Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 7
Gaje kamar daga sama ta zo wajensu, suka kalleta sama da kasa. Suka tabe baki, sannan Lante tace "Yau kuma kin ga daman fitowa ne? Ai mun yi alkawari ba za mu taba binki gida ba, dan mu tambaye ki ko mai ke hanaki shiga cikinmu ba. Daga mun tambaye ki tsakaninki da Lamido, ta hs kenan kike gudunmu. To kin dode ba ki daina shiga .nıru ba" Su Kandala suka ce "Ke ma kika NMANEADILA 22 saurareta, har ma kike mata bayani, sai kace in babu ita, za mu daina abinda muke yi ne." Gaje na tsaye tana jin su kawai, sai hawaye ya shiga gangaro mata a kumatu. Binto tace "Haba Gaje, daga magana, sai kuma ki ka yi mana kuka? To kiyi hakuri." Gaje tayi ajiyar zuciya tace "Ku ba ku san tashin hankalin dana fuskanta bane da irin bakin cikin da nake ciki ba." Suka ce "Ya zamu yi mu sani, tunda ba ki sanar da mu ba." Gaje tace "Wai Lamido duk garin nan, ya rasa wacce zai ce zai aura. Wai sai ni." Kandala tace "A'uzubillahi, Lamido ya zama mijin aurenki. Da kuwa kin yi asara babba." Binto tace "To yanzun Me gidanku suka ce? Gaje tace "Kin san Babana yaron Baban Lamido ne, dan haka shi goyan bayan abin yayi sosai. Kuma kun san Ummah bata da wani abun da ta isa tace akan duk hukuncin da Baba ya yanke. Komi rashin kyan abin, to amma duk da haka dai tana dan tabukawa, sai dai na san zai yi wuya ta ci galaba akan Baba. Ni dai yanzun kawai ku tayani Addu'a. Allah ya kawo sauki akan lamuran." Binto tace "Ai ko zamu tayaki Addu'a. To ke ma ki dage ki koyi rashin mutumci, ki shiga karanta ma Lamido, ba sansanci." Kandala tace "Ki gwada masa ba ki kaunar shi." Lante tace "Balle ma ya sa ran za ki aure shi." DA SANNU... 23 Sannu ahankali watan Ramadan ya kama.Azumin yayi nisa, dan har ya kai goma ga wata ma. Mata da Maza kowa yana shirye-shiryen zuwa yin tashe, to su ma su Gaje ita da kawayenta shirin tashen suka yi. Ga sunan su shiga wannan gida, su fita wannan gida. In sun ga jama'a zaune, su yi musu tashe. Sun samu kyauttukan hatsi, babu laifi, abin ka ga kauye. Ba sai nayi dogon sharhi ba. Su Gaje ba su samu kudi wajen tashen ba. Dan haka. Suka zauna, suka yi tunanin ina za su je su samo kyautar kudi. Da duk suka gama tunanin nasu, sai suka rasa inda zasu su samo kyautar kudi. Sai suka yanke shawarar su ketara su tsallaka su je gidan Hakimi su yi masa tashe, kila ya basu kudi, tunda mutumin kirki ne. To amma kuma ba zuwa gidan Hakimin ba, kowa yana tsoru. Nan suka dunga muhawara, ko waye zai ba da tashen in sun shiga gidan Hakimin? Tirkashi! Daman haka yake. Wani lokaci mai hakuri kan yi saurin kawo masa raini ba. Duk kowa ya ki yarda ya ba da tashe a gidan Hakimi. Sai suka sanya Gaje a gaba da nufin cewa ita zata bada tashe a gidan Hakimi. Sai kawai suka dungu ma, suka mika zuwa gidan Hakimi. Dan ba karamin tazara ke tsakanin gidan Hakimin da cikin unguwarsu ba. Suna isa bakin get. Masu gadi suka fara tambayarsu abinda ya kawosu? MAMAN FADILA 24 Cikin fargaba suka ce "Mun zo yin tashe ne? Da yake Hakimi daman ya fada ma masu gadi, duk dan tashen da ya zo, su bar shi ya shiga, musamman Hakimi da iyalan shi suka yi shinfada ta alfarma, suka baje tsakar gida suna sauraran masu zuwa yin tashe. Ga akwati na mussamman gefen Hakimi. Kudi ne cike cikinsa. Su yake rabawa duk wanda suka shigo. Koda su Binto suka shiga, suka tsaya daga zaure. Sai Gaje tayi shiru. Kandala tace "Ke fa muke saurara. Kuma ba ma son ki mana wanda aka saba ji, sabo za ki yi mana." Gaje tace "To ai ni ban iya ba." Kandala tace "Dole ko ki iya." Gaje tace "To komi nace, ku ce tautaushe." Gaje ta fara. "Ina zamu kwana? Suka ce "Tautaushe! "Ina mazanku? "Tautaushe! "Ina matanku? "Tautaushe! "Ina 'Ya'yanku? Tauttaushe! "Allah ba ku, mu saти." "Tautaushe! Gaje ta gaji, ba ta ji ance ku zo ku karba ba. Ita kuma bata da sauran wata kalmar da zata ce. Sai kawai ta ci gaba da fadin: "Gidanku da rowa." "Tautaush.... DA SANNU... 25 ......Ba su karasa ba, suka yi shiru, zasu gudu. Sai ga "Ya'yan Hakimi su biyu mata Naziyatu da Nusaiba. 'Yan biyu ne. Sun yi sa'an su Gaje, suka ce "Kai ku zo Hakimi na kiranku? Ai duk sai suka tsure. Lante tace "Wallahi ba ruwanmu." Kandala tace "Gaje ke kadai za a a daure, tunda ke ce kika ce ma Hakimi gidansa da rowa." Binto tace "Dama mun sani, ba mu zo ba, ga shi kin ja mana za a dauremu. Sai Allah ya saka mana." Ita dai Gaje kwaba-kwaba tayi, kamar mai shirin yin kuka. Su kuwa su Naziyatu da Nusaiba, in ban da dariya, babu abinda suke yi, suka tasa keyansu Gaje, suka gurfanar da su gaban Hakimi. Duk a tsuren. Hakimi da uwargidan shi, suna ta dariya, yace "Ina wacce ke ba da amshin tashen? Da sauri su Binto suka nuna Gaje. Suka ce "Ga ta nan, mu babu ruwanmu." Gaje ido ya raina fata, tace "Wallahi ba ka da rowa. Ban iya bane, suka ce dole sai nayi. Ni kuma ina tayi ba a kiramu ba, kuma in-har muka koma ba mu samu kudi ba anan gidan. Wallahi zasu yi ta yi min masifa ne. Su dunga jin haushina, shine kawai na ji bakina yace gidanku da rowa. Dan Allah ayi min hakuri." Naziyatu tace "To ke ba kwayenki bane? In sun yi miki masifa, ba sai ki dunga ramawa ba" Lante tace "Ta rama me? Wacce kanninmu ma in sun yi mata ba iya ramawa zata yi ba, balle kuma mu." Gaje tace "Ni bana son tashin hankali, shi yasa ba zan rama ba, gara kawai in kyale. Ba sai na rama MAMAN FADILA 26 ba." Nusaiba tace "Kin ko kyautawa rayuwar ki, ina amfanin tashin hankali. Wallahi ma kin zama kawata daga yau." Naziyatu ta dubi Nusaiba tace "Ai sai ku yi ta kyalewa, ni dai babu wanda ya isa ya raina min hankali, na kyale shi. Mahaifiyarsu, uwargidan Hakimi da suke kiranta Hajiya. Tace "To ya isa haka nan, ba dogon surutu mu ke so ba." Hakimi da ya rasa bakin magana, ba ya ga murmushi da yake ta yi tun farkon fara tashen Gaje. Dan shi ba wai ya ji haushin abinda Gaje ta fadi bane, dan shi mutum ne mai son raha sosai, kuma dama tashe ya gaji haka. Ka ji mai ban dariya, ka ji mai ban haushi. Dan haka shi Hakimi. Gaje birge shi tayi, musamman dama ya ga ita mai hakuri ce, ba mai son rigima bace. Hakimi yace "Duk na ji bayaninki. Ya sunanki? Gaje ta fada masa sunanta, yace "To da dai nayi niyyar na tura ku can birni ne a daure min ku. To amma yanzun na fasa. Anan zan sa a kulleku." Gaba dayansu suka firgicewa Hakimi, suka kuma yiwa Gaje ca da surutu. Hakimi yace "Ya isa haka nan." Yana dariya, yace "Ina Gaje? Tana mutsu-mutsu tace "Ga ni Hakimi." Yace "To zo nan." Ya bude akwati, ya ciro kudi, yace "Ke Gaje, karbi wannan dubu daya ce. Na ki ne ke kadai. Kuma ga kawa kin samu anan gidan. Wato Nusaiba. Tace tana son ki zama kawarta. DA SANNU... 27 Dan haka kada ki damu, wannan kawance, mun amince da shi, kuma duk lokain da kika ga kin shiga cikin wani hali, wanda kike neman taimako, to ki yi gaggawan zuwa, ki sanar da ni. Da yardan Allah in har taimakon, bai fi karfinmu ba. Na yi miki alkawarin zan taimaka miki." Ya kuma ciro wasu kudin ya ba su Kandala. Dari biyar-biyar ko wacce a cikinsu, yace "Korafi ya kare, kada na samu labarin cikinku wata ta tayar da wannan magana, komai ya wuce." Nan suka yi godiya, kowa baki har kunni. Hakimi ya sallame su. Nusaiba tace "Kawata, bari, na taka miki, zuwa bakin get." Naziyatu tace "Ko ni ma da bani da kawa a cikinsu. Sai na taka musu zuwa get din." Koda suka je bakin get, suka yi sallama. Sai Naziyatu tace ma Gaje "Gidanmu da rowa. Bye-bye! Duk sai suka yi dariya. Su Nusaiba suka shige gida da gudu. Su ma su Binto da gudun suka nufi unguwarsu, suna murna. Kowa rike da kudin shi a hannu. ASALIN HAKIMI Yaa gaji kujeran ne waje mahaifin shi da ya mutu. Saboda ya cancanci ya maye gurbin mahaifin nasa, dan irin kwazon shi, tun yana yaro. Shi mahaifin Hakimi, kafin ya mutu. Shi Hakimi ne a birni. Sai suka samu wata matsala da ainihin Mai MAMAN FADILA 28 Martaba babban Sarki, bisa rashin biyayya da yayi a cikin rashin sani. To da yake duk inda sarauta ta ke, sarauta се, kuma sarauta bata yarda da raini ko rashin biyayya ga na gaba ba. Dan haka fada ta gargadi Hakimi da ladabtarwa da ya koma Hakimin kauye. Shine aka turo shi nan kauyen Yan Warin Daji. Sarauta ba ayi mata musu, ko gardama. Sai dai godiya, ko wane irin hukunci ta yanke maka, dan haka Hakimi ya koma kauye da zama. Amma ban da iyalan shi. Sai dai yana yawan zuwa ya ga iyalan nasa, yа koma. Babban Dan Hakimi a lokacin yana karatu e jami'a, har ma ya kusa gamawa. Abin mamaki, koda ya kare jami'arsa. Sai kawai yayi zaman shi tare da mahaifin shi anan kauye. Sai dai ya je birni, ya gaida mahaifiyar shi da sauran dangin shi. A wannan lokaci ne abokin Hakimi ya ba shi kyautar 'yar shi aure. Dan ya zauna da ita anan kauyen. Hakimi duk da ya manyanta, haka nan ya karbi kyautar 'yar abokin shi, ya aura. Suka zauna nan a kauyen. Allah ya hada jinin Ibrahim. Babban Dan Hakimi da yake zaune tare da ubansa da matar uban nasa, dan tana da kirki da biyayya. Dan Mahaifiyar Ibrahim har nan kauye, ta kan zo ta ci zarafin Asabe amaryan Hakimi. DA SANNU... 29 Amma sam bata ko damuwa. Sun samu shekara biyu, har yanzun Asabe bata haihu ba. Sai ga shi kwatsam! Allah ya bata shigan ciki, kuma lokacin shi ma aka sha ruguntsumin shagalin biki Ibrahim. A birnin ya auri yarinyar suka zauna nan tare da matar nasa a kauyen, cikin gidan Hakimi. Kuma Allah yasa yayi dacen mata, ita ma mai hankali ce. Dan haka zamansu yayi daidai da Asabe, zama mai tsafta. Wata rana mahaifiyar Ibrahim ta shiryo zata zo kauyen, tayi ma Asabe halin irin nata, tsarin kishin da ta iya. Dan kishi, tabbas akwai shi. Sai dai kowa da irin nasa kishin, dan duk mace da tace bata kishin kishiyarta. Karya take. Ni na karyatata, sai dai kawai tace ni ba irin kishin wance da wancan na ke yi ba. Ko kuma bana kishin zuwanta, amma ba zai hana kishin mijinki ba. Dan ma fi yawanci mata, kadan Mace tace tana son mijinta ya kara aure. To ba fa tace bata da kishi bane akan mijinta.Jama'a ina son ku gane haka. Namiji don ya kara aure, duk taimakon juna ne, ta bangarori da yawa. Kishi ke hanamu gane haka din, dan ya dauko asali ne tun zamanin matan Manzon Rahama. To tunda matan Manzon Rahama suka yi, mu su waye da zamu ce mun fi karfin kishi? Sai dai 'Yan-uwa ku tuna, ku kuma gane kishin matan Manzon Rahama, shi ya kamata mu kwaikwaya, mu dan kwatanta. Ba kishi irin ntamu na wannan zamani ba. MAMAN FADILA 30 Kishin kafirci, ki zauna ke da kishiyarki, zaman gaba, babu taimakon juna. Ki rika banbance Ya'yanki da Ya'yan kishiyarki, a rika kishi na shedanci, kishin jahilci da hauka da dabbanci. Dan Allah Yan-uwana masu hankali, ku fahimceni. Kada ayi mini wata fassara. Ace (Mrs. Abdullahi Dan-fali). Tace kada mata su yi kishi akan mijinsu, ko kuma ace nace bana tsoron kishiya. Ko ba ni da kishi. To ina gudun kishiya ne, kuma ina tsoronta, in har mai mugayen halaya ce, mai bin gidan Bokaye. Ban fatan Allah ya hadani da irinta, koda dai na kan ji wasu matan suna cewa, duk kyawawan halayyan kishiya, gara dai babu ita. To mu yi hakuri da addu'a. In Allah yasa zata zo. Ya zama mai kyawawan halaye ne Allah ya bamu. Ba mu dunga kiran za a kawo mana masifa da bala'i ba. To ke mijinki ya tashi yin aure, ki na furta mijinki zai kawo miki jaraba. Wacce zata rabaki da 'Ya'yanki da Mijinki, to ba ke kika dunga furtawa da bakinki ba. Dole ki ga kuwa ba daidai ba, in har kishiyar ta shigo. Mu daina kiran ma kanmu alkaba'i da sharri, gara mu dunga kiran ma kanmu alheri. Sai abin ya zo mana da sauki. Haka kuma ni (Mrs. Abdullahi Dan-fali). Ina da kishi sosai. Ina kuma addu'a kullum kishina, kada ya kaini ga kauce hanyar gaskiya, ya jefani hanyar karya. Kada kuma kishina yasa na biyewa sharrin zuciya. Ina fata kishina, in yi koyi da kishin Matan Manzo Muhammad (S.A.W.). DA SANNU... 31 Dan haka mu guji rudin zuciyarmu. Na dai san wanda suka yi nisa a kishi. Suna nan suna min dariya, da tsaki, suna dai karantawa ne kawai. Na cika su da surutu kawai. To ayi hakuri. Muna da kanni da Ya'yan da ba mu aurar dasu ba. To dan Allah 'Yan-uwana da ba su yi aure ba, kada ku yi kishin da za ku kaucewa hanyaа. Ku yi koyi da Matan Manzon Rahama. Wanda kuma suka yi auren, suke da irin wannan tsananin kishin na kafirci. Mu dunga yi musu addu'a. Allah ya ganar dasu, don ance wandada suka yi nisa. Ba sa jin kira. To Allah yasa ni dai su ji kiran da nayi musu, ba dan na isa ba. Koda oda mahaifiyar !brahim uwar gidan Hakimi, ta fito dan zuwa kauye 'Yan Warin Daji. Motar da mahaifiyar Ibrahim ta shiga, ta fada hannun bata gari ne masu satar mutane. To ashe kuma an sami sabanin tafiyar da shi ma Hakimi ya nufi birnin, dan ya ga saùran iyalan shi. Koda ya isa, suka fada masa. Ai ita ma ta tafi can kauyen. Sai kawai ya dan yi wasu lalurorin ya koma, koda ya je, ya ga bai ganta ba. Sai ya tambayesu, ko ta zo nan? Suka sanar da shi ba ta zo ba. Abu sannu-sannu har gari ya waye bata, ba dalilinta. Sai Ibrahim ya shirya ya tafi birnin. Tirkashi! Wasa, sabon girki. Da Ibrahim ya isa garin. Nan hankalin kowa ya tashi. Nan aka ba za rahotannin MAMAN FADILA 32 nemanta, ko ina birni da kauye. Amma ina! Kwana bakwai. Shiru, wata daya shiru. Daga nan Hakimi ya kwanta ciwo, saboda tsananin damuwa da tunani. Ciwon da bai tashi ba kenan. Sai makwancinsa. Gidan gaskiya. Ya Allah ya gafartawa tsohon Hakimi. Ita kuma mahaifiyar Ibrahim, har yanzun babu wani kwakkwaran labari a kanta. Kanni Ibrahim da suke can birni wajen Hakimi mai rasuwa. Shi ya ci gaba da rikonsu. Kullum suna addu'a. In mahaifiyarsu tana raye. Allah ya bayyana musu ita. Ita kuwa Asabe ta ci gaba da zama tare da Ibrahim, har ta haifi Danta namiji. Aka mayar masa da sunan Hakimi Abdullahi. Suna kiransa Magajin Hakimi. Koda Asabe ta ga ta haihu lafiya. Ta so ta koma wajen iyayenta. Amma Ibrahim yayi ta rokon tayi hakuri, har sai ta samu wani mijin. Sai ta bar gidan. Mussamman ya je ya roki iyayenta suka amince da haka din. Cancantar Ibrahim da dacewar shi, yasa aka nada shi. Ya ci gaba da zama Hakimi. Kwanci tashi, babuwuya wajen mahaliccinmu. Asabe tana yaye Magaji. Ta samu miji a birni. Aka daura mata aure, ta koma can birni gidan sabon mijin ta, ta bar wa Hakimi Ibrahim Danta Magajin Malam. Saboda irin shakuwar da suka yi da Ibrahim da matar shi Safiya, tana samun matsala da zaran ta dauki ciki. Sai ya bare. DA SANNU... 33 Suna ta dai faman zaryan Asibiti, dan haka gaba dayansu suka kwallafa rai akan Magajin Hakimi. Suna gwada masa kauna da soyayya, dan haka suka сі gaba da rainon Magajin Hakimi. Bai san kowa ba, sai su. Har ya kai shiga makaranta. Aka sa shi. Yana (Primary 3). Allah ya ba Safiya ciki. Ya zauna. Har ta haife shi. Da namiji, ya ci sunan Auwalu. Har Auwalu ya gama (Nursery). Ya shiga (Primary). Sannan Allah yasa Safiya ta haifi tagwaye, duka mata. Naziyatu da Nusaiba. Ga shi yanzun halin da ake a ciki Auwalu yana shekaran shi na karshe a (Secondry). Nusaiba da Naziyatu suna (J.S 3). Duk sun dawo gida hutu ne. Yayin da Magajin ke can birni yana digirinsa. Su Naziyatu suna da Kanni uku. Yakubu, Amira. Sunan mahaifiyar Ibrahim. Sannan Jamilu. Shine auta. Rayuwar gidan Hakimi a yanzu. Rayuwa ce mai kyau, mai tsafta, mai tattare da adalci da kaunar talakawa. Babu kyama a tare da iyalan Hakimi. Kowa nasu ne. Cikin gidan Hakimi babu mai tsiwar Naziyatu, tana da kirki, tana da masifa sosai. Haka kuma, duk cikin gidan Hakimi, babu mai hakurin Nusaiba, bata da fada, ko kadan. Yayin da Auwalu safgar gaban shi kawai yake. Haka su Yakubu da Jamilu. Ita kuwa Amira rigima ke damunta da shagwaba. Ita uwar masu gida. Yayin kuma da Magajin Hakimi ya gaji mai sunan, dan ya tsare gida. Dan gaba daya gidan, in har Magajin Hakimi ya yanke hukunci, babu wanda ya isa ya ja. Duk wani iya MAMAN FADILA 34 shegantaka, babu wanda ya isa yayi shi kusa da Magajin Hakimi. Gaba daya gidan Hakimi da Hakimi suke kiran Ibrahim. Ita kuma uwargidan Hakimin, suna ce mata Hajiya. Magajin Hakimi yana matukar kaunan Dan-uwan shi Hakimi. Duk wani abun da zai yi, ya batawa Hakimi rai. To ya na saurin kauce ma abin. Duk kuma abinda zai yi ya faranta ran Hakimi. To yana sauri yayi shi. Gajeaje fa ta dauki shawaran su Lante, dan tana ta turzawa, tana nuna ma Lamido ya rabu da ita. Abinda yake ba Lamido mamaki sosai, irin yadda Gaje ke masa. Wata rana da yamma ne. Binto da Kandala sun dawo talla. Lamido ya tsaresu, yace "Kai, ku dakata anan. Duk wace ta jirga daga nan. Sai ta gane kurenta." Nan fa suka tsaya cak! Suna kyarma, har ya zo ya samesu. Shi da abokan shi guda biyu. Lamido yace "Ku dan ubanku, ku ne kuke koyawa Gaje rashin mutumci, ku ke zugata ko? Na samu labari. Yau ubanku zan ci, in yaso ku sake. Ni kuma ba zan fasa karta muku rashin mutumci ba. Ni dama ba mu gaji mutuncin ba." Duk suka yi narai-narai da fuska, zasu yi kuka. Lamido yace "Duk 'yar da yarda, shegiyar na ga kwaran hawaye bisa fuskarta, to.... 'Yan koran Lamido da suke tare, suka ce "Kawai oga, ba sai mu afka musu ba, tunda sun yi mana rashin DA SANNU... 35 mutumci. Mu ma mu yi musu. Shegu, kananan munafukai." Lamido ya daka musu tsawa, yace "Na sha fada muku, bana son ku dunga cewa zaku fadawa yaran kauyen nan namu. Yanzu abun da nake so da ku, shine ga wani fashashen galan can da kwano, ku dauko ku yi ta yin musu kida, suna rawa, har sai sun gaji." Masu nema a duhu. Nan suka shiga doka musu kida. Lamido na rike da tsumagiya. Haka su Binto suka rinka cashewa, sai ka ce mahaukata. Da zaran sun nemi su huta. Lamido zai daga tsumangiya. Lamido bai rabu da su ba, sai da ya ga sun yi tubus! Sun yi zufa sosai. Sannan yace "Kai, in na kirga goma, ku bace daga nan. In kuma ba haka ba, na sa a kamo min ku, na sake muku wata tarbiyyar." Su Binto da suka zamiye takalmansu, suka rantaya da na kare, ko waiwaye basu yi ba, suka nufi gidan iyayensu. Lamido ya je ya samu mahaifin shi, yana zaune yace "Baba ina son na sanar da kai. Ni fa na samu diyar da nake son na aura." Dakaci yace "Alhamadullahi. Haka nake so. 'Yar gidan uban waye yarinyar? Lamido yana wani daci, ya kwaba fuska, sai kace Biri, yace "Ba 'yar kowa bace, face 'yar mai unguwa Dan-tani." Dakaci yace "To shi kenan, daman Dan-tani ya zo yayi min bayani, na ce masa babu abinda na ji. Sai in har kai ne ka yi min bayani da kanka, shine zan yarda. To yanzun kamar yaushe kake da bukata a daura muku aure? MAMAN FADILA 36 Lamido yayi mika, yace "To ni Baba, in dai son raina ne, ai ko nan da kwana bakwai." Dakaci yace "Haba Lamido, cikin azumin? Lamido yace "To menene Baba? Allah ya haramta yin aure a watan azumi n? Dakaci yace "A'a Allah bai haramta ba. Halas ne, sai dai kawai dan dai baki a bude, za a fi sakewa, yadda ake so." Lamido yace, "A kuma ji dadin yin bidi'o'in, shi kenan, babu matsala. Ni ma kaina na san dole ne mu yi bidi'o'i kala-kala. Da waskewa. Ba komai, bayan sallah ko ad kwana bakwai sai a daura mana auren." Lamido koda yake tantirin Daл iska ne, amma duk da haka yana da ilimin Muhammadiya da na boko, wanda ba a rasawa. **** Gaje da mahaifiyarta sun saki jikinsu sosai, dan tunda Dan-tani yaje wa Dakaci da maganan Gaje da Lamido. Dakaci ya gwale shi, dan yana ganin Dan shi ya fi karfin Gaje. Karya yake fada masa, sai shi ma Dan-tani ya watsar da maganan, bai kuma cewa kowa komi ba. Shi kuma Lamido tunda ya ci uban kawayen Gaje. Bai kuma kula Gaje ba, balle ya zo wajenta. Rashin sani dalilin hak,a yasa suke ganin maganan ta mutu. Ba zai yuwu ba, shi yasa suka saki ransu, basu ko tunani. Kwatsam! Dan-tani ya shigo da dariyarsa yace "Lantana, anjima bayan an sha ruwa, gidan Dakaci DA SANNU.... 37 zasu kawo goron sa ranan Gaje da Lamido. Dan haka ki na iya sanar da danginki, dan su zo, a sa ranan dasu." Gaje da karfi tace "Ummah na shiga uku! Ya zan yi? Wallahi gara na mutu. Da na auri Lamido." Dan-tani yace "Don uwarki za ki mutu. Daura aure tsakaninki da Lamido, babu fashi, dole ayi shi." Ya kai mata duka. Lantana ta kare, tace "Wallahi Maigida. Allah zai tambayeka hakkinmu, muddin ba ka canza halayyarka ba. Ya za'ayi yaron da bai da tarbiya, bai san mutumcin kowa ba, ka ce shi zaka hada aure da 'yar cikinka? Gaskiya ba ka yi mana adalci ba. Allah ya ganad da kai." Dan-tani yace "Na ji ban da adalci. To amma in dai kan wannan auren ne, sai dai kada na taba yin adalcin. Marasa fahimtar gaskiya Ni dai na gama magana, babu canji, dole abi yadda nace." Yasa kai, ya fice gidan, yana sababin da ya saba. Lantana tace "Ai kuwa in dai akan maganan auren nan ne, ba zamu taba fahimtar gaskiyarka ba."Ta kama Gaje ta rungume tana lallashinta "Ki yi hakuri Gaje, babu yadda zamu yi da halin mahaifinki, dole mu yi biyayya a gare shi. Mu dunga masa addu'a. Allah ya ganad da shi, ya kuma zaba mana abinda zai zama alheri a garemu." Gaje tana hawaye, tace "Ummah na shiga uku! Ni ce zan zama matar Lamido? Ni ba zan iya zama da shi ba. Ni dai ki san yadda za ku yi da ni. Wallahi gara ku aurar da ni ga kowa da dai ace Lamido nake aure." MAMAN FADILA 38 To kamar yadda Dan-taniyayi niyya, ya kuma so. To haka ta kasance. An raba goro. Makwabta da dangi na kusa da na nesa, ciki har da Hakimi duk sun halirci kofar gidan mai unguwa wajen sa ranan Lamido da Gaje. Bayan sallah da kwana bakwai. Ti-ki-Sa! Gaje ta shiga cikin halin kaka nika yi, domin Gaje ta fito daga gida, ta nufi inda suke zama ita da kawayenta suna tauttauna abin da ya damesu. Gaje ta tafi, domin samun shawaran kawayen nata. Abin mamaki kawayen Gaje suna hangota, duk sai suka tarwatse. Gaje tana fadin "Ku tsaya mana, lafiya kuke gudu? Lante dan Allah ke ki tsaya." Lante tace "Allah ya tsareni, na tsaya. Abin da ya samu su Binto. Ni ma ya sameni. Lamido da abokin shi. Su tsareni, ai ki yi hakuri kawai. Allah ya baku zaman lafiya."Tana fadin haka, ta kara da gudu. Gaje ta tsaya tana tunanin maganan Lante. "Me su Lamido da abokan nasa suka yi ma su Binto da bani da labari? Wata sabuwa! Gaje bata koma gida ba, sai ta nufi gidan su Kandala, tayi sa'a ta sameta. Da yake daman ita bata je inda suke zaman ba, bata san abinda su Binto suka yiwa Gajen ba. Yanzun anan ma Gaje bata fada mata ba. Sai ta fara fada mata matsalar da take damunta. Kandala tace "Gaje ki je ki rungumi kadaran da Allah ya dora miki, kin ga duk mun sa abin da yake faruwa dake, kuma Wallahi dukanmu muna jajanta DA SANNU... 39 miki, ba kuma mun rabu dake bane akan wannan auren naki da Lamido ba, sai dan ba mu da yadda zamu yi ne. Muddin muna son mu tsira da mutumcinmu. Wallahi in ba dole ba, ko hira ba ma son ta hadamu da ke. Saboda muna gudun kada Lamido ya kuma cin mana mutumci. Da kyar muka sha. Nan gaba in har ba mu ba mu yi hankali ba, muka kuma shiga hannun Lamido. To Allah kadai ya san yadda zai yi da mu. Ki dangana kawai." Gaje ta dafa kirji, tace "Wai mai Lamido yayiu muku ne? Kandala duk ta kwashe yadda suka yi da Lamido da abokan shi, ta fada mata. Gaje tana hawaye tace. "Ku yi hakuri, ni na jawo muku. Ki ba Binto hakuri. Ni zan hakura na ci gaba da harkokina na daya. Kuma Allah zai saka min, tunda haka kuma ya bullo, dan ya rabani da kawayena." Gaje sosai ta ci gaba da lallashinta, ita ma har tana zubar da hawaye. Tana bata hakuri. Haka rayuwa ta kasancewa Gaje. Bata zuwa ko'ina, tana gida. In Lamido ya aiko kirata, ta ki fita. In mahaifinta na nan ta fita, tana guna-guni. Da sassafe Gaje tana ta juyi bisa gadon bononta, ta kwana cikin bakin ciki, ta tashi cikin shi. Ta rasa tudun dafawa. Yau saura kwana uku sallah. Ita kuma saura kwana goma bikinta. Zuciyarta na bata shawaran ta gudu. Amma sai tayi tunanin gudun bai da amfani. Wata zuciyar tace bayan an daura mata aure da Lamido, ta mamaye shi ta kashe shi. MAMAN FADILA 40 Nan na ta tuna haduwarta da mahalicinmu.. Ta rasa mafita. Sai kawai ta tuno da Hakimi, wanda take ganin shine ya isa da kauyen baki daya. Dakaci ma a karkashin Hakimin yake, dan haka ta san Hakimi yana da ikon ya takawa Dakaci birki, akan aurenta da Lamido. Kuma dole yasa Dan shi Lamido janye. Haba ai wannan tunani yana zuwa mata. Gaje bata san lokacin da tayi zunbur ta mike ta nufi kofar

Chapter 2 of 7