Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 3
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels SKAR TSAL ALLIRL MAjej MUHD tag Not for stic ABDUL'AZIZ SANI M/GIN Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini TASKAR TSAFI-3 Lokacin da aka ruguntsume da azababben yaki tsakanin tawagar gimbiya Abidatul Azmal da mutanen birnin Nurul Kalbi, sai dakarun Abidatul Azmal suka lulluße garin gaba daya, tamkar kudan zuma akan kwason da ya sa zubi. Nan fa aka ci gaba da fafatawa, inda aljanu, dodanni, da dakaru marasa adadi suka yiwa mutane kalilan rubdugu. Amma saboda karfin addu'a, sai gashi kalilan mutane na taka muhimmiyar rawa. In banda Karar karafa, ihun mazaje, da kururuwar aljanu babu al in da mutum ke ji a wajen. Idan Musulrni ya sari kafirin aljani da, takobinsa, sai ka ga aljanin ya kama da wuta ya kone kurmus. Haka kuma idan suka sarki dodo ko mutum, sai ka ga ya darc biyu. Ana cikin wannan ruguntsumin fadane gimbiya Abidatul Azmal ta hango Himal, sadaiki Kurbas, da Hasilatul Kurbas suna ragargazar jama'ar ta. Nan takoe ta fusata, ta bayyana a tsakiyar su, ta afka musu da sara da suka. Su ukun suka rufar mata, amma sai ta zame musu annoba. Abidatul Azmal ta sami nasarar kaftawa kowanne su sara da dai-dai, ta zub da su kasa, kowannen su na murkusus a kasa ya kasa motsi. Abidatul Azmal ta tsaya akansu tana murmushin mugunya. A wannan lokaci sarki Maharaz na can 3 Taskar Ts tsakiyar abokan gaba sun lullube shi yana ta ragargazar su. Abidatul Azmal ta dubi su sadauki Kurbas daya bayan daya, ta bushe da dariya, sannan ta ce, "Ashe har kuna tsammanin zaku iya bijire mini ne, kuma ku tsira daga sharrina? Kun yi kuskure babba, kuma yanzun nan zan zare muku ruhin numfashin ku". Koda gama fadin haka, sai ta yunkura da nufin ta sare musu kawuna. Kawai sai taji an tari takobinta da wata. Ba kowane ya kawo wannan agaji ba face sarki Maharaz. Nan fa suka fara mugun artabu shi da iya cikin tsananin zafin nama, juriya, bajinta, da kwarewa. Duk su biyun suka wanzu suna kaiwa juna sara da suka tamkar jikinsu na karfe ne ba na jini da tsoka ba. A wannan lokacin ne su sadauki Kurbas suka sami kwarin gwiwa suka mike tsaye suka ci gaba da yaki. Sai da aka sami sa'a tara ana wannan yaki. Amma mutanen Abidatul Azmal ba su sami nasarar balla katuwar kofar da za su shiga inda aka bоуе yara da mata da tsofaffi ba. Haka kuma mutanen birnin Nurul Kalbi sun kasa karar da koda kaso daya daga goma na dakarun Abidatul Azmal, gashi kuma kowanne 4 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini bangarc sun fara gajiya. Amma aljanun da dodannin ko kadan babu alamar gajiya a tare da su. Yayin da aljani Marwanul Hasanu ke taka muhimmiyár rawa a wannan yakj. Sai ya fuskanci cewa jama'ar sarki Maharaz na cikin mugun hali, domin kuwa idan aka sake samun sa'a uku ana wannan gumurzu za su iya gajiya a cisu da yaki, tun da su aljanun da dodannin basa gajiya. Kuma gashi kashe su ake ta yi, amma kamar dada karuwa suke. Nan take Marwanul Hasanu ya sulale ya gudu daga wannan filin yaki, ya nufi wani babbar birni na jama'ar aljanu ma'abota addinin Musulunci, wanda ake kira Baitul Asmar. Daga birnin Nurul Kalbi zuwa birnin Baitul Asmar tafiya ce ta kwana biyar, amma sai Marwanul Hasanu ya dage iya karfinsa, ya dinga tsala hudu yana mi kada fuka-fukansa da sauri, domin ya isa wannan birni a cikin kwanakin da ba su haura uku ba. Burin sa shi ne a kawowa su sarki Maharaz dauki kafin a ci karfin su. *** A can birnin Nurul Kalbi kuwa, yaki ya kara tsamari ainun. Musamman kaurewar Abidatul Azmal da sarki Maharaz, wadda ta haddasa rugujewar gine-gine da dama da kuma kamawar 5 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini wuta bisa tsananin karfinsu, da kuma amfani da karfin sihirin da Abidatul Azmal ke yi. Sai dai duk tsafin da take yi ya ki ya yi tasiri akan sarki Maharaz, kasancewar shima yana ta karanto addu'o'in neman tsari. Ana cikin wannan dauki ba dadine daya daga cikin dakarun Abidatul Azmal ya gano cewa an boye mata da yara, da tsofaffi a cikin wani gida na Karkashin Kasa. Koda gano haka, sai yaja tawagar aljanu suka durfafi kofar wajen, wacce ta kasance Katuwar gaske ta bakin karfe. Aljanun na zuwa bakin kofar, sai sadauki Kurbas ya hangosu, kuma ya gane nufinsu. Ai kuwa sai ya falfala da gudu izuwa wajen. Kafin ya karasa ya daka tsalle ya dirga a gabansu ya hausu da sara. Suma suka rufar masa, amma sai gashi yana tarwatsa su suna konewa. Amma saboda naci, da taurin zuciya, wasun su nė suka yi ta tattudowa. Sai da aka sami sa'a guda Kurbas na ta ragargazar aljanun nan. Shi kađai ya zame musu alakakai, ya hanasu 6alla wannan kofa. Ana cikin haka ne wani shaidani ya ja wasu daga cikin aljanun suka kewayo ta bayan' Kurbas suka shammace shi suka sure shi izuwa sama, har takobinsa ta subuce daga hannunsa, kuma wani daga cikinsu ya watsa masa wata laka a baki ya kasa ci gaba da addu'a. 6 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini Koda ganin sun sami wannan nasara, sai wani daga cikin su ya taso sama daga kasa rike da takobin haske irin ta su ta tsafi, da nufin ya sare kan sadauki Kurbas. Ba zato ba tsammani, sia aka ga wata mace wadda ta rufe duk jikinta, har da fuskarta ta rugo da gudu rike da zabgegiyar takobi tana mai karanta wadansu addu'o'i a bakinta. Kawai sai ta yi tsalle ta dinga taka kan abokan gaba tana kara yin sama, har ta riski wanda ke shirin hallaka sadauki Kurbas, ta tsarga shi gida biyu, ya zama gawayi. Sannan ta tarwatsa wadanda ke rike da Kurbas, duk suka watse, sannan ta tallafo Kurbas a hannu kamar ta riko karamin yaro, ta sauko kasa kamar tsuntsuwa ta dira a hankali, ta dire Kurbas a kasa. A lokacin Kurbas ya furzar da lakoar da ke bakinsa, ya dubi wadda ta ceci rayuwar cikin tsananin mamaki, ya ce, "Wace ce ke?". Maimakon ta bashi amsa, sai ta yaye mayafin da ke fuskarta, suka yi arba da juna. Ba wata bace face gimbiya Zuhura, mahaifiyar sarki Maharaz. Nan fa mamaki ya turnuke sadauki Kurbas ya kasa cewa komai. Zuhura tayi murmushi a gare shi, sannan ta yi wuf ta tsugunar da shi kasa, takobin abokin gaba ta wuce ta saman kansa. Kafin ya yi wani yunkuri ta soke abokin gabar da takobin ta, ya sulale kasa. 7 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini A lokacin ne kuma wasu abokan gabar suka yo ca! a kansu, aka ci gaba da dauki ba dadi. A bangaren sarauniya Abidatul Azmal da Sarki Maharaz kuwa, al'amarin yafi gaban kwatance, domin wannan karon masifaffen yakin da suke yi ya ninka wanda suka yi a farko gamuwar su sau dari. Saboda bala'i, sai da suka bar kusa da birnin suka koma can gefe daya suna faffatawa, suna yaki irin na su na manyan sadaukai. Lokacin da gumurzu yai gumurzu, ya zamana gaba daya makaman Maharaz da na Abidatul Azmal sun lallace, sun kakkarye, sai suka ajiye batun tsafi da addu'a, suka kaure da matsanaicin sabon fada, suna naushi da bugun juna hannu da kafa. Wohoho! Hakika duk wanda bai ga wannan turnukun ba ya yi asarar kallo, domin a wannan fada ne mutum zai tabbatar da cewa sadaukantaka baiwa ce. Babu abin da zai baiwa mutum mamaki face irin yadda karfinjaruman biyu ya zo daya. Hatta juriya, bajinta, da kwarewar ma duk iri daya ne. Duk wanda ya sami nasarar naushin wani, kafin ya ankara dayan ya rama naushinsa. Sai da suka sake shafe sa'a uku suna laftar juna, sannan suka rabu da kansu, kawai sai suka fara ja da baya-baya. Sai da suka yi nisa da juna, kimanin taku arba'in a tsakanin su, sanan suka sake 8 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini rugowa ga juna, kowannensu zuciyarsa cike da mugun nufi. Koda ya rage saura taku goma kacal su hadu, sai duk suka daka tsalle a lokaci guda, suka hadu a sama suka yiwa juna gware da ka, fuskokinsu suka manne. Al'amarin da ya janyo kowannensu ya fita daga hayyacinsa, suka fado kasa a sume, kowannesu jini na zuba a hancinsa. Nan fa suka baje a kas kamar matattu. Bayan dan lokaci sai iska ta kada, Abidatul Azmal ta fara farkawa. Koda ta bude idanunta ta ga Maharaz a kwance, sai tayi murmushin farin ciki. Nan take tayi tsafi, wata takobi ta bayyana a hannunta, kawai sai taje kan Maharaz ta tsaya, sannan ta daga takobin sama da nufin ta caka masa a kirji. Amma sai ta tsay kyam ta kasa. A dai-dai lokacin ne Maharaz ya farka. Koda ya bude idanunsa ya ga Abidatul Azmal tsaye akansa rike da takobi ta kasa caka masa, sai ya cika da tsananin mamaki. Tsawon 'yan dakiku suka kurawa juna ido, sannan ya ce, "Me ya sa kika kasa kasheni, alhali kin sami babbar dama?". Abidatul Azmal ta yi ajiyar numfashi, sannan ta ce, "Kai kadaine sa'an fada na, idan na kasheka da wa zan yi? Rayuwa in ba makiyi babu abokan gaba ai ba dadi!". Sa'adda Maharaz yaji wannan batu, sai yayi murmushi, ya yi mata kallo mai nuna rashin yarda 9 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini ya ce, "Kunne yaji abin da kika fada, amma zuciya ba ta gamsu ba. Kiyi sani cewa ni da ke babu abin da zai tsai da gabar mu face fitar ruhin numfashi, domin har abada babu sulhu tsakanin wuta da ruwa". Abidatul Azmal ta yi murmushi ta ce, "Kwarai kuwa. Amma na tabbata cewa bayan na yi wannan yaki gabarmu ta kare". "Idan kika ga gabar mu ta kare, sai idan kin daina tsafi, ki karbi addinin gaskiya, in kuwa ba haka ba, to ki tabbata cewa bana numfashi a doron Kasa, shine kadai dalilin da zai sa ki ci birnin Nurul Kalbi da yaki". Kafin Maharaz ya gama rufe bakinsa, tuni Abidatul Azmal ta kawo masa wawar suka a ciki da wannan takobin tsafin. Cikin tsananin zafin nama ya goce, amma duk da haka sai da takobin ta huda rigar jikinsa. Maharaz ya yi wata irin katantanwa kamar an murza mazari, ya doki hannun Abidatul Azmal mai rike da takobin. Take takobin ta yi sama, taje ta tsire kanta a can saman wata bishiya mai tsawon gaske. Nan fa suka ci gaba da sabon turnuku da ruguntsumi. A can birnin Nurul Kalbi kuwa, masifa ta kai masifa, domin suma dakarun Musulunci an fara yi musu barna, domin an kashe sama da mutum dari 10 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini biyar, saboda azababben nacin aljanun da dodannin, wanda ya hadda sa rudewar wasu dakarun suka kasa ci gaba da yin addu'a. A wannan lokaci kuwa, Hasilatul Kurbas, yarima Himal, gimbiya Zuhura, da sadauki Kurbas, sun tsare bakin kofar nan inda za'a shiga a riski mata, tsofaffi, da kananan yara, sai dauki ba dadi ake yi da su a wajen. Dakarun Abidatul Azmal sun ci gaba da nacewa akan sai sun balla kogar sun shiga wannan gida na karkashin kasa, su kuma su Kurbas suka hanasu, aka ci gaba da cinikin rayuka a wajen. Haka dai aka ci gaba da wannan bala'i, har tsawon kwana da yini. Ba ma mutane ba, su kansu aljanu da dodannin da basa gajiya, sai da suka kagu a tsaida wannan yaki, saboda ganin yadda ake kaşhe 'yan uwansu tamkar ana zubo ruwan gawa daga sama. Su kuwa Dakarunun Musulunci, kishirwa da yunwa ce ta fara galabaitar da su. A 6angaren manyan zakuna kuwa, wato gimbiya Abidatul Azmal da sarki Maharaz, al'amarin ya wucea gaban kwatance, domin sai da suka sake suma har sau biyu, wato ya zamo kenan sun suma sau uku. Yayin da Abidatul Azmal ta farfado a karo na ukun, sai tayi tsafi, wani kaho ya baiyana a 11 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini hannunta. Take ta busa kahon, sautinsa ya cika dodon kunen komai. Hatta halittar da ke nesa da birnin Nurul Kalbi kimanin tafiyar sa'a goma sai da ta jiyo sautin kahon. Ana cikin tsakiyar yaki, sa Dakarun Abidatul Azmal suka jiyo sautin wannan kaho. Kawai sai duk suka daina yakin suka dinga tashi sama suna barin wajen yaki. Kafin kiftawar ido sun yi dandazo a can gaban Abidatul Azmal sun kewayeta a tsakiya ita da sarki Maharaz tamkar tsibiri a tsakiyar teku. A wannan lokaci sarki Maharaz ya farfado. Koda ya ga kansa a tsakiyar dumbin Dakarun gimbiya Abidatul Azmal, sai ya mike zumbur, yayi tsayuwa irin ta jaruman gaske ba tare da wata alama ta tsorata ba. Abidatul Azmal ta sa hannu ta share jinin da ke diga a hancinta, sannan ta dubi Maharaz cikin murmushi ta ce, "Gaishe ka namijin duniya, sarkin sadaukai. Ka yi şani cewa babu wanda zai yake ka anan, kuma kada kayi mamakin ganin dukkanin mayakana anan, ni ce na tsaida wannan yaki izuwa wani dan lokaci kadan, domin damu da ku, kowa ya sami lokacin hutu da kuma. sake tattaunawa da mayakansa bisa shawarar samun nasara". Gama fadin haka ke da wuya, sai tayi nuni da hannunta izuwa ga bayan Maharaz, take dakarun suka da re gaba daya suka ba da hanya. Abidatul 12 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini Azmal ta nuna hanyar ga Maharaz ta ce, "Ka tafi izuwa jama'ar ka, na baka kwana daya, ku sakc sabuwar damara, domin duk abin da aka yi yanzu share fage ne" Maharaz ya maida mata martanin murmushi ya cc, "Ko zamu shckara muna wannan yaki ba za ki sami nasara akan mu ba, domin mun kasance haske, ku kuwa duhu ne. Lallai ko yaushe gaskiya na bisa karya, ina tabbatar miki da ccwa Ubangijin mu ba zai bari muji kunya ba albarkacin Manzon Allah (S.A.W.), wanda'yai duniya da lahira dominsa". Yana gama fadin hakan yabi ta tsakiyar Dakarun ya kama tafiya. Sai da yai sa'a biyu yana tafiya a cikin su, sannan kuma ya sakc yin sa'a guda yana tafiyar, ya isa kofar birnin Nurul Kalbi. Tun daga nesa ya hango hayaki tsibi-tsibi na tashi, sakamakon wutar da aka karkashc. Gawarwaki kuwa, gasu nan birjik kamar an watsa tsakuwoyi a sahara. Nan fa ya fara jiyo kukan mata da yara kanana, wadanda suka rasa danginsu a wannan yaki. Al'amarin da ya karya zuciyar Sarki Maharaz kc nan, tausayi ya dabaibaye zuciyarsa. Haka dai ya ci gaba da wuce gawarwaki har ya iso tsakiyar gari, inda ya iske gaba ſaya Dakarunsa a tsaitsayc sun yi cirko-cirko, a gefe daya kuma sadauki Kurbas, yarima Himal, Hasilätul Kurbas, da 13 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S M/Gini gimbiya Zuhura nc a tsayc, kowannen su jikinsa ya rune da jini. Cikin tsananin mamaki Maharaz ya karaso gaban gimbiya Zuhura, ya kama hannunta ya jata gefe guda, inda babu mai jin abin da zai fada, sanna ya dubeta ta ce,"Ya ke Ummi na, shin ba kin cc ba za ki sake yin yaki ba a rayuwar ki? Wane dali ne ya sa yanzu kika sauya shawara?". Yayin da Zuhura taji wannan tambaya, sai tayi ajiyar zuciya, ta ce, "Ya kai dana, ka sani cewa tunda aka kafa birnin nan namu bamu taba ganin tashin hankali ba irin na yau. A yau na gha mayaka masu tsananin yawan da suka ninka Dakarun mua sau ba adadi. Na ga yadda 'yan uwana Musulmi ke ta yin shahada. Ba zan iya zuba ido ba kawai ina kallon wannan bala'i, dolc ne na bada gudunmawata ko dan saboda ma na samu rabon shahada a cikin wannan gagarumin yaki." Lokacin da gimbiya Zuhura ke wannan magana da dan sarki Maharaz, shi kuwa sadauki Kurbas ya Kurawa Zuhura idanu kawai yana mai tunani da mamakin dalilin da ya sa ta sai da rayuwar ta ta cete tasa. Haka kuma kyawunta ya kara jefashi cikin kogin begenta da kaunarta. Bayan Maharaz ya gama jin hujjar Zuhura ta wannan yaki, sai ya baro inda Zuhura ke tsayc уа laho gaban Dakarunsa, ya hau kan mumbari, sai 14 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini suka yi ta matsowa gaba, har sai da aka taru a wajc guda, gaba daya mutanen birnin, kuma aka yi tsit kamar mutuwa ta gifta. Sarki Maharaz yai gyaran murya ya ce, "Ya ku 'yan uwana, ku yi sani cewa ba a gama wannan yaki ba, yanzu ne ma aka fara shi. Ina ma kira a garemu da mu sallama al'amarin mu ga Allah, madaukakin sarki, wanda shi ne masanin yau da gobc. Kada mu yarda muji tsoron kafirai, saboda a yawansu da yawan makamansu, ko kuma saboda karfin sihirinsu. Lallai wanda ya yarda da Allah ya mika wuyansa garc shi, Allah na tare da shi. Da wannan furuci nake sallamar kowa domin muje mu binne 'yan uwanmu wadanda suka yi shahada. Bayan nan kuma ina kira ga dukkanin Malaman Kasar nan da mayakanmu da su taru a fada domin mu tattauna bisa hanyar da zamu bi mu sami nasara a wannan gagarumin yaki". Ba tarc da bata lokaci ba aka shiga dibar gawarwaki, sannan aka binnc su, tare da yi musu addu'a. Bayan an kammala ne Malamai da Dakarun yaki suka taru a fadar Sarki Maharaz.. Sa'adda Sarki Maharaz ya ga kowa ya hallara, sai ya mike tsaye ya cc, "Ya ku madafar birnin Nurul Kalbi, kuyi san cewa abokiyar gabarmu gimbiya Abidatul Azmal ta tsaida wannan yaki ne 15 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini izuwa tsawon kwana daya rak domin kowanc Bangare ya sami damar hutawa da yin shawara 6usa tadda zai samu nasara. Yanzu a cikin ku wayc zai bamu shawara mafi inganci bisa yadda zamu sami nasarar wannan yaki?". Koda jin wannan tambaya, sai kow ayai shiru, aka rasa wanda zai cc wani abu, har izuwa tsawon lokaci. Ba zato ba tsammani sai aka ga kofa ta bude, gimbiya Zuhura ta shigo ratayc da takobin mijinta marigayi sarki Makawi, kuma ta sha lullubo. Zuhura ta wucc taje har inda sarki Maharaz ke tsayc ta tsaya kusa da shi, sannan ta yayc mayafinta, sai ga kwalla a cikin idanunta. A lokacin ne ta hada idanu da sadauki Kurbas, ta saki tattausan murmushi a garcshi, wanda ya jefashi a cikin dimauya da rudewa har yaji kamar ya fashe da dariya dan murna, amma sai ya kannc. Zuhura ta matso hawayc daga idanunya, sannan ta sa hannu ta share shi, ta cc, "Ya kai dirkar birnin Nurul Kalbi, kayi sani cewa a yau ni gimbiya Zuhura, ina zub da hawaye saboda tunowa da namijin duniya, wato maigidana, kuma mahaifin sarkin ku. Idan baku manta ba, har sarki Makawi ya bar duniya ba'a taba cin kasarsa da yaki ba. Wannan takobi da ke ratayc a kafadata, ita cе takobin da Sarki Makawi ya yi yake-yakensa da ita. 16 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini Ni matarsa zan danka wannan takobi ga wanda ya cancanta ya mallaketa." Tana gama fadin haka, ta juya ta mikawa sarki Maharaz. Cikin sanyin jiki Maharaz ya karbi takobin, sa'adda hawaye ya subuce masa, sannan ya rataya takobin a kadadarsa. Zuhura ta dube shi ta cc "Da ikon Allah wannan takobi za ta zamo sanadin nasarar mu а wannan yaki. Ya kai dana, a iya kwarewata da sanin tuggun yaki, shawarar da zan bayar guda daya cc. Lallai a bude kofar nan ta can bayan gari a sirrancc, dukkanin matayen mu, yara da tsofaffi su fita ta cikinta su bar cikin birnin nan a daren yau, dimin idan abokan gaba suka dawo mana bala'in da za 'ayi sai ya ninka wanda aka yi a baya. Ina tabbatar muku da ccwa duk ginin da ke tsayc a birnin nan sai yajc kasa, kuma sai an kone komai namu ya zama toka. Mu tura mutanen mu izuwa can birnin Nurul Salam, in ya zo mu bar mayakan mu zalla anan aci gaba da fafatawa. Kun snai cewa birnin Nurul salam ya kasance hada ka ta Musulmai da kafirai, duk da cewar suna zaman amana da juna ba za'a rasa wakilan gimbiya Abidatul Azmal ba, dan haka ina mai da ba shawa rar idan matan mu, tsofaffin mu, da yaranmu za su 17 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini tafi can din, a hadasu da wadansu manyan Dakarun mu su yi musu rakiya". Koda gimbiya Zuhura ta zo nan a zancen ta, sai gaba daya Malaman goma suka yi kabbara, kuma aka yaba da wannan shawara ta ta, Nann fa aka fara tunanin jaruman da ya kamataa zaba su yiwa makaskantar rakiya izuwa birnin Nurul Salam, sai gardama ta karke. A Karshe sai gimbiya Zuhura ta ce, "Babu wadanda suka dace da yin wannan rakiya fa ce ni da sadauki Kurbas. Dalilina anan shi ne, mu kadai ne shekarun mu suka fi na sauran sadaukan mu, su kuwa sauran sadaukan sun fimu karfi da kuruciya, su ya kamata su tsaya suyi babban yakin". Yayin da manyan Malamai goma suka ji wannan shawara ta biyu, sai suka sake yin na'am da ita. Nan takc aka bada umarnin aje a fara shirycshiryc. Nan fa kowa ya watse daga fadar, aka bar sarki Maharaz shi kadai a zaunc, inda ya shiga sabon tunani. Kawai sai ya fara tunano abubuwan da suka faru tsakaninsa da gimbiya Abidatul Azmal, tun daga farkon haduwar su da ita, kawo i yanzu. Sa'adda ya zo kan lokacin da ta sami damar kashc shi, amma taki, sai ya dada cika da mamaki, yana mai tambayar kansa cikin zuciya, ya c, "Wai shin mene ne dalilin da ya sa Abidatul Azmal taki Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini kashe ni, alhali ta sami dama, kuma na kasance babban makiyinta a duniya?". Maharaz ya tunano da wani lokaci, sa'adda Abidatul Azmal ta yi masa wani irin kallo mai tattare da alamun tambaya. Tabbas irin wannan kallo baya rasa nasaba da kamuwa da kauna. "Idan dai har Abidatul Azmal ta kamu da kaunata, dan me take yakin neman rayuwata? Mе zai hana ta daina tsafi ta karbi addinin Allah?" Haka dai Maharaz yai ta tunani iri-iri, ya kasa samun amsoshin tambayoyin da yakc yiwa kansa. Wata zuciyar kuma sia ta ce da shi, "Hakika ya kamata kayi aurc ya kai Maharaz. To amma fa babu macen da ta dace da kai fa ce Abidatul Azmal. Domin a fegen kyau sai dai kuyi kunnen doki. Haka ma fagen jarumta da sadaukantaka. Koda Maharaz ya zo nan a zancen zucinsa, sai yaji zuciyarsa ta kamu da kaunar gimbiya Abidatul Azmal. Nan takoe cikin fushi ya mike ya dakawa kansa tsawa, ya ce, "Kai Maharaz, ka shiga hankalin ka! batun soyayya babu shi a tsakaninka da Abidatul Azmal har abada, babu sulhu tsakanin baki da fari, domin duk wanda ya sami dama zai disashe dayan ne. Wannan shi nc abin da ya faru ga sarki Maharaz bayan an gama shawara fadarsa bisa yadda za'a bullowa wannan gagarumin yaki. 19 Al'amarin sadauki Kurbas da gimbiya Zuhura kuwa, suna fitowa daga cikin fadar sarki Maharaz suka yi ta shiga gida-gida suna fito da mata, tsofaffi, da yara, tare da kayayyakinsu suna dora su akan dawakai da kekunan doki. Sai.da suka shafc sa'a shida suna wannan aiki, sannan suka kammala. A lokacin ne Sarki Maharaz da Hasilatul Kurbas suka zo garesu dan yin sallama da su, wanda ta kasance tamkar bankwana, tun da babu wanda ke da tabbacin zai sake saduwa da wani. Hasilatul Kurbas ta dubi mahaifinta sadauki Kurbas tana kuka, ta cc, "Ya kai Abbana, kayi sani ccwa yau ne karo na biyu da zan yi rabuwa da kai, irin waccc ba zan taba mantawa da ita ba. Rabuwar farko ita ce ranar da aka daura min aurc da mijina Himal, na bar gidanka. Yau kuma gashi zamu rabu bisa Jihadi, dan daukaka kalmar Allah. Wata Kila wannan rabuwa za ta zamo ta karshe a tsakanin mu. Idan har hakan ta faru, ina mai rokonka da ka gafarce ni bisa duk irin laifukan da nai maka na fili da na 6oye". Koda jin wannan batu, sai hawayc ya zubowa sadauki Kurbas, ya ce, "Ya ke 'yata, ki yi sani ccwa baki taba yi mini laifi ba tun ma kina karamar ki 20 Taskar Tsafi-3 Abdul'aziz S. M/Gini kawo izuwa yanzu. Idan ma kin yi mini ban sani ba, to na yafe miki duniya da lahira. Ina yi

Chapter 1 of 3