Reading Deen Marshal By Mamuhgee Chapter 23 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

takesha tunda ita kadaice Saida yamma tayi na Daren idan yadawo suci tare.


Duk da kadaici da rashin zamansa sosai sai yamma bai Hana shaquwa me qarfiba Shiga tsakanin rayuwar auren nasu sbd baya fita aiki sai goma na safe ta wuce hakama karfe hudu zuwa biyar yadawo daganan Kuma shikenan bata wani motsi sai acikin jikinsa musamman da cikinta ya fito sosai Dan yanzu Yana wata shida haryana shiga na bakwai,
Tunda cikinya yafara tsufa kamar ansake jona musu juna sbd shi gabaki daya hannunsa koyaushe Yana cikin rigarta Kan cikin kokuma saman cikin duk yabi ya zare Mata cikin gidan bazaka taba cewama yasan yanda ake kame fuska ba duk da idan yanata tareda wasu kokuma suka fita kamewan dawowa take har itama Yana cika idonta.


Naj Bata samu kantaba Saida ya tabbatarda Babu wani sauran kunya a idanuwanta gurinsa musamman yanda ya mugun lalatata da saka 'yan iskan kayanda dasu gwara Babu Wanda harta Saba Dan idan tasaka Masa wasu kayan kasa zuwa office yake Haka zai lalace acikin gidan suna zuba soyayyarda duk motsi daya idan tayi saiya furta Mata kalmar I love you.


Sayayya kayan baby kuwa harta gaji da kaiwa dakin da akaiwa jeren komai na baby,
Asibiti Kuma dama duk bayan 10 days suke zuwa Ana dubata.


Cikinta baizo Mata da matsalar komaiba shiyasa tananan ayanda take saidai haske data qara sosai na samun lafiyayyar rayuwar hutu da Jin Dadi ko kumburi bataiba saidai tsini da cikin kawai yakeyi Wanda koyaushe yake cikin daukanta hoto.


Lokacinda su Hanifa suka dawo US tareda Isma'eel a _Ala Moana_ sunkai musu ziyara inda suka sauka a wani babban hotel Amma a gidansu Hanifan suka wuni duk da Hanifan zata koma taqarasa shiryowa tadawo gabaki daya.
Kwanansu biyar a garin kafin suka tafi saidai ba Honolulu suka komaba New York suka tafi taron wani aikin sojoji da akai acanma Saida sukai kwanaba goma kafin suka nufo hanyar dawowa gida.


Da daddare sosai suka iso Dan Haka suna isowa wanka kawai tayi ta kwanta sbd Yar gajiyan zama jirgi duk da Babu wani nisa sosai.
##MAMUH#




*****************************
*_AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE_*
08067558902
Manyan Mata,manyan yara dasukasan sunsan kansu afagen zagewa suyi gyara me kyau na musamman suzo ga gwanarmu wadda muka tabbatarda aikinta da kyawun kayanta,
*_AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE_* nada kayan gyaran Amare da masu haihuwa,gyaran jiki Dana cikin jiki harma dana fata Wanda take aikawa koina a fadin Nigeria.
Ta bangaren kayan Mata ma kuwa dukkanin kayan gyaran dakike buqata tanadasu kala kala masu kyau da tsafta tareda inganci da qarfi,
Mun tabbatarda aikinta shiyasa muka kawo muku tallarta.
*_AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE_*
08067558902






*_DM 52_*


*_AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE_*
08067558902
Manyan Mata,manyan yara dasukasan sunsan kansu afagen zagewa suyi gyara me kyau na musamman suzo ga gwanarmu wadda muka tabbatarda aikinta da kyawun kayanta,
*_AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE_* nada kayan gyaran Amare da masu haihuwa,gyaran jiki Dana cikin jiki harma dana fata Wanda take aikawa koina a fadin Nigeria.
Ta bangaren kayan Mata ma kuwa dukkanin kayan gyaran dakike buqata tanadasu kala kala masu kyau da tsafta tareda inganci da qarfi,
Mun tabbatarda aikinta shiyasa muka kawo muku tallarta.
*_AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE_*
08067558902
******************************


*_52_*
Washe gari Bata Farkaba sai qarfe goma na safe shima sbd ya tada itane da dumin numfashinsa dayake sauke Mata a cikin wuyanta Yana yawo da hannuwansa cikin fingalalliyar rigar baccinta wadda Koda cikin daya tsufa Bata daina saka Masa ire irensuba.


Wani irin numfashi ta sauke tana ware idanuwanta masu sauran bacci akan fuskarsa Dake daf da tata Yana Mata wani kallon da ita kadaice tasan ma'anarsa.
Ta dan lumshe idanu ahankali tana sake numfashin kiss din daya sakar Mata a bayan kunne tareda sake cusa kansa cikin kirjinta duk da girman cikinta na hanasa manne Mata yanda yasaba ta bude idanuwanta tareda zura hannuwanta ta saqalo wuyansa tana nufar bakinsa da nata kafin ta Isa ya qarasa zuro kansa ya hade bakinsu sukahau kissing juna cikin nutsuwa da soyayyar dasukeji me qarfin gaske akan junansu daga nan lalabo rigar jikinta yayi yaqarasa zareta ya jefar Yana mannuwa da jikinta sunan cigaba da kissing juna.


Wanka tafito ta shirya tareda sakan gown Mara nauyi me Fadi sosai guntuwa wadda take ta masu ciki ce, ta daure gashinta da ko kafin barowarsu New York taje beauty parlor angyara matashi tafito tana qamshin Tom Ford dinsa da wani lokacin shi take shafawa wayarta Kan kunnenta tana waya da Hanifa dake sanar da ita komawarta Nigeria cikin satin Inshallah.


Hanifa Nima inason zuwa sbd na haihu acan din amma nasan bazai yadda ba.


Hanifa tace"


Tabbas bazai yardaba sbd Nima munyi mgna dashi din na tambayesa yaushe Zaki koma ki haihu agida yace Babu inda Zaki anan Zaki haihu kafin kuje gidan daga baya.


Ajiyar zuciya ta sauke tana cewa"


Dama nasan bazai yardaba yanzu ke yaushene ranar tafi........kasa qarasawa tayi sbd cak muryarta ta dauke da abinda idanuwanta suka ganar Mata ahankali ta furta sunan Hannah tana kallon dining din da hannahn ke zaune sanyeda Jean and blouse na Burberry kanta da wula qarama Wanda ke nuni da kamar a gidan takwana,tasake maimaita sunan Hannah din tana qin yarda da itadince.


Hanifa dataji Naj takira sunan Hannah itama Saida gabanta ya Fadi cikin mamaki tace"


Wace Hannah Kuma?
Ba karatu takeba a qasar?yakamata ace tadawo tunda duka duka program din na 1year ne suna gabanin kammalawa me tazo Nan bayan ta tsaya tayi abinda yakaita qasar.


Cikin rashin sanin abin fada Naj tace"


Bari idan naji abinda tazo Yi zankiraki.


Kashe wayar tayi ta nufi dining din Kai tsaye
Hannah dataji tahowar qamshin Marshal ta waiwayo da sauri tana Kiran sunansa,ganin Wadda ke tsaye akanta yasata hadiye wani mugun abu daya taso Mata tana qurawa cikin Naj din data tsufa ido shedan na saka Mata fata da adduar Allah ya barar da cikin.
Daure fuska tayi Kamar yanda Naj ta Dan kame fuska ta dauke Kai Yana maida hankali kan abincin datake kokarin fara zubawa taci"


Kai tsaye Naj tabude Baki tace"


Zaki dakata sai maigidan yafito kafin kici komai,sbd koni danake Matar gidan banacin abinci saiyazo..


Isowarsa dining din Yana zuba qamshi yasa Naj sake Dan kame fuska ya Dan ranqwafa yayi kissing din gefen fuskarta kafin ya zauna Yana kamo hannunta daga tsayen datake ya zaunar a cinyarsa Yana kallon cikinta kafin ya kalleta cikin kulawa yace"


All ok??


Kallonsa tayi tana kasa hadiye zancen Dake ranta ahankali a natse tace"


Kasan da zuwantane??
Yaushe tazo??


Hannunta daya riqe yai kissing kafin yace"


Yes nasan dazuwanta,
Tazo jiyane,
Munacan takirani jiya akan ta kawo Mana ziyara bama Nan,inda taxo da nisa bazata iya komawaba a jiyan shiyasa nace Brian yaje ya daukota da mota ya kawo tunda muma a jiyan muka dawo.


Daga hakan baiqaraba ya kalleta Yana cewa"


Zauna kici abinci kinajin yunwa.


Gyada Kai kawai tayi batareda tace komaiba ko sake kallon Hannah din ta zauna a kujeran kusadashi tana fara cin abincin.


Har suka Gama bakin Hannah ne kawai ke tashi agurin Wanda duk da Marshal din take maganar Naj dai bayan kunnuwanta Dake saurare ko idanuwanta taqi Basu musamman dataga yanda yakeyi Yana kallonta akaikai.
Tana gamawa ta miqe tabar gurin Takoma bedroom ta zauna kan kujera tana sauraron yanda zuciyarta ke bugawa da zafi take idanuwanta suka cikoda hawayen baqin cikin barin Hannah ta zuwar musu harma da kwana gashi bataga alamar Hannah din zata tafiba ayau.


Saidata lallashi zuciyarta ta nutsu kafin ta miqe tasake fitowa lokacin tuni sukabaro dining Yana zaune Palo Yana waya Hannah din na zaune ta kafesa da idanuwa Kamar mayya tana kallon izzarsa da kamewarsa tareda ainihin sirrin kyau da kwarjini da Allah yayi Masa.


Qarasowa tayi fuskarta akansa tana sauya yanayinta zuwa bayyanarda nauyin da cikinta yayi Mata
Yana wayar ya dago yana kallonta tana tahowar ya miqa Mata hannunsa daya ta Kama ya zaunar da ita Kan qafafunsa da Yana kallon fuskarta da alamar lafiya dai ko?


Gyada Masa Kai tayi kafin ta Dan kalli Hannah data bala'in hade fuskar takaicin Naj da baqin cikinta Yana bayyane Kan fuskarta.
Cikin nutsuwa da muryarta me sanyi da Bata canjaba tace"


Hannah Yaya aiki zance ko karatu?


Banza Hannah din Tai Mata Kamar Bata jitaba saidataga Marshal din na kokarin Gama wayar kafin ta Dan kalli Naj din a wulaqance tace"


Ko wanne kike nufi lafiya kalau musamman yanzu dazan zauna Nan cikin na gida karatun zaifi tafiya kalau.
Gama wayar yayi tareda kallon Naj dake jikinsa ya kamo fuskarta da hannunsa dayan yakama bakinta yayi kissing kafin ya miqe Yana riqeda hannunta suka nufa kofa yakuma kissing hannunta yace"


Saina dawo,ki kula da kanki da Bby okay?????


Murmushi tasakar masa tana gyada Kai kafin tace"


Take care too.


Bayan fitarsa komawa tayi palonta ta zauna tareda daukan remote ta kunna TV tana kallo tana karba waya akai akai Bata sake bi takan Hannah ba.


Kamar yanda tasaba zuwan Hannah Bai hanata komaiba,data Gama abincin yamma taje tayin wanka ta sauya ado duk da ko lokacin ba wasu kaya masu takura tasakaba sai qamshinta takeyi tana fitowa Palo Yana dawowa,
Yana shigowa da Hannah dake zaune tana chatting a waya yafara cin Karo taci adonta Sama sama yake amsa gaisuwarta sbd Mrs dinsa daya hango tana tahowa gabaki daya tauke hankalinsa,
Wani murmushinda Hannah Bata taba gani a fuskar Saba taga ya sakarwa Naj din Yana Dan bude Mata hannu daya ta qaraso ta shige tareda rungumesa tana cewa"


Barka da dawowa.


Da ido ya amsa Mata suna wucewa zuwa bedroom dinsa Dan yayi freshen up.


Zuwan Hannah gidan Bai qareta da komaiba bayan gagarumin baqin ciki da takaici Dan tunda tazo babu iskan datake shaqa a gidan bana baqin ciki da takaiciba.


Naj gabaki daya ta iskance a gidan tagama lalacewa Marshal Wanda shikuma dama hakan yafiso shiyasa gidan yafara gundurar Hannah Amma ta nace taqi tafi,
Ko ina,kowane lokaci Naj cikin jikinsa acikin gidan,
Kiss kuwa a gidan Kamar ruwan Sha suka daukesa ya koyar da ita hakan,
Dakansa yafara gundura da zaman Hannah a gidan sbd sunsaba koina harkokinsu sukeyi Amma yanzu kamai ya dauko saidai bedroom dinsu.


Itadai Naj Bata bi takan Hannah sbd yanzu batada wani fargaba akanta damuwanta dayane yanda tayi tayi dashi akan Hannah din Takoma inda tafito Amma yace tabarta ta zauna harta tafi Dan kanta sbd kamar sun samu Dan break ne program din datake.


Hannah Bata fara kawowa Naj matsala ba sai dataga Naj dai dagake tako Ina tagama cike Marshal da rayuwarsa Baya iya ganin kowace mace sai ita Dan Haka taqi yadda da amincewa hakan tafara yiwa Marshal din shishigin son nuna itama matarsa zata zama Nan gaba.


Gabaki daya shi baisan abinda yake faruwaba a gidan sbd rashin zamansa dakuma koya dawo yanzu Bai cika zama Nan palonba Yana dakinsa wannan sabon tsarin Naj ne wadda Hannah takaita iya maqurar hakurnta Dan kuwa yanzu dai da qarfi da yaji take Kai kanta garesa musamman idan Yana dakin geamin acan tafi samunsa sbd lokacin Naj na baccin safiya.


Al'amarin yafara isar Naj takira Hanifa cikin damuwa take fada Mata maganar sbd Yan kwanakin har fada sunyi akan tace sai Hannah ta tafi shikuma can mum Malika takirasa tasakasa Masa tattausan lafuzan roqan alfarman Hannah ta zauna gidan taqarasa 'yan kwanakin program na karatunta daya rage Mata.
Ya amince da hakan shiyasa yanzu zamanta gidan yakeda matsayi tunda ta tashi daga baquwar datace tazo weekend gashi yanzu kullum idan zai fita da safe kusan tare suke fita ya ajeta a Hanya taqarasa da taxi ko bus.


Numfashi Mai zafi Hanifa tasake cikin mamakin mum Malikan da Hannah dama takaicinsu tace"


Mezaisa qatuwar tsohuwar budurwa kamar Hannah tazo tazauna gidanku bayan ko haihuwar farko bakuiba,bayan hakan kowa yasan cewa son mijinki take batun yanzu ba.


Kalmar sonsa da Hannah keyi da Hanifan tafada ita tasake kashe jikin Naj din ta rintse ido kanta na neman sarawa zuwan Hannah gabaki daya ya hanata sukuni yanzu duk da Bata taba Bari Hannah din tagano rashin kunin nataba dashima kansa sbd karya gano zafin kishinta me tsanani.


Hajjo Dake zaune gefen Hanifa tanajin duk abinda suka tattauna tana Kuma iya jiyo damuwar dake cikin muryar Naj din itama al'amarin ya matuqar bata mamakin halin Malika Dan kuwa batai tunanin rashin tunanin nasu yakai can ba Dan Haka sai ranta ya soma baci da al'amarin tasan idan takira Marshal Tai Masa maganar ko yayane zaiji rashin Jin dadin Naj sbd ganin Kamar qararsa takawo akan wannan abun dazasu iya magana a tsakaninsu Dan hakan Bata kirasaba Saida aka kwana daya da maganar takira Dad Alfa ta sanar dashi komai tareda dorawa da cewan yasaka mum Malika takira Hannah tabar gidan Takoma masaukinta kokuma akama Mata wani gidan idan batason zama can.


Dad Sam baiji dadin al'amarinba musamman ya zaunarda Malika yafada Mata Marshal din yafada Masa baida ra'ayin auren Mata biyu kowace mace ma ba Hannah kawai ba,
Yayi Mata bayanin hakan yakuma fahimtar da ita ta zaunar da Hannah tafada Mata tabawa masu Sonta dama kawai tabar maganar JALAL din Amma shine ta turata sbd kawo fitina tsakanin Marshal din da matarsa.


Rufe ido yayi yai Mata fada sosai tareda cewa takira Hannah tabar gidan zai tura Mata isasun kudi takama wani gidan ta zauna Kuma tana gamawa ko sati Bai yadda taqara a qasarba Bata dawo gidaba.


Duk inda Rai yakai maqurar baci ran mum Malika yabaci sai kawai takira Naj tayi Mata fada tatas Wanda bayan Gori Babu abin daya qunsa Wanda duk yanda taso riqe kanta kasawa tayi Saida kuka yazo Mata ta kashe wayar tanayi.
Bayan Gama wayarsu mum Malika Marshal din takira shima tafada Masa irin fadan da Dad dinsa da hajjo sukai tareda Bata laifi tafada Masa takira matarsa tabata hakuri sbd ita Bata dauka abun zaizama abinda har Naj zata kasa tsayawa ayi maganarba anan tsakaninsu harsaita Kira hajjo da Dad Alfa tafada musu.


Zancen Bai Masa dadiba ko kadan musamman daya Kira dad dinsa yasake Masa maganar tareda sake bayyanar Masa da umarninsa na Hannah tabar gidan,
Hajjo ma fada Tai Masa sosai hakan duk saiya sakar Masa pressure sbd abinda Bai taba faruwa bane yau din yafaru sai yabawa Naj laifin rashin hakurinta data kasa fuskantarsa akan zancen harta kirasu hajjo da Dad Dan Haka daya dawo gidan dama itama kukan datasha zuciyarta tagama daukan 'daci sai kawai shedan yashiga tsakaninsu suka samu sabani me girma Wanda yasata kukan da Bata taba yiba tun aurenta dashi.


Shima fita yayi gidan sbd kukanta Dake neman qarasa rusa zuciyarsa Dan har cikin ransa yake jinsa Amma Dolene yayi Mata fadan abinda tai din.
Yini guda tayi adaki tana kuka cikin tsananin damuwa,fuskarta ta kumbura tayi jajir ahaka saiga Kiran Anty Amina tana dauka sai kawai ta fashewa Anty Aminan da kuka tana kasa magana,gabaki daya hankalin anty Amina dake taredasu hajjo yatashi Suma hankalinsu yatashi musamman hajjo anty Amina cikin damuwa me girma tace"


Naj lafiya kike wannan kukan Haka?
Meyake faruwane??


Cikin kuka tafara fadawa anty Amina komai taqare maganar da cewa"


Anty Amina Dan Allah nidai Zan dawo gida zuciyata takasa dauka,
Da wanne zanji?
Da kishinta Dake cina kokuwa da wannan masifar dazsuyita haddasa tsakanina dashi,
Zan dawo gida kawai sbd idan ban Dan tafiba zasu cigaba da hada fitanarda zata kawo babban fada a tsakaninmu banaso...


Shiru Anty Amina tayi sbd zamansu hajjo da Hanifa dake gurin yasa bazata iya fadar wata maganar ba sai kawai tahau bawa Naj din hakuri tana tausarta Akan karta taho gidan,
Katsewa wayar tayi batareda kowa yace komaiba ta kalli hajjo cikin tausasa al'amarin tace"


Bawani abun damuwa bane ai zasu daidaitane Daman Dole za'a ringa fada irin Haka.


Qala dai hajjo bataceba saima wayar dad alfa data lalubo ta saka Kira Yana dauka ta sanar dashi tanason ganinsa da matarsa.


Anty Amina dai sake Dan tausar hajjon tayi sbd ko Batai magana taga alamar Kamar yadauka zafi ranta ya baci,
Ta Jima gidan sai maraice tana ganin shigowar Dad Alfa da mum Malika tasan Magana zasuyi da hajjo ta miqe itada Hanifa suka nufi dakin Hanifa ta dauko gyalenta ta fice bayan ta gaidasu cikin biyayya.


Zama sukai bayan sun gaida hajjon wadda Bata tsaya batawa kanta lokaciba ta kallesu Kai tsaye tace"


Nace Hannah tabar gidan JALAL Bata bariba gashi matsalar tashin hankali tafara shigowa tsakaninsu yarinya da tsohon ciki za'a sakata damuwa matsala tabiyo baya,
Dan Haka ke Malika tunda kekika turata da manufar cusa kanta akansa bayan anfada Miki shi me auren yace baya ra'ayi yanzu duk da bamu San me gaba ta tanadarba sanin gaibu sai Allah Amma kisani wlh karki bini bashin rantsuwa duk aka samu babbar matsala akan Hannah har Najma tabaro gidanta tadawo to wlh ko sati bazata cikeba da dawowa zansa naki mijin yaqara aure sai kema kisamu lokacin fuskantar matsalar gabanki Dan Naga hadda rashin zafin hakan yasa kikeson mijin wata koreta yaqara aure.


Mum Malika dataji saukar zancen kamar saukar Aradu a girgice take kallon hajjon tana son gane ko rikicin tsufa ne murya na Dan rawa da mamaki tace"


Hajjo meya kawo maganar qarin aure ga mutumin daya manyanta?
Maganar Marshal da matarsa Kuma ai tsakaninsu ne Ni menene nawa daza'a mun qarin kishiya akan sabanin dasuka samu.....


Hajjo dai Bata bi takan zancen mum Malikan ba ta kalli Dad Alfa tace"


Kaji abinda nafada Kai ko?


Inshallah hajjo za'ai yanda kikace.


Ja matarka kuje banson maimaicin zancen yanzu.


Suna fita mum Malika taso haukace Masa sbd maganar auren sai yanzu tasake tabbatarwa dataga ya amsawa hajjon a ladabce ma musantawa,
Qafafunta na rawar disco ta Isa dakinta tashige ta lalubo wayarta tashin farko Hannah takira murya na rawa cikin ihu tace"


Hannah ki tattara kayanki yanzu yanzu kibar gidan nan....


Cikin mamaki ta kalli wayarta Jin yanda mum din ke maganar hankali tashe tace"


Mum Kamar Yaya nabar gidan bayan yanzunema nakejin dadin gidan da masu gidan ke fada,Babu inda zani mum Malika gskia.


Kutumar uba,Ina cewa kibar gidan yanzu shine kike fadamun Babu inda zakiยฟTo saurara kiji maganar aurenki da Marshal ba kubarta yanzu babuta Dan kuwa hajjo tamun barazana da kishiya duk Kika kawo matsala ga aurensu......


Cikin zallar mamakin mum din Hannah tace"


Mum menene Dan anmiki kishiya idan har zansamu shiga gidan Marshal?Naga ai kin Gama manyanta Babu wani abinda yarage Dan anmiki kishiya akan farin cikina,nidai Babu inda zani yanzu danake ganin haske kiyi hkr kawai mum.


Zagi da fada Kamar mum zata tashi sama ta ringa jehowa Hannah din Amma Hanna ta kashe wayarta tana cewa"


Lallai mum tafara batan lissafi.


Mum dakejin Kamar ta Ari hauka akan al'amarin idan ba barin gidan Hannah tayiba batada nutsuwa Dan Haka Kai tsaye Marshal takira Yana ganin kiranta yaqi dauka sbd bayason wata damuwar akan wadda yake ciki da matarsa tsawon kwanakin ko dakin kwanciya sun Raba sbd tadaina kwana dakinsa.
Ganin ta dage da Kiran yasashi dauka sai kawai ta fashe masa da kuka tana fada Masa batasan me Naj din tasake fadawa hajjo ba Amma hajjo ranta yayi matuqar baci ta tursasa dad dinsa qarin aure baiyi niyyaba itadai yanzu yaje Hannah tabar gidansa.


Innalillahi yafada acikin ransa Yana rintse idanuwa gabaki daya baisan meyake damun kowaba musamman Naj gashinan ta gana musu azabar rashin juna dagashi har ita.


Koda yadawo gida Ashe mum takira Naj tai Mata tas akan hukuncin hajjon ta Dora da fadin idan ma Bai aura Hannah bakisan wazai iya auraba gaba..
Kiran yasa Naj sake shiga yanayi na damuwa me tsanani Tasha kukan bazataso hajjo tasa Dad Alfa yayi auren rashin niyaba da girmansa Dan Haka sai kawai taji ta yanke shawaran komawa gida sbd komai ya lafa zuciyoyin kowa su sauka Dan idan tabar gidan ne kawai zai iya binta subarwa Hannah gidan idan bazata tafiba itama tana ganin sunbar gidan zata tattara Dole tabar gidan koba komai cikinta yashiga watan haihuwa gida takeson haihuwan.


Koda yadawo Bai nema Naj dinba sbd bayason su sake samun damuwa akan maganar Kai tsaye yakira Hannah a waya yace ta hada kayanta driver zai maidata gidanta sai kawai tasaka Masa kuka ya kashe wayarsa Yana jifa da wayar.


Booking ticket da komai tayi na tafiyarta batareda tafada Masa ba sai Ana gobe jirginta zaintashi tasamesa har dakinsa Yana zaune Yana aiki a laptop ta kallesa shima ita din ya Dan kalla Kai tsaye tace"


Nasiya ticket gobe Zan tafi Nigeria Inshallah.


Takaicin maganarta yasa Bai dagoba ya kalleta cikin zafin Zuciya yace"


A sauka lafiya.


Juyawa tayi tabar dakin tata zuciyar na tafasa da zafi na yanda yaqi hanata tafiyar Dan Haka tana zuwa daki tahau hada kayanta kafin ta kwanta Dan tafiyar safe zatai.


Washe gari ko data fito yafita office da mota bayan yasa andauki Hannah data Sha kukan maganar daya fada Mata na Babu wani so ko Abu makamancin hakan aransa gameda ita shi matarsa Naj kawai yakeso bayan ita baya ra'ayin wata,shiyasa Koda aka kaita masaukinta Jin tayi qasar gabaki daya ta fita ranta dama dama danshi ta jona karatun yanzu Kuma tunda harya fito yafada Mata hakan bazata iya cigaba da zama anan dinba itama ticket din tasiya na barin qasar Amma gidan qanwar namanta dake Ghana ta nufa taqi komawa gida.


Taxi tahau takaita airport kaita airport idanuwanta sai cikowa da hawaye suke tana maidawa sbd kewarsa datakeji tun batabar qasarba,
Jirginsu na tashi ta rintse ido tana sakin hawayenta dasuka kasa tsayuwa.
##MAMUH#






*_ZAFAFA BIYAR 2022๐Ÿ”ฅ_*


*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_


*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_


*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_


*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_


*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_


*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡
Dโ€™aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k


*_Zaku tura kudin a_*


6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*


*Sai shedar payment dinki a*๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡


08184017082


*Kokuma katin waya na MTN anan*๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡


09134848107






*_DEEN MARSHAL_*
*_Mamuhgee_*




*_53_*
Jirginsu na sauka taxi ta dauka ta nufo gida fuskarta a kumbure da zallan kukan datasha acikin jirgin gakuma gajiyar zaman jirgi da tsohon ciki dan hakama Koda suka sauka kamarma batajin Dadi sosai Haka ta lallaba tabi taxi ta iso gida.
Securities na ganinta jiki na rawa suka dauka akwatinta zuwa ciki har gate na biyu daganan Allah yasa ruqayyat tafito kawo musu abincin Daren su sai ganin Naj tayi cikin farin ciki da girmamawa ta qaraso ta karba akwatin da handbag dinta tana Mata sannu da zuwa suka nufi ciki.


Hajjo da Hanifa ne zaune a palon suna fira sai ganin ruqayyat janyeda akwati sukai Naj na bayanta tafe da tsohon ciki fuska a kumbure
Da sauri hanifa ta tashi tarbota tana zaunar da ita gefen hajjo Dake kallonta kamar zata miqe.


Rungume hajjo tayi hawayen idanuwanta na gangarowa tana qaqalo murmushi tace"


Nayi kewarki hajjo da fatan nasameku lafiya?


Dafa kanta hajjo tayi tana qaqalo nata murmushin cikin kulawa tace"


Sannu da hanya Najma ke kadai Kika taho ko??
Kasa amsawa Naj tayi tana kallon Hanifa dake Mata sannu cikin kulawa.


Hanifa kaita dakinki tayi wanka akawo Mata abinci taci takwanta tayi bacci ta huta.


Miqewa tayi suka nufa dakin Hanifa lokacin tuni ruqayyat tabude dakin Naj din tafara gyarawa.


Bacci tayi Sosai Wanda ta manta rabonta dashi tun fara rigimarsu da mijinta.
Sai yamma ta farka lokacin tuni anty Amina tashigo suna murnar zuwanta duk da kowa yaqi tada maganar da akasan akantane dawowar tata kamar yanda Bata fadaba Suma Basu tada zancenba musamman hajjo har aka kwana biyu da dawowar tata.


Ranarda ta biyar da dawowa ranar aka daura auren Dad Alfa da anty Amina auren daya girgiza kowa sbd Babu Wanda yasan meyake faruwa bayan hajjo data saka dad din neman auren anty Aminan gurin Dattijo Kuma ta roqa alfarman adaura kawai Babu wani janye janyen saka Rana da shela.


Mum Malika hannu ta Dora akai ta ringa tsinewa Naj da Hannah akan sukeda laifin wannan muguwar qaddarar data sameta musamman Hannah sai kiranta take tana zunduma Mata zagi da fada Dan tarasa inda zata sauke haushinta.


Naj ma bataji dadin wannan aurenba Sosai daga ita har anty Aminan da ummansu sbd gujewa fitina Amma tunda andaura Babu yanda zasu iya Haka suka runguma qaddara anty Amina ta tare sashen Dad Alfa na qasa shikuma Yana sama.


Saida aka gama rikici da hidimar auren anty Amina tata damuwar tadawo sabuwa ta kewar mijinta sbd har cikin ranta batason ta haihu mijinta baya tareda ita.
Kullum wayarta ahannunta take tana jiran Kira ko massage dinsa Amma shiru Babu tun tana daurewa dai harta kasa damuwarta ta bayyanar Mata danma koyaushe daga hajjo har Hanifa da Anty Amina suna kokarin kulawa da ita ga Dadah ma da kusan lokaci lokaci tana shigowa dubata tunda yanzu ji da ita akeyi.


Yau zaune take a Palon hajjo tana Shan furar dataji nono sosai Hanifa na gefenta tana waya da mijinta
Hajjo Kuma tana cin apple din da anty Amina ke yanka Mata cikin kulawa.


Qamshin turaren dataji yashiga hancinta ko a mafarki tajisa tasan meyake nufi Dan Haka ta dago kanta ahankali ta kalli kofar palon idanuwanta suka sauka akan Wanda yake shigowa palon sanye cikin qananun kayan _Hermรฉs_ navy blue yayi wani irin kyau da kwarjini fuskarsa a kame idanuwansa suka sauka cikin nata ya sauke wani boyayyan numfashi Yana dauke Kai daga kallonta

Please Login or Register in order to submit comment