Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
da bakin naci tamkar talauci. 19 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini Bayan Hasilatul Kurbas ta shafe sa'a uku tana gudu bisa dokinta a cikin wannan dare sai ta iso daf dainda take iya hango wannan tsibiri, inda kurkukun Ukubatul dukkan yake daga can nesa kai kace dan mitsitsin dutsene aka azashi bisa tsibirin, wannan wuri inda Hasilatul Kurbas ta iso dajine fatal mai dauke da wadansu irin manya-manyan bishiyoi. Ba tare da bata wnai lokacin ba Hasilatul Kurbas ta sauko daga kan dokinta ta daureshi a jikin wata bishiya sannan ta fara nazarin dajin, koda ta dubi wata makekeyar bishiya sai ta daka tsalle sama ta doketa da kafa daya, abinda da basadaukiya, wadda tayi gadon sadaukantaka take bishiyar ta fadi ta tsuguna sannan ta fiddo wani zabgegeb gatarinta ta kama sassaka bishiyar. Har sai da gari yawe rana ta kwalle tana wannan aiki sanna ta hattama kera kwale-kwalen nan. Bayan ta kimtsa cikinta sannan ta bude jakarta ta fiddo abin kalaci ta kimtsa cikinta sannan ta haye kan wata doguwar bishiya ta kama aikin rago domin ta rama bashin barcinta na daren jiya, amma kafin ta hau kan bishiyar sai da ta kwance dokinta domin ya sami damar tafiya kiwo don ya ciyar da kansa. Sa'adda Hasilatul Kurbas ta sami kimanin sa'o'i hudu tana barci ne wasu dakaru masu tsaron kurkukun Ukubatul Dukkan sun kan kimanin su 20 1 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini dari suka shigo kwalc-kwale guda hamsin suka haye wannan kogi suka iso wannan daji inda Hasilatul Kurbas taya da zango. Dama a ka'ida kullum da safc sai sun zo wannan wuri don a tabbatar da tsaro a nahiyar saboda kada a kawo farmakin sumame. Ai kuwa wadan nan dakaru na zuwa sukayi arba da kwale kwalen nan wanda Hasilatul Kurbas ta kera, koda ganinsa sai suka fara tafiyar sanda da lebe labe kuma suka rarrabu don sun tabbatar da cewa akwai wadansu bakin dake a dajin masu shirin zuwa can kurkukun. Sai da wadan nan dakaru suka shafe kusan rabin sa'a a cikin dajin suna dubc-dube amma basu ga kowa ba face dokin Hasilatul Kurbas wanda ya je bakin wata korama ya kafa bakinsa yana shan ruwa. Lokacin guda dakarun su duka suka yi wa dokin kawanya suka zusa idanu kawai, shugaban dakarun wani barde da ake kira Uzaima ya dubesu gaba daya yace lallai muna da bako a cikin dajin nan kuma tabbas shine mai wannan doki kuma shine ya sassaka wancan jirgin ruwa. Abin da za muyi kawai mu kashc wannan doki tunda ba muga mai shi ba in yaso muci gaba da neman mamallakinsa, koda gama fadin hakan sai Uzaima ya dubi wani barde cikin in kiya. Barden ya zare mashinsa ya ja da baya sannan ya saita dokin Hasilatul Kurbas da mashin, koda ya 21 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini tabe hannunsa da nufin ya cilla mashin izuwa ga dokin kawai sai aka ga kibiya ta zo ta nutse a cikin makogwaronsa, take barden ya saki mashin dake hannunsa suka sulale kasa tareshi da mashin cikin firgici su duka dakarun suka waigo baya suna duban inda kibiyar ta fito, kawai sai sukayi arba da jaruma Hasilatul Kurbas ta durfafosu cikin tafiyar takama tana ruke da sharbebiyar takobinta, nan fa suka fara yi mata lugudan kibiyoyi, kawai sai tasa takobinta ta dunga kakkabe kibiyoyin cikin zafin nama ko daya bata samu damar shiga jikinta ba. Al'amarin da ya firgita dakarun kenan suka tabbatar da cewa lallai sun gamu da gamowa amma saboda sun kasance marasa tsoro sai suka ci gaba da cillo mata masu. Nan ma tayi ta kadesu da takobinta suna kakkacyewa da zubewa kasa. Ya yinda suka ga tya kusa cimmasu sai duk suka zare takubbansu suka yi ca akanta da niyar yi mata rubdugu. Wogogo, nan fa ta shiga ragargazarsu, sai dai kaga kafafu da hannaye suna tsinkewa daga cikin gangar jikin bil adama, kawuna kuwa suka rinka shawagi a sararin sama tamkar yara na wasan tamola, cikin kankanin lokaci jaruma Hasilatul Kurbas ta kashesu gaba daya ya rage saura shugaba Uzaima- shi kadai a tsayc a gabanta jikinsa na kyarma shi bai gudu ba kuma bai tunkareta ba sai kallan kallo suke kawai, duk jikinta ya baci da jinin maza kuma ko kwarzane 22 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini daya ba'ayi maya ba. Cikin murya mai. rawa Uzaima ya dubi Hasilatul Kurbas ya ce "Ya kai wannan gawurtaccen sadauki wanene kai? kuma menene manufarka na son zuwa Ukubatul Dukkan?" Koda jin wannan tambaya sai Hasilatul Kurbas ta mai da takobinta cikin kufe sannan ta cire hular karfen dake kanta Uzaima yai arba da fuskarta. Al'amarin da ya matukar razanashi kenan, bai san sa'adda ya tsuguna kasa ba yana tuba da neman afuwa. Hasilatul Kurbas ta daka masa tsawa ta ce "Ya kai Uzaima na sanka tun kana matsayin sauriyin bawa a gidanmu, ina so ka koma Ukubatul Dukkan ka sanar da Babban shugabanku sadauki Muhukur Azbalu cewa gani nan tafe don fitar dfa mijina yarioma Himal, ko dai ku bani shi cikin ruwan sanyi ko kuma takobina tashi jininku gaba daya, ka gaya masa cewa ba zan iso ba sai gobe da hantsi domin ku sami damar yin. duk irin shirin da kuke son kuyi, maza kaje ka isar da wannan sakо, kuma ka gaya masa cewa ko tsuntsune na gani zai giffa ta wannan dajin da nufin zuwa cikin birnin Babila sai na mai dashi gawa." Koda gama fadin haka sai Uzaima ya mike zumbur ya juya da gudu har ya isa bakin kogi inda jiragensu suke, nan da nan ya shiga kwalo-kwalc 23 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini guda ya nufi tsibirin da kurkukun Ukubatul Dukkan yake. Ita kuwa Hasilatul Kurbas sai ta sake komawa kan bishiyar nan da take barci tasake kwanciya don ta Karasa barcinta ashc dama tun sa'adda dakaru suka shigo dajin wani tsuntsu ta tasheta sakamakon digomata kashinsa a kofar hancinta. Ai kuwa tana farkawarne taji motsin tafiyar laben dakarun ta farga dasu, wannan shine abin da ya faru tsakanin jaruma Hasilatul Kurbas da dakaru bayanta baro cikin cikin birnin Babila don kubutar da mijinta daga kurkukun Ukubatul Dukkaa. A can tsibirin Ukubatul Dukkan kuwa tunda aka shigar da yarima Himal cikin wani daki mai duhu bai sake ganin koda tafin hannun saba har sai da ya kwana ya yinnni, kuma ko ruwa ba'a bashi ba bare ayi maganar abinci, koda Himal y tuna cewa shifa dan sarkine amma kuma gashi anyi masa irin wannan wulakanci sai takaici ya kamashi gami da tsananin bakin ciki wanda ya haddasa fitowar kwalla a cikin idanunsa. Yana cikin wannan tunani ne shugaban kurkukun Hukunul Azbalu tare da wasu barade biye dashi şuka zo kofar dakin ruke da fitila a hannu da kuma wata tsohuwar tasa. Koda Himal ya ji motsin tafioyarsu sai ya yunkura ya mike tsaye, da zuwa suka tsaya a gaban kofar dakin wacce ta kasance ta sandunan karafa suna iya shima haka. Bayan sun dallare fuskarsa da ganinsa 24 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini hasken fitila sai Muhukul Azbalu ya bushe da mahaukaciyar dariya sannan ya ce "Ya kai Himal shin zaka iya tunowa da wannan fuska tawa?" Himal ya dubi Muhukul Azbalu da kyau kawai sai ya gyada kai cikin alamun karayar zuci. Muhukul Azbalu ya sake bushewa da dariya ya cc "A she dai zaka gane ni duk da cewar yau shckara goma sha biyar kenan rabon da muga juna, ni ne dai wannan wanda ka taba yiwa dukan kawo wuka sa'adda na yiwa wata yarinya fyde a bayan gari, in ba don sirikinka sadauki Kurbas ya kawo mini dauki ba a wannan lokaci da tuni ka sheka dani barzahu, yau fa gaka a hannuna ya kai yarima, daga yanzu na zama sarkinka ka zama bawana, na rantse da darajar gemun ubana shekaru uku nan da zakayi anan sai na gana maka azaba irin wacce ba'a taba yiwa wani ba a gidan nan." Koda gama fadin hakan sai Muhukul Azbalu ya karbi wannan tsohowar tasa daga hannun wani badakare ya mikawa Hamil ya ce "Wannan shine daddadan abincinmu anan gidan wanda yafi kowanne dadi, a matsayinka na dan sarki naga ya dace mu fara yi maka marhaban da shi. Nasan kana jin yunwa sai ka hanzarta cika cikinka don kada cutar yunwa tayi maka lahani." Yayinda Himal ya karbi tasar ya duba abin dake ciki sai yaga ashewasu irin kananan tsutsotsine 25 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini a ciki har suna wani irin mugunyar doyi, cikin fushi Himal ya watsowa Muhukul Azbalu tsutsotsin a fuskarsa ya ce "Ku barni na mutu da yunwa ba zanci abin cin ku ba." Faruwar hakan ce ta fusata Hukumul Azbalu, nan take yasa aka bude kofar dakin ya shiga ya rufe Himal da duka da wani shirgegen kulki har sai da ya kaishi kas. Bai gushe ba yana dukansa sai da yaga ya suma sannan ya kyaleshi. Tabbas in ba don cewa hannayen Himal da kafafunsa a daure suke ba cikin sarkoki da hakan bata faru ba. Bayan Hukumul Azbalu ya ga cewar Himal ya suma sai yasa aka ciccibeshi aka fito dashi waje izuwa tsakiyar wani babban fil a harabar kurkukun aka sake bankareshi ajikin wani katako mai gwafa biyu aka daureshi tamau da wasu manyan sarkokin karfen sanna aka kwara masa ruwa ya farfado. Bude idanunsa ke da wuya ya yi arba da Hukumul Azbalu zaune a gabansa bisa wata kujera an hura wuta yana gasa wadansu tsitakoki guda biyu acikin wutar har sunyi jajawur. Hukumul Azbalu ya zaro tsitakokin daga cikin wutar ya nufo Himal gadan gadan yana murmushin mugunta da nufin ya gakasu a jikinsa, al'amarin. da ya duguzuma hankalin yarima Himal kenan don yasan cewa in dai ya caka masa tsitakokin ba karamin lahani zai yi masa ba. Sai da ya rage saura taku biyu ya iso gabansa kawai 26 Taskar Tsafi Abdul'áziz Sani M/Gini sai yaji an kira sunansa a baya, cikin fushi Hukumul Azbalu ya waigo. Take ya yi arba da Uzaima durkushe bisa guiwoyinsa yana faman haki. Hukumul Azbalu ya yarda tsitakokin dake hannunsa ya rugo wajen Uzaima yana mai tambayarsa cikin firgici, ina abokan nan aikinka? me ya faru gareku? Nan take Uzaima ya kwashe labarin gamonsu da Hasjlatul Kurbas ya zaiyane har da sakon da ta bashi cewar gatanan tafe gobe da hantsi don karbar mijinta. Ko dajin wannan batu sai yarima Himal ya bushe da dariyar farin ciki shi kuwa Hukumul Azbalu sai hankalinsa ya duguzuma ya rasa abin da zai yi. Nan take yasa aka dauke Himal aka kaishi can cikin wani daki dake karkashin kasa aka kulle sannan ya tara dukkanin dakarun gidan aka fara shawarar yadda za'a bullowa wannan gagarumar basadaukiya mai zuwa gobe. A can cikin birnin Babila kuwa sarki Asmaru na zaune bisa karagar mulki ana tsakiyar fadanci sai. ga wani shahonsa na tsafi ya dira a gabansa. Shahon ya yi wani irin kuka mai ta da hankali, sannan ya bude fukafukanshi ya tashi sama, ya fice daga cikin fadar. Ko da faruwar hakan sai sarki Amsaru ya mike zumbur ya nufi cikin gida da sauri-sauri, gudu-gudu. Al'amarin da ya razana sauran fadawansa kenan da sauran mutanen gari, domin bisa al'ada duk sa'adda wannan shaho ya zo ya yi 27 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini irin wannan kuka tabbas wani mugun abu ne zai faru. Luhura mahaifiyar yarima Himal na zaune a harabar gidan sarautar kuyangi sun kewaycta, ana yị mata hidima, kawai sai ta ga sarki ya zo ya wuce da sauri cikin tsananin damuwa. Ai kuwa sai ta mike zumbir ta bishi a guje, don ta taushe shi kamar yadda ta saba, a duk lokacin da taga ransa ya baci. Sarki Asmaru dai bai dangane da ko'ina ba, sai cikin turakarsa. Da zuwa ya bude wata karamar akwatu ya dauko, madubinsa na tsafi. A daidai lokacin ne Luhura ta iso daf da shi ta tsaya a bayansa. Asmaru ya shafi madubin tsafin da tafin hannunsa, take ya ga duk abin da ya faru tsakanin Hasilatul Kurbas da dakarun nan dari, wato. su Uzaima, sannan ya ga yadda hankalin su Hukumul Azbalu ya dungunzuma, a can kurkukun Ukubatu Dukkan. Nan take zuciyar sarki Asmaru ta kama tafarfasa, ya jiyo a fusace ya dubi Luhura ya ce, "Tabbas wannan karon sai na kashe dan nan naki." Koda jin haka sai Luhura ta fashe da kuka, sannan ta durukusa bisa gwiwuyinta, ta kama kafar sarki Asmaru tana mai rokonsa ta ce, "Ya kai sarkin sarakai ka tuna cewa ni ce matarka mafi soyuwa à ranka, fiye da dukkanin matanka. Na sani cewa na rokeka wannan alfarma sau biyu a baya kuma ka yi 28 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Ginİ mini. Ina mai dada rokonka a karo na uku da kada ka kashe mini dana, domin ina sonsa fiye da komai na rayuwata. Idan ka kashe shi tamkar ka yanke mini farin cikin duniya ne. Na sani cewa Himal ba jinin ka ba ne, domin da cikinsa na zo gidan nan, wazirinka mijina na da wanda ka kashe, shi ne mahaifinsa. Ka sani cewa kai ne ka umarce ni da na 6oye wannan sirri ga kowa, kuma na bi umarninka. Ina son na ci albarkacin bin wannan umarnin naka ka janyc hukuncin kisa akan yarima Himal." Yayin da Luhura ta zo nan a jawabinta, saі jikin sarki Asmaru ya yi dan sanyi, amma har yanzu fuskarsa a murtuke takc, babu alamar tausayi ko imani. Cikin kunan rai ya cakumo kwalar rigar Luhura ya tasheta tsayc. Ya dube ta da kakkausar murya yа сс, "Na ji zan yi miki wannan alfarma, amma ita ce ta karshc, kuma duk da haka sai na yi wa dan ki azaba mai radadi, tare da matarsa Hasilatul Kurbas, sannan zan huce takaicin da nake ciki." Yana gama fadin hakan ne ya bangajс Lahura ta fadi kasa, sannan ya fice daga cikin turakar da sauri. Koda sarki Asmaru ya isa fada sai ya tura a kira masa sarkin yaki sadauki Kurbas. Cikin kankanin lokaci kuwa ya bayyana gabansa. Asmaru ya dubi Kurbas fuskarsa cike da yanayin fushi ya ce, "Sarkin yaki ka yi sani cewa 'yarka a 29 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini halin yanzu ta kusan isa kurkukun mu na Ukubatul Dukkan, domin kubutar da mijinta wato dan mu yarima Himal, har ma ta kashe mini dakaru casa'in da tara, masu tsaron kurkukun. Hakika wannan abu ya matukar kona mini rai, don haka na umarce ka da ka hanzarta ka je ka riske ta, kafin ta sami nasarar fito da shi kuma ka zo mini da ita nan a raye, domin na yi mata hukunci daidai da abin da ta aikata." Sa'adda sarki Asmaru ya zo nan a zancensa, sai hankalin sadauki Kurbas ya dungunzuma, ba dan komai ba sai don tsananinn kaunar da yake yi wa 'yarsa, Hasilatul Kurbas. Tabbas inda ya san za ta aikata wannan mummunan aiki da ya hanata. Yanzu ga shi da hannunsa zai je ya kamota a yi mata hukunci. Tabbas ya san cewa hukuncin bai zai wuce na azaba ba, da kuma dauri. Ba tare da nuna damuwa ba, cikin karfin hali sai sadauki Kurbas ya risina ya ce da sarki. "Ya shugabana hakika ina goyon bayanka bisa hakan, domin yarinya ta aikata babban laifi, lallai ta cancanci horo sai dai ya kamata ka ba ni taimako yadda zan risketa akan lokaci, kafin ta isa can tsiburin Ukubatul Dukkan." Koda sarki Asmaru uya ji wannan batu, sai ya tuntsure da dariya ya ce, "Kada ka damu ya sarkin yaki, za mu hadaka da daya daga cikin 30 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini dakarun mu, wanda zai kai ka a cikin yini daya." Nan take sarki Asmaru ya yi nuni da hannunsa a cikin dan yatsansa ta tsaga kasa. Wani murgujejen aljani mai mummunar siffa ya fito ta cikin karkashin kasar ya risina a gaban sarki ya kwashi gaisuwa, a lokacin da kasar ta koma ta hade tamkar ba ta taba tsagewa ba. Sarki Asmaru ya dubi aljanin mai siffar mikiya ya ce, "Ya kai Kaiduzil Azman ka yi sani cewa ban kira ka ba, don komai sai domin ka dauki sarkin yakina ka kai shi izuwa jejin tsibirin Ukubatul Dukkan, domin ya kamo 'yarsa, jaruma Hasilatul Kurbas, ku zo mini da ita nan a cikin abin da bai wuce kwana daya ba." Aljani Kalduzil Azman ya yi murmushi ya ce, 'An gama ya shugabana tabbas, shan ruwa ya fi wannan aiki wahala a gareni." Koda jin haka sai sarki Asmaru ya dubi sadauki Kurbas, shi kuma sai ya daka tsalle ya dane bayan Kalduzul Azman. Ba tare da bata lokaci ba aljani Kalduzil Azman, ya bude fukafukinsa ya btashi sama, cikin 'yan dakiku kadan ya kule a cikin sararin samaniya. t Wannan shi ne abin da ya faru tsakanin sarki Asmaru da sarkin yaki sadauki Kurbas, a can cikin birnin Babila. Al'amarin jaruma Hasilatul Kurbas kuwa tun bayan rabuwarta da Uzaima sai ta fara tunani, mai 31 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini zurfi inda ta gano kuskurenta na shaidawa Uzaima lokacin da za ta iso tsibirin Ukubatul Dukkan. Tabbas ta san cewa za su iya daukar kyakkyawan mataki, wata kila ma su dana mata wani mugun tarkon da za ta kasa hayewa duk da cewa ta yarda da jarumatakarta. Koda Hasibatul Kurbas ta zo nan a tunaninta sai ta sauya shawara. Nan take ta mike tsayc ta kwashi duk makaman ta na yaki, ta daura a jikinta, sannan ta gyara damararta. Kawai sai ta je ta ja kwalekwalenta izuwa cikin kogin nan ta shiga ciki ta kama tafiya a cikin kogin ta nufi tsibirin Ukubatul Dukkan kai tsaye ba tare da shakkar komai ba. A can tsibirin Ukubatul Dukkan kuwa, su Hukumul Azbalu na ta shirye-shiryen makaman yaki, da kuma dana tərkuna iri-iri da raba mayaka rukuni-rukuni a kowanne sashi, na katangun kurkukun. Kuma gaba daya kofofin gidan da tagoginsa sai da aka rufe su ruf. Babu wata kafa wadda ko sauro zai iya shiga cikin gidan kurkukun. Ba zato, ba tsammani sai kawai aka hango kwalekwalen jaruma Hasilatul Kurbas ya ci rabin tafiya, a cikin kogin wato saura bai fi tafiyar rabin sa'a ba, ta iso tsibirin. Nan fa hankalin hukumul Azbalu ya dungunzuma, kawai sai ya raba dakarunsa kaso biyu, ya tura kaso guda cikin kwalekwale da umarnin su tari Hasilatul Kubas su 32 Taskur Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini kashc ta ta kowannc hali, lallai kar so barta ta iso tsibirin. Tun daea nesa Hasibatul Kurbas ta hango kwalckwale kimanin guda Cyu sut adinaro ta. Ko da ta hango su sai ta yi murmushi, don ta san cewa ita aka kawowa farmaki. Hasilatul Kurbas ta kara tuka kwalekwalenta da sauri tana jan marar da hanzari, har tana jin kamar ta yi fiffike ta riski wadannan abokan gaba. Suma dakarun sai suka kara azama don su riske ta, suna kwarara uban ihu mai tabbatar da cewa ana daf da fara azababben yaki. Ai kuwa nan da nan aka yi mugun gamo. Wohoho! Hakika mai karfi sai Allah ya isa. Nan fa Hasilatul Kurbas ta nuna tsagwaron jarumtaka, bajinta da kwarcwa, domin sai da ta zamo kəmar tsuntsuwa mai tashi sama. Sai dai ka ga ta daka tsalle sama ta ci kasuwar kawunann dakarun. Duk kwalelen da ta dira a cikin dakiku uku take gamawa da dakarun ciki, duk da cewa wasu na kawo mata sara da suka. Kai wasu ma har da ka tsalle suke su duro kanta, amma sai dai ka ga ta tarwatsasu tamkar tana faskara itace. Nan da nan jini ya dinga malala akan koginb yana gudu, kai da bala'i ya yi bala'i sai Hasilatul Kurbus ta ga cewar jikin dakarunma ya yi mata kadan don haka har jiragen na suma ta hada ta dinga ragargazarsu sai da ta yi filla-filla da jiragen 33 Tuskur Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini da kuma sassan jikin dakarun. Nan fa saman ruwan ya cika da kananan sassan jiki marasa nauyi kamar irin su kunnuwa, idanuwa da sauransu. Amma kamar kawuna, kafafuwa da hannuwa kuwa nutsewa suka yi a karkashin kogin, cikin abin da bai wuce rabin sa'a ba komai ya bajc akan kogin babu komai face jaruma Hasilatul Kurbas da kwalc-kwalenta kacal. A daidai wannan lokaci ne aljani Kalduzil Azman ya sauko kasa a can dajin nan na baya inda Hasilatul Kurbas ta yada zango har ta kera kwale- kwalcnta. Aljani Kalduzil Azman ya shaki kamshin bil adama ya dubi sadauki Kurbas ya ce "Tabbas jaruma Hasilatul Kurfas ta shigo dajin nan sai mu hanzarta nemanta." Sadauki Kurbas ya gyada kai ya ce "Gaskiya ne nima na ji kamshin wani turare-nata wanda ni ne na ba ta shi kuma duk duniya babu mai irinsa face ni." Yana gama fadin baka ne idanunsa suka ciko ds kwalla, al'amarin da ya baiwa aljani Kalduzi) Azman mamaki kenan, ya so ya tambayi Kurbas dalilin zubar da hawayen amma da yake babu lokaci sai ya yi shiru bai ce komai ba. Nan dai suka bazama a cikin dajin suna neman Hasilatul Kurbas. A can tsaunin Ukubatul Dukkan kuwa duk abin da ya faru a cikin kogin nan tsakanin jaruma Hasilatul Kurbas da rabin dakarun nan, Hukumul 34 Taskar Tsaji Abdul’aziz Sani M/Gini Azbalu ya gani a cikin abin hangen nesa don haka sai ya kwarara uban ihu ya zare takobinsa, suma ragowar dakarun nasa sai suka yi yadda ya yi suka yi cirko-cirko suna sauraren isowar Hasilatul Kurbas. Shi kuwa Yarima Himal dake can cikin dakin karkashin kasa a kulle koda ya jiyo ihun dakarun gidan sai ya cika da farin ciki don ya san cewa matarsa ce ta iso tabbas lokacin fitarsa daga cikin wannan kurkuku ya zo. Ai kuwa bai dade ba da jin wannan ihu na farko sai ya ji na biyu wanda ya fi na farko karfi, kai har ma wani irin rugugi ya rinka ji wanda ya haddasa girgizar gidan kurkuku gaba daya. Ashe kuwa a wannan lokaci tuni Hasilatul Kurbas ta iso har ta afkawa dakarun gidan kan mai uwa da wabi. Duk tarkunan da aka kafa mata sai suka zamo a banza tamkar dama ta san dasu domin kafin ta je kansu ma ta lalatasu. Nan fa ta bude kasuwar daukar rayuka, duk inda ta sa gabanta sai dai ka ga maza na zubewa kasa kamar tana sassabe a gona. Kuma duk wanda ya zo gabanta ta ke yake zama gawa. Hukumul Azbalu nc kadai yakc iya dan kokari shima kuma ya ki yarda ya tsaya su kafsa sosai da ya sha wuya sai ya gudu, sannan ya sakc sumamowa ya dawo. Koda ganin yadda Hukumul 35 از Taskar Trafi Abdul'aziz Sani M/ini Azbalu ke yi sai Hasilatul Kurbas ta fusata ta kara himma wajen kashe dakarun don ta karar dasu da wuri. Ai kuwa ana samun sa'a guda sai ta gama da kaso biyu cikin uku al'amarin da ya firgita dakarun kenan suka rinka gudu suna neman табоya. Shi kuwa Hukumul Azbalu sai ya fusata ya cire dukkan tsoro ya tareta gaba da gaba suka fara kafsawa, hakika Hukumul Azabatul ya yi matukar kokari, domin yana fadan ne iyakar karfinsa, da kwarewarsa don ceton ransa da cika umarnin sarki. Sai da suka bata dan lokaci bai samu nasarar yi mata komai ba, ita ma haka. Nan take zuciyar Hasilatul Kurbas ta harzuko ta sauya salon fada, inda ta yi jifa da takobinta ta rugo kan Hukumul Azbalu. Koda ya ga haka sai murna ta kama shi don yana zaton tabbas, zai samu nasara akan ta, tun da babu makami a hannunta. Koda ta iso daf da shi, sai ya kawo mata wawan sara, cikin zafin nama ta goce, takobin ta bugi iska. Kafin ya yi wani yunkuri ta yi masa barin makauniya a fuska ya ga taurarin mutuwa. Kawai sai ta kama wuyansa ta murde da karfin tsiya ta yi jifa da gawarsa. Nan take ta sake ja da baya ta ruga inda kofar kurkukun take ta dokita, da kafa daya. Saboda karfin naushin kafar tata sai da kofar ta jijjige daga cikin gini, ta fadi kasa rikica. Hasilatu ta kunna kai cikin kurkukun ta dunga balle kofofin 36 Tuskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini dakunan tana fito da fursunoni, tana kwalawa Himal kira, amma shiru ba ta ji ya amsa ba. Al'amarin da ya dugunzuma hankalinta kenan ta fara tunanin ko an kashe shi ne, don haka sai ta fara kuka. Su kuwa fursunonin nan sai suka kama murna, suka yi ta guje-guje suna neman kwalckwalen da za su shiga su fita daga wannan tsibiri. Hasilatul Kurbas ta ci gaba da kuka tana kwalawa Himal kira, tana kara kutsawa cikin gidan. Ba zato, ba tsammani sai ta ji muryar Himal yana amsa kiran. Nan fa murna ta kama ta, ta yi ta bin sautin muryar har ta gano cewa a cikin gidan kasa yake. Nan take ta ga wata kofa mai matattakala izuwa kasa. Cikin hanzari ta ruga ciki har ta iso dakin da Himal yake ciki. Da isarta ta bake kofar ta shige ciki ta ciccißo Himal ta goyo shi a bayanta ta fito da shi har waje, sanna suka rungume juna suna kukan farin ciki. Har a lokacin hannayen Himal da Kafafunsa a daddaure suke da sarkoki. Suna manne da juna cikin tsananin farin cikin ne, kawai suka ji wata irin iska mai karfi a samansu cikin razani suka daga kawunansu sama, suka yi arba da su. Ba wani ba ne face sadauki Kurbas, bisa aljani Kalduzil Azman. Kalduzil Azman ya sauko kasa-kasa daidai tsawon su Hasilatul Kurbas, aka fara katlan-kallo tsakanin sadauki Kurbas da su Himal. Cikin 37 Taskar Tsafi Ahdul'aziz Sani M/Gini tsananin fuskata Kurbas ya dubi Hasilat ya ce, "Ya ke 'yata don me za ki aikata wannan danyen hukuncin? To ki sani ccwa yanbzu sarki ya aiko ni na tafi da ke garc shi, kuma ba makawa sai na je da kc." Ko da ya zo nan a jawabinsa, sai hawaye ya subuto masa. Ita ma Hasilat sai idanunta suka ciko da kwalla, ta ce, "Ya kai Abbana ka yi sani cewa wajibi ne a gareni na ceci rayuwar mijina, kuma kai ma wajibi ne a gareka ka cika umarnin sarkinka, domin idan ka ki hallaka ka zai yi. Abin da nake so da kai shi ne kowa dabararsa ta kwace shi. Ni kam daga yau na zama 'yar tawaye ga sarki Asmaru kai ma ina shawartarka da ka yi masa tawayen....." Kafin Hasilatul Kurbas ta gama rufe bakinta, tuni Kurbas ya kawo mata wawan naushi a fuska. In ba don ta sunkuya ba, cikin zafin nama da tuni ta sume. Nan fa suka fara azababben fada, suka wanzu suna kai wa juna naushi kafa da hannu. Hakika duk wanda bai ga wannan fadan ba, bai more

Chapter 2 of 3