ta tashi zaune ne na shiga jera ma ta sannu.
"Halan baki jin daɗi, naga kinyi barcin marice, sannu bari imfadawa Abba ya siyo ma ki magani." Nai maganar ina kallon yanda Mama ta dafe kanta.
Cikin sanyi murya ta furta.
"A,ah Mubeenah! lafiya lau kawai naɗanyi barci ne shine jikina yai sanyi, zan warware da zarar nai sallah."
Sannu na sake yi mata gami da lallaɓawa na tashi tsaye na nufi wajen ruwa na ɗauki ƴar gudaliyar butar gidanmu na cikata da ruwa na nufi kewaye dan in watsa ruwa saboda rashin daɗin da jikina ke min, raɓewa na yi ta samu na watsa ruwan sannan na fito na fara gabatarda alwala cikin nutsuwa, ina alfahari da yanda ni ke nutsuwa idan zan gana da mahaliccina, ni mutumce me tsananin son ibada da tsoron Allah, bana wasa wajen kiyaye haƙoƙin ubangijina, nakan yi iya bakin ƙoƙarina wajen kaucewa saɓo, da wannan nike kira ga ƴan uwana musulmai da muji tsoron Allah mu kyautata makomarmu, mu dinga kiyaye haƙoƙin Allah dan samun sakamako me kyau a lahirarmh, Allah ya datar da mu Ameen.
Bayan na kammala alwalar nai tasbihi kamar yanda mazonmu ya koyar, sannan na zubawa Mama ruwa a buta na shigar ma ta da ita sannan na dawo na shiga ɗakina wanda ko arziƙin fitila babu, gashi babu ko taga se wasu ƴan bulillika da aka jera a can sama, da lalube na ɗauki hijabi da abin Sallah ta, da yake na haddace inda komi ya ke a cikin ɗaki a haka nike gudanar da rayuwata ba tare da na takura ba.
A zaune na gabatar da Sallar saboda yanda kaina ke sarawa, bayan na gama ne na shiga yin azkar ɗin marice da bansamu damar yi ba, da yake na riga da na hardace shi tas a kaina, bayan na gama ne na jingina da jikin bango ina sauraren yanda bugun zuciyata ya sauya lokcinda na farka naga na yi barci wanda bansan lokacinda ya kwasheni ba, ina jin sauyi sosai a jikina wanda kafin in kwanta sam banji hakan ba, hakanan kawai na ji a jikina akwai abin da ya faru wanda ban sa ni ba, a gefe ɗaya kuma ina tunani akan abin da ya hana Umma da Abba fitowa yin alwala, ina jiyo tashin muryarsu a ɗakin Umma, hakanan kawai na ji ina so inje in taso su dan suyi sallah ƙila basusan an kira ba tun da ba wani ji ake sosaiba daga masallaci idan aka kira, ni da Mama mune masu ƙoƙarin yin sallah akan lokacinta.
Cikin amincewa da shawarar zuciyata na tashi ina dafe bango na nufi ɗakin Umma, ina tura ƙofar naci burki ganin Abba zaune akan taƙunanniyar dadumar Umma ya na sallah, gefe ɗaya kuma babbar robar Umma ce da buta a jiye sai wasu ruwa a cikin robar masu datti da alama awala akai ciki.
Cikin shanye mamakina na yi sallama cikin sanyi murya, abin da ya ɗaure min kai be wuce yanda naga firgici da razana ba kwance akan fuskar Yaya Habiba da Yaya Sumayya waɗanɗa suka salame Sallah.
"Innalilahi wa'inna ilaihi raju'un!!! Mubeena lafiya kika zo kikai min tsaye a bakin ƙofa." Umma ta faɗi da yanayin tsoro.
Kallon tsaf nai ma ta, ina ganin yanda ta ke ƙoƙarin haɗiyar yawun da ya maƙale ma ta a maƙoshi, idanuwanta da alamun tsoro ƙarara.
Bangama ƙare ma ta kalloba na tsinayo muryar Abba shima a sanyaye ya na faɗin.
"Mubeenah lafiya dai ko? ko wani abu kike buƙata." yai maganar shina maƙogwaromshi na kai komo.
"Dama naga baku fito yin sallah ba shine na ce bari inzo in sanar muku." nai maganar ina kokonto akan yanda naga su na wani ɗari-ɗari da ni.
"A'ah ai da kin barshi ba sai kinzo ba, yau a tasha da zan dawo na siyo sabuwar gora, shine nace ba sai mun dinga yin alwala a waje ba mayi a ɗaki kawai tunda tsakar gidan caɓewa ya ke harmu gaza samun wajen kwanciya ga kuma saurayen da ke yo gayya idan wajen ya caɓe." Umma tai tsulum ta bani amsa.
Haka kawai naji ban yarda da wannan maganar ta ta ba, hakanan ma Umma idan ta bushi iska sai ta tsiro wanki da marice dan kawai ta jiƙe inda muke kwanciya ni da Mama, musamman idan ranar ita ke da girki.
Bance komi ba na juya na nufi ɗakin Mama na isketa akan dadduma ta gama sallah, gaishe ta nai cike da girmamawa, amsawa tai cike da kulawa tare da tambayata lafiyata, bayan na bata amsa mukai zaman shiru na tsawon lokaci, ganin shirun yai yawa ne yau ko ƴar fira bamuyiba ya saka nace.
"Wai Mama yau babu aikin girkin dare ne, naga har yanzu baki ce inhura rushi ba."
"Da yake kinga Ummanku ta dawo to shine Abbanku ya ce imbar ma ta girkin tunda nata ne dama, ban musaba na bata abinta."
Mama ta bani amsa ta na ƙoƙarin kunna ragwargwaɓaɓɓiyar redionta wacce taci uban ɗauri da robali, shiru mukai muna sauraren labaranda ake a gidan redion.
Bamu daɗe da fara sauraren labaranba Abba ya aiko Yaya Habiba akan Mama ta fito tai shimfiɗa zamuci abinci.
Firgigit na dawo daga tunanin da na tafi.
"Mubeena ki ci abincin mana kar ya yi sanyi, wai kodai baki jin daɗi ne tun ɗazu nike lura da ke sam baki da walwala." Mama tai maganar ta na jiran amsata.
"Dan Allah Mama za ki iya gayamin abin da ya faru ɗazu, haka kawai nike ji a jikina akwai abin da ya faru, kinga su Yaya Habiba basa kula ni kamarma tsorona suke bayan ba gaka muke ba, Abbama bai yi min faɗa ba yanzu, shiyasa nike son insan abin da ya faru.
"Ke ko wannan yarinya kin shiga uku, haka kika koma kuma bayan sa ido yanzu harda bin ƙwaƙwaf kike yi, to ni gaskiya bazan iya ɗaukar wannan rainin hankalin naki ba, tabbas wani abu ya faru kuma ba komi bane face aljannun da kika tada kika nemi hallakamu da ruwa, kuma mun riga mun yanke hukunci akanki ni da Abbanku, ba za ki sake ƙara kwana a gidannan ba daga gobe, dan tsaf za ki hallakamu alhalin da sauran lokacinmu, mun shirya tsaf dan mu kai ki aikatau can bariki."
Sak kowa na wajen yai jin abin da Umma ta ce, Abba kuwa cike da ƙulewa ya banka ma ta uwar harara ya na takaicin hali irinnata na rashin siri, inde tonon sililine to fa Umma ta yi dgree akanshi, sam ba ta da sirri ko kaɗan, sai Abba yajata gefe suyi magana ba tare sanin Mama ba amma mudin za'azauna da Umma sai ta faɗi wannan maganar, ga shi Allah ya ɗaurawa Abba son yin shawara ko sirri da Umma.
Kallon yanda nike kokowa da hawayen da suka dage akan dole sai sun zubo, ni kuma naƙi basu damar hakan Mama ta yi, cikin sanyi jiki ta janyo ni ta kwantar akan kafaɗarta ta na jin babu daɗi da maganar da Umma ta faɗa min alhalin ba ita na tambaya ba.
Gyaran murya Abba yai tare da janyo hankullanmu akan zai yi magana kowa ya nutsu, ɗago kaina nai ina son jin abin da Abban zai faɗa.
"Ke Mubeenah ki natsu domin maganar ta ki ce, bayan zuwan Yayanku Hashimu ya yi min wani abishir akan ya samo ma ki aikatau a can cikin bariki, na yi murna sosai da hakan dan idan ba ki manta ba nace ma ki, ko dai ki fidda miji in aurar da ke, ko kuma inbawa abokina aurenki ko ki fita ki barmin gida dan na gaji da ciyar da ke hakanan babu wa ta riba, ga matsalolinki da sukafi ƙarfin kanki bare kuma ni Iroro wanda ban aje ba kuma ban bama wani ajiya ba, na rigada na yanke shawara akan gobe da yardar Allah zan ɗaukeki da kaina in kaiki can gidan aikin, mutanen a matse suke da son samun wacce za tai aikin,yanzu abin da nike so da ke shine, ki tattaro dukannin abubuwan da kikasan ki na buƙata ki shirya gobe tun da sassafe zamu kama hanyar tafiya dan kuwa ana so muje kafin wani me magani ya iso, kuma ban amince kiyi magana da Mamanki ba akan wannan aikin, umarni ne na zartar a kanki ban amince kiyi magana da kowa ba akan wannan aikin face ni kaɗai ko Ummanku idan kika yi magana da wani Allah ya isa ban yafe muku ba wallahi, dan ba shawararki na nema ba na riga na zartar da hukunci."
Zuciyata ta shiga dokawa da tsananin ƙarfi, ya yinda na gama jin kalaman Abba, hakanan na ji na amince da hukuncin da ya zartar a kaina, hakanan nike ji na gaji da rayuwa a ƙarƙashin innuwar kulawar Abba, na daɗe da gane cewa Abba baya so na, ban san daliliba sai tsintar kaina na yi a cikin farin ciki, ban san wane zaren ƙaddara ba ne ya ke jana akan amimcewa da aikin, ni dai kawai ina jin daɗin zan nisanta da Abba na tsawon lokaci, zan yi nisanda zan samu nutsuwar gangar jiki da zuciya, ina buƙatar samun inda zan zauna inyi tunani akan rayuwata tun daga farko har izuwa yanzu da tarin ƙaddarori suka samu muhallin zama a rayuwata.
Bancewa kowa komi ba sai tashi da nai babu alamun damuwa atare da ni na wuce ɗaƙina, Mama ce ta bawa Yaya Habiba ƴar ƙaramar fitilarta ta kawo min, aiko na ji daɗin hakan dan so nike in sadu da ma'ajiyar ƙur'ani na dan amma duhu ya hana hakan.
Jakar iskamiyya ta na ɗauko na fito da ƙur'ani na izufi sittin, na buɗe shi tare da fatan samun salama da dangana akan ƙaddarar da ke tunkaro ni, a lokacinda na fara karanta alƙur'ani me girma da tsarki, wani irin raunine ya baibaye ni har ban san sanda na fara hawayeba, ban daina karatunba kuma ban daina kukanba, hakanan nike ji a jikina wannan hawayen da nike na samun salama da sauƙin zuciya ne.
Ban daina karatun ba sai da na tabbatar da na samu gamsashiyar nutsuwa, sannan na rufe alƙur'ani nai addu'ata tare da tashi na gabatar da Sallar Isha'i.
Bayan na gama ne na ta gyara wajen kwanciyata sannan na ɗauki fitilar Mama na mufi ɗakin ta, turus na yi ganinta durƙushe a ƙasa ga Abba tsaye a kant sai huci ya ke, ban ce komi ba na nufi inda ta ke ajiye fitilar na ajiye tare da juyawa na fice zuwa ɗakina, azkar ɗin kwanciya narci na gabatar sannan na haye yamusashiyar katifata nai lamo ina jin yanda har yanzu zuciyata bata bar dokawa da ƙarfiba, ban bawa kaina damar tunani akan komi ba haka na kwanta har barci me nauyi yai nasarar tafiya da ni.
Kyakkyawan matashi ne zaune a wa ta kujerar alfarma ya na aiki, sai wa ta mummunar halitta marar kyan gado ta zo ta bayanshi ta buɗe mumunan bakinta ta shiga yo aman wuta, juyawa yai ya na salatin jin ZAFIN WUTA amma sai wannan hallitar tai amfani da wannan damar ta sake amayo wa ta wutar me yawa akanshi, sai da halittar ta cike inda matashin ya ke da wuta sannan ta fice da jikin gini, wa ta mata ce ta zo kusa da wamda aka sakawa wutar ta na kuka tare da tattaɓa jikinshi, amma duk inda ta taɓa sai ya kwalje ita kuma sai hanunta ya ƙone, a haka ta zauna ta na ta kuka babu me rarrashi, yayinda muka zo wucewa ta wajen ni da Abba sai muka ga wannan matar shine Abba ya ja hannuna ya bata ya na faɗin nice kaɗai zan nemo maganin da zai warkar da wannan matashin wanda wuta ke ƙonawa, hannu biyu matar ta amshe ni tare da yiwa Abba alkairi me yawa ya juya ya barni da ita, da na tunkari inda wannan matashin ya ke, sai ruwa me ƙarfi ya zo ya maido da ni, haka na dage sai na isa gareshi har nai nasarar kama hanunshi, abin mamaki ina kama hanunshi sai wannan wutar ta ɓace ɓat sai de baƙin hayaƙi da ya karaɗe daƙin wanda wa ta murya marar daɗin amo ke faɗin, "kin yi nasarar rabani da shi amma tabbas zan dawo, zan dawo domin ɗaukar fansa."
A firgice na farka cikin matsanancin tsoro.
WANNAN LITTAFIN NA KUƊI NE, GA WACCE TA SHIRYA BIYA GA ACCOUNT.
9136291920
MARYAM UMAR
OPAY
TAKU HAR ƘULLUM.
MARYAM STAR⭐⭐⭐
Follow the 𝑀𝐴𝑅𝑌𝐴𝑀 𝑆𝑇𝐴𝑅 𝑌𝐴𝑅 𝐵𝐴𝐼𝑊𝐴𝑅 𝐽𝐴𝐽𝐼𝑅𝑇𝐴𝑇𝑇𝑈 𝐻𝐴𝑈𝑆𝐴 𝑁𝑂𝑉𝐸𝐿𝑆 𝐶𝐻𝐴𝑁𝑁𝐸𝐿✍️📚📙✏️ channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb5xdoy2975BcTM5m133
🔥𝐙𝐀𝐅𝐈𝐍 𝐖𝐔𝐓𝐀🔥
LABARI ME CIKE DA
BAN TAUSAYI,😩
MATSANANCIYAR DAMUWA,😭
KUNCIN CUZIYA,💔
SADAUKARWA,💌
ZAZZAFAR SOYAYYA ME TSAYAWA A RUHI.💋💘
WRITING BY
MARYAM STAR ⭐⭐
YAR BAIWAR JJRT.
MARUBUCIYAR📒✍️
RAYUWAR SAMHAD
DAFIN MACIJI
A DAREN AURENA
AND NOW
ZAFIN WUTA🔥
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
"Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨
🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚
(🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚)
Typing...📲
PAID BOOK 500 ONLY👌
SEASON TWO
PAGE 35
Ina karanto addu'o'inda Manzonmu ya koyar idan mutum yai mummunan mafarki, zuciyata har lokacin bata daina dokawa da ƙarfi ba, sai ma sake tsananta dokawa da tai fiye da baya, hakanan naji jikina yai sanyi sam bani da kuzari ko kaɗan.
Tunanika barkayai suka dinga bijiromin na abubuwanda suka faru da ni tun wayuwar garin yau, idan da sabo ya kamata ace na saba da yanda rayuwa ke gara ni kamar kwallon ƙafa, aduk lokacinda zan wayi gari d irin ƙalubalen da zan fuskanta, sam babu wani abu na birgewa a cikin rayuwata, hakanan nike gudanar da rayuwata sam babu farin ciki.
Sake juyawa nai ɗayan sashen ina ji a jikina dole ne in tashi in nemawa kaina mafita, ina buƙatar farin ciki kamar kowace mace, ina buƙatar samun ƴancin kai kamar kowace budurwa wacce ke gaban iyayenta, amma ta yaya zan samu hakan? na tambayi zuciyata da take saƙamin tunanika daban-daban.
'Zan samu ƴanci kamar kowa amma sai na cire tsoro, dole sai na aro mayafin juriya na aje na haƙuri dan samun damar cimma muradina, to amma kuma ai Abba ya ce gobe zan bar gidan, ko da yake wannan ma wa ta damace zan samu dan in canza rayuwata, ban san gidan da zan rayu a cikinshi ba, haka zalika bansan wane irin mutanene a cikin gidan ba, zan tsaya imfara karantar mutanen wajen dan insan ta yanda zan gyara rayuwata kamar kowa.'
Ina ta tunani daban-daban da haka har barci ya ɗauke ni me nauyi.
BANANA ISLAND
Ƙwance Mommy ta ke a kan katafaren gadonta wanda ya lashe miliyoyin kudaɗe kafin kafuwarshi a daɗin, kallon farko zakai me ka gane ba ɗan ƙasar ba ne, ko daga wace ƙasa aka ƙerashi lallai me tsananin tsada ne.
Sulaima ce zaune akan kagon kusa da Mommy wacce Doctor ke duba lafiyarta, fuskarnan ta ta tai jazur musamman saman hancinta abinka da farin mutun.
A gefe kuma wannan Dattijuwar matar ce zaune ta yi tagumi ta na kallon yanda Mommy duk ta bi ta fice a hayyacinta.
Bayan Dr. ya gama ba ta taimakon gaugawa ya juyo ya fuskanci wannan Dattijuwar ya na faɗin.
"Hajjo, wai dan Allah mi yasa bakwa kiyaye lafiyar baiwar Allarnan, ta na cikin mawuyacin hali yanzu haka, jininta yayi mugun hawa, ga ciwon zuciya, mi yasa kuke barinta cikin damuwa har haka, ina Fauzan ya ke ne, nasan shi kaɗaine zai fahimci abin da nike nufi." Doctor yai maganar fuskarshi da alamun ɓacin rai gami da damuwa.
"Kayya dai dakat, ai baka sa ni ba, Fauzan ɗin shine wanda yai silar shigarta wannan halin, ya na can kwance cikin mawuyacin hali rai a hannun Allah, kasande akwai shaƙuwa me tsanani tsakanin Fatima da Fauzan, halinda Fauzan ɗin ke ciki ne ya asassa ma ta tashin ciwon, wallahi muna yin bakin ƙoƙarinmu wajen ganin mun fitar da ita daga damuwa, amma abin ya ci tura, da zarar ta ga halin da ɗanta ke ciki sai jikin na ta ya rikice."
Hajjo tai maganar muryarta na jimanta lamarin.
"Wai dama Hajjo har yanzu Fauzan be warke ba, na yi tunanin da kuka fita da shi India ya samu lafiya." Dr. yai maganar ya na jimanta lamarin.
"Kai de bari Dakta! lamarin Fauzan se du'a'i, yanzu abin ya wuce yanda ake tunani, ciwo sai gaba ya ke ba wani sauƙi sai a wajen Allah, da zaka ga Fauzan yanzu na tabbata ƙafafuwanka ba zasu taku ta daɗin rai ba, yaronan yana ganin jarabawar rayuwa, sai de kawai muci gaba da taya shi da addu'a Allah ya yanke ma shi wannan wahala da yake ciki."
Jinjina kai kawai Dr. yai cike da jimami, dan bai mance yanda aka kawo Fauzan asibitinsu ba cikin matsanancin ciwo da zafin jiki, fatan samun sauƙi yai musu tare da bada shawarwari akan yanda zasu dinga kiyaye lafiyar Mommy gudun samun matsala sannan ya tafi.
Zaman shiru sukai a ɗakin kowa na tunanin zuci, da haka har barci me nauyi yai awon gaba da Hajjo, da wannan damar Sulaima tai amfani wajen sulalewa ta tafi ɗakin Fauzan dan ta ƙara ganinshi, sam hankalinta baya kwance, ga tashin hankalin yanda jikin ɗan uwanta ke tsananta, ga guma tashin hankalin yanayin Mommy ke ciki.
Zuwa bakin ƙofar glass ɗin ɗakin Sulaima ta yi, tare da jingina jikinta akan ƙofar ɗakin idanuwanta na zubarda hawaye, ta na ɓatuƙar ƙaunar ɗan uwanta, sam batason abin da zai ɓata ma shi rai, ta na kiyaye abin da zai saka yai fushi da ita, shima kuma ya shaƙu da ita, ita kaɗaice abokiyar nishaɗinshi, da ita yake sirri da ita ya ke shawara, ya yarda da ita fiye da kowa.
Ta ɗauki tsawon lokaci a hakan ta na tunani kafin daga bisani ta zabura tare da janyo ƙofar ta fito ta nufi kan stairs, da bibiyu ta ke hawa benen hakan ya bata damar hayewa cikin sauri, wa ta tsadaddiyar waya ta ɗauka akan luntsumemiyar kujerar da ke jere a ƙayataccen parloun, cikin sauri ta buɗe mabuɗan sirrin tare da laluba wa ta numbar da akai save da Pahpah, ta danna calling.
Amsa kiran akai daga can ɓangaren tare da furta.
"Assalamu alaikum"
"Wa,alaika salam pahpah!🥹"
Sulaima tai maganar ta na ƙoƙarin haɗe kukanda ya sake taso ma ta.
"Sulaima lafiya dai ko! ina Mommynku ina kuma Fauzan ya na lafiya dai ko, jikin da sauƙi ko!!!."
Ya jero tambayoyin cike da ruɗewa.
"Pahpah dan Allah ka dawo hakanan, wallahi Yah Fauzan ya na cikin matsanancin ciwo, Pahpah kullum abin gaba yake sake yi, please idan maganin bazai samu ba ka taho hakanan, banaso yah Fauzan ya mutu bakuyi bankwana ba, Pahpah jikinshi sam babu kyawun gani, yau kwana uku kenan rabon da ya saka koda ruwa ne a cikin....!
Sai kuma wani sabon kukan ya sake ɓalle ma ta.
Cike da damuwa Ya fara rarrashinta tare da tabbatar ma ta da yana hanya yau komi dare a legos zai kwana, sannan yai ma ta albishir da ansamu maganin.
Ta ɗanji daɗi jin cewa zai dawo yau, ko babu komi zai tsaya wajen ganin ko yayane Fauzan ya saka wani abu a cikinshi, dan kaf a gidan shi kaɗai ne ya isa ya taɓa Fauzan ba tare da ya ƙone ba.
𝑃𝑙𝑒𝑎𝑠𝑒 𝑘𝑢𝑦𝑖 𝑚𝑎𝑛𝑎𝑔𝑒 𝑑𝑎 𝑤𝑎𝑛𝑛𝑎𝑛 𝑤𝑎𝑙𝑙𝑎ℎ𝑖 𝑖𝑛𝑎 𝑏𝑢𝑠𝑦 𝑛𝑒 𝑘𝑤𝑎𝑛𝑎 𝑏𝑖𝑦𝑢 𝑎𝑚𝑚𝑎 𝑖𝑛𝑠ℎ𝑎 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑑𝑎𝑔𝑎 𝑦𝑎𝑛𝑧𝑢 𝑧𝑎𝑘𝑢 𝑑𝑖𝑛𝑔𝑎 𝑠𝑎𝑚𝑢𝑛 𝑙𝑖𝑡𝑡𝑎𝑓𝑖𝑛 𝑍𝐴𝐹𝐼𝑁 𝑊𝑈𝑇𝐴 𝑎 𝑘𝑎𝑖 𝑎 𝑘𝑎𝑖.
𝐺𝐴 𝑊𝐴𝐷𝐴𝑁𝐷𝐴 𝑆𝑈𝐾𝐴 𝑆𝐻𝐼𝑅𝑌𝐴 𝐵𝐼𝑌𝐴𝑁 𝐾𝐷𝐼𝑁 𝐷𝐴 𝐴𝐶𝐶𝑂𝑈𝑁𝑇.
9136291920
𝑀𝐴𝑅𝑌𝐴𝑀 𝑈𝑀𝐴𝑅
𝑂𝑃𝐴𝑌
TAKU HAR KULLUM
MARYAM STAR⭐⭐⭐
Follow the 𝑀𝐴𝑅𝑌𝐴𝑀 𝑆𝑇𝐴𝑅 𝑌𝐴𝑅 𝐵𝐴𝐼𝑊𝐴𝑅 𝐽𝐴𝐽𝐼𝑅𝑇𝐴𝑇𝑇𝑈 𝐻𝐴𝑈𝑆𝐴 𝑁𝑂𝑉𝐸𝐿𝑆 𝐶𝐻𝐴𝑁𝑁𝐸𝐿✍️📚📙✏️ channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb5xdoy2975BcTM5m133
🔥𝐙𝐀𝐅𝐈𝐍 𝐖𝐔𝐓𝐀🔥
LABARI ME CIKE DA
BAN TAUSAYI,😩
MATSANANCIYAR DAMUWA,😭
KUNCIN CUZIYA,💔
SADAUKARWA,💌
ZAZZAFAR SOYAYYA ME TSAYAWA A RUHI.💋💘
WRITING BY
MARYAM STAR ⭐⭐
YAR BAIWAR JJRT.
MARUBUCIYAR📒✍️
RAYUWAR SAMHAD
DAFIN MACIJI
A DAREN AURENA
AND NOW
ZAFIN WUTA🔥
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
"Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨
🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚
(🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚)
Typing...📲
PAID BOOK 500 ONLY👌
CHAPTER 35-40
بسم الله الرحمن الرحيم.
Ajiyar zuciya Pahpah ya saki lokacinda Sulaima ta kashe wayar, kallonshi farin mutum da ke zaune kan sallaya tai tare da girgiza kai sannan ya ce.
"Mudin haskenta ya sadu da ɗanka tabbas ƙarshen wahalarsa ya zo, ita kaɗaice za ta iya karya wannan mugun sihirin, sannan kuma ta bashi garkuwa da izinin ubangijinmu."
Shiru Pahpah yai tare da zurfafa a cikin tunanin yanda zai sadu da wannan tauraruwa me haske, wacce zata zamo tsanin takawar Fauzan ta hanyar samun lafiyarshi.
"Ka tashi ka je, kana tare da nasara, ka riƙe Allah domin shine kaɗai zai tallafa maka."
Wani abin al'ajabi da bammamaki, mutumin na gama maganar sai ya ɓace ɓat kamar be taɓa wanzuwa a wajen ba.
Tsam Pahpah ya tashi ya fice cikim tsoro, direct wajen motarshi ya nufa, bayan ya shiga ya saka drivar ya ja da sauri suka bar wajen.
MUBEENAH AGEGE
Can cikin barci ni ke jiyo muryar Mama sama-sama, ban buɗe ido ba sai juyi da na sake yi ina shirin gyara kwanciyata, sai na ji an jijjiga ni da ƙarfin gaske ana faɗin.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raju'un, jama'a Mubeenah wai lafiyarki ƙalau kuwa? dan Allah ki tashi hakanan, rana har ta fito amma kin gagara tashi, tun asubahi nike tashinki."
Zaram na tashi zaune tun lokacin da na ji salatin da Mama ta saki, cikin sauri na buɗe idanuwana, amma abin mamaki shine, sun buɗe tar amma sam bana ganin komi, sake kai hannuna nai ina shafa idon dawa, amma abin al'ajabi sai naji ashe a buɗe suke.
"Allahu Akbar, kaji ƙudirar Ubangiji mabuwayi gagara misali, me hanawa kuma me bayarwa, Wallahi Allah Mama idanuwana basa ganin komi, duhu nike gani, zo ki duba ki gani."
Nai maganar cikin jinjina ƙarfin buwayar Ubangiji, me bayarwa kuma me hanawa aduk lokacin da ya so, idan ba Ikon Ubangijiba waye zai baka alokacin da ya so, kuma ya amsa a lokacinda ya so?.
"Ke Mubeena ban son iskanci, ta gidan ubanwa ke baki gani, alhalin ga idanuwanki nan tarrrr ma sha Allah, ki daina wasa ki taso muje kiyi sallah lokaci na wucewa."
Mama tai maganar ta na hana kanta gasgata cewa da nai bana gani.
"To Mama bara in tashi."
Nai maganar ina ƙoƙarin tashi, amma mi ta tabbata dai bana gani sam, dan kuwa ina taka ƙafata ban sauke ta a ko ina ba sai cikin kwanon da nike aje ruwa idan zan kwanta, cike da razani na janye ƙafata nai baya ina salati.
Sak Mama ta yi, ta kasa taɓuka komi domin kuwa ko ta so ko kar ta so ya tabbata bana gani.
Maganar Abba ce ta yanke min jimamin da na shiga.
"Ke Halima! wai har yanzu ita Mubeenar ba ta tashi ba, ki watsa ma ta ruwa manah, kinga rana ta soma yi, kuma ana jiranmu dan yanzu na sake yin waya da Hashimu ya sanar da ni cewa, me gidan ya dawo jiya cikin dare, muyi sauri muje dan...."
Maganarshi ta yanke ne lokacin da ya lura da Mama