Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 4
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels MAI RABON GANIN Bно 1 Hainna ABashir MAI RABON GANIN BADI NA HAUWA A. BASHIR AYAGI KANO STATE. GODIYА Da sunan Allah mai rahama mai Jin kai Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, Annabi shugabanmu Muhanımadu (SAW) da Sahabbansa da wadanda suka yi riko da sunnanrsa da wadanda suka yi riko da su nnarsa har zuwa ranar sakamako. Ina gode Allah da ya azurta ni da lafiya da basirar rubuta wannan littafi mai su na MAI RABON GANIN BADI" yanzu ga shi har ya kammala Ina matukar godiyata ga mutanen da suka taimaka min yayin rubuta wannan littafin irin su mai gidana ALHAJI BASHIR, da BABA INUSA SANI MAINAGGE. da TIJJANI DISO, da MALAM NASIRU DAHIRU zage na shashen harsunan Nigeria Jami'ar Bayaro Kano. da LAMI AL HAJI BASHIR da SALWA HAMISU KANO da Hajiya Hauwa Kulu Musa, Ina godewa duk mutumin da ya taimaka mini ta kowace hanya Allah ya saka da alherinsa amin. Wassalamu Alaikum. HAUWA A. BASHIR AYAGI KANO STATE. * HAKKIN MALLAKA CM) НАAUWA A. BASHIR AYAGI. MAI RABON GANIN BADI AN FARA BUGAWA 1993. * SADAUKARWA, NA SADAUKAR DA WANNAN LITTAFI GA MAHAIFINA ALHAЛ MUНАAMMAD. ALLAH YA JI KANSA AMIN SUMMA AMIN. WASSALAMU ALAIKUM HAUWA A. BASIIIR. * DOKA. BA A YARDA WANI YA BUGA KO YA JUYI WANNAN LITTAFI TA KOWACCE HANYA BA SAI DA IZININ MAI SHK A RUBUCE. DON HAKKIN MALLAKA YA RATAYA A KANTA. 11 * LITTATAFAN DANA WALLAFA SUNE KAMAR HAKA:- SO SARTSE NA DAYA, DA NA BIYU, MASOYINA NA DAYA DA NA BIYU BAKIN CIKIN RAYUWATA NA DAYA, MASU FITOWA NAN GABA SUNE - SO AJIYAR ZUCIYA, RAYUWAR SOYAYYA, BAKIN CIKIN RAYUWATA NA BIYU. Ana iya samun su a Garba Mohd. Bookshop, kofa mai kallon BATA, kasuwar Sabongari, No. 92, Sauki Bookship No 92 Jan Bulo, No 25 Jakara Bookshop. B ayan da Alhaji Bello suka idar da sallar Isha a masallaci, sai ya isa gida, ya na mai yin sallama! Hajiya Zainab ta amsa, ta yi masa barka da zuwa kuma ta hada m asa kayan abinci ta kawo masa, a yayin da diyar ta FIDDAUSI take biye da ita. Hajiya ta ajiye kayan abincin tana mai murmushi ga sashin wato mijinta,. Fiddausi ta yi wa Babanta barka da zu wa ya amsa. Ya fara cin abincinsa nan ne Fiddausi take eewa Baba nima zanci! Idan ci za ki yi, zo mu je in zuba miki. Alhaji ya ce Hajiya rabu da ita mu ci tare, take nan Fiddausi ta zauna su ka ci gaba da cin abincin tare, bayan da su ka gama cin abinci Alhaji ya ce Hajiya dama ina son in gaya miki cewa zan je Umarah. In sha Allahu do min na gama duk shirye-shiryen da ya kamata na yi. Kuma ina kyautata tsammanin cewar ranar Alhamis za mu tafi in Allah ya yarda, koda Hajiya ta ji, sai ta yi matukar farin ciki da jin wannan zance, ta ce, Allah ya kai ku lafiya kuma ya dawo da ku lafiya amin. In ji Alhaji. nan dai suka ci gaba da tattaunawa. a Abin lura da fahimta shine Alahaji Bello wani hamshakin mai kudi na da kashin arzuki yana zau ne ne wata unguwa mai suna `SANI MAINAGGE" a cikin binin Kano. Alhaji Bello Allah ya bashi hakuri da rikon amana ga alheri ga kowa. Hajiya Zainab ita ce matar Alhaji Bello! Mace ce mai hankali da nutsuwa ga ladabi da biyayya ga hakuri sannan tana da son jama'a sosai. Alhaji Bello Alah ya bashi 'ya'ya maza da mata, amma duk Allah ya karbi abinsa. Sai wannan yarinyar ita kadai wato Fiddausi Allah ya bar musu ita. Alhaji Bello yana da 'yan uwa da dama, amma mafi yawancinsu sun rasu yanzu su biyu suka rage shi da kaninsa wanda suke uba daya kuma duk iyayensu sun rasu tun wani zamani da ya huce. Alhaji Bello y ana da kamfanoni masu yawa a wannan Jiha kuma kowacce takardar mallakar kamfani da ciniki sunan Fiddausi ne, a jiki. Kuma ya kafa shedu cewar koda ya rasu, to wadannan kamfanoni ba sa cikin gado. Domin ya mallakawa Fiddausi su duka. Fiddausi yarinya ce karama kimanin shekarunta na haihuwa biyar. Fidddausi yarinya cea kyakkyawa son kowa kin wanda ya rasa. Allah ya bata hakuri ga ladabi ga biyayya, ga nutsuwa sannan tana da kwazo a makaranta, kuma da it da mahifiyarta halinsu daya. A halin yanzu Fiddausi tana makaranta ne a "Nursery/Primary School" dake Gwauron Duse, kuma tun lokacin da aka sata a makaranta bata taßa yin fada da yara 'yan uwanta ba. don haka malaman su suke kau narta bayan wasu kwanaki da maganar tafiya "UMRAH" sai Alhaji ya kintsa domin lokacin tafiya ya yi da gamawarsa, sai ga wani abokinsa mai suna Alhaji Hamisu. Ya yi sallama koda Alhaji ya ji sai ya gane muryarsa,, inda ya fita, a inda yake ce m asa kai mai isa kake haka ne ai nan gidan kane, me ye abin tsayawa ka shigo mana Alhaji Hamisu ya yi murmushi. Suka shiga falon Alhaji Bello. Nan ne Hajiya zainab ta zo ta gaishe shi har kasa, ta yi masa barka da zuwa, nan ma Fiddausi ta zo ta gaishe shi, nan ne Alhaji ya bawa Fiddausi biskit, ta ce an gode. nan dai Alhazawan suka gaisa da juna. Bayan da su ka gama gai sawa Alhaji Bello yake cewa dama yanzu nake shirin yi maka waya. Sai ga shi Allah ya kawo ka. Alhaji Hamisu ya ce lafiya! Alhaji Bello ya ce au har ka manta da tafiyar da zan yi, Alhaji Hamisu ya ce na sha'afa. Nan Alhaji Bello ya ci gaba da yiwa Hajiya Zainab gargadin cewar ta kula da gida. Kuma ta kula da Fiddausi sosai Hajiya Zainab ta yi na'am da maganar mai gidanta, kuma ta yi alkawarin rike dukkan abin da ya umarce ta da ta yi. Bayan gama wannan gargadi sai Alhaji ya mike, ya buga kararrawa nan da nan sai ga m ai gadi y a zo ya ce gani, Alhaji ya ce dauki akwatin nan ka kai ta cikin mota ni ma ina fitowa. Nan da nan mai gadi y'a dauki akwatin sai cikin mota. 2 Hajıya da diyarta Fiddausi suka. shirya domin su yiwa Alhaji rakiya, suka fito gaba daya, lokacin da suka fito ne duk masu gadı suka fito suka gaida Alhaji da abokinsa. Yayi mus gargadi da cewar su kula da aikinsu sosai. Kar a sami wani cikas. Nan dai suka yi masa a dawo lafiy a, kuma su ka tabbatar masa da cewar idan Allah yarda babu abin da zai faru. Direba ya bude musu kofa da Alhaji da abokinsa hadar da Hajiya da 'yarta Fiddausi suka shiga a wannan lokaci ne direba ya ja sai filin Jirgin saman "MALAM AMINU KANO INTERNATIONAL AIRPORT" Bayan da su ka isa direba ya tsaya ya yi parking" duk suka fito. Nan Alhaji ya y bankwana da iyalinsa da amininsa da diyarsa Fiddausi, ya shiga dakin bincike. Bayan da Alhaji ya fito suka yi masa a dawo lafiya, nan ne Alhaji ya ce wa da Hajiya Zainab ta aikawa da Kaninsa Alhaji Abba cewar ya tafi sai ya dawo nan ne ya shiga cikin jirgi, lokacin da da jirghi ya cika, ya farn zarya a titinsa sai nan da nan ya daga suka tashi gaba daya da sauran maniyyata. Bayan da su Alhaji suka tashi ne, Hajiya da diyarta Fiddausi da aminin mijinta da direba suka juyo gida. Alhaji Hamisu ya yi sallamna da Hajiya, ta ce ya gaida Hajiya ya ce ya ji. Bayan tafiyarsa Hajiya ta yi kiran direbansu wato Abbas ta aike shi gidan Allahji Abba don ya isar da sakon. Bayan da Abbas ya ji sakon sai ya tafi, da isarsa sai ya tarar da Jamila da dan uwanta Jamilu, ko da suka ga Abbas sai suka ce masa sannu da zuwa, ya ce yauwa. Suka ce ina Fiddausi ya ce tana nan kuma tana gaishe ku. Sannan Abbas direba ya ce ina abbanku suka ce yana nan, ya ce ku je ku yi min magana da shì nan da nan suka shiga bayan jumawa kadan sai ga Alhaji Abba ya fito fuskar nan ba ko annuri, sai Abbas ya ce dama Alhaji ne ya ce na zo na gaya maka ya tAfiUMRAH AMMA MAKO DAYA ZAI YI. Daga nan Abbas a mike tsaye Alhaji Abba ya ce to a gaida mutanen gidan. Ya ce sa ji. 3 Shi Alhaji Abba mutu n ne mai mummunan hali domin ba shi da kirki ko kadan, halinsa ya banbanta da na Alhaji Bello. Kuma duk abin da Alhaji yake masa a raine yake ganinsa. Kuma shi bai ki Alhaji Bello ya mutu ba, don ya ci amanar wannan 'yar tasa Fiddausi ba. Haka ma matarsa Hajiya Gaji ita ma Allah ya ba ta son abin duniya sosai. Amma shi Alhaji Bello duk bai damu da haka ba. Haka zalika duk abin da zai yi tare yake hada 'ya'yansu gaba daya yake yi musu. Amma duk da haka a banza domin shi Alhaji Abba a banza yake ganin komai da aka yi masa Wannan shi ne kadan daga cikin tarihin Alhaji Abba. Lamarin gidan Alhaji Bello kuwa, bayan da Abbas direba ya koma ya sanar da Hajiya cewa ya sanar da su sakon Alhaji kuma sun ce a gaishe ku, yayin da Hajiya Zainab ta ce muna amsawa sai ta ci gaba harkokinta. Amma ita Fiddausi kuwa ta ci gaba da zuwa makaranta kuma tana ta kokari so sai. Shi kuwa Alhaji Bello bayan da ya sami sati daya, a Saudia, sai ya fara shirin dawowa gida. Bayan ya gama shirye-shiryen da suka dace, sai ya biyo Jirgin adalici wato "DAN KABO" Bayan tafiyar awa hudu sai suka iso Kano, bayan da suka sauka, sai Alhaji Bello ya shiga dakin hutawar baki, dama kafin ashinsa sun yi da amininsa Alhaji Hamisu ya ce za zo ya dauke shi, bay an da aka sami kimanin awa biyu da saukar Alhaji, sai ga Alhaji Hamisu ya zo daukarsa, da shigarsa sai ya ga Alhaji, nan da nan suka gałsa yana mai tambayarsa yaya hanya. Ya ce na dawo lafiya kalau Suka sa aka dauko musu kaya aka kai mota, sannan Alhaji Hamisu ya tuka mota sura tafi. Bayan da su ka isa gidan Alhaji Bello, sai masu gadi su ka bude musu kofa suka taryi Alhaji da murna mayalwaciya. Kuma suka je gindin "but" din motar suka jido kayayakin da aka zo da su, su kuwa Alhaji Bello suka shiga gida suka yi sallama, koda Fidausi ta ji muryar mahaifnta sai ta fito da sauri tana mai yi masa barka da zuwa, Hajiya ma ta 4 fito da vauri tana mai yi masa barka da zuwa domin lokacin tana banſaki a nan ne ta ji Fiddausi na yi masa sannu da zuwa shine ta fito ita ma Alhaji ya shiga falonsa yana hutawa, sai ga Hajiya Zainab ta shigo tana yi masa barka da zuwa a nitse. Ta kuma yi musu barka da zuwa bakidaya, ta koma ta hado musu kayan abinci iri-iri masu inganci. Da lemo mai sanyi: ta ajiye miisu, a bisa tebirin dake gabansu nan dai suka fara cin abinci suna masu nishadi. Bayan da suka gama, Alhaji Hamisu ya ce ni zan koma rida, Alhaji Bello ya ce na fa gode, nan ya tashi suka fito tare, li ajiya Zainab! Ta ce har zaka tafi ya cc, "E," ta ce to a gaida Ilajiya Tafadan" suka fito ya shiga mota Alhaji Bello ya leka taga ya ce na rode sai na zo. nan Alhaji Harnisu ya ja mota ya nıfi gida. Alhaji Bello ya koma cikin gida ya dau TI LEPHONE" ya yiwa kaninsa waya, a lokacin Alhaji Abba va dauka ya ce "Waye"Alhaji Bello ya ce ni ne, nan da nan ya gaishe shi. Ya ce, yaushe ka dawo? Alhaji Bello ya ce dazu na iso. Alhaji Abba ya ce ka dawo lafiya, shi kuwa ya се sumul Kalau, Alhaji Bello ya sanar da shi cewa ya auno kaya masu yawa, kuma za'a sami alheri sosai, sai nan da nan Alhaji Abba ya dunga murma, ya ce ni ma yanzu zan taho domin maganar taa li karfin TELEPHONE" Yayin da suka vi sallama ya ajiye waya, ya gayava Hajiya Gaji cewa Alhaji ya dawo kuma ya auno kaya kuma za a sami alheri, nan da nan ita ma ta yi muma, kuma nima yanzu gurinsa zani ta ce a gaishesu. Abba ya ce za su ji. Ya in da Alhaji Abba ya fito da dau mota ya nifi gidan Alhajı Bello, bayan da ya iso ne masu gadi suka bude masa kofa, ya shiga sannan suka rufc, Alhaji Abba ya ajiye mota yayin da masu gadi suka gaishe shi, Abba ya shiga ya yi sallama Hajiya Zainab, ta ce kai! Ashe babban mai maigida ne shigo mana da ka mant da ni ne, ko kudin cefane ba a kawo min, Abba ya yi murmushi ya ce yanzu duk wanda nake kawo miki kin raina ne, ta ce a'a ni ba wanda ya kawo 5 Ta ce da shi shiga min ko (asi) suna wasa da dariya. Ta ce yana wanka, a nan suka gaisa, ya shiga yana jiransa ba'a dade ba Alhaji ya fito ya ce Abba ha: ka iso ne, ya ce, `E" Alhaji ya kintsa ya zauna suka sake gaisawa nan Abba ya ce ka dawo lafiya Alhaji ya ce, lafiya kalau. Alhaji ya ce, ina Jamila da Jamilu, ya ce suna nan lafiya Gaji ma ta ce a gaishe ka, ya ce ina amsawa, nan dai suka ci gaba da hira. A inda Alhaji Bello ya ke bashi labari Saudia da irin canje-canjen da aka yi mata, Abba a ce yaushe kayan za su zo, Alhaji ya ce sai ranar Talata. Abba ya ce Allah ya kaimu. Nan suka yi ta yin hira har wani lokaci. Abba ya ce ni zan koma, sai da safe! Suka yi sallama da Alhaji da Hajiya Zainab, nan ne ta ce ya gaishe mata da Hajiya Gaji ya ce ta ji, ya fito ya hau mota sai gida. Bayan da Alhaji Bello ya sami kwana biyu da komowa sai ya bude akwatin da ya zo da ita ya raba, ya bawa Fiddausi nata. Wanda suke kaya masu yawan gaske, haka ma Jamila da Jamilu ya ware musu nasu, ya bawa Hajiya Zainab "Set" na yari-da sarka. Ta yi mutukar farin ciki da godiya da fatan Allah ya kara arziki. Alhaji ya dannan kararrawa sai nan da nan direba, masu gadi, da sauran ma'aikatan gida suka zo, suka shiga su ka gaida Alhaji ya amsa, ya raba musu kaya kowanne ya karba ya yi godiya. A lokacin ne ya aiki Abbas direba ya kaiwa Alhaji Abba nasa da shi da iyalansa, nan dai Alhaji ya yi ta rabawa jama'a kaya. Abokan arziki da sauran jama'a Musulmai danganta ga wanda rabonsa ya tsaga, ya aikawa amininsa Alhaji Hamisu nasa, sannan, bayan komai ya nutsa, Alhaji ya koma harkokinsa na yau da kullum. Lamarin Fiddausi kuwa, ai ba'a cewa komai domin, tana nan tana bada kokari, gashi a wannan shekarar ta gama, NURSARY/PRIMARY" a hade. Bayan da sakamako ya fito sai ya kasance ta yi sa'a, amma saboda Fiddausi yarinya ce karama, Alhaji ba zai batta ta je makarantar Sikandire ba. Bayan d aka nutsu, sai Alhají ya kai Fiddausi wata makarantar 6 koyon TAJWID, mai suna TAHAFISUL QUR'AN, do min ta sami ilimin dahir, nan dai Fiddausi ta ci gaba da bada himma wajen karatu, kasancewarta mai himma, bayan ta sami shekara daya a makarantar sai suka fara gasar karatun Kur'ani na Lokal Gammen din jiharsu. Fiddausi tana daya daga cikin wadanda aka dauka, bayan an sami kwanaki ana gasa aka kammala, alkalan gasaa suka fadi wadandaa suka yi nasara, sai ya kasance karamar hukumar su Fiddausi ita ta yi nasara, domin makarantarsu ce ta yi nasara. Fidddausi ita ce dama yarinyar da ta wakilci makarantar don haka aka dunga raba kyaututtuka ga wanda ya yi nasara, Fiddausi Bello ta yi na daya, ta biyu Salwa Abdullahi ta uku Hafsat Hassan, bayan da aka yi kwanaki da yin musabakar, sai Alhaji Bello ya shirya walimar murnar Fiddausi ta yi nasara, aka shirya komai guri ya hadu domin an shirya kujeru tsarin ya yi kyau. Jama'a da dama suka hallara ciki har da Malaman TAHAFIZUL QUR'AN, kamar su Mlam Bature - ya sami halarta har da Malama Lubabatu duk sun je domin taya dalibarsu murna. Bayan taro ya nutsu sai aka bude taro da addu 'a. Sai dalibai suka yi ta karatu. Kowanne yana karanta ayar da yake haddarta bayan sun gama sai Fiddau sai ta karanata Suratul "MALIKI JALLA WA AZZA," har karshen ayar mutane suka yi ta yabon Fiddausi Yayin a ta gama karatu sai Alhaji ya bada umarni da kowa ya ci abinci. Nan aka dunga wadabge da abinci iri-iri. Wanda a wannan lokaci ko da cokali kake yawo to ka yi hani'an. aka dunga daukar hotuna iri-iri, har bidiyo kaaset sai da aka yi a wannan walima mai dimbin tarihi wajen kowa musamman Alhaji Bello, yayin da aka gama wannan taro kowa ya koma gida, Fiddausi ta ci gaba da karatunta ba ji ba gani bare wasa, ana ta bada hazaka. Wata rana sai aka wayi gari Alhaji Bello bashi da lafiya, wato cutar ciwon Sukari ce take damunsa, kuma dama tana yawan damunsa, Hajiya Zai 7 nab, hankalinta ya yi matukar tashi sosai,nan da nan ta yi wa Alhaji Abba waya ta sanar da shi abin da ake ciki, ya ce Allah ya sauwake nima gani nan tawowa, sannan ta yiwa Alhaji Hamisu waya ta sanar da shi abin da ake ciki. Bayan da ta a jiye ne sai ga Alhaji Abba ya yi sallama, Hajiya ta amsa masa suka gaisa, yayiwa Alhaji sannu, ya cer da Hajiya wanne Hospital ya kamata a kai shi.. Hjiya ta ce da dai da ya yi AHMADIYYA aka kai shi, amma yanzu akwai wani da aka bude, Alhaji Abba ya ce wanne kenan, Hajiya ta ce, INTERNATION CLINIC," Abba ya ce sabo ne amma, ta ce "E sabo ne a gurinka domin ya dade saninsa ne baka yi ba." Ya ce a ina yake ta ce yana nan "AIR PORT ROAD." Alhaji Abba ya ce to ai shi kenan. Lokacin da suka dauki Alhaji-suka fita da shi suka saka shi a cikin mota sai can asibiti bayan da suka kai shi. Likita ya bashi kwanciya, sai ya kasance Hajiya ita take zama a g urinsa ta wuni, shi kuma Alhaji Abba idan ya dawo daga kasuwa sai ya zo ya kwana tare da shi. Idan ka je asibitin daki mai lamba "No 30" aka bashi. Haka Alhaji ya yi ta shan maaganai, amma ina babu batun sauki, domin duk 'yan uwan Alhaji sun fitar da rai da shi. Wata rana Alhaji yana kwance Alhaji Hamisu yana kusa da shi kuma ita ma Hajiya Zainab tana kusa da shi tana kuka saboda halin da mijinta yake ciki na rashin lafiya mai tsanani, lokacin ne shi Alhaji Hamisu yake bata hakuri, a wannan lokaci ne Alhaji ya dan daure ya yi magana, Hajiya Zainab ta share hawayenta domin ta ji abin da Alhaji zai sanar da ita, Alhaji Bello ya ce, "Alhaji Hamisu! Zan baka amana idan zaka rike," Alhaji Hamisu ya ce, `'Zan rike," ya ce amanar da zan baka ita ce ta i yalina baki daya gasu nan a hannunka domin wannan cutar ba za ta bar ni ba kuma ku yafe ni bisa abin da na y i muku wan dana sani da wanda ban sani ba." Alhaji Hamisu ya ce, "Na karba kuma Allah ya bamu ikon rikewa amin," in ji Alhaji Bello, 8 nan Alhaji Hamisu ya ce, "Ai mu baka yi mana komai ba, kuma ko ka yi mana mun yafe maka duniya da lahira, kuma Allah ya baka lafiya, amin," in ji Hajiya Zainab! yayin da take zubar da hawaye. Alhaji Bello ya sanar da Alhaji Hamisu inda Kamfanoninsa da takardunsu suke ya ce ya rike a wajansa ya ajiye su amana, daga nan Alhaji Hamisu ya yi sallama da Hajiya Zainab! Ya fita ya ce Allah ya sauwake, ta ce amin. A lokacin ta ci gaba da zubar da hawaye da rokon Allah ya bashi sauki, lokacin da yamma ta yi sai Alhaji Abba ya taho da Fiddausi da 'ya'yansa Jamila da Jamilu don su gai da Alhaji, don tun da aka kawo shi basu taba zuwa ba. Kasancewar ita Fiddausi tunda aka kawo shi bata taba zuwa taga abinda yake ciki ba domin a lokacin ta koma gidan Alhaji Abba, koda suka shigo dakin da aka kwantar da shi sai Fiddausi ta fara hawayen tausayawa mahaifinta, ta gai da mahaifinta ta yi masa sannu, sannan Jamila da Jamilu suka yi masa sannu da fatan Allah ya bashi lafiya, Zainab ta ce amin. Bayan sun sami lokaci mai tsaho ku ma dare ya yi so sai, sai Hajiya Zainab ta ce wa da Alhaji Abba zamu tafi sai da safe. ta cewa su Jamila sai ku zo mu tafi, sai suka fito za su tafi, Hajiya ta kallo Alhaji a kwance ta sake hawaye, direba Abbas ya ce sai hakuri, dalilin da ya sa Hajiya take kuka shine saboda jikin Alhaji ya yi tsanani. Tana sharre hawaye, suna tafiya har suka isa gida. Bayan da suka isa gida ne Hajiya ta ce da direba ya huce ya kai su Jamila gida, ya sanar da Hajiya Gaji cewar jikin Alhaji ya yi tsanani, ya ce to ya fita don kai su Jamila gida ya kuma zarce don ya sanar da mahaifin Hajiya cewar jikin Alhaji ya yi tsanani. Lokacin da Hajiya, ta zauna a gida sai ta rasa abin da yake mata dadi a duniya, Hajiya ta kasa zaune ta kuma kasa tsaye, tana cikin haka har Abbas ya dawo ya ce na gayawa alhajin ya ce Allah ya sauwake kuma ya ce zai zo da safe ya ita duba shi. Sannan Abbas ya koma waje ya bude dakinsa, kuwa hajiya Zainab ta kasa barci domin ita yau ji kin Alhaji ya bata tsoro, tanan nan zaune cikin rashin sanin halin da Alhaji yake ciki, tana ta yin kuka, kuma tana share hawaye, nan ta duba agogo taga har karfe biyu da kwata na dare, Hajiya ta yi alwala, ta yi Kiyamul Laili, bayan ta idar ta yi wa mi jinta addu'a Allah ya bashi lafiya. Lamarin da ta kasance kenan. Amma shi direba Abbas yana can shi ma wajan jinyar Allhaji, ya kasa yin barci, yana ta yi wa Alhaji Bello addu 'a, sai ya ji an bugo waya, "TELEPHONE" sai nan da nan gabansa ya fadi ya kasa dauka, sai da aka yi bugowa ta biyu sanan ya dauka hannunsa yana rawa, ya yi sallama ya ce daga ina? Sai Alhaji Abba ya ce ni ne Alhaji Abba daga asibiti, ya ce Allah ya yi wa Alhaji Bello rasuwa da misalin karfe uku, ai tun da Abbas ya ji bai san lokacin da wayare ta subule daga hanunsa ba. Sai gumi ya dunga karyo masa yana cewa I nna lillahi wa inna ilaihirraji'un. Yana cewa Allah ya ji kan Alhaji kuma ya yafe masa kura kuran da ya yi amin. Ya ce wai ni dannan yanzu yaya zan shiga na cewa Hajiya, kafin Abbas ya shiga duk sai ya tashi masu gadi wadanda ba sune da aiki a ranar ba ya sanar da su, sannan

Chapter 1 of 4