Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
ce "Kin sa ni tun farko ki yi min worning." Na ce "Ai yanzu ma bata baci ba, ga shi na yi maka wannan din." Ya ce "Daman ni bani da ra'ayi tara mata in dai da zaman lafiya. To daya matar ta isheni." na yi dariya na ce "Ka dawo hanya kenan..." Ya damki hannuna. "Taso mu zaga gidan nan kiga yadda ya ke." Na ce "Ai dare ya yi, ka bari sai gobe." ya ce "A'a mu dai zagaya yanzu." na ce "To muje."Muka fara zagayawa, da ya ke ko ina yana da haske, duk sai da muka zage dakunan nan kaf, sannan muka dawo falo. Na ce "Hakika Sadik gidan nan ya tsaru so sai." Sadik y ace "Inda kika ga wannan to haka na Ibrahim ya ke ba banbanci." na ce "To yanzu aiki yake, ko sai ya yi aure sai shiga.?" Ya cc "A ciki ya ke da zama. Tun da Alhaji ya bamu mukulli ya koma can da zama." na ce "Ibarahim kenan, dan rigima yanzu fa ya yi nadama." ya ce "Ibarahim fa da gaskiyarsa." Na yi saurin dubansa 60 "Kamar ya ya.?" "Ai ba wanda zai ga zukekiyar kyakkyawar yarinya ga kyan diri ya kyalla, ai sai inda karfinsa ya Kare. Wallahia haduwar kice ta rikita shi, haka kawai yana son zai yi min kwance." na yi dariya na ce "Kai dai zuga kake." ya ce "A'a ba zancen zuga bace, zo muje mu kalli mudubi mu gani." ya kama hannuna, na yi kokarin kwacewa na kasa sai na ce "Dan Allah Sadik ka cika ni, ni ba sai na je ba." Ya ce "Wallahi sai munje ki gani. Yana gama fadar haka ya sure ni, sai dakin barcinsa. A she kofar dakin a kulle ta ke, tun sa'inda muka gama kewayawa dakunan gidan ya rufe, don haka sai ya zama dole sai ya dire ni zai bude kofar. Ni ko yana direni na fita da gudu, na barshi yana kokarin bude kofar. A bayan kujerun falo na buya, ina jinsa yana ta faman nemana. na yi shiru, dariya ta kusa ta kwace min, na dai cije, shima sai ya sami guri ya laße. Nima sai na yi zaton ya gaji ne ya koma fakin shi. sai na fito ina dariya a gadarance. Haba ai kuwa sai na kicubus da shi a wajen dakina a labe. Haba sai na juya da gudu. Ina tuni ya caf koni, muka fadi muna dariya, Ya ce da ni cikin rada "Wallahi a duk sakwan daya, miliyoyin kaunar kine suke shigar min zuciya." Na yi murmushi, ya yin da na yi shiru ina sauraron irin bugun da kirjinsa ya ke yi, a jikinsa na sa ke murmushi domin na dago, na dan zame na dube shi na dan rausayar da manyan fararen idanuwana na ce "Ka je ka kwanta, barci ka ke ji." Ya mike gami da ruko hannuna ya ce 'To ta so mu je mu kwanta." na ce "Jeka gani nan zuwa, zai je dakina 'tukunnan ya ce "Ina jiranki fa." na ce "To ka jirani." na 61 mike na zaga na je na shiga bandakin cikin dakina na fesa wankana, na zauna a gaban dressing mirrow na shafa mayuka masu mutukar kamshi da taushin fata, har sai da na ji fatata tayi limis tukunna, sannan na saka rigar barci mai shara-shara mai kyan gaske dafaffiya, na saka, nan takamani so sai, sannan na sami turaremaikamshi da jan hankali na feshe jikina da shi. Na gama shiryawata tsaf. na cire 'yan kunnayen na da sarka da abin hannu, dama tunina saka silifa, na fita da niyar inje dakin Sadik, sai wata zuciyar ta hanani da cewa "Lallai ma Hamdiyyar nan, kina 'ya mace za ki fara zuwa wajensa.? Ka wai yi zamanki, in kumaya ji shiru ya zo da kansa, sai na juya da nufin in je in kwanta sai na ji an cafke min hannu na. na yi saurin juyawa a razane cikin tsananin kaduwa. Ashe Sadik ne. Na се "Yau she ka shigo.?" Ya ce "Ai na jima a dakin nan." Na ce "Amma ban ganka ba." ya ce "Hankalinki bai je kaina bane, amma na jima a dakin nan." na yi murmushi. Ya cc "Amma fa kin hadu, ya fara shakar kamshin turaren da na fesa, ai sai ya rikice sai dafin kis take, tun ina kokarin kwatar kain,har ya fara galaba a kaina, to dama ya abu ya hadu da mtsanaiciyar kauna, ban san lokacin da na fara mayar masa da martani ba Ta ke na kara rikita shi, gaba daya idonsa ya rufe hankalinsa ya kifu a kaina, ya riga ya yi nisa. A hankalı na ringa jansa da baya zuwa gado, domin hankalinsa ya riga ya gushe, anan na dada sakankancewa, na yi dace da masoyi maitsananin kaunata. Nan fa na fara raa masa kalaman kauna tsan-tsa masu faranta ran mai bege, musamman ma a irin wannan daren da ma'abota 62 soyayya kan kira shi da daren bayyanar da kauna. Duk kuwa ma'abocin soyyya yana cin burin riskar wannan dare. To mu ma dai a kwadaice muke, dan gann mu raya wannan daren. don haka muka dauki aniyar farantawa juna, A wannan lokaci Sadik na daga baya, ma'ana bayansa na fuskantar gado, ya yin da ni kuma ina manne a kirjinsa muka isa gadon. Wata kara da na kwala, na fisge dan gudun kar ya Karasa gadon, ita ta mai da shi cikin hankalinsa, muka zube a kasa cikin kaduwa da firgita, cikin karaji na ce "Sadik duba kan gadon nan ka gani, meye wannan ?" ya juya da sauri, ya yinda ya yi ido biyu da wani katon miciji mai sauya launika, in ya yi baki, bakinsa ya kan yi ja, ko kuma ya juya ya zama kore ko yalo ko blue, kaurinsa kuwa ya yi kaurin cinyar kato, sai wani irin murmurdewa ya ke a gadon. Da gudu muka kai bakin kofa muna haki, muka sake juyowa muka kalle shi, yana nan a inda ya ke. Na dubi Sadik wanda mamaki ya hana shi yin magana, ya dubi a gogon bango dake sakale a daki, karfe biyun dare saura kwata, ya girgiza kai ya dubeni "Mu rufe wannan kofar mu koma dakin ki mu kwanta har sai da safe a zo a fidda shi. Ha! Ha!! Ha!! Muka ji dariya, kamar daga sama. "Ina son ka gaya min inda aka taba yin aure akan aure, kuma ni nafi karfin ka fidda ni daga cikin gidan nan, in kuma har kana ganin za ka iya ka jarraba in gani........" "To fa mai karatu, tsugunne bata kare ba,wai an sai da mage an sayi biri, domin suna ganin sun yi aure sun tsallake duk wata gwagwarmaya da suka sha. to abin ba haka yake ba, rikici na gaba, dan sanin yadda aka yi 63 kuma za'a kaya sai a nemi littafin SHARRIN JINNI 3 na uku don jin yadda zata kasance. Daga mai Gaunarku a kullum 'Yar mutan Sharada AMEENA ABDULLAНІ (Mrs Ahmad Yusif) Hadcjia 08085389470 64 LITATTAFAN MARUBUCIYAR ZAZZAFAR KAUNA 1, 2 & 3 TALLAFIN KAUNA 1 & 2 SIRRIN JUNA 1 & 2 HAKURI DA MASOYI 1 & 2 RASHIN HALAC GI 1&2 TSAYA KALLON RUWA... 1 & 2 SHARRIN JINN PRINTED BY: AL-AMIN B/PRINTING & PUBLISHING COMPANY No.; 156 S/TITIN MANDAWARI KANO CITY. 08028411703 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5