miki fatan cikawa dą imani, tare da
samun sakamakon aljanna".
Wannan kalami ne ya jefa karayar zuciya ga
sarki Maharaz, har shma ya ruga ga gimbiya
Zuhura. Duk su biyun suka kama kuka a lokaci
guda. Nan takc suka yiwa juna addu'o'in nasara,
sannan suka yi bankwana suna ta zub da hawaye.
Ba tare da 6ata lokaci ba aka bude kofar sirri
ta bayan gari, sadauki Kurbas, gimbiya Zuhura da
sauran makaskantan birnin gaba daya suka bi ta
cikinta suka bar birnin Nurul Kalbi.
Bayan kulewar su, Sarki Maharaz suka ci gaba
da shiryc-shiryen yaki, aka yi ta fito da sabbin
makamai, kuma aka fara kirkiro sabbin dabaru,w
adanda suka hada da kera katuwar majaujawa mai
cilla dutsen wuta, wanda idan aka jefashi kan
makiya ya fashe zai haddasa gagarumar wuta.
Haka dai mutancn Nurul Kalbi suka wanzu
suna ta wannan aiki tambar ba za su daina ba.
Rashin snai yafi darc duhu. Hakika in da su
sarki Maharaz sun san irin shirin da su Abidatul
Azmal ke yi da sun san cewa na su wasa ne. Domin
abin yafi gaban kwakwalwar bil'adama.
Da farko dai, a shawarar da suka yanke, akwai
batun tabbatar da cewa an bajc birnin Nurul Kalbi
Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini
ya zamo babu wani gini a tsayc a cikinsa, sannan
kuma dole ne a konc komai na cikinsa, ya zama
toka a wannan karon, ko ta wanne hali.
Aljanu suka ce lallai sunc da alhakin ruguje
birnin. Su kuma dodanni suka ce sune za su konc
shi. Su kuwa bil'adama suka ce sune da alhakin
kashe dukkanin wani abu mai rai na cikinsa. Suka yi
rantsuwa da cewa ba za su bar koda kiyashi guda
daya ba.
Koda gama yanke wannan shawara, sai aka
shiga kcra sabbin muggan kayan yaki, inda aljanu
suka dinga kwakule manyan duwatsu suna cusa
makamashin wuta a ciki, tare da danyan mai. Su
kuma dodanni suka kcra kiboyoyin wuya masu
mugun yawa. Su kuwa bil'adama takubba, masu, da
sauran makamai sukayi ta tanada.
Sai da sa'a biyar ta shude ana wannan shiryeshirye cikin tsananin gaggawa da basira, sannan aka
kammala.
Bayan an gama sai farin ciki ya lullube
gimibiya Abidatul Azmal. Ta dubi dakarunta gaba
dayan su, ta ce, "Kowa ya zauna cikin shiri, lallai
gobe da asuba za mu afkawa birnin Nurul Kalbi mu
kawar da shi tamkar bai taba wanzuwa ba a doron
Kasa."
Wannan shi nc abin da ya faru dangane da
kowannc bangarc na abokan gaba.
22
Task Abdul BZIZ S. M/GINI
***
Al'amarin su sadauki Kurbas kuwa, lokacin da
suka jagoranci tsofaffi, yaram da dukkanin matan
birnin Nurul Kalbi, suka fita ta boyayyiyar kofa da
ke bayan garin, sai suka ci gaba da tafiya a cikin
daji ba sassautawa. Da yakc an basu karin dakaru
dari, sai suka rabasu kaso uku. Kaso guda suka
tsaya a farkon jama'ar. Kaso na biyu a tsakiyar su.
Su kuma kaso na uku a can gabansu, dan tabbatar da
tsaro.
Sadauki Kurbas da gimbiya Zuhura kuwa, su
ne akan gaba, kowannen su akan doki yana duban
gaba da baya.
Sai da suka shafe fiye da rabin daren suna
tafiya, sannan suka fuskanci cewa jama'a fa sun gaji
ainun. Tsawon wannan lokaci Zuhura da Kurbas
basu yi magana da juna ba.
Nan take Zuhura ta daga hannunta sama,
alamar a tsaya. Ai kuwa sai Dakarun da ke kan
gaba suka ja tunga. A sannan ne ya dubi sadauki
Kurbas, ta ce, "Ya kai abal Hasilat, yanzu mene ne
abin yi? Hakika idan muka ci gaba da wannan
tafiya mutanen mu za su gaji su shiga mugun hali.
Haka kuma idan muka tsaya anan har aka ci gaba da
yaki a can birnin Nurul Kalbi abokan gaba za su iya
23
Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini
gano ccwa bama can, dan haka za su iya biyo sahun
mu su cimmana".
Yayin da sadauki Kurbas ya ji wannan
tambaya, sai yai shirus yana tunani. Daga can sai ya
dago kai ya dubi gimbiya Zuhura ya cc, "Ya kc
Ummul Maharaz, in dia haka ne, dole ne mu
nemawa mutanen mu maboya mai kyau yadda koda
abokan gabar mu sun biyo sahun mu ba za su gan
mu ba".
Zuhura ta ce, "Kwarai kuwa, hakika ka zo da
shawara mai kyau". Nan take suka raba wasu
dakaru su goma, suka ce su tafi neman kogon dutse
mai zurfi da duhu, ko kuma babban rami, wanda ke
cikin boyayyen sako.
Nan yake dakarun suka bi umarni. Suma sai
suka tafi laluben tare suka bar jama'ar a kar kashin
tsaron sauran dakarun.
Bayan kamar sa'a hudu, daf da gabatowar
asuba, sai Kurbas da Zuhura suka gano wani tsohon
kogon dutse a cikin wasu bishiyoyi masu duhuwas.
Saboda duhun wajen, sai da suka kunna fitilar
wuta,s annan suka iya haska hanya suka shiga cik.
Abin takaici kuma shi ne, suna shiga cikin
kogon sai suka ga ashe karamin kogo ne, wanda
baifi mutum ashirin su shiga cikin sa ba. Ba zato
kuma, sai suka ga wata tsohuwar rijiya a cikinsa,
24
Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini
wadda aka rufeta da wani katon mummulallen murfi
na karfe.
Sadauki Kurbas ya sa hannaycnsa biyu da
nufin ya daga murfin rijiyar ya janyc shi,amma sai
yaji ya kasa. Al'amarin da ya matukar bashi mamaki
kenan, domin da farko ya raina nauyin murfin,
kuma ya sha daga wadanda suka fi wannan girma
da nauyi. Dan haka sai ya dubi gimbiya Zuhura ya
cc, ta kawo masa agaji. Nan fa suka hada karfi su
biyun suka kama murfin dan su daga, amma sai
yaki daguwa. Mamaki ya kara turnukc su su duka.
suka dubi juna, kawai suka yi shiru suna tunani.
Daga can sai Zuhura ta dubi Kurbas ta cc, "Muyi
bisimillah, da izinin Allah zamu bude rijiyar nan".
Ba tare da yin gardama ba, Kurbas ya bi
umarninta, suka yi bisimillah a tarc. Ai kuwa suna
gama karfi suka daga murfin cak, wanda duk jikinsa
yana cc ya lullubc, suka ajiyc shi a gefc guda.
Koda suka haska cikin rijiyar, sai suka ga ashe
ma matattakala ce ciki. Nan takc suka kunna kai
ciki, suna masu karanto addu'o'in neman tsari. Ai
kuwa suna sauka karshcn matattakalar sai suka ga
ashe wata katuwar fada ce a ciki ta wani boka, da
gani ya dade da yin zamanin sa shckaru aru-aru da
suka gabata.
Babu komai a cikin fadar fa cc kayayyakin
tsafc-tsafc. Girman fadar ya kai girman birnin Nurul
25
bdul'aziz S. M/Gini
Kalbi. Nan fa Zuhura da Kurbas suka cika da
mamakin ganin girman wannan waje da yadda aka gina shi a cikin karkashin kasa.
Gaba daua abubuwan da ke cikin fadar sun
kamc sun zama gunki, kuma yanah ta lullubc shi.
Koda su Zuhura suka gama nazarin cikin fadar,
suka tabbatar ccwa babu wani mugun abu a ciki, sai
suka fita da sauri, suka je suka taho da dukkan
sauran,jama'ar tasu, suka sake shiga cikin wannan
rijiya. Da yake Zuhura da Kurbas ne suka shiga
daga karshc, sai suka sake yin bisimillah suka janyo
murfin rijiyar suka rufe ruf, tamkar ba'a taba
budcwa ba.
Nan fa gaba dayansu suka duru a cikin rijiyar,
suka isa karshenta, suka bayyana a cikin wannan
tsohuwar fada.
Koda tsofaffi, yara, da mata suka tsinci kansu a
cikin wannan wuri, sai suka shiga kalle-kale cikin
ta'ajibi.
Anan dai kowa ya sami wuri ya kwanta saboda
gajiya. Cikin 'yan dakiku kadan jama'a suka kama
barci. Kurbas da Zuhura nc kadai idanunsa kekashc
sun kasa rintsawa.
A lokacin suna zaune nesa kadan da juna, sai
wannan ya kalli wannan kawai suna murmushi, an
rasa wanda zai cc kala.
26
Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini
Daga can sai Kurbas ya mike tsaye daga inda voke zaune. va je kusa da Zuhura ya zauna, sannan
ya ce, "Ya kc wannan babba jaruma, wadda ta ceci rayuwata, ina mai gödiya garcki bisa sai da ranki da kika yi saboa ni".
Koda jin wannan batu, sai Zuhura ta yi murmushi ta ce, "Babu bukata ka yi miní godiya,
domin wajibi ne a gareni na ceto rayuwar babban
mayakin addinin Allah. Ba karamar asara ba ce mu
rasa irinka a cikin mu".
Kurbas yayi murmushi, sannan ya ce, "Amma
kuma naji danki ya cc kin yi alkawarin ccwa ba za
ki sake yin yaki ba a rayuwa ki. Shin me yasa kuma
kika yi yanzu?",
Koda jin haka, sai Zuhura ta cika da tsananin
mamaki, dan haka sai ta cc, "Ya aka yi kaji wannan
zance, alhali a sirrance mu ka yi shi ni da dana?".
Kurbas ya sake yin murmushi, sannan ya cс,
Allah ya bani wata irin baiwa, wacce koda rada
kayi a kusa dani ina iya jin abin da aka fada. Haka
kuma idan mutum na tafiya ncsa daga inda na ke
tsawon zura'i dubu, idan na aza kunne na akan Kasa
ina iya jiyo sautin sahun tafiyarsa, kuma ina iya
sanin lokacin da zai iya izuwa inda na ke".
Koda gama fadin haka, sai Zuhura ta yi ajiyar
zuciya, gami da kabbara, sannan ta ce, "Hakika
Allah shi ne mabuwayi mai bayar da kyauta ga duk
27
Taskar 1safi-3 Abdul'aziz S. M/Gini
wanda ya so. Tabbas kana daga cikin bayin Allah
masu baiwa.
a
Ya kai wnanan sadauki, y sani cewa ba
komai ne ya sa na ce na daina yaki ba, sai domin
yaki ne na rasa babban masoyina, kuma mijina uban
dana Maharaz sarki Makawi. A duk sa'adda na ga
ana yaki sai hankalina ya dugunzuma na tuno da shi
na yi ta kuka. Domin na san cewa na rasa wanda
har abada babu mai maye min gurbinsa a zuciyata.
Bisa wannan daliline na diana yaki, kuma na ke
tsoron na ga yaki.
Lokacin da yaki ya zo mana bakatantan, kuma
na ga irin kokarin da kakc yi a yakin na kare
Musulunci da Musulmai, sai na ga komai na ka irin
na mijina nc. Hatta yadda ya kc rike takobinsa, da
kuma salon yakinsa. Nan take naji sonka ya
kwarara a zuciyata, har na ji na gamsu cewa za ka
iya mayc mini gurbin tsohon mijina. Saboda haka
ne na sallama rayuwata dan ccto taka, ina fatan zaka
bani matsuguni a cikin zuciyarka?".
Koda gimbiya Zuhura ta zo nan a zancenta, sai
farin ciki ya turnukc Kurbas, ya cc, "Ya kc wannan
sarauniyar kyawawan duniya, ki yi sani cewa ranar
da na fara ganin ki na karyata kaina na tabbatar da
ccwa matąta margayiya kyawunta kalilan ne daga
cikin naki. Alhali a zamaninta babu wata mace man
kyanta a garin mu. Ina ganin ki na ji gaba daa
28
Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini
begen da na ke ma ta ya dawo kanki. Dan haka tun
tuni kina da matsuguni a cikin zuciyata".
Koda jin wannan batu, sai hawayen farin ciki
ya zubowa gimbiya Zuhura, taji kamar ta rungume
sadauiki Kurbas, amma sai ta kanne.
Haka dai suka ci gaba da hirar soyayya cikin
nishadi da nutsuwa har alfijir ya keto.
Wannan shi ne abin da ya faru tsakanin
gimbiya Zuhura da sadauki Kurbas bayan sun buya
cikin fadar wani tsohon boka da ke karkashin
kasa, wanda yai zamaninsa shekaru aru masu yawa.
a
***
Acan Nurul Kalbi kuwa, alfijir na ketowa sai
aka ga sararin samaniya ta kece da ruwan duwatsun
wuta.
Nan fa duwatsun suka ringa fadowa kan ginin
gidaje suna rushesu. Sannan kuma sai ruwan
kibiyoyin wuta ya biyo bayansu. Kafin kiftawar ido
duk wnai gini da ke tsaye ya baje kasa, kuma wuta
ta kama ko ina, sai ci take ganga-ganga, tamkar an
yi ambaliyar gobara.
Allahu Akbar! A wannan lokaci sama da
Musulmi dubu dari bakwai ne suka yi shahada. In
ba dan su sarki Maharaz sun kwanta a kas ba, sun
rufe jikinsu da garkuwoyi ba, da tuni sun halaka
49
Taskar Tsafi-3 Abdul aziz S. M/Gini
gaba daya. Duk da hakan ma sai da wadansu daga
cikinsu da yawa suka hallaka.
Babbar dabarar da su Maharaz suka yi, ita ce,
sai suka yi lam6o kamar sun mutu gaba daya.
Saboda haka, bayan abokan gaba sun daina sako
ruwan kibbau,sai suka sauko kasa cikin tsananin
farin ciki, su duba gawarwakin da ke wajen, wacce
ba ta mutu ba su karasa ta.
Ai kuwa suna saukowa sai su Maharaz suka
mike aka kaure da sabon azababben yaki.
A lokacin ne gimbiya Abidatul Azmal ma ta
sauko kasa. Koda ta hango sarki Maharaz yana
karkade dakarunta tamkar mai sassabe a gona. Sai
ta cilla kanta tamkar an harba kibiya daga cikin
kwari, ta dirga a gabansa, ta tare shi suka fara
masifaffen yaki. Nan fa wuri ya kara hautsinewa, in
banda ihun maza, karar karafa, da karajin aljanu da
dodanni babu abin da mutum ke ji.
A wannan rana Hasilatul Kurbas da yarima
Himal sun yi gagarumin aiki, domin duk inda suka
sa gabansu sai dai ka ga kafirai na zubowa kasa,
babu mai iya tsai da su.
Suma sauran mayakan Musulmai sun yi rawar gani
ainun, domin duk wanda ka duba sai ka ga
zuciyarsa a tafarfashe taje, banda kisa babu abin da
yake, saboda sun fusata sosai bisa ganin muguwar
Garnar da aka yi musu, ta baje wannan babban birni
30
Taskar Tsafi -3 Abdul'aziz $. M/Gini da kone shi, da kuma asarar dumbin rayukan 'yan'uwansu. A Gangaren gimbiya Abidatul Azmal da sarki Maharaz kuwa, abin yafi gaban kwatance, domin a wannan karon babu abin da Abidatul Azmal ke kokarin yi masa face ta kama shi ta daure, domin a tunanin ta ta gama cin wannan yaki, tun da ta gama rushe birnin, kuima ta kashe da yawan dakarunsa. Abidatul Azmal ta yi ta jefawa Maharaz tarkuna irin su
raga da kejin karfe na tsafi, domin ta kama shi, amma sai ya yi ta lalata su da takobinsa bisa taimakon addu'a da kuma tsagwaron-jarumtakarsa.
Lokacin da aka sami sa'a uku a haka, ba ta sami nasarar
kama shi ba, sai ta tabbatar da cewa lallai abin na yi ne, domin
tsafi ba zai taba nasạra ba, sai dai ta yi amfani da tsagwaron
karfin dantse. Nan take Abidatul Azmal ta yi jifa da duk
makamanta na yaki, ta rugo kan Maharaz, shi ma sai ya yi watsi
da na sa makaman ya tare ta, suka fara naushi da dukan juna
cikin fusata, zafin nama da juriya. Nan fa al'amarin ya sauya,
domin wannan karon kowannensu na wahala ainun. Nan da nan
suka hadawa kan su jini da majina. Kai tun suna bugun juna a
tsaye, har ma suka fadi kasa suna numfashi da haki, suka kasa
motsi. Koda suka huta, sai suka sake kaurewa da sabon
azababben fada.
A can bangaren su jarumi Himal kuwa, suma ba su daina
ragargazar arna ba. To amma fa da yake sarkin yawa yafi sarkin
karfi, an dada kashe Musulmai sama da dubu dari hudu.
Al'amarin da ya firgita su Hasilatul Kurbas kenan, suka tabbatar
da cewa idan aka kara sa'a hudu nan gaba a haka za a iya Karar
da dukkanin Musulman da ke taimaka musu, ya zama saura ita
da yarima Himal kadai. Tabbas su biyu kacal ba za su iya ba da
abokan gabar. Haka kuma sun hanga ko'ina ba su ga sarki
Maharaz da gimbiya Abidatul Azmal ba. Al'amarin da ya
dugunzuma hankalinsu kenan, suka rasa abin da ke musu dadi.
Haka dai suka ci gaba da wannan yaki, zuciyoyinsu cike da
fargaba. Ga shi a wannan lokaci rana ta fadi, gari ya soma duhu.
31
Daga can sai su Hasilatul Kurbas suka hangi Maharaz da Abidatul Azmal a can nesa da su kan wani katon dutse mai tsawo suna kwarmazuwa. Suna cikin fafan ne Abidatul Azmal
ta yi duba izuwa sansanin yakin, ta ga sauran kiris jama'arta su
gama da jama'ar sarki Maharaz, kuma nan take sai wani tunani
ya fado mata a rai. Ta tambayi kanta a zuciya ta ce, 'Wai shin
ina mata, yara, da tsofaffin garin nan ne? Tun da aka fara yakin
nan ban ga an kashe koda daya daga cikin su ba? Lallai duk yadda aka yi an foye su ne a wani wurin. Wai shin ma ina
sadauki Kurbas yake? Shi ma tun da aka fara yakin ban ganshi
ba. Kai duk yadda aka yi akwai tuggun da mutanen nan suka
shirya, ya zama wajibi na je 'na taimakawa mayakana mu karar
da makiyan can namu, sannan na juya kan Maharaz na nemi sa'a
akansa ta kowanne hali."
Abidatul Azmal na gama wannan tunani, sai ta tashi sama
kamar tsuntsuwa, ta tunkaro sansanin yakin, ta baro Maharaz
akan wannan dutse. Koda Maharaz ya ga haka, sai ya gangaro
kasa daka kan dutsen cikin azababben gudu, domin ya san cewa
idan bai yi sauri ya riski Abidatul Azmal a can ba, za ta yi
mummunar Garna. Wata kila ma ta sami nasarar hallaka
Hasilatul Kurbas da mijinta Himal.
Abin ka da wanda ke tafiya a sana, kafin Maharaz ya isa
sansanin yakin tuni Abidatul Azmal ia riga shi. Ai kuwa tana
dira ta fkawa Hasilatul Kurbas da yarima Himal, suka fara
mugun artabu. Ko dakika sittin ba a yi ba, Abidatul Azmal ta yi
wa Himal wani mugun duka da kafarta a fuskarsa. Saboda karfin
dukan sai da ya yi tsalle sama, sannan ya fado kasa a sume jini
na zuba a hancinsa da bakinsa. Al'amarin da ya fusata Hasilatul
Kurbas kenan, ta rusa uban ihu ta afkawa Abidatul A/mal da
dukkanin karfinta, cikin tsananin fusata.
Kafin Abidatul Azmal ta ankara Hasilatul Kurbas ta yi
tsalle a sama ta jera mata duka tara da kafarta a kirji. Duk da
juriya da sadaukantaka irin ta Abidatul Azmal, sai da ta yi baya
taga-taga ta fadi da baya.
32
Taskar Tsafi-3 _Abdul'aziz Hasilatul S. M/Gini Kurbas ta diro kasa za ta sake dukan kirjin
maida
Abidatul
Hasilatul
Azmal.
Kurbas
Ai kuwa sai Abidatul Azmal ta sa kafarta ta Kurbas ta
baya da karfin duka. Take Hasilatul
ya
lali da gudu da baya ta gwaru da wani dutse, har kanta fusho,
A
jini ya yi tsarluwa, ila ma ta sulale kasa sumammiya. daidai wannan lokaci ne sarki Maharąz ya įso sansanin yakin.
Himal, Koda ya ga abin da ya faru ga Hasilatul Kurbas da yarima sai ya fusata ainun, ya afkawa Abidatul Azmal suka cigaba da azababben yaki. Abidatul Azmal kuwa, sai ta dinga gudu daga gare shi tana yawo a sama kamar tsuntsuwa tana girbar kawunan Musulmai,
Al'amarin da ya dugunzuma hankalin sarki Maharaz kenan, domin shi kafai ne ya rage mai iya tabuka wani abų daga cikin Musulmai, tun da Himal da Hasilatul Kurbas sun suma.
Ba zato, ba tsammani sai aka ga wadansu halittu kamar tsuntsayc sun durfafo sansanin yakin daga can sama. Koda suka
matso kusa, sai sarki Maharaz ya ga ashe aljani Marwanul
Hasanu ne ya taho da gudunmawar wadansu Musulman aljanu
dakarun yaki, ga su nan birjik ba adadi.
Koda ganin wannan runduna, sai farin ciki ya mamaye
sarki Maharaz.. Ita kuwa Abidatul Azmal da jama'arta, sai
hankalinsu ya dugunzuına, domin sun san cewa sabon yaki ya
same su.
Kafin kiftawar ido su aljani Marwanul Hasanu sun sauko
Kasa sun afkawa dakarun Abidatul Azmal. Nan fa guri ya
hautsine, ihu da karaji da sararraki suka cika dodon kunne.
A wannan lokaci ne sarki Maharaz ya sami damar zuwa
inda Hasilatul Kurbas da Himal suke, ya yayyafa musu ruwa
suka farfado. Duk su ukun suka sake mikewa suka ci gaba da
yaki suna taimakawa aljani Marwanul Hasanu.
Abidatul Azmal ta wanzu a tsakiyar Muslman aljanu tana
ragargazar su da takobinta. Su kuwa suka kasa hallaka ta, amma
kuma suna ta hallaka aljanunta da dodanninta.
33
Haka aka ci gaba da wannan azababben zazzafan
matsanancin yakin mai tsanani, yakin mutuwa, yakin bala'i
yakin masifa, har dare ya raba, gari ya sake wayewa. Abin ka da
jiki mai jini da tsoka, sai Abidatul Azmal da su Maharaz suka
jigata, suka kasa ci gaba da yakin, dole suka zama 'yan kallo. yakin ya zamo na aljanu da dodanni kawai.
Koda ganin haka, sai Abidatul Azmal ta yi tsali ta bace
bat tare da ragowar dakarunta na bil'adama tsiraru. Koda ganin
haka, sai hankalin su sarki Maharaz ya tashi, domin sun San
cewa Abidatul Azmal za ta iya bin sawun su sadauki Kurbas la
hallaka su gaba daya. Nan take Maharaz, Hasilatul Kurbas
yarima Himal, suka nemi dawakai suka hau suka nausa cikn
daji a sukwane, suka tafi neman su sadauki Kurbas.
Su kuwa aljanu da dodanni da sauran bil'adaman
Musulmi, sai suka ci gaba da yaki. Koda aka jima ana yi, sai aka karar da duk bil'adaman, ya rage saura aljanu da dodanni. Nan la yaki ya zamo sabo tamkar sannan aka fara.
Sai da aka kwana ashirin da tara ana wannan yaki, sannan
aka gama shi. Ya zama su aljani Marwanul Hasanu sun sami
nasarar kashe dukkannin dakarun Abidatul Azmal. Bayan sun sha muguwar wuya, musamman aljani Marwanul Hasanu. wanda shi ne yafi kowa sara da yanka kimanin dari bakwai da tamanin da biyar. A karslie shi ma faduwa ya yi kasa a sume, sai da aka yi ta yayyafa masa ruwa, sannan ya farfado. In ka ganshi sai ka yi tsammanin a kogin jini aka tsamo shi. Nan dai aka shiga yi masa magani don a ceto rayuwarsa.
Wannan shi ne abin da ya faru a birnin Nurul Kalbi, bayan
an fafata kazamin yaki irin wanda ko a tarihi ba a taba jin kamarsa ba a nahiyar gaba daya.
***
Al'amarin Abidatul Azmal kuwa, lokacin da ta bace bat daga sansanin yakin tare da tsirarun dakarunta, ba su bayyana а
ko'ina ba sai a dajin da ke can bayan birnin Nurul Kalbi.
34
Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini
madubin
Bayyanar su ke da wuya sai Abidatul Azmal ta dauko
Kurbas ya
tsafi
bayyana
ta shafe shi da hannu. Nan take hoton su sadauki Kalbi, tun
a ciki, su da tsofaffi, yara da matan Nurul daga lokacin da suka baro cikin birnin izuwa lokacin
hoton
da suka shiga kogon dutsen nan. Suna shiga cikin kogon sai
cikin
ya daukc. Abidatul Azmal ta cigaba da kokarin ganin kogon, amma sai abu ya faskara. Koda ta matsa, sai madubin tsafin ya yi bíndiga ya farfashe. Al'amarin da ya dugunzuma hankalinta kenan, ta takarkare ta kwarara uban ihu cikin tsananin takaici da bakin ciki. Daga cai sai ta yi ajiyar zuciya, ta ce, "Lallai wafannan mutane suna nan a cikin kogon tsafin boka Auradul Azagab, bokan da ya yi zamanínsa shekaru dubu biyu da dari hudu da suka gabata. Tun daga lokacin da ya mutu kawo i yanzu ba a sami wani mahaluki da ya iya shiga
cikin fadarsa ba da ke cikin kogon. Ku zo mu je can kogon mu riski su Kurbas a can mu hallaka su."
Tana gama fadin haka ta sake yin tsafi suka bace bat, suka
bayyana a bakin kogon dutsen. Nan fa kowa ya ja da baya, aka
rasa wanda zai shiga ciki, sai da aka ga Abidatul Azmal ta shiga.
Sannan wasu kalilan suka bi bayanta. Da shigar su sai suka ga
babu kowa a ciki, kuma suka ga tsohuwar rijiyar nan wadda
yana ta lullube murfinta a rufe, babu alamar an bude ta. Abidatul
Azmal ta kurawa rijiyar idanu, sannan ta lumshe idanunta tana
karanta wadansu kalmomin tsafi. Kamar a mafarki sai ta ga
hoton lokacin da gimbiya Zuhura da sadauki Kurbas suka hada
karfi suka bude murfin rijiyar bisa taimakon karanta Bisimillah.
Sannan suka shiga cikin rijiyar tare da mata, yara da tsofaffi
gaba daya.
Koda ganin wannan al'amari, sai Abidatul Azmal ta fara
jarraba kokarin bude murfin rijiyar da karfin sihirin tsafi, amma
sam sai abu ya faskara. Nan da nan ta hada gumi, ta jike sharkaf.
Yayin da ta Kara matsawa sai ta ji kamar ana kona ta da wuta, ba
ta san sa'adda ta kwala ihu ba ta fadi kasa magashiyan kamar ta
suma. Al'amarin da ya dugunzuma hankalin dakarunta da ke
35
wajen kenan, suka rasa abin yi. Bayan Abidatul Azmal ta dawo
cikin hayyacinta, sai ta mike tsaye ta sake yin tsafi, takardu da
alkaluma suka bayyana a hannunta, nan take ta rubuta gajeriyar
wasika ta dorata akan murfin rijiyar. Sannan ta sake yin tsafi ta
Bace 6at tare da dakarunta. Lokacin da suk sarki Maharaz suka
baro birnin Nurul Kalbi bisa dawakai su uku, suka nusa cikin
daji. Sai da suka kwana bakwai suna neman su sadauki Kurbas,
amma ko duriyar su ba su gani ba. Al'amarin da ya tayar musu
da hankali kenan, har suka fara zub da hawaye, domin suna
ganin cewa an hallaka su gaba daya.
Sarki Maharaz ya tuna da yadda aka ruguje birninsa aka
kona shi gaba daya, sannan ya tuno da dumbin jama'arsa
wadanda suka yi JIHADI a wannan yaki, kuma ya tuno, da
mahaifiyarsa gimbiya Zuhura. Kawai sai ya fashe da kuka. Nan
take tausayi ya kama Himal da Hasilatul Kurbas, suka shiga
rarrashinsa, da.kyar dai suka lallashe shi, ya daina kuka. Sannan
suka mike suka hau dawakansu suka cigaba da neman da ba su
da tabbaci, domin sun gama karaya.
Sai da suka shafe kwana tara a cikin daji suna neman su
Kurbas, amma shiru babu alamunsu. A yammacin kwana na
goma sha shida ne suka ga sawayen kafafun mutane izuwa cikin
kogon boka Auradul Azagab. Cikin sauri suka sauka daga kan
dawakansu suka ruga cikin kogon. Ai kuwa suna shiga sai sarki
Maharaz ya yi arba da wasikar nan wacce Abidatul Azmal ta
rubuta ta ajiye akan murfin rijiyar nan. Cikin hanzar Maharaz ya
dauki wasikar ya ware ta, sannan ya fara karantawa kamar haka:
"Sako a gare ka ya kai sadauki Kurbas, ka yi sani cewa ni
gimbiya Abidatul Azmal ban san cewa kana cikin wannan rijiya
tare da mata, yara da tsofaffin birnin Nurul Kalbi ba.
Tabbas ba zan iya shigowa cikin wannan rijiya ba na riske
ku. To amma ina yi maka tuni da cewa jikokinka guda biyu,
wato 'ya'yan 'yarka Hasilatul Kurbas na tare da ni a can fadata.
Idan har kana son rayuwar jikokinka lallai ka zo mini da
36
Taskar I safi -3 Abdul'aziz S. M'Gini dukkanin
wana
wannan jama'a da ke tare da kai. Na ba ka wa'adin talatin, idan ba ka zo ba zan kashe jikokin naka. Sarauniya Abidatul Azmal."
Koda gama karanta wannan wasika, sai hankalin Hasilatul Kurbas da ma yarima Himal ya dugunzuma, suka fara kwalla. Nan dai suka hadu su ukun suka fara kokarin bude murfin rijiyar, amma sai suka kasa, sai da suka shafe sa'a uku a wajen suna ta yi dabaru iri-iri dan su bude rijiyar, amma babu nasara. Har sai da suka saduda suka zauna suka yi tagumi. Kowannensu ya yi zugum yana tunani. Daga can sai Maharaz ya mike tsaye ya nufi rijiyar cikin harzuka, sai kuwa su Himal suka bi shi da kallo kawai, suna mamakin abin đa yaké son yi, ålhali babu