akan
tray. Sannan ta zuba ruwan zafi a flask ta kai
masa falo. A gabansa ta ajiye komai ya share
dankalin da kwai ya rage mata bread. Bata nuna
bacin rai ba ta hada tea ta sha da sauran bread
sannan ta dan yi gyare gyare a gidan.
RASHIN GODIYA ✂ 9
Dayake aikin ba wani mai yawa bane bata dade
ba ta gama tayi wanka. Duk da ita ba mai yin
kwalliya bace amma yau ta bata lokaci sosai a
gaban madubi. Addua take Fahad ya dena
fushin da yake da ita har ta sami damar rokonsa
ya barta ta cigaba da karatu.
Riga da skirt ta saka dinkin yayi mata kyau
sosai. Jikinta yasha turare kala kala ta fito falo
ta same shi zaune yana duba wasu takardu.
Wata kujerar ta samu ta zauna Fahad zan sauka
kasa mu gaisa da matar Yaya Khalid. Ko kadan
bai nuna alamun ya ji ta ba bare ya bata amsa.
Fahad magana nake fa...Aisha shiru nake fa ya
bata amsa. Tasowa tayi ta durkusa a
gabansa...don Allah kayi hakuri da dukkan
abinda ya faru kafin muyi aure. Na gane
kuskure na kuma in Allah Ya yarda zan gyara. A
hankali ya dago suka hada ido....ko baa fada ba
Fahad kyakkyawa ne sai dai kuma kyan dan
maciji gareshi tunda bashi da halin kirki. Aisha
kenan daga kwana daya har kin rissina, ko dai
kazar da na ci jiya ban baki bace kike neman
yin rigakafi? To bari kiji in fada miki, na so ki
sosai da farko amma yanzu kin sire min. Auren
ma don na nuna miki kinyi kankanta ki ja dani
ne. Duk da ta tsorata da kalamansa bata karaya
ba ta rinka bashi hakuri. Kafa yasa ya shureta
ya fice.
A haka suka yi sati uku da aure ko matattakalar
benen yace Allah Ya isa idan taje. Tana daga
sama kamar tsuntsu sai dai ta ji hayaniyar yaran
shima ba sosai ba. Wata ranar litinin da safe
Fahad yana ta sauri zai je makaranta don a
lokacin yake level 4. Lectures gare shi karfe
takwas na wani malami mara kirki irinsa. Sai
sauri yake kamar zai tashi saboda ya makara.
Sai da ya gama shiryawa ya nemi assignment
dinsa da ya kai karfe ukun dare yana yi ya rasa.
Ga takardu da sauran books dinsa amma babu
paper din da yayi aikin. Aishatu tana goge
kitchen ya shigo rai a bace..to yar mara
mutumci ina paper din da kika sace min?
Kallonsa tayi ta watsar ta cigaba da aikin ta. Ya
daka mata tsawa Aisha ba magana nake miki
ba? Lokaci ya kure wallahi idan har ya shiga ajin
bazai karba ba. Nan ma shiru yaji ba magana.
Fizgota yayi cikin fushi idan na makara jikinki ne
zai fada miki. Naga yana miki kaikayi saboda
ban taba dukanki ba. A nutse ta yi masa
magana..ni ban taba maka komai naka ba.
Gudun kada wani abu ya faru ma yasa ko falon
ban gyara ba na bari sai ka fita.
Idan baki taba ba ubanki ne ya dauka?
Ba dai ubana ba ta bashi amsa tana kokarin
kwace hannunta da ya murde.
Idanunsa kamar garwashi jin agogon falo yana
kara alamun karfe takwas din tayi. Hannunta
yaja har falo yayi wurgi da ita akan kujera.
Goshinta ya bige da kujerar ta kwala ihu. Bai
barta haka ba ya soma dukanta.
Kofin tea din da ke hannun Khalide ne ya fadi
da yaji wani gigitaccen ihu da Aishatu ta saka.
Mikewa yayi da sauri sai ga Maryam ta fito da
gudu. Kaji ihun amarya ko? Don Allah kaje ka
duba kada ya kashe musu 'ya. Khalid yace
maryam kamar baki san Fahad ba. Yaron nan
bashi da kirki ko kadan yanzu ina zuwa sai ya
hada ni da Alhaji, shi kuma baya son laifinsa.
Matar ma ko sau daya bata shigo nan ba fa.
Maryam tace kaima ka biye masa ka hanani
hawa saman ba. Wani ihun suka ji tana bashi
hakuri ba shiri suka hau saman. A kwance take
ya daga kafa zai bige ta Khalid yayi saurin janye
shi. Ita kuma Maryam ta daga Aishatu wadda
goshinta ya tashi saboda buguwa ga jini a
bakinta. Tana kuka ta kankame Maryam tace
Fahad Allah zai saka min kuma in sha Allah sai
kayi carryover.
Khalid ya kalli kaninsa cike da takaici me tayi
maka haka kake dukanta. Yaya ba ruwanka da
iyalina,idan ba rainin hankali ba in zauna har
karfe ukun dare ina aiki ta dauke takardar don
mugunta. Khalid yace ka duba ko ina baka gani
ba. Na duba mana yana magana ya dauko
jakarsa kinji dadi tunda kin hanani zuwa
makaranta zan zauna a gidan muci uwar da
zamu ci dake. Kayan jakar ne gaba daya suka
zube a kasa saboda zip din a bude yake.
Papers dinne suka fara fadowa ya daukosu cike
da farinciki...Subhanallahi ashe da na gama a
jaka na saka don kada na manta su a gida. Duk
su ukun yaga suna masa kallon tuhuma yayo
wurin su Maryam. Don Allah Aisha kiyi hakuri
wallahi tsautsayi ne. kukanta kawai take taki
kallonsa. Daga yau na amince ki rinka zuwa
wurin Anti Maryam hira idan na fita. Nan ma
bata ce komai ba da yake bashi da kunya yace
Yaya ku tayani bata hakuri mana. Shi Khalid
ficewa yayi yana sauka ya kwalawa Maryam
kira. Aishatu ta kalle shi a tsorace kada ya
sake dukanta.
RASHIN GODIYA ✂ 10
Matsowa yayi kusa da ita yaja hannunta suka
zauna a bakin kujera. Kana ganinta kasan a
tsorace take. Hankici ya dauko daga aljihunsa
ya soma goge mata lebenta da ya fashe. Kiyi
hakuri Aisha nasan ban kyauta miki ba. Ina da
saurin fushi ne da riko amma zanyi kokarin
canjawa kinji. Kai kawai ta daga don bakinta ya
kumbura. Ya yi dan murmushi kinga bakinki
kuwa kamar an cusa fanke. A wahale tayi
murmushi yace ko ke fa. Ki daure mu gina
rayuwa mai kyau mu manta da dukkan abinda
ya wuce. Kin hakura? A yadda ya tsareta da ido
ai dole tace ta hakura ko don kada ya sake
dukanta.
Tun daga ranar Fahad ya koma lallabata. Sunje
gidan iyayenta da nasa sun gaishe su sannan ya
barta tana zuwa wurin Maryam ko ita ta zo ko
yaranta. Zaman su abin shaawa a lokacin
saboda Aishatu ta iya zama da mutane. Kuma
ladabin da take masa yasa ya kara sassauta
mata.
Matsalar da suka fara fuskanta ta fara daga
abinci da suke ci tare. Kullum suka zauna cin
abinci ita ce karshen tashi. Tun baya magana
har abin ya soma damunsa. idan ta fiye cin
abinci kiba zata yi, shi kuma baya son tayi kiba.
Dan jikinta a yanzu yayi masa shiyasa ko ciki
baya son tayi sai an kwana biyu tunda da
kuruciyarta. Wata shawara ya yankewa
zuciyarsa washegari ya fara amfani da ita.
Dama idan bashi da lectures kasuwa yake tafiya
wurin babansa. Ranar zai tafi kasuwa sun gama
breakfast tana fitowa daga kitchen taga ya kulle
kofar yasa key a aljihunsa. Lafiya ka rufe
kitchen din Fahad? Lafiya kalau, kawai na fi son
sai na dawo zaki rinka dora abinci sai muci a
alokacin. Likitoci sun ce yafi lafiya. Tohhh idan
naji yunwa fa ko nayi baki? Kada ki damu zan
saka fridge a falo sai a cika shi da ruwa. hannu
ta zira a aljihun rigarsa inda ya sa key din...kaga
bana son wasa Fahad ka bani don yau sinasir
zanyi har da su Anti Maryam nake son aikawa
kaga gara na fara da wuri. Hannun nata ya
kama ya matse tare da zaro key din Allah da
gaske fa nake. Wannan shegen cin da kika tsira
kwana biyu kamar gara bazan jura ba. Salon kiyi
muni kisa na fara kallon sirara a waje. Abu
kamar wasa sai ga Fahad ya fice da key din
kitchen. Haka ta koma girki biyu a rana. Daga
na safe sai na yamma bayan laasar. Shima da
kansa yake auna mata abinda zata dafa. Shi
kuwa a waje zai take cikinsa. Babu wanda tayi
yunkurin fadawa sirrin gidan ta. Kullum addua
take Allah Ya sa ya canja hali. Wata daya da
fara horon yunwar da Fahad yake mata ta rame
sosai ta kara haske. Anti Maryam tace kanwata
ko dai ciki gareki. Dariya kawai tayi ina ciki zai
shiga ana fama da yunwa??? Cikinta taji ya fara
murdawa saboda tsabar yunwa. Lipton kawai
suka sha yau da wani guntun bread. Da farko
daurewa ta rinka yi, a hankali abin ya fara
tsanani har Maryam ta lura. Aishatu ya dai me
ya sameki...jini ta gani yana bin kafar Aishatu ta
kamata da kyar suka shiga toilet sai ga wani
gudan jini kato ya fado. Anti Maryam ta ce
Aishatu bari kika yi fa. Dama ciki ne da ke?
Jikinta duk a mace tace ban san dashi ba anti.
Anti Maryam ta kira Khalid a waya yazo ya
kaisu asibiti lokacin Aishatu ko tsayawa bata iya
yi. Likita na dubata yace da Khalid ai dole tayi
bari. Mace da ciki ga yunwa tana neman yi
mata illa. Ai baa biyewa mata idan suna laulayi
mai hana cin abinci. Ko yaya sai a basu wani
abin da zai zauna. Shi khalid mamaki ne ya
kamashi wai yunwa! A gidan Fahad din? Lallai
dole Alhaji yaji wanan magana.
Sai da aka gama komai na asibitin aka sanar da
Fahad yazo. Iyayensu da sauran yan dubiya na
fita Fahad ya matso kusa da gadon ya rikewa
Aishatu hannu. Meyasa baki sanar dani kina da
ciki ba Aisha? Hawaye suna zubo mata tace
nima ban sani ba. Share mata hawayen dena
kuka kinji dama ni ba son haihuwar nake yanzu
ba. Sai na gama makaranta nayi service sai ki
haihu. Ashe shiyasa kika rinka shegen cin nan
kwanaki kamar ahalin yunwa. Kada ki damu zan
karbar miki maganin planning. Khalid da ke jikin
kofa yana jin abinda kaninsa ke fada yayi tsaki.
Allah wadaran halin yaron nan.
RASHIN GODIYA ✂ 11
Kwananta biyar aka sallameta. Kulawa kam tana
samu a wurin Fahad sai dai kullum dare kafin su
ci abinci zai bata kwayar magani. Lallabata yayi
yace maganin zai hanata daukab ciki yadda zata
samu damar komawa makaranta tayi WAEC da
NECO. Sai dai lokacin yanayi ya tsiri abinda zai
hadasu fada yadda bazai biya mata kudin ba sai
wata shekarar. A haka suka zauna har yayi
jarabawarsa ta karshe. Da murnarsa yaje
makaranta duba result. Abin bakin ciki yana da
spillover a course din da Aishatu tayi masa
addua ranar da yayi mata duka. Da bacin rai ya
nufi gida yau jikin Aisha zaiyi tsami ya fada a
ransa. Muguwar yarinya ashe da gaske tayi
masa wannan adduar.
A tsorace ta fito daga bandakin da PT strip a
hannu, Anti Maryam kin gani layi biyu ne.
Maryam ta rungumeta tana murna Alhamdulillah
Aishatu Allah Ya raba lafiya. Aishatu kuwa
jikinta har rawa yake tace na shiga uku na yau
me zan fadawa Fahad? Bangane ba Maryam ta
tambayeta. Abin arzikin ne kike cewa me zaki ce
masa? Karar babur dinsa ta ji yana turo shi cikin
gate din. Cikinta yayi wani mugun murdawa don
tsoro. Sosai Fahad yake jaddada mata rashin
son haihuwa a yanzu. Gashi ta dan samu saukin
irin yadda yake zama da ita. Ta fara zubar da
hawaye ba kakkautawa Maryam ta rike
hannunta suka zauna. Aishatu ko planning kuke
yi ne? Ita dai bata bada amsa ba ta tashi ta hau
sama a sanyaye.
Irin kallon tuhumar da yake mata yasa ta kara
tsorata kamar yasan abinda ya faru. Suna shiga
falo ya kama kofar ya kulle ya zaro belt din
wandonsa. Akan gwiwarta ta durkusa tana bashi
hakuri. Wallahi Fahad bansan haka zai faru ba.
Tsautsayi ne kayi hakuri.
Bai ko saurareta ba ya fara tsula mata. Har ni
zaki yiwa cuta irin wannan. Ta bude baki zata
kara magana yace rufa min baki makira. Dama
nasan har yanzu ba sona kike ba ahiyasa kike
min muguwar addua. To burinki ya cika na sami
carryover saboda haka kema haihuwarki ta kara
nisa. Sai na gama makaranta kamar yadda na
fada miki nayi service kuma sai na sami aiki. Ai
fadan da taji yana yi yasa ta fasa fada masa
tana da ciki. Gara tayi shiru kawai idan ya fito
idonsa ya gane masa.
Tun daga ranar aka koma gidan jiya. Ga rashin
wadataccen abinci ga wulakanci kala kala. Ko
kadan bata fada masa tana da ciki ba.
Wata alhamis ya dawo daga kasuwa a gajiye ga
yunwa bazai iya jira ya auna abincin da zata
dafa a lokacin ba. Indomie biyu ya dauko mata
yace ta dafa masa. Tun da ta dora amai yake
taso mata tana daurewa. Da kyar ta gama ta kai
masa ya bata guda daya yace ta dafa tace ya
kula jikinta ya fara budewa. Tana mikewa amai
ya kwace mata ta rinka kwarawa a wurin. Ya
tashi a fusace wai me kike nufi dani ne Aisha?
Ya zaki rinka min amai don ki haramta min
abinci. Abba dan maryam yana bakin benen ya
jiyo kakarin amanta ya ruga wurin mamansa.
Anti Aishatu zata yi amai Mummy. Da sauri ta
hau saman ta bude kofar falon. Aishatu ta gani
tana amai tana gyara wurin da ta bata. Duk tayi
kaca kaca da wurin. Maryam ta harare shi
amma kai dai Allah wadaran halinka. Mace na
fama da ciki kana kallo ka zuba mata ido tana
wahala. Ya kalli Aishatu da ta tsure ya kalli
Maryam. Ciki kuma??? Garin yaya? Me yasa baki
fada min ba. Baki na rawa zata yi magana
Maryam tayi saurin gyara zancen...dama
surprise zata maka to kuma yadda kayi mata
yanzu ne ya bani haushi shine na fasa kwan.
Sai da ta gyare wurin ta sauka a ranta tana
fargabar abinda zata jawowa Aishatu. Ai kuwa
taba fita sabanin ya nuna fushi sai ya nuna
kamar yana murna da cikin. Ai da kin fada min
da wuri saboda zuwa asibiti. Wata nawa ne
yanzu. Kai a kasa tace nima ban sani ba. Amma
ina jin zai kai uku. Masha Allah sannu kinji.
Sai dare yace ta dauko masa maganin da yake
bata na planning. Ya duba ya tabbatar bata
fashin shan maganin. Dan murmushin yake yayi
yana tunanin yadda zaiyi yasa cikin ya zube. Ina
shi ina 'ya'ya yanzu. Kuma sai ya rama abinda
tayi masa na muguwar addua. Ita kuwa Aishatu
ta gama saka rai da abinda ke cikinta. Duk
abinda Fahad ke yi mata bata damuwa burinta
ta haihu lafiya. Su Mama sai murna da ganin
cikin wanda har ya kai wata hudu. Fahad na
kwance akan gado lokacin ya rasa me ke masa
dadi don mamansa tace ya bawa Aishatu dubu
hamsin ta fara siyan kayan haihuwa. Sassaken
maganin daya karbo ya dauko yana kallo.
Gaskiya bazai iya bari ta haihu ba. Baya kaunar
'ya'ya yanzu ko kadan. Falo ya bita ya mika
mata jikon. Aisha ga wannan kisha saboda
saukin haihuwa. ta karba da hannu biyu nagoda
Allah Ya saka da alkhairi. Amin, bari na dauko
miki cup. Da kansa ya zuba ya bata. bata kawo
komai a ranta ba ta shanye shi tas. Cikin dare
suna kwance cikinta ya soma murdawa. Ta dan
taba shi Fahad cikina ciwo...wani murmushi ne
ya kwace masa yayi wata munafukar mika
sannu ko inyi miki tausa ne? Tana yunkurin
tashi daga kan gadon jini ya balle mata.
RASHIN GODIYA ✂ 12
Kuka Aishatu tasa masa Fahad don Allah ka
taimakeni kada na rasa wannan ma. Tasowa
yayi kamar gaske duk a rude. Bari na shiga toilet
gani nan zuwa. Bandaki ya shige ya bata lokaci
sannan ya fito. Zuwa lokacin Aishatu har ta fara
fita hayyacinta. Kinkimarta yayi kasa ya
bugawa su Khalid kofa Yaya don Allah ka
taimaka ka zo muje asibiti Aishatu ce ba lafiya.
Su ma duk sun rude haka Khalid yazo ya fitar da
mota suka tafi asibiti. Kafin su karasa Aishatu
tayi karamar haihuwa tayi barin cikin wata hudu.
Likitoci sun bata dukkan taimako don har wankin
ciki aka yi mata. Sai gabanin asuba ta farka
taga Mama da Hajiyan su Fahad a dakin. Suna
hada ido da Mama ta fashe da kuka. Hajiya ta
zo ta rungumeta...yi hakuri Aishatu qaddara ce
wadda bawa ba yadda zaiyi da ita. Ita dai
Aishatu kuka take yi kawai Mama tana bata
hakuri. Sai dare Fahad ya shigo...Hajiya ta fara
masa fada yace Hajiya ni bazan iya ganin
Aishatu a wannan yanayin ba. Duk mun gama
sa rai...sai hawaye sharr kamar yaro. Har kudi
na hada zan bata ta fara siyayya ashe ba
rabonmu bane. Mama tace haba Fahad kaine ya
kamata ka bata hakuri. Ku karfafi zuciyarku.
Haka suka yi ta basu baki. Baban Aishatu shima
yaji tausayin Fahad sosai don abinci ma baya ci
a cewarsa duk jikin matarsa ke damunsa.
Kwanaki uku da kwanciyar Aishatu tana bacci
dakin shiru Maryam ta tafi gida dama mata
kunu. Su Mama basu karaso ba sai ga Fahad ya
shigo. Ganin tana bacci ya hakince akan kujera
yana waya da Audu Kulli mai magani. Audu yace
mutumina kuma sai naji ka shiru ko maganin
baiyi bane.
Fahad yace inaaa mutumina ai gamu a asibiti
ma magani yayi kyau. Wallahi a ranar ma cikin
ya zube da daddare. Ai wannan karon allura
zansa ta rinka yi don naga maganin baya hana
daukar ciki. Da su na taho ma zan mayar da
sauran.
Sai da ya gama maganarsa Aishatu ta tashi rai
a bace. Allah Ya isa Fahad kuma wallahi sai na
fadawa su Hajiya. Ni ba karatu ba ni ba ga
haihuwa ba. Wace irin rayuwa ce wannan? Gara
ka sake ni in huta.
Mama ce ta bude kofar ta shigo...Aishatu ashe
baki da hankali har yanzu? Har yanzu baki
kwantar da hankalinki a gidan mijinki ba shine
kike cewa ya sake ki. Hajiya da ke bayanta tace
Hassana baki san halin Fahad ba. Allah kadai
yasan me yayi mata. Cikin kuka tace Hajiya
magani ya bani cikina ya zube.
Laaaahhhhh haba Aisha kada ki tona sirrinmu a
wurin nan. Mu bar zancen nan kawai bana son
abinda zai hada iyayenmu. Mama tace ko meye
Fahad ka fada don a gyara idan ma matsala ce
da ku ai gara kowa ya sani a daidaita ku. Ba
komai fa mama rigimarta ce kawai. Aishatu da
tayi saroro tana kallon Fahad don ta rasa inda
ya dosa. Hajiya ta ce kaga ba sa'anninka a
wurin nan ka fadi me ya faru ko mu fita mu
barka da matarka.
Hannunsa yasa a aljihu ya fito da maganin
planning da yake bawa Aishatu. Wanda ya
dauko ma har ya kusa rabi ya mikawa Mama.
Dazu da zan dauko mata kaya naga maganin.
Ashe shi take sha don kada tayi ciki. To da
Allah Ya kawo kuma shine suke zubewa. Ya fara
kuka....tace bata sona bazata yarda ta hada
zuria dani ba. Aishatu tasa ihu wallahi karya
yake min. Mama ta bige bakinta rufe min baki
mutuniyar banza. Duk abinda kika fada naji kafin
na shigo. Mungode tunda kin nunawa duniya
bamu isa ba. Hajiya ma bata ji dadi ba amma ta
daure kiyi hakuri Hassana mu bita a hankali.
Fahad yace banso fada ba don Allah kada baba
yaji zancen nan. Zamu daidaita a tsakaninmu.
Zance dai bai kare ba har aka sallameta. Kowa
ya juya mata baya banda Khalid da matarsa.
Har fadawa Alhaji abinda yaji Fahad na fadawa
Aishatu game da hana haihuwa yayi aka karyata
shi a gida. Sai da akayi mata fada sosai sannan
ta koma gidanta. Haka ta koma cikin rayuwar
kunci da bacin rai don wulakancinsa yafi na da
saboda goyon bayan iyaye da ya samu.
Wata shida da dawowarta yanzu ko abincinta
baya ci. Idan ya dawo gida zai auna mata
abinda yaga dama ta dafa taci sauran taci da
safe. Duk ta kara ramewa ga rashin kwanciyar
hankali. Wata rana tana zaune tana jin radio taji
ana bada labarin wata mata da ta zane mijinta
saboda baya bata abinci. Tayi dariya sosai taji
ina ma ita ce ta zane Fahad. Ai kuwa daren
ranar ya auna mata wake wai ta dafa taci da
mai. Yanzu don Allah a daren nan zanci wake?
Kaga fa tara da kwata idan naci cikina zai baci.
Daki yayi shigewarsa idan bazaki dafa ba ki
barshi mana. Nan take dabara ta fado mata,
tana jin alamun ya fara wanka ta tsala ihu iya
karfinta. shiru bai fito ba ta kuma yin ihun ga
maciji nan zai shigo bandakin ka fito Fahad.
Bata rufe baki ba ya fito jikinsa duk kumfa.
Akan kujera ya ganta a tsaye tana tsalle. Yana
ina ya rinka waige waige. Karkashin kofar daki
ya shije. Ni dai bazan kwana a nan ba kasa
zani. Ke bana son shirme bari na nemo maza a
waje su kore shi. Tace kai ma namiji ne...sarai
tasan ko a tv aka nuna maciji canja tasha yake
saboda ya taba saransa yana yaro a yadda ya
bata labari. Duk inda yaga abu a dan murde a
kasa ko tsumma ne ya rinka fada kenan.
RASHIN GODIYA ✂ 13
A baibai ya saka doguwar riga jikinsa duk yayi
jirwaye saboda kumfa da ta fara bushewa ya ce
ke ki tsaya a nan zan nemo masu taya ni fitar
dashi. Tace nima sauka zanyi, ko ka tsaya ka
fitar dashi kawai. Sai dai naga kato ne jikinsa
har sheki yake. Tsawa ya daka mata don a
tsorace yake yana ta waige waige...malama kiyi
min shiru kuma ban yarda ki sauka kasa ba, ya
fita da sauri. Tana jin ya sauka kasa ta
kyalkyale da dariya. Amma Fahad ya shahara a
keta, shine zai barta ita kadai da gaske ne ma
sai dai ya cutar da ita. Dakin ta shiga ta lalubu
keys din kitchen da yake fita dashi kullum ta
shiga toilet ta dauki sabulun wanka ta manna a
jiki yadda shatin key din zai fito a jikin sabulun
sannan ta mayar da key din inda ta dauko shi.
Wani bakin mayafinta ta dauko mai ratsin ja ta
murde shi sosai sannan ta jefa karkashin kujera.
Bayan ta gama ta ta koma falo ta cigaba da
ihun maciji.
A haka suka dawo suka tarar da ita. Ku shigo
tace hanyar daki yayi.

Please Login or Register in order to submit comment