dagudu wata yarinya wada bazafi 14year tafito daga ruga tana dariya innaji ce ta nifota ruƙe da ɗan kwali "dannijo kitsayaa kisa nace" tafaɗa cikin hausarta ta fualani murmushi yarinya tayi tana kallon innaji kafin kuma ta tawo da gudu ta rungumeta ɗaura mata ɗan kwalin innaji tayi tana murmushi "yauwa yanzu sai ki maza ki ɗauka kafin su hansai su zo suna jiranki ko?" ɗaga kai tayi tana nufar in da ƙwaryar take daura mata innaji tayi ta kama janya ta fita tana yan waƙe waƙen su na fulani a hanya ta haɗu da su hansai suka jera suna tafiya, suna isa cikin kasuwar yauma Kamar kullum tana isa taga wannan mutumin a dai-dai in da take zama hansai ce ta taɓota "ke dannijo yo aradu yauma wance balaraban sai da ya tsaya a wajanki" ita dai bata bata amsa ba dan gaba ɗaya hankalinta nakan mutumin da murmushi ya karaso yana sauke mata ƙwarya dake kanta farine tass mai matuƙar kyau gashinsa ya kwanta lip ga girarsa mai matikar kyau da sheƙi mutumin dai ya haɗu sosai
nuna mata wajen yayi da hannu alamar ta zauna zama tayi kuma har lokacin bata fasa kallonsa ba yanan zaune har taga ma sai da fura da nono tashi suka yi zasu tafi da sauri ya karɓi kwaryar tata "muje na rakaki ko?" bata ce masa komai ba tai gaba abunta suna zuwa dai-dai mararaba da zasu shiga rugasu ta miƙa hannu dan ya bata ƙwaryar, murmushi yayi yana dubanta "karki hanani rakaki Please ki bari na ƙarasa ladana" "a'a ? "Kayiwa Allah kabani kayana Saboda kada Baffana ya ganka" bata gama rufe bakinta ba taga Baffa ya nufosu yana kora shanu da gudu ta karasa tana rungumesa shafa kanta Baffa yayi kafin ya ɗaga idanu ya kalli wannan mutumin da sauri ya ƙarasa yana gaidasa cikin fara'a Baffa ya masa yana tambayarsa lafiya ya biyo su dannijo? ...
"Da sauri hansai ta ce Baffa a radu kullum mukaje kasuwa sai ya je wajan dannijo" murmushi Baffa yayi yana kallonsa sunkuyar da kansa kasa yai "idan babu damuwa anjima kazo nan ina nemanka" Baffa ya faɗa "shikenan Baffa insha Allah zanzo nagode" sukai musa baha kama hannu dannijo Baffa yayi suka shiga cikin ruga
3 month later
Biki ake yi nagani na faɗa irin bikinsu na fulani sanye take cikin saƙi blue an tufke mata gashinta waje guda sai sarƙa da ke wuyan ta da abun hannu duk na shiri a hankali suke tafiya suna waƙoƙin Fulani Baffa ne ya dubi Mahir da yasha fararen kayansa masu matukar kyau hannusa ya kama ya haɗa dana dannijo "karike min ita amana Mahir duk da nasan bazaka taɓa cutar da ita ba kasani bata da kowa sai Allah sai kuma kai a yanzu ina roƙanka ka ruƙeta da hannu biyu" Baffa ya faɗa yana hawaye, da sauri Mahir ya rungume Baffa shima yana hawayen tabbas yayi Alƙawarin bazai taɓa bari wani abu ya taɓa dannijonsa ba da gudu ta karasa wajan innaji ta rungume ta wani irin kuka take mai tsanani tabbas tasan zata yi kewar iyayen ta a hankali innaji ta ɗagota murmushi ta sakar mata,"Ki daina kuka kin ji Aminatu na Allah yayi miki albarka ina rokanki kiyiwa mijinki biyaya" ɗaga mata kai tayi alamar tom kuma har lokacin bata bar kuka ba. kama hannunta tayi ta sata cikin motar da zasu tafi dan Baffa yace babu wani wanda zai bisu daga baya aje ganin gidan nata haka kuwa akayi su kaɗai suka kama hanya zuwa ayi nayin cikin garin abuja...
Rayuwa ta cigaba da tafiya Mahir sosai yake bawa matar sa kulawa wadda ke ɗauke da ciki karami. kallonsa tayi cikin shagwaɓɓa tace "Allah ni bana son cin abinci nan" murmushi yayi yana dubanta "me zakici toh"? tana jin haka ta dawo in da yake tana murmushi "ni dai mangoro nake so"Angama ranki yadaɗe gimbiya sarauta mata" murmushi tayi tana rungumesa tsam, kamar wani zai ƙwace mata shi.
6month later.
A hankali ya ke dubanta da wani irin yana yi shafa cikin dake jikinta yayi yana magana "haka Allah yatsara naso ace naga abun da zaki haifa Aminatu na basa kulawa fiye da tinani ashe hakan bazai faruba ki kulamin da ɗana ko yata Aminatu ina rokanki idan ansamu mace ki samata sunan mahaifiyata" hawaye ne kawai ke ambaliya akan fuskarta "Ka daina faɗan haka yaya Insha Allah zaka tashi zamu cigaba da rayuwa kasan bani da kowa sai Allah sai kai, sai kuma abun da zamu haifa" ta faɗa tana ƙara sautin kukanta murmushi ƙarfin hali yayi yana dubanta "Insha Allah Allah na tare daku a koda yaushe" wani irin tarine ya sarƙafesa tin yanayi a hankali har ya yi masa yawa saliti yake yi kafin wani lokaci kuma yayi shiru ihu tasaka tana jijiga gashi
Da guduta tafita tana kuka malam lima da fitowarsa kenan daga gidan ya ƙaraso yana tambayarta lafiya? kasa magana tayi sai nuna masa cikin gidan da take shiga yayi da sauri dan ganin mai ke faruwa innalilayi wainna ilayi rajiƙun shine kaɗai abun da yake ambata lokacin da ya taɓa Mahir tabbas Allah ya karɓi abunsa zani ya samu ya rufa masa kafin ya fita daga gidan dan samun kira mutane a suturtasa alokacin kuma dannijo ta daɗe da sumawa tabbas wannan itace sular gaddarasu wannan shine sular tarwatsa duk wani farin ciki na dannijo dama tun kwanaki da sukaje rugasu ake sanar musu tuni mahaifanta suka yi kaura daga ruga shin wananan wace kalar kaddara ce ina zata saka rayuwarta alokacin da suka dawo tayi kuka sosai da ƙyar Mahir ya lalasheta tayi shiru to shima gashi yanzu ya tafi ya barta tafiya kuma ta har abada..
Haka rayuwa ta cigaba da tafiya shekaru suka shuɗe kullum sai tayi wankau suke samun abun da zasu ci ita da yarta malam liman shine yasa Fatima makarnata wadda taci sunan kakarta suna kiranta Ayrah
Kuma har lokacin su kaɗai suke rayuwarsu tunda dama Mahir bai taba kaita wajan danginsa ba tin yana raye idan tamai maganr sai dan-danan ya kama hawaye hakan yasa ta daina ma masa maganar
kwanci tashi akace asarar mai rai yau fatima ta yi candy wanda yayi dai-dai da tana da 17years a duniya
[8/13, 4:06 PM] Masoyiya 🤗🔥: https://chat.whatsapp.com/BW8T7i1jpeZ5QpVVl4hxuZ
A WANI COMPANY
By
HAUWAU OMAR
CUTIE MEEYRAT
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATIONS
Fallow my account Arewabook
Arewabook@hauwauomar
Page 5,
A hankali ta muraɗa handle ɗin tashiga zaune ta samasa akan kujera office ɗin ƙarasawa tayi wajan tana sunkuyar da kanta kasa murmushi yayi yana dubanta "Fatima Zarah" ya faɗa yana murmushi ɗagowa tayi tana kallonsa "zauna mana" ya bata umarni zama tayi tana miƙa masa takarda dake hannunta
Karɓar takarda yayi yana dubawa murmushi yayi ya kalleta "Kema sa'a ce daughter tabbas Mdee ya karɓeki sosai tin da ake kawo ma'aikata ƙananu basu taɓa samun dama Kamar taki ba tabbas ke mai Sa'a ce" ya kara mai-maitawa yana murmushi "menene ya faru dad"? "Suhail ya baki aiki zaki zama mai kai masa coffee saboda matakin karatunki bai kai ki samun office ba sanan zaina baki salary 500th"
Zaro idanu tayi waje tana kallonsa "yanzu dad ni ce zanna ɗaukar salary har na 500th?" ta faɗa tana kallonsa
Sai da yamma liƙis kafin suka fito dan tafiya gida.
A hankali yake fitowa daga left ɗin haɗa idanu suka yi da Ayrah da za su shiga mota da sauri ta sunkuyar da kanta ƙasa murmushi gefan baki kawai yayi ya nufi mota security ne ya buɗe masa motar ya shiga da sauri suma suka shiga suka ja motar suna isa unguwar su ya sauke ta dai-dai ƙofar gidan, "Ki shirya tun wuri gobe daughter saboda Mdee bai yarda da let ba" "insha Allah zan shirya da wuri Nagode sosai Dad Allah ya saka da alkhairi Allah yasa kafi haka" "babu komai daughter ki gaidamin da Mamanki"ya faɗa yana jan motar ta na shiga ciki da gudu ta karasa cikin ɗakin ta rungume Mama murmushi tayi tana ɗagota "washh Allah ni karki karyani" turo baki tayi gaba "ni da bani da wani nauyi taya zan karyaki Mama" "waya gaya miki baki da nauyi" ai ni na sani" tafaɗa a shagwaɓɓe
"Mama albishirinki" "goro" Mama ta bata amsa "na samu aiki kuma Mdee ɗin ya ce zaina bani 500th" zaro idanu waje Mama tayi tana kallonta "nikam ban son wasa Ayrah" "wollah Mama ba wasa nake ba"
Yana shiga cikin katafaran ɗakin nasa kai tsaye ya nufi badroom dan watsa ruwa sai da ya ɗau tsawan lokaci kafin ya fito daure yake da farin towel wanda ya tsaya masa iya gwiwa sai ɗan ƙarami daya ke tsane gashinsa da shi nufar wajan mero yayi ya na shafa lotion ajikin sa, ya na gama waya ya nufi wata ƙofa yanasa hannusa ƙofar ta buɗe ya salam wani ƙayatatan gurine wan da aka kaya tashi da kaya yan uban su ɓarin ƙanan kaya ya nufa treecotar ya ɗako blue da teshat White mai aɗon blue a jiki.
A hankali ya fito zuwa bakin semonfull ɗin dake gidan zama yayi a ɗaya daga cikin kujerin yana shan isaka wayan shi dake aje agun ce ta fara ring da sauri ya daga yana duba mai kiransa Dad shine sunan da ya bayyana akan secreem ɗin wayar ɗagawa yayi da Salama ɗaya bangaran kuma ajiyar zuciya dad ya sauke "Suhail" ya ambata a hankali "na'am dad" "na yi kewarka sosai" "nima haka ina kewarka" "ina fata dai kana lafiya ko"? "lafiya qlau sai dai aiki da yamin yawa" "Allah sarki son Allah ya taimaka Allah ya bada sa'a" "Ameen dad" ya faɗa yana jingina ajikin kujera. sai da suka ɗauki tsawan lokaci suna waya kafin suyi salama, tashi yayi ya nufi ciki dan kwanciya saboda gobe yanada meeting da wasu baƙinsa da suka zo daga Uk.
Washegari tun wuri ta tashi tashirya dan tafiya Mama ce ta miƙa mata wani foodfulas murmushi tayi tana karɓa *Mama menene wannan kuma?" "abinci ne amma ban yarda ki buɗe ba sai kinje cen tin da kinga baki karya ba" "tom Mamana na tafi sai na dawo" ta faɗa tana fita daga gidan "Allah ya tsare hanya Allah ya karemin ke aduk inda kika shiga Fatima na" Ta na fita ta tadda alh hadi zaune cikin motar shiga tayi tana gaidasa amsawa yayi cikin sakin fuska kafin yaja motar su tafi su na isa ya ce taje office ɗin Mdee dan kai masa abun da yake bukata to tace tana nufar left a tsorace ta danna ganin ta buɗe yasa tayi murmushi ta mai Kyau wanda ya kara futo da ainayin kyanta shiga tayi, tana isa tafito ta nufi ƙofar nocking tayi ciki-ciki p.a ta bata umarnin shiga haɗa ido suka yi ta galla mata harara ita dai bata ce komai ba tayi gaba abunta dan ita duk irin wannan abun ba sabawa ta yi da suba zaune ta samashi ya ɗorw kansa akan kujera idanunsa alumshe Kamar mai jin bacci "good Morning sir" "morning" ya masa mata kuma har lokacin idanunsa a rufe suke zama tayi akan kujera tana ɗora filas dinta akan table ɗin "menene wannan?" shine abun da taji ya faɗa "abinci ne Mamana ta dafamin" "okay baki breakfast ba kenan"" eh" ta bashi masa a taƙaice "buɗe muci ko bazaki saminba" zaro idanu tayi tana kallonsa bata san sanda tace "ai abincin na talakawa ne ba irin naku bane" murmushi da bai shirya yinsa bane ya subuce masa tabbas ya yarda yarinya ce karama idan banda abunta dama abunci masu kuɗi da ban na talakawa daban
"Ki buɗe to naga ni zanga idan irin namu ne" a hankali ta saka zara-zaran yatsunta tana dubawa zubawa ya tsun hannu nata idanu yayi yana kallo washh Allah ya faɗa a hankali ita dai komai nata na dabane ita kuma jin yace wash Allah sai ta zata ko wani abunne ya faru sannu tace masa buɗewa wa tayi tana tura masa fisal ɗin wow lafiyayiyar jallof ɗin taliya ce wadda tasha kayan miya da cori sefun ya ɗauka ya kai abinci bakinsa wani irin daɗin abincine ya ke fuzgarsa yanaci yana lumshe idanu ita dai kallonsa kawai take sai da yaci ya ƙoshi kafin ya tura mata rogawar mazakici ya faɗa yana kafe ta da idanu a'a na ƙoshi kacinye kawai ko kina ƙyanƙyamina ne a'a ta faɗa da sauri tana jan filas din gabanta tsayawa yayi yaga yanda take tauna a hankali tabbas komai na yarinyar abun burgewa ne.
P.a ce tashigo cikin Office din suna haɗa ido da Ayarh ta harareta "sir lokacin gabatar da meeting ɗinka yayi" tafaɗa tana miƙe masa takarda tashi yayi ya nufi cikin wani ɗaki dake Office ɗin after 5m ya fito cikin wasu cuz ɗin farare ƙal baƙaramin kyau yayi ba ya haɗe gashinsa waje ɗaya kama hanya yayi zai fita "taso muje ki rakani ko" tashi tayi tabi bayansa har suka fito wani irin baƙin ciki da takaici shine ya rufe p.a wai shin me wannan yarinya take nufi daga zuwanta jiya Company gaba daya ta sauyawa Mdee tunani "Tabb wllh da sake ta faɗa tana huci ita ce wace zata rakasa meeting amma yaja wata kucakar yarinya ina wollah bazai yuwu ba dole ne tun wuri ta san abunda ya kamata tayi
Suna fita ya miƙa mata katardu dake hannusa left suka shiga ta kaisu ƙasa shiga mota yayi.Tsayawa tayi tana kallonsa dan ita bata san me zata yiba "shima shiga motar sai na koya miki ne" taji Muryarsa cikin dodon kunnanta da sauri ta zagaya ta shiga drive ne ya jasu zuwa wani ɓangare na Company tabbas wannan Company mai girmane tafaɗa a zuciyarta
Fitowa yayi suka nufi ciki suna isa ya nuna mata wata kujera nesa da su "Kije canki zauna" nufar wajan da ya nuna mata yayi shikuma yai gaba abinsa tun tana saran zai tawo su tafi har ta fidda rai gaba daya ta galabaita bacci takeji amma tarasa ta yadda zatayi baccin. kwantar da kanta tayi akan kujera cikin yan mutuna da basu wuce biyar ba bacci ya ɗauketa.
suna tashi daga meeting ɗin yayo hanyar wajan da take tun ɗazu hankalinsa na kan yarinya ya san tabbas ba ƙaramin gajiya tayi ba.
Yana zuwa ya sameta tana bacci tsayawa yayi yana kallon fusakarta sai yagama Kamar idan ta rufe fuskarta tafi kyau , rasa yadda zai tasheta yayi a hankali ya fara buga kujera da take kwance buɗe idanunta tayi tana kallonsa "tashi muje ko" miƙewa tayi cikin sauri bata yi tunanin ma tayi bacci ba
*Ayi haƙuri wollah ban samu damar typing da yawa ba bana jin daɗi kuma ga wayana ba chaji naso na muku page mai tsayi sosai*[8/13, 4:06 PM] Masoyiya 🤗🔥: https://chat.whatsapp.com/BW8T7i1jpeZ5QpVVl4hxuZ
# SQUAD 2024
A WANI COMPANY
BY
HAUWAU OMAR
CUTIE MEEYRAT
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATIONS
Fallow my account.
Arewabook@hauwauomar
Page 6.
Miƙewa tayi da sauri tana gyara zaman hijjab ɗinta. kama hanya yayi ya tafi bin shi tayi abaya zuwa wajan pearking lot ɗin shiga yayi cikin motar itama tashiga suka nufi cikin Company har sun kai yace ya juya su fita gaba ɗaya daga company haka kuwa akayi sai da sukayi tafiya mai nisa kafin ya ɗago kai ya kalleta "inane anguwarku?" ya faɗa a hankali "lokogoma dai-dai gidan lima" shiru yayi dan shi baima san inane hakan ba drive ya duba "kasan in da ta faɗa?" "eh na sani sir" "maza ka kaimu cen ɗin" sun yi tafiya mai nisa kafin su isa kasan cewar unguwar na da nisa da Company suna isa ta fito zata nufi gida "babu Salama kenan" ya faɗa a takaice murmushi tayi mai kyau "nagode sosai sir" shima murmushi ya maida mata drive ne ya ja motar suka yi gaba tana shiga ciki ta samu Mamanta a bakin murhu da gudu ta karasa ta na rungumeta ta baya murmushi Mama tayi tana juyota "yar gidan Mamanta har andawo" "eh Mama yau bama da Dad su habib muka dawo ba" "dawa kika dawo" "Mdee guri namu ne na raka sa wajan meeting shine da aka tashi ya kawoni gida" "okay mun gode sosai Allah ya saka masa da alkhairi amma dai ki dunga kula" "Insha Allah Mama"
Da da-dare suna zaune a ɗakin Ayrah ta ke bawa Mama labarin Company, "Wollah Mama baki ga Company ba babba nifa wallahi jiya da muka shiga sai naga kamar ba a Nigeria ba, kuma ma wai kinsa me?" girgiza mata kai Mama tayi alamar a'a "idan zaka hau sama tawani abu fa ka ke shiga sai yayi sama da kai" ta faɗi hakan tana dariya mai sauti ita dai Mama sai kallonta ta ke a duniya ta na ƙaunar farin cikin yar'tata matiƙa.
Kwance yake ya rufe idanunsa kamar mai bacci gaba ɗaya ya rasa mai yake masa daɗi juyi kawai yake akan bed ɗin nasa ganin ciwon na kara masa tsanani ya sa ya yi saurin tashi daga kwanciyar bude freeg yayi ya ɗako ruwa mai sanyi tare da tablet ya kora dan-danan kuma ya fara zufa kamar wanda yake acikin zafi tashi yayi ya hau kan bed ɗin cikin muntina da basu shige biyar ba bacci ɓarawo ya ɗaukesa niko nace asuba ta gari Mdee Suhail.
Washegari dawuri ya tashi ya shirya dan fita aiki sai da suka yi waya da dad ɗinsa kafin ya fita
Sanye ta ke cikin wata doguwar riga mai kyau Mama ce ta daure mata gashinta da rebom ɗan ƙaramin hijjab ta saka wanda bai fi iya rabin ta ba Masha Allah tayi matiƙar kyau kyawun da duk wani namiji ya ganta dole ne ya ruɗe sunbatar Mama tayi agoshi kafinta fice daga gidan tana fita taga habib a tsaye babu dad murmushi tayi suka gaisa "amma ya habib ina dad ya ke koshi ba zai je bane"yau" ta tambayesa "a'a Daddy zai tawo daga baya, yaje wani aiki ne legos so idan ya dawo yau zaizo shine ya ce na zo na kaiki" "Allah sarki Daddy" ta faɗa ta na murmushi buɗe motar tayi ta shiga shima shiga yayi ya ja suka tafi.
A hankali ta ke tafiya gaba ɗaya ta daburce sai wani irin tafiya ta ke ta marasa gaskiya, dai-dai bakin kofar ta zuba wani abu mai ƙauri kafin ta koma wajan zamanta tana sakin murmushi mugunta. Cikin tafiyarta da ta saba ta tawo dan shiga cikin office ɗin ko kallon p.a ba taiba. Da sauri ya miƙe ya nufo ƙofar yana buɗewa dai-dai zata taka abun yayi saurin dakatar da ita wani irin kallo ya watsawa p.a mai cike da tsantsar tsana da ƙyama sunkuyar da kanta tayi ƙasa "five minutes na baki ki goge abunda kika zuba agun nan sha-sha-sha kawai" ita dai Ayrah tsayawa tayi tana kallonsa dan bata san akan me yakewa p.a faɗa ba
Da sauri ta ta so ta ɗako mofa ta na nufo gun sai da ta goge tass kafin ya bawa Ayrah umarnin ta shiga p.a komawa ta yi wajan zamanta wani irin kuka ta fashe dashi mai tsima rai shikenan yarinya nan ta ɓata mata duk wani shiri da ta ke da shi akan Mdee ina wollah da sa ke mudum tana raye sai ta sa ka yarinyar kuka da idanunta bazata taɓa barin yarinyar ba aje zuwa "yarinya sai shegen kyau kamar yar aljannu" ta faɗa tana jan tsuka
Nuna mata wajan haɗa coffee ya yi da sauri ta karasa dan haɗa masa sai da tabi komai a hankali tana karantawa kafin ta gama a hankali ta ƙaraso gabansa ta aje masa "Thanks" taji ya ambata "sir ina so naje waje idan babu damuwa" "me zakiyi a wajen" babu komai" bai kara mata magana ba sai da ya shanye coffee ɗinsa tass dan ba ƙaramin daɗi ya mai ba telephone pole ɗin ya danna "ina son ganinki" shine abun da yace yana aje wayar kanta a ƙasa ta shigo cikin office ɗin ko kallonta baiba ya ce "ki kaita office ɗin ƙanan ma'aikata, idan kinje ki haɗani da ɗaya daga cikin su" "okay sir" tafaɗa ta na dubansa "ta so mu tafi ta cewa Ayrah" tashi tayi ta bi bayanta lumshe idanunsa ya yi a hankali ya na sakin ajiyar zuciya suna fita suka nufi wata hanya wadda zata sadasu da left ta bene hawa sukayi ya kaisu ƙasa shiga cikin wani office tayi binta Ayrah tayi suna shiga suhailat ta sakarwa Ayrah murmushi, karasawa p.a ɗin tayi wajanta ganin babu kowa sai ita kaɗai a office ɗin "dama Mdee ne ya ce na kawota nan sanann kuma na haɗaku a waya" "okay" suhailat ta ce tana murmushi kiransa p.a ta yi ya na dagawa ta miƙewa suhailat sai da suka yi magana sosai kafin ta kashe wayar ta na murmushi, kama hannu Ayrah ta yi ta na zaunar da ita akan ɗaya daga cikin kujerin "Zaki iya tafiya" ta bawa p.a umarni murmushi tayi wanda iya ka cinsa laɓɓanta tana fita daga office ɗin. "Ya sunanki?" suhailat ta tambaye ta "Fatima Mahir" "amma ana kirana Ayarh" "Wow nice name" "nikuma sunana suhailat ki daukeni tamkar ƙawarki kinji" murmushi tayi tana ɗaga kanta
Hira suke sosai gwanin sha'awa duk da Ayrah bata da yawan magana amma yau sai da suka yi hira sosai lokacin sallah ne yayi suka fita dan zuwa masallaci fitowarsa kenan daga office ɗinsa ya nufi masallaci dai-dai sun nufo hanyar kanta aƙasa take tafiya jinta bugi abu yasa da sauri ta ɗako tana kallonsa wani irin kallo ya watsa mana ke baki da hankali ya faɗa a zafafe hawaye ne ya fara zuba daga fuskarta ɗaga hannu yayi a zafafa zai mareta jin an ruƙe masa hannu ta baya yasa yayi saurin juyowa yana kallon wanda ya masa haka wani irin kallo ya watsa masa yana cije laɓensa sun kuyar da kansa ƙasa yayi kus-kure ɗaya zaka yi rayuwar ka shine kus kuran marin fusakarta da ace ka aikata haka tabbas da sai dai ka zauna babu hannu har karshen rayuwarka yar fa da hannusa ƙasa yayi ya na cigaba da tafiya da sauri Suhailat ta kama Ayrah suka cigaba da tafiya suna isar da Sallah suka kama hanya dawowa ciki suna isa cikin office ɗin nasu Ayrah tafashe da wani irin kuka mai cin rai menene abun kuka Ayrah ki yi haƙuri kuma ai kinga Mdee ya zo "ke mai Sa'a ce Ayrah"
Kirane ya shigo cikin photo ɗin dake wajan da sauri ta ƙarasa ta na ɗaga wayar "ki turomin ita" ya faɗa a hankali "okay sir" "tashi kije Mdee na kiranki Ayrah" "okay" ta ce ta miƙa tana barin office ɗin da salama ta shiga ciki ɗogowa yayi yana kallon idanunta wanda suka yi ja daga gani kasan tayi kuka zama tayi tana sunkuyar da kanta "Ayarh" taji ya ambati sunanta akaran farko ɗagowa tayi tana kallonsa ba tare da tayi magana ba "menene abun da ya haɗaki da shi?" turo baki tayi dan-danan kuma hawaye ya fara zarya "Ya salam" ya furta ya na dafe kansa "Please ki bar kuka bana son ji" cikn shagwaɓɓa ta ce to ba shine kawai dan mun taho da aunty Suhailat, ban sani ba na bigesa shine ya ke tamin faɗa kuma wollah babu abunda na masa" tsayawa yayi yana kallonta abun ba karamin burgesa yayi ba ganin yadda ta ke magana.
"Shikenan ki tashi kije ƙasa office ɗinsu Suhailat ɗin saboda zan yi magana da wasu anan kuma kin ga maza ne bai kamata ki zauna ba gyaɗa masa kai tayi ta miƙe tana tafiya"
ta na fita ta ga Daddy su Habib