Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
daga bakin 'yarsa, sai ya fashe da kuka yana mai cewa, "Ki gafarce ni ya ke 'yata, domin ba zan iya mancewa da mahaifiyarki ba, kuma ba zan iya daina begenta ba, domin har yau har gobe ban ga wata 'ya mace mai kyau kamar ta ba, kuma na san cewa bazan gani ba daga nan har izuwa ajalina." Nan dai Hasilatul Kurbas ta ci gaba da rarrashin sa ta jashi izuwa masaukinsu inda Sahal yai musu jagora. Al'amarin Sarki Maharaz kuwa, bayan ya rabu da su Kurbas sai ya wuce izuwa bangaren da mahaifiyarsa gimbiya Zuhura take, wato matar marigayi Sarki Makawi. Da shigarsa cikin turakarta sai ya iske ta a zaune ruke da wata tsohuwar alkyabba ta mahaifinsa tana shafarta da hannu, idanunta cike da kwallah. Yayin da Zuhura taji motsin shigowar sa ta dago kai suka yi arba, sai tayi jifa da alkyabbar ta mike tsaye ta rugo gareshi tana mai farin cikin ganinsa. Maharaz ya kama hannunta suka zauna tare a gefen gado lokacin da hawaye ya subuto masa sannan ya dubeta ya ce, "Ya ke ummi na, shin ba za ki daina yawan begen mahaifina ba? Ina tsoron kada yin hakan ya haifar da wata lalura a 16 gareki". Zuhura ta sa hannu ta share hawayen Maharaz ta ce, "Ya kai dana ka yi sani cewa mahaifinka ya cika gwarzo, kuma namijin duniya, domin a zamaninsa shi ne ya zamo gagara badau, kuma dodo ga dukkan makiya Allah. Kayi sani cewa mahaifinka da ban yake da sauran maza, dan haka ba zan iya rage begensa ba a cikin zuciyata. Tabbas mutuwa ta yi min gaggawa da ta rabani da masoyina a lokacin da muke kan tsakiyar kauna da kula da juna. Ga shi har yanzu na kasa yin wani auren. domin na'san cewa ba zan taba samun kamarsa ba". Sa'adda Zuhura ta zo nban a zanceta, sai Maharaz ya fashe 'da kuka, ya mike ya ce, "Ummina ina mai shawartarki da ki rungumi kaddara ki yi aure, domin koda ajalinki zai riskeki ya riskeki a dakin mijinki, domin baki tsufan da kika wuce kiyi aure ba. Ki tuna cewa shekaruna ashirin da bakwai kacal, ke kuma yanzu kina da shekaru arba'in da biyar. Shin bakya son na ga na sami kanne kafin nima nayi aure na haihu". Koda ji haka sai Zuhura ta fashe da kuka, ta ce, "Ya kai dana, ina son ka samu kanne. To amma ka сі gaba da yi mini addu'a Allah ya bani mijin da ya dace dani." Maharaz ya yi murmush cikin yanayin farin ciki ya ce, "Amin." Daga wannan rana su sadauki Kurbas suka tsinci 'kansu a cikin sabuwar rayuwa, a cikin Birnin Nurul Kalbi, rayuwar da ta zame musu mafi dadi a duniya, domin sun ga cewa Musulmai suna rayuwa mafi inganci da kwanciyar da hankali. Sun yi mamakin yadda mutane suke zaman gaskiya da gaskiya, ga amana, ga adalci, babu zancen wani yafi wani. Da attajirai da talaka da 17 mai mulki babu wanda yafi wani. Duk wanda yai laifi komai girmansa da matsayinsa za'a yi masa hukunci irin wanda ake yiwa kowa. Tsawon kwana ashirin da daya da suka yi a birnin basu taba jin an ce yau ga barawo ba. Ba su ji ance ga wani yayi fyade ko kwace ba. Kai ko cin zali tsakanin mai karfi da mara karfi basu taba gani ba. Kullum ko yaushe jama'a na cikin zaman lafiya, taimako da kaunar juna. Wannan al'amari ne ya janyo hankalin sadauki Kurbas, Hasilatu! da yarima Himal suka ji kaunar addinin Musulunci ta shiga cikin zuciyoyinsu, musamman ma ganin yadda mutanen gari suka kaunace su ba da tsangwama ba. A daren kwana na ashirin da daya ne suka kai kansu fada a matsayin suna son su musulunta. Koda jin wannan batu daga garesu sai farin ciki ya kama Sarki Maharaz da manyan Malaman nan, wato su ammar bn Safiyan. Ba tare da 6ata wani lokaci ba aka biya musu kalmar shahada, suka maimaita, sannan aka fara koya musu ilimin addini. Kafin Sarki Maharaz ya bar fadarsa ya dubi su Kurbas ya ce, "Na shirya muku walima a gidana gobe da yammaci, dan haka zan turo ayi muku jagora izuwa gidan nawa, idan lokaci ya yi. Yayin da su yarim Himal suka ji haka sai suka yi murna da godiya. Lokacin da Maharaz ya isa gida, sai Zuhura ta dube shi ta ce, "Ya kai dana, wane irin abin farin ciki ne ya sameka haka na ga fuskarka cikin annuri da annashuwa?". Maharaz ya yi murmushi ya ce, "Ai ina murna ne saboda bakin nan nawa wadanda na zo da su sun karbi addinin Musulunci a yau din nan. Kuma a dalilin haka ma na ke son na shirya musu walima ta musamman anna gidan gobe da yammaci."18 Sa'adda Zuhura taji wannan batu sai ita ma ta cika da farin ciki, ta ce ai kuwa ni da kaina zan shirya wannan walima, kuma da kaina zan karbi wadannan manyan baki, domin yanzu sun zama cikakkun 'yan uwanmu." Yayin da Maharaz yaji wannan batu daga bakin mahaifiyarsa sai ya kara cika da farin ciki fiye da da, yai ta yi mata godiya. Wannan shi ne abin da ya faru tsakanin Sarki Maharaz da su sadauki Kurbas bayan aljani Marwanul Hasanu ya daukosu daga can kurkukun Ukubatul Dukkan. Al'amarin gimbiya Abidatul Azmal kuwa, lokacin da ta koma fadarta, bayan ta rabu da Sarki Maharaz, sun gama fafata azababben yaki. Sai ta kira maga takardarta ta sa shi ya rubuta wasika guda daya rak, ta gayyatar gaba daya wakilanta na kasashe dubu biyu da ashirin da uku, wadanda ke karkashin mulkinta. Sa'adda maga takardar ya gama rubuta wasikar guda daya, sai Abidatul Azmal ta nunata da yatsa, take wasikar ta zama guda dubu hudu da ashirin da uku. Abidatul Azmal ta runtse idanunta ta fara kiran sunayen wadansu aljanu har guda dubu hudu da ashirin da uku. Ai kuwa tana fadın sunan na karshe, sai ga su sun bayyana gaba daya. Cikin izza da nuna isa ta dubesu ta ce, "Ko wannen ku ya dauki wasika guda ku rabu izuwa kasashena na bil'adama guda dubu biyu da ashirin da uku, da kuma kasashe na na aljanu da dodanni ku kai musu wadannan wasiku na gayyata izuwa yaki ga birnin Nurul kalbi. Duk kasar da kuka je ku sanar da sarkin su cewa ina son 19 ya hada min runduna ta mayakansa guda dubu dari, kuma lallai ya hallara a nan fadata nan da kwana saba'in zamu dunguma a wannan rana, ina son mu baje birnin gaba daya, mu hallakar da duk mahalukin da ke numfashi a cikinsa face mutum daya, wato Sarkin su Maharaz. Lallai bana son koda kuda ya taba lafiyarsa". Nan take aljanun guda dubu hudu da ashirin da uku suka dauki wasikun nan dai-dai suka tashi sama, suka cika sararin samaniya, kamar dangin 'yar tsewala na shagalin biki. Bayan tafiyar manazannin ne, wazirin gimbiya Abidatul Azmal yai karambani ya tambayeta ya ce, "Ya shugabata mene ne dalilin da ya sa ba kya son a taba lafiyar Sarki Maharaz? Shin ba kya tsoron cewa idan kika barshi a raye kamar kin kashe maciji ne ba ki sare kansa ba." Koda jin haka, sai fuskar Abidatul Azmal ta murtuke izuwa tsananin fushi. Cikin zafin nama ta yiwa waziri barin makauniya a fuskarsa da kafarta. Saboda Karfin dukan, sai da ya yi tsalle sama ya hadu da rufin saman fadar, sannan ya fado kasa tim, jini yana zuba ta hancinsa da bakinsa. Ko kyakkyawan motsi bai yi ba rai ya yi halinsa. Abidatul Azmal ta dakawa wasu dakary biyu tsawa da ke gabanta, ta ce, "Ku dauke min gawar wannan tsohon banzan". Dakarun suka kinkimi gawar jikinsu na tsuma suka yi waje da ita. Abidatul Azmal ta dubi sauran fadawanta daya bayan daya, kowannensu sai ya sunkwi da kansa kasa yana makyarkyata cikin fargaba. "Daga yau duk wanda ya sake yi min katsalandan a cikin harkokina daga cikinku, zai fuskanci irin hukuncin da na yiwa waziri a yanzu. Ku tashi ku bani 20 wuri na sallame ku!". Cikin rawar jiki su duka suka mike suka fice daga fadar, kowa ya watse, ya zamana saura Abidatul Azmal ita kadai a zaune bisa karagar mulki. In ka dauke fitar numfashinta baka jin sautin komai a fadar. Nan fa Abidatul Azmal ta shiga tunani mai zurfi, inda ta dinga tuno da irin azababben yakin da tayi da sarki Maharaz. Sannan ta tuno da lokacin da ya ceci rayuwarta, sa'adda ta zama mashi zata soke shi da ya doketa ta fada cikin rami mai zurfi, kuma ya bita da gudu cikin ramin ya rikota. A lokacin da ta dawo siffarta ta bil'adama sun sami damar kurawa juna ido, a wannan lokacin ne ta lura da tsananin kyawunsa ta tabbatar da cewa inda shi mace ne babu makawa sai ya fita kyau. Abidatul Azmal ta tuno da tsagwaron jarumtaka irin ta Maharaz sai ta ga cewa tabbas duk duniya babu da namiji da ya fi dacewa da ita sama da shi. Nan take ta ayyana a ranta cewa bayan taci birnin Nurul Kalbi da yaki za ta tursasa Maharaz tayi masa dole ya fita daga addinin Musulunci sannan ta aure shi. Haka dai Abidatul Azmal tayi ta wannan tunani, ba ta gushe ba tana yi har ta tsinci kanta a cikin tsanani kauna da begen Maharaz. Koda ta dawo cikin hayyacinta, sai ta gane cewa hakika tayi kuskure, domin babu yadda za'ayi tayi wannan soyayya da wanda shi ne babban makiyinta a duniya, domin gabar da ke tsakaninsu ta asali ce mai hjja. Kuma ta ya ya' shi Maharaz zai yarda da ita har ya karbcta a matsayin abar kauna?. Amsar da ba ta sani ba kenan, kuma ita ce ta sake jefata cikin sabon tunani. Wannan shi ne abin da ya faru ga Abidatul Azmal bayan tayi kazamin fada da Sarki Maharaz na birnin/ Nurul Kalbi. 21 A can birnin Nurul Kalbi kuwa, kashe gari, wato ranar da aka shiryawa su Kurbas walima, sai suka ci ado suka yi shiga ta kamala irin ta addinin Musuluncu, aka turo manzo ya yi musu jagora izuwa gidan Sarki Maharaz. Da shigar su babban falon gidan, suka hango babbar shimfida cike da abinci da abin sha iri-iri. Zaune a gefe guda Sarki Maharaz ne tare da mahaidiyarsa gimbiya Zunura wacce ker sanye da fararen tufafi, kuma ta rufe fuskarta da wani farin kyalle, wanda shi ne ya lullube kanta gaba daya, kuma ya kasance mai dishidishi. Da yake jarumi Himal ne akan gaba, sai ya yi sallama, a lokacin da Hasilatul Kurbas ke biye da shi, sannan sadauki Kurbas. Koda jin sallamarsu, sai Maharaz ya amsa suka mike tsaye shid a Zuhura suka tahi bakin kofa domin taryar bakin nasu. Da zuwa aka hadu a bakin kofa, inda Zuhura ta yaye lullubinta, kyakkyawar fuskarta ta bayyana garesu. Nan fa su duka sukoa kame tamkar gumaka, saboda tsananin mamakin ganin kyawun da Allah ya ba ta. Duk da cewar shekarun gimbiya Zuhura sun kai arba'in da biyar, ba za ka taba cewa ita ce ta haifi Sarki Maharaz ba, domin ta kasance tamkar budurwa 'yar shekara goma sha takwas, domin Allah ya bata jiki mai kyawun křra. Anna ne fa sadauki Kurbas ya tabbatarwa da kansa cewa ya yi karya da yake zaton cewa ba zai sake ganin mace mai kyauba kamar matarsa marigayiya Anisa. Lokacin da Maharaz ya fuskanci cewa su !limal sun shiga wani hali bisa ganin kyawun mahaifiyarsa, sai 22 yayi gyaran murya da karfi, suka dawo hayyacinsu, sannan ya gabatar da mahaifiyarsa a garesu inda suka kara cika da mamaki, domin su a zatonsu yayarsa ce ko kuma 'yar uwarsa. Nan dai suka koma gaba daya suka zauna akan wannan shimfida mai dauke da kayan ciycciyc da shaye-shaye. Tun da sukoa zauna Kurbas ya kasa samun sukuni, ya yi ta satar kallon gimbiya Zuhura. Ita ma kuma haka taui ta satar kallonsa, amma in banda Hasilatul Kurbas babu wanda ya lura da abin da ke faruwa. Nan dai aka ci aka sha, tare, sannan aka yi hira, har izuwa lokaci mai tsawo, sannan su Kurbas suka yi sallama da godiya suka koma masaukinsu. Tun daga wannan rana da aka yi wannan walima, Zuhura da Kurbas suka shiga cikin wani irin sabon yanayi na yawan tunani da damuwa. Domin a wannan rana ma da aka yi walimar sadauki Kurbas kasa barci ya yi saboda tsananin bege gimbiya Zuhura. Har ma Hasilatul Kurbas ta fito daga dakin mijinta Himal ta zo ta ganshi a zaune ya yi tagumi yana tunani. Cikin matukar damuwa ta zo gabansa ta ce, "Ya kai Abbana, kayi sani cewa ka daukowa kanka babban aiki, wanda yafi karfika. Na sani cewa ba komai ne ya hanaka barci ba a wannan dare ba face tunanin gimbiya Zuhura mahaifiyar Sarki Maharaz. Ina mai shawartarka da ka cire sonta a cikin ranka da gaggawa, domin banyi zaton aure zai iya kulluwa ba a tsakaninku. Saboda na samu labarin cewa tun da mijinta ya mutu ba ta sake sha'awar kara aure ba." Koda jin haka sai Kurbas yai shiru bai ce komai ba. Har dai Hasilatul Kurbas ta gaji da surutanta ta fice. Kamar yadda Kurbas ya zamo a cikin yawan begen Zuhura, haka itama ta kasance, amma sai ta daure 23 ta danne abin a cikin zuciyarta, ba ta yarda wani ya fahimta ba. Amma har satar hanya take, tayi bad da kama ta wuce ta inda aka sauke su ta kare masa kallo ba tare da ya sani ba. Wata rana da sassafe, sai ga aljani Marwanul Hasabu ya zowa Sarki Maharaz a galabaice,. kai da ganinsa ka san ya sha bakar wuya. Marwanul Hasabu ya fadi gaban Maharaz yana numfashi ya сe, "Ya shugabana kayi sani cewa ga gimbiya Abidatul Azmal can tafe da dakarun yaki marasa adadi daga jinsin mutane, aljanu, dodanni. Tabbas wannan karon tayi rantsuwa cewa sai ta mai da birnin Nurul Kalbi ya zama turbaya. Duk mahalukin da ke numfashi a cikinsa, walau mace ko namiji, sai ta zare masa ruhin numfashi, face kai kadai kawai". Koda jin wannan batu sai hankalin kowa ya dugunzuma, jama'a suka rude suka dimauce, aka kama salati, wasu kuwa suka hau surutai iri-iri da tunanin guduwa. Koda ganin haka sai sarki Maharaz ya daka tsawa aka yi tsit, sannan ya ce "Ya, ku 'yan uwana Musulmi, yanzu zan baku wani labari wanda zai Kara muku kwarin gwiwa bisa wannan al'amari." Nan fa mutane suka yi tsit aka fara sauraren Sarki Maharaz inda ya fara bayar da labari kamar haka. "A wani zamani can baya, an yi wata babbar daula mai suna Sharmur, anan yankin Kasashenmu. Daular Sharmur ta hada garuruwa da dama, kimanin dari biyu da arba'in, kuma kowanne gari yana da Sarkinsa mai iko Wani babban abin sha'awa shi ne wadannan garueruwa guda fari biyu da arba'in suna zaman lafiya fiye da shekaru hamsin baya, babu wata kasa da ta taba yakar wata, kasancewar akwai kyakkyawar mu'amala a 24 tsakaninsu, kuma al'adar su duk iri daya ce, wasu suna butar rana, ko wata, wasu giwa, wasu dutse. Kai wasu ma basu da addini. Daga cikin wadannan kasashe akwai wani babban gari, wanda yafi duk sauran girma, arziki da karfin mayaka, wanda ake kira Darul Hasmar. Darul Hashmar na karkashin jagorancin wata sarauniya 'yar kimanin shekaru tamanin da uku mai suna Ummul Nisai. Ba komai ya sa ake kiranta da wnanan suna ba face 'ya'yanta bakwai, kuma duk matane budurwoyi wadanda suka kasace sako dasako. Ummul Niusai ta gaji sarautane a wajen mijinta sarki Darusul Hamaru, wanda farautar nenman wani tsibiri ya zamo ajalinsa. Ance a zamaninsa babu irin abin da bai yi ba don ya sami haihuwar da namiji, amma abu ya gagara. Sarki Darusul Hamaru ya auri mata sama da dari, amma babu wadda ta taba haihuwa face Ummul Nisai. Kuma duk sa'adda tazo haihuwa sai yaga 'ya mace take haihuwa. A duk sa'adda hakan ya faru sai sarki Darusul Hamanu yayi gagarumi bakin ciki, sannan kuma ya dinga kukan takaici kenan, dare da rana har izuwa lokacin da za'a radawa jaririya suna. Ba wani abu bane ya sa sarki Darusul Hamanu tsananin bakin ciki da damuwa ba bisa rashin samun haihuwar da namiji face wata gaba ta asali tsakanin zuriyar wani sarki da ake kira Hurmas bn Salkas, wanda ke muli a wata daula dan daban da ake kira Dulkar. Daular Dulkar ta kunshi garuruwa sama da guda dari uku. Kuma ita garuruwanta gaba daya a karkashin Jagorancin Sarki Hurmas bn Salkas suke, sabanin daular Sharmura wacce ko wané gari na da nasa sarki mai cikakken iko 25 Asalin gabar da ke tsakanin sarki Darusul IHamanu, wato mijin sarauniya Ummul Nisai da kuma sarki Hurmas bn Salkas ta faru ne a wasu shekaru kimanin sittin baya, sa'adda kowannesu ya fita yawon rangadi tare da dakarunsa, masu tsaron lafiyarsa. Masana tarihi sun ce a wannan lokaci Sarki Darusul Hamanu ya fita wannan rangadi nbe da dakaru dubu da da hamsin. Shi kuwa Sarki Hurmas bn Salkas na daular Daulkar, ya fita ne da dakaru dubu dari biyar da arba'in. Wato ninkin baninkin na Sarki Darusul Hamanu. Gaba dayansu sun fito wannan rangadi ne domin neman wnai kyakkyawan tsibiri wanda suka sami labarinsa a wajen bokayensu. Shi dai wannan tsibiri ana yi masa lakabi da tsibirin rayuwa. Tsibirin rayuwa ya kasance guri ne mai yalwar ni'ima, wacce a wannan zamani babu wani wuri mai ni'imarsa, kasancewar yana da kasa mai albarka ta noma, da kuma ma'adanan kasa mai yawa, kamar su zinare, yakutu, da lu'u-lu'u. Haka kuma kogin da ya zagaye wannan tsibiri yana da ruwa mai kyau da dadin dandano. Gashi da haske garai-garai gwanin sha'awa. Mutane sun canfa wannan tsuburi cewar duk abin da yake zaune a cikin sa ko kuma ya shigo cikinsa dole ne ya zamo a cikin-koshin lafiya a ko yaushe. Babu abin da zai baiwa- mutum mamaki face koda mutum zai shekara dari a wajen ba zai taba hanin kuda ko sauro ba. Haka kuna ba za ka taba ganin kwaro ko dabba ba mai cutarwa a tsibirin face wadda za ta iya zama abinci ga bil'adama. Kash! Duk wannan ni'ima da ke cikin wannan tsibiri sai ta zamo a banza, domin masu bincike sun gano cewa babu wani mahaluki daya taba ketare 26 wannan kogi ya isa tsibirin rayuwa har ya yi sa'a guda kacal a cikinsa. Ma'ana duk mutumin da ya sami damar zuwa tsiburin mutuwa yake yi, kuma an kasa gano abin da ke kashe mutane. Babu irin bincikend a matsafa basu yi ba, amma sun kasa ganowa. A wannan shekaru da sarki Darusul Hamanu da kuma Sarki Humras bn Salkas suka tafi neman tsuburin rayuwa, a sannan ne bokayensu suka smai nasarar gano abin da ke hallaka mutane a wajne, sanann suka sami maganin abin. Ba wani abu bane ya ke hallaka mutane face wasu fatalwoyi na wadansu tsofaffin aljanu, wadanda tun ainahi su suka fara gina fadarsu a cikin wannan tsuburi. An ce aljanun sun fi shekara dubu hudu da mutuwa, amma har kwanan gobe sunki yarda su bar wani mahaluki yaji dadin wannan tsuburi. Boka Shamnas wanda ke wakiltar Sarki Darusul Hamanu da kuma boka Salbatu mai wakiltar Sarki Hurmas bn Salkas, sun kirkiri wani kuttun fata wanda suka cikashi da wata irin jar iska ta tsafi, wacce in dai aka bude kuttun iskar ta fita a can tsibirin rayuwa, sai gaba daya fatalwoyin nan sun kone kurmus. A rana guda bokayen biyu suka sami nasarra kammala wannan aiki, kuma kowannesu ya sanar da sarkinsa da gaggawa. Bisa rashin sa'a sai sarakunan biyu suka shirya a lokaci guda suka baro kasashen su izuwa wannan tsuburi na rayuwa. Daga kasashen su zuwa wannan tsibiri, nisan tafiyar iri daya ce, wato tsawon kwana arba'in da daya ce kacal. Ba zato ba tsammani sai wannan runduna biyu tayi gamon bazato a bakin wannan kogi na tsuburin rayuwa. Nan fa aka tsaya ana kallon-kallo cikin tsananin 27 mamaki. Musamman boka Shamnas da boka Salbatu, saboda ganin cewa kowannensu na rike da kuttun jar iska. Sarki Hurmas da sarki Darusul Hamanu suka kurawa juna ido cikin harara da takaici. Dama tuntuni basa ga maciji, domin babu wata alaka ta kasuwanci a tsakanin daulolin biyu. Kuma doka ce babba dan kowacce daula kada ya shiga cikin dayar da ba ta sa ba. In kuwa ya shiga a bakin ransa. Cikin tsananin fusaya sarki Hurmas ya dubi Sarki Darusul Hamanu ya daka masa tsawa, ya ce, "Ya kai wannan makaskancin sarki, ka sani cewa daulata tafi taka yawa da karfi, dan haka ina mai shawartarka da ku koma da baya ku hakura da wannan tsibiri, in ba haka ba kuwa yanzun nan zamu karar da ku ánan wajen. Dayanku ba zai tsira da rayuwarsa ba". Yayin da sarki Darusul Hamanu ya ji wannan batu, sai ya kyalkyale da dariya, ya ce, "Karyarka ta sha karya ya kai wannan azzalumin Sarki. Ko dai kai da jama'arka ku janye mana ku koma da baya, ko kuma ku zama gawa. Tabbas mune muka fiku cancanta da mallakar wannan tsibiri". Carafn sai bokayen biyu suka ce "Ku tsaya". Cikin hadin baki. Daga nan sai suka runtse idanuwansu suka shiga bincike acikin tsafi. Bayan 'yan dakıku kadna sai kowane boka ya matsa kusa da sarkinsa yai masa 'magana cikin rada. Faruwar hakan ke da wuya sai sarki Hurmas ya kyalkyale da dariya, sannan ya turbune fuska kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa. Ya dubi Darusul Hamanu ya ce, "Ya kai wannan sarki, bincike ya nuna cewa idan muka yaki junanmu dayanmu anan ba zai tsira da rayuwarsa ba. Zai fi kyau ka hakura ka 28 tsibirin nan domin ni ba zan iya bar maka ba" bar mını Darusul Hamanu ya kyalkyale da dariya ya сe, "Kamar yadda kake jin ba za ka iya bar mani ba, nima ba zan iya bar maka ba. Abu daya zana iya yarda da shi shi ne mu raba tsiburin biyu, kai ka dauki rabi, nima na duaki rabi". Cikin tsawa Hurmas ya ce, "Ba zan yiwu ba, domin nan fadata zata dawo. Kai ma kuma na san taka nan za ta dawo. Ka sani cewa ba'à sarki biyu a birni guda. Na rantse da girman karagata da dai ayi haka gwara muyi ragas." Sarki Hurmas na gama fadın haka ya baiwa dakarunsa umarni su afkawa su sarki Darusul Hamanu. Al'amarin da bai yiwa bokayen biyu dadi ba kenan, Hankalinsu ya dugunzuma, amma babu yadda za su yí, dole suma suka aſkawa junansu domin aikin gama ya gama. Nan fa wuri ya yamutse, kura ta tashi ta turnuke sararin samaniya. Hayaniyar dawakai, karar makamai, da ihun kuwar mazaje suka cika dodon kunen. Wohoho! A wannan rana anyi azababben yaki, domin sai da dakarun Sarki Darusul Hamanu suka bajwa dakarun Sarki Hurmas mamaki, duk da cewar sun ninka su yawa, domin kasuwar cinikin rayuka ce ta bude, sai ka kawunan bil'adama na shawagi a sararin sama kamar 'ya'yan balbelu, jini kuwa ya dinga tartsatsi da fantsama kamar cali na fesar da ruwa. Sai da aka yini ana wannan yaki, ya zamana saura mutum hudu kadal a tsaye suna fafatawa. Amma gaba daya wajen ya cika da gawarwaki, jini kuwa har shanye kafafuwansu yake yi, iya idon kofar. Wadannan mutane hudu da suka rage ba wasu bane fa ce Sarki Darusul Hamanu, Sarki Humras bn 291 sun Salkas, jigaya, boka Shamnas, da boka Salbatu. Dukkanin su sun yi jina-jina. Su kuwa su Boka Shamnas, a jikinsu mai har da ma kunar wuta sihiri. yawa ba adadi, sbaoda amfani da karfin Hamanu Sarki Hurmas ya sake tasowa Sarki Darusul ya taso masa. da dukkan karfinsa, ya rugo gareshi, shima sai Koda suka hadu a tsakiya sai kowa ya soke kowa da takobi a ciki suka kame a tsaye rukunkume da juna kamar gumaka ba tare da sun fadi ba. A wannan lokaci su Boka Shamnas na kwance a kas suna haki da numfashi da kyar, sun kasa ci gaba da fada. Boka Salbatu ya dubi boka Shamnas ya budi baki da kyar ya ce, "Ya kai Shamnas, me za hana mu yiwa juna sulhu mu hakura da komai, domin mu tsira da rayuwar mu mu koma ga iyalanmu. Ka sani cewa kana da da karamin yaro guda daya, nima haka. Kuma bamu gama basu dukkanin Boka ilimin mu na tsafi ba." Shamnas ya bushe da dariya ya ce, "Kwarai kuwa, maganar ka gaskiya ce. To amma ka sani cewa bakin alkalami ya bushe, domin mun riga mun mutu nan da dakika biyar. Wadannan kuttun iska kuwa, suma nan da dakika biyar za su fashe iskar ciki ta watse. Ka sani cewa duk duniya in ban da ni da kai babu wand aya san yadda za'a sake tattaro wannan iska. Daga karshe ina Kiai shawartar ka d aka rungumi kaddara kada ka yi wani yunkuri na ceton rayuwar ka, domin babu lokacin yin hakan". Ai kuwa Shamnas biyun suka kama na gama ſadin hakan ne duk su yin amai, suna zubar da wata irin kumfa daga bakinsu. Cikin matukar Karfin hali Boka 30 Salbatu ya yi tsafi, wani gabjejen aljani babban hadiminsa mai suna Karbulu ya faso ta karkashin kasa ya Salbatu gabata gare shi. Cikin rawar murya da numfashi boka ya dubi Karbulu ya ce,"Yai sauri ya dauke shi ya kaishi gidansa da ke daular Dulkar." Cikin tsananin zafin nama Karbalu ya suri Salbatu ya aza shi a gadon bayansa ya tashi da shi sama. A dai- dai lokacin ne kuttunan iskar nan guda biyu suka yi bindiga, suka haifar da wata irin gagarumar wuta wadda ta narkar da komai na wajen, har da duwatsu kuwa. Ilatta fatalwoyin nan da ke kan tsibirin rayuwa sai da suka shige cikin karkashin kasa suka buya, domin inda sun tsaya kamshin iskar kawai zai iya hallakasu. Sai da ya rage saura dakika goma aljani Karbatu ya iso gidan boka Salbatu, sai rai ya yi halinsa, wato Salbatu ya mutu akan aljani Karbalu. Sai dai kafin ya mutu ya umarci Karbalu da ya kaiwa mutanen gari labarin abin da ya faru a can bakin kogin tsibirin rayuwa. Kuma ya umarce shi da ya binne gawarsa a cikin gidansa, domin za ta yi amfani nan gaba ga dan sa Arufa. Lokacin da aljani Karbalu ya sauke gawar boka Salbatu a tsakiyar gidansa, Arufa na zaune a tsakar gida yana wasa shi kadai. A lokacin bai fi shekara biyar ba. Koda ya ga aljani Karbalu ya sauke Salbatu, kuma jikin Salbatu a sandare ya ke baya motsi, sai ya kwala ihu. Nan take mahaifiyarsa Hazila ta rugo daga cikin daki a firgice. Koda tayi arba da gawar mijinta sai ta kwala ihu, la isa kan gawar ta tsugunna ta ci gaba da

Chapter 2 of 3