shi, ai ba kamar mu ba, da za ki
damu mutanc da a nemo shi. to anki a nemo shi din,sai
ki dau zani ki tafi nemansa." bansan lokacin da hawayc
ya zubo min ba, na yi wajc ba shiri, zuciyata cike da
kunci, na rasa abinda ya ke yimin dadi, na rasa abin yi,
kawai sai na shiga dakina na sa kuka,
Wasa-wasa, 6atan Sadik ya yi sati biyu, ba shi
babu dalilınsa, in kin ganni sai ki tausaya min. duk na
rame ra lalace, kullum ina cikin halin tunanin ko wanne
hali Sadik ya ke ciki oho. Na rasa wanda zai taimake ni
akan wannan lamari, ga Alhaji baya nan. Ko kaďan
abinda ya faru bai damu Mami da Ibrahim ba, ko
ajikinsu ma, sai da su ka ga na tada hankalina, nane ma
su ka ce za su yiwa Alhaji waya su sanar da shi abinda
ya ke faruwa. Shiru kusan kwana uku ba su yiwa Alhaji
waya ba, na sami Mami na ce "Ko kun yiwa Alhaji wayar.?
Tace da ni "An yi masa, yace ba zai samu damar
zuwa yanzu ba." Ina ji nasan wannan karya ne, domin
da Alhaji ya san wannnan zancen da tuni ya bayyyana a
garin nan, komai yake yi."
Na ce "Ko inje in sanarwa da Dakaci.?"
"Wai ke meyc naki ne a cikin wannan lamarine.?
Daga yau in kika kara yimin zancen Sadik sai ranki ya yi mummunan baci wallahi." Mami tace cikin fada.
Abin ba karamin mamaki ya bani ba, sai na yi tunanin
kawai tana yin kishin Sadik ne saboda danta Ibrahim, da
17
na kiya in aure shi. Don haka sai na tattara komai na
barwa Allah, na shiga yawaita addu'a a kan Allah ya bayyana min shi.
Ina zaunc gaban Alhaji, carbi a hannuna. Kallo
daya za ki yimin ki tausaya wa rayuwata, domin na kode na jeme, na zama tamkar mai yin takaba, idanuna
kuwa ja, saboda tsantsar kuka.
Alhaji ya rtinga kwararo min tambayoyi kamar
haka.:- "Lokacin da ya tafi ba kowa a gurin."
"Ni dai bana gurin, ina da niyar zuwa dai, domin in je in
same shi a gurin, sai da na tsaya shiryawa, da na isa
gurin bayan na gama shiryawa, sai na ga banga kowa ba,
sai nayi zaton ko yajc wani wajen ne yanzu zai dawo, sai
na zauna har na gaji sa zama bai zoba, do haka na yi
komawata daki na yi zamana da niyar in yazo ya yimin
magana. To shine dawowar da bai yi ba kenan har yau."
Alhaji ya ce. "Nayi iyakacin bincike na an rasa
gano inda ya shiga, wannan abu ba karamin abin
mamaki bane, domin shi Sadik yarone da ba ruwansa da
harkar mutane ma barc wani abu ya haďa shi tashin
hankali, barc ya yi fada da wani, gashi yaro mai
girmama na gaba, bare a ce ko ya yiwa wani rashin
kunya ne. Ni na rasa ta yadda wannan lamari ya faru,
kuma ba fada ku ka yi ba ya yi fushi.? na cc "Wallahi ni
bamu taba yin fada da shi ba."
"Shi kenan na yarda, yanzu zanje can kauyen na
sanar da Dakaci abinda ya faru, kuma dama tuni nasa
ayi ta rokon Allah akan wannan lamari mai ban mamaki.
18
Abu fa ya zame min kamar cuta, kullum kuka, har
su Mami sun fara jin haushina, sai wulakanci take yi
min iri-iri gashi Alhaji ya hanani komawa gida. In nace
zan koma garinmu sai ya ce In Kara hakuri dai, ana nan
ana bincike akan lamarin, kai karshema cewa ya yi ba
maganar komawa, domin shi a yanda ya dauke nitamkar
'yarsa ta cikinsa, domin duk abinda zai wa Nusaiba sai
ya yimin, a cewarsa ai ni marainiyace.
Ranan ina zaune a harabar gida nayi tagumi ina
kallon inda nake yawan zama da Abubakar muna zance
da irin dadadan kalaman da yake fada min, sai naji
hawaye na gangaromin na fara kuka ina kiran Sadik, sai
na ji kamar daga sama an ce min "Wahalalliya sai kiyi
tayi, haka ki nacewa abinda ba samu za ki yi ba." tuni
tun kafin ma Hajiya ns fahimci mai muryar, dan haka
nayi saurin juyawana dubeshi raina a bаce паce masa
"Tsaya kaji Ibrahim duk abinda za ka ce dani sai dai
kace, Kunar Sadik kuwa yanzu ma na soma, kuma misali
a ce Sadik mutuwa ya yi to ba ni ba aurc, duk fadin
duniyar nan banga wanda ya yi min ba sai shi." ina rufc
baki naji wasu kyawawan mari guda biyu tas!tas!tas! har
su uku. Na dafe kunci na na fara kuka. ya ce, "Ko kin ki
ko kin so Auren ki kamar na na gama ne domin babu
fashi." yana gama fadar haka ya yi tafiyarsa ya barni a
gurin ina ta kuka na, sai da na gaji sannan na tashi na
koma ciki, na same shi a falo, muna hada ido wani irin
harara ya doka min, sai da gabana ya fadi, na karasa ciki
zuciyata cike da takaici.
Ina kwance a daki, can kusan asuba barci
daukeni domin kullum bana barci sai na gama sallolina
19
da addu'o't ina neman Allah ya bayyanar da Abubakar
Sadik, ya komo gida a duk inda ya ke. Ban dade da fara
barcina ba sai nayi mafarki ina cikin dokar daji ni kadai,
ina gudu ina kiran sunan Sadik, sai na gamu da wani
gida a kulle, na tsaya a Rofar gidan nayi kiransa, sai naji
ya amsamin a sanyayae alamar yana cikinmawuyacin
hali, sai nayi kokarin bude kofar, na ko yi sa'a Rofar ta
bude, na shiga na sami Sadik a daddaure, duk ya rame
ya vi baki, kamar ba shi da lafiya. Ina gann haka sai na
fada jikin shi na saka kuka. Ya bude ido a hankali ya
dubeni, ya girgiza kai cikin mutukar tausayawa ya ce da
kyar. "In kwance shi." na shiga kwance shi ina ta faman
sauri, nayi sa'a na kwance masa igiyar ya warware
sauran. Na kama hannunsa muka fito muka fara gudu,
sai ga wasu samari majiya karfi suka biyo mu a baya da
bindigogi a hannunsu suna harbinmu, mu kuma muna
gocewa. Can sai wani daga cikin su ya tsaya ya saita
Sadik a baya ya sakar masa, ya yi sa'a kuwa ya same shi
a baya. Sadik ya yi kara gamıda kiran sunana ya fadi.
Ina ganin haka nima na kwala wata kara mai tsanani na
akansa "A dai-dai wannan lokaci na
farka, bansan cewa karar da nayi ta fito sarari ba, sai
gani nayi su Mami da Alhaji da Ibrahim sun shigo da
gudu suna tambaya ta "Lafiya.?" Cikin tsananin razana
da kuka па сс, "Alhaji Sadik!Sadik!!Sadik!!!
Alhaji......."
"Ina yake.?" cikin kidima Alhaji ya ke tambaya.
Nace. "Ya mutu, wayyyo na shiga uku, Sadik ya mutu."
"Wa ya fada.?" Alhaji ya tambaya cikin tashin
hankali.
20
"Mafarki na yi.?" na bashi amsa.
"Au. ai mafarki ba gaskiya bane, addu'a ya kamata
kiyı, alherin da yake cikin mafarkin Allah ya tabbatar da
shi. Sharrin da yake cikin sa kuwa Allah ya kauda shi."
Alhaji ne ya yi wadannan ınaganganu domin ya kwantar
nin da hankali.
Nan nayi ta jero addu'o'i, shima Alhajin yana taya
ni. Su Mami kuwa ficewa su ka yi da suka ji abinda ya
faru. Ibrahim tun da ya shigo ya ji nace mafarki nake sai
naji ya yi tsaki ya fice abinsa. Shi ko Alhaji sai da ya ga
na nutsu sannan ya tafi dakinsa, bayan ya yimin fada
akan in yi hakuri In ina yawan sa abun a raina dan kar
wani ciwon kuma ya same ni." Na dai amsa nasa da to
ne, amma ba zan iya ba, domin kaunar Sadik ta zamar
min tamkar mahadin rayuwata.
Alhaji da kansa ya je ya sanar da Dakaci abinda ya faru. Dakaci ya yi mamakin wannan abu matuka, kuma
ya yi bakin ciki so sai, sai ya dinga addu'ar Allah ya bayyanar masa da fansa kwaya daya tilo.
Da zance ya bazu a kauye, kowa ya ringa
mamakin wannan abu, wasu suka yi bakin ciki, ya yin da wasu suka dinga addu'ar Allah ya kara, domin iyayine irin na Dagaci ya fauki dan ya kai can birni wai
ya yi karatu, to ai ga irin tanan, ya bar dansa a gabansa yaki ya kama ya kaishi wani gari. haka akayi ta 'yan tsegungumi a garin.
***
Ibrahim na zaune shi da Mami a dakin Mamin
suna tattaunawa, ya yin da Mami ke cewa "Abinda naga
21
ya kamata ayi Ibrahim kawai shine A hada Alhaji da
Malamai, kawai ya amince a hada auren naku."
"Au dà kika je mai ya ce miki.?" Ibrahim ya tambaye ta.
"Cewa ya yi wai ai wannan ma ba mai yuwu wa
bace, suna sa ran dawowar Sadik, ya ya ma za'ai wai ace
kai ka aurcta, sai dai in Sadik din mutuwa ya yi, kuma
ko hakannne sai in tana sonka ne za'ayi, in bata sonka
shikenan sai ta fidda wanda take so a aura ma ta."
"Wallabi íami sai insa a kashc Sadik muga ta
tsiya...." Cikin tsawa Mami ta katse shi. "Kar ma ka
soma, baka da hankali ne.? Wallahi sai in daina gaya ma
ka baya, ya ya za'ai kasa a kasheshi, kai kayi ma sa ran
nasa."
"To Mami ai gani nayi ina neman rasata."
"Ga shawarar da na kawo maka, muje mu hada su
da Malamai, sai kaga komai ya yiwu cikin sauki." Mami
tace masa.
"Shi kenan Mami na bar miki wuka da nama.
Yau kusan wata uku kenan da 6atan Sadik. Ina
zaune ina tunanin anya kuwa za'a ga Sadik dina kuwa,
ni fa wannan zaman ya fara damuna, ya ma za'ayi ace
wai ba zan koma gida ba, bayan kuma na riga na gama
karatuna na sakandire. Ga Nusaiba ta tafi makarantar
gaba da sikandire. ni ina nan ina nan ina farma da tunanin
da ba shi da amfan: !na nan zaune ina tunani, sai ga
Mami ta shigo ta same ni. "In kin gama abinda kike yi
kizo ina son ganin ki."
"To.na ce da ita, sannan mike na fita na sameta a
dakinta tana faman daddanna waya, ko wa take so kira
22
oho.
"Gani." na ce da ita bayan na durkusa.
"Zauna mana so sai, magana nake son yi da ke."
Ta juyo da fara'arta ta ce dani. Na zauna, nan ta dubeni
tace, "Hamdiyya, wata shawara nake son na ba ki."
"To. na ce da ita."
Taci gaba da cewa "Mai zai hana ki auri yaron nan
Ibrahim tunda Sadik bai dawo ba, ko ince ba'a ganshi
ba........ ta dan dakata ta hadiyi yawu, sannan taci gaba
da cewa "Wallahi yaron nan yana kaunarki so sai."
"To Mami zanyi tunani akai." na ce da ita.
"A'a. ba wani batun tunani,ni yanzu nake son jin
amsar. "Eh." ko "A'a."
"Mami ina son Sadik, kuma ina mutukar Kaunarsa
fiyc da yadda kike zato,ina sa ran dawowarsa, kin ga
kuwa batun ince na yarda da auren Ibrahim abune
mawuyaci......"
Ta katseta "Au irin sakayyar da za ki yi mana
kenan.? Mun daukoki daga kauye mun kawe ki birmi,
mu gyaraki, mun ba ki ilimi, muu maida ke mutum, mun
nuna miki soyayya kamar da da iyayensa,amma za ki
nuna mana kiyayyar ko ince kin riga kin nuna mana ma,
to wallahi ba ki isa ba, aurene kamar anyi shi an gama,
wa za ki wulakanta.?"
"Maini da Sadik da Ibrahim duk daya ne a wajen ki, to meyc abin bacin rai.....?" Ta katseta. "Kin ga ma
za ki fice min daga daki na duk denyan ubanki.? Za ki
yi mamakin wallahi, za ki gwammace kida da karatu."
Na tashi na fice, zuciyata cike d bacin rai, bansan lokacin
da na fashe da kuka ba, har na hada kayana zan bar
23
gidan, sai na tuna da Alhaji,naga in na tafi zai ce banyi
masa mutunci ba, sai na hakura na ajiyc kayan ina ta kuka bar wani lokaci.
A bankali aka turo kofa, ya yin da na daga kai sai
muka yi ido biyu da Ibrahim, gabana ya yanke ya fadi,
na mike tsaye da sauri dami da dora hannu na a kan kirji
па па сс, "Ibrahim mai ya kawoka dakina a cikin
wannan darc.?"!!!
"Shecet! abinda yace kenan ya yinda ya dora
danya tsansa akan lebensa ya Karso inda na ke, ya tsaya
daga shi sai gajcran wando; ya sa hannu ya janyo ni jikinsa da karfi, sannan ya ce, "In kikai min kuka saina
wulakantaki a dakinnan." Na sa hannuna na rufe bakina,
idoa cikc da hawaye, zuciyata tana barazanar tsaga
kirjina ta fito."
"sai ki zabi dayan biyu. Ko ki yarda ki aurc ni, ko
kuma na 6ata miki rayuwa yanzu-yanzun nan."
"Na yar..da za.n a..ure ka." Na fada masa
cikin shashshekar kuka, muryata na sarkewa.
Ya yimurmushi. "In gari ya waye, zan kira Alhaji
ki bayyana masa a gabansa, in kuma kika sabamin sai
kinyi nadama, domin zan nuna miki nima kwararre ne,
kar kuma kiyi tunanin guduwa, domin in kinje gidan
naku ma, iyayenki ba yarda za su yi da maganar ki ba,
domin na riga na toshe bakinsu da kudi, in kuma kina
shakka ki jarraba ki gani." yana fadin haka ya sa keni
ya juya. Na yi ajiyar zuciya gami da komawa na zauna
ina ta tunanin abinda ya faru. gaskiya gara in bar musu
gidan su tun kafin in gama wulakanta a hannun Ibrahim,
afuskanci duk abinda ya yi ba'ayi masa fada,
24
kuma ma ko dukansa za'ayi ya riga ya gama
wulakantani, in na sa ke Mami ma ccwa zata yi sharri
zan yiwa danta, gidan kawai zan bari shine mafita a
gareni, domin na tsaira da mutunci na, ko da yake ya ce
innaje gidan ma ba goyon baya zasu bani ba, domin
abinda yace, gaskiya suma suna goyon bayan in auri
Ibrahim, daman ba son Abubakar suke yi ba. Nan na
fara tunanin lokcin da muka je gaishe da Inna, Ibrahim
dinne ya kai ni, bayan ba tun Abubakar. Inna tacc "In
har ban bar maganar Abubakar Sadik ba zata tsine min
in lalacc." To ita kenan ma ta fadi haka, balle kuma
Kubra Baba Ta sallah da ko sunan Abubakar bata son na
ambata, in na ambata sai tayi kamar ta shake n, yanzu
ma abinda ya sa basu ce shi Ibrahim din ya fito ba shine,
Dan dai Alhaji bai bayar da goyon baya bane shi yasa
har yanzu ba'a sa ranar bikin mu da Ibrahim ba.
Da gari ya wayc, tun da safe, sai ga Ibrahim ya
shigo ya same ni a zaune ina jan carbi a hannuna ina ta
faman hawaye, ya a fusace, "Ki zo inji Alhaji, kuma
wallahi ki tabbatar kin fada masa abinda kika ce da ni
jiya, in ba haka ba sai kinyi mamaki." Na mike ban ce
da shi komai ba na mike zan fice, sai ya sa hannu ya
kamoni ya dawo da ni, "Haka za ki tafi kin kukan kalen,
Alhaji yace tilasta miki nayi na yi.? To koma sai kin
share hawayen za ki fita." Na sa mayafina na share sarai,
sannan na fice ya biyoni a baya. Muka tarar da Alhaji da
Mami zaune a falon Alhaji, na durkusa na gaishe shi."
"Naji wata magana daga bakin Ibrahim, kuma nayi
mamakin jinta, shine nace a yi kiranki domin inji haka
ne.? In hakan ne shikenan, in kuma ba hakan bane to.
25
daman magana a bakin mai ita tafi da di. Wai da gaskc
za ki auri Ibrahim din kin hakura da Sadik.?" Alhaji ya
yi wadannan maganganu bayan ya amsa min gaisuwata.
Na sunkuyar da kai, hawayc na gangaro min daga
idanuna. Dukakan su idanuwansu na kaina, suna
sauraron abinda zance, sai nace Eh. kawai, domin in
nace A'a shima kansa Alhaji a nawa ganin zai ji haushin
irin kiyayar da na kc yiwa dansa bayan irin abin alherin
da ya ke yi min, kuma sannan babu makawa Ibrahim zai
keta min mutunci na." Alhaji yana jin abinda na ce sai
ya yi murmushi ya ce, "Shi kenan daman nayi masu gida
a jere ma'ana kusa da kusa shida Sadik, yanzu saura
shirin biki kenan ya rage min.
"Kai Ibrahim sai kaje ka fara shirye-shiryen ka ba
wani bata lokci za'a dauka ba." Cikin tsananin murna
Ibrahim ya mikc ya fita yana farin ciki, nima na tashi na
bar su da Mami na shiga dakina na fada gado ina ta
faman kuka kamar raina zai fita, nace bana sonka
Ibrahim bana kaunar ka. Wallahi-wallahi ba zan zauna
ba ko anyi auren mu.
Tuni Alhaji ya je ya sami su Inna an tattauna
maganar aurc, kowa ya yi farin ciki da wannan lamari.
Baba Ta sallah ta ce. "Alhaji kaine wuka kaine nama,
saboda haka mun bar maka duk komai a hannunka."
Alhaji yace "Ai babu komai, shi da duka na kowa ne."
Haka ya yi sallama da su ya tafi zuciyarsa cike da farin
cikin ganinsu yake kamar 'yan uwansa na jini. Suma su
Inna sun dauke shi tamkar dan uwansu.
26
Wata guda kacal aka sa bikin mu, bakin ciki a
gurina ba'a magana, na rasa yadda zanyi da rayuwata, na
je na sami Ibrahim a dakinsa alokacin Mami ta fita
unguwa, na sa masa kuka akan ya janye maganar auren
mu." Nan yace "Wallahi in har kinga an fasa auren nan
sai dai in mutuwa na yi ko kika mutu, amma ba bu fa
shi." Na rasa yadda zan bullowa masa, sai nace "Dan
Allah Ibarahim ka ceci rayuwata, ka taimake ni kayo
hakuri ka janyc." Ya cc "Wallahi ba zan janye ba, kamar
fa mayunwacine yaga lafiyayyen abinci sai yawunsa ya
gudana yana shirin a janyc kwanon ace ya hakura ya
bawa wani, kinsan abin da kamar wuya wai gurguwa da
auren nesa." yana gama fadin haka ya janyo hannuna
gami da lallatsawa, nayis aurin fusge hannuna na tashi
zan fice daga dakin, ya yi saurin tare kofa. "Au ina za
ki.? Ba hira kika zo muyi ba." Nace "Ni ba hira na zo
muyi ba, rokonka ne zanyi akan ka hakura ka gyale ni in
ba haka ba........." na yi shiru. ya ce "To ke nake saurare
in ba haka ba meye.?"
A
"Ba komai." Na ce masa.
"Wallahi sai kin fada." ya ce da ni.
"Na ce maka ba komai, to mai kake son in fada.?"
ya ce "Bari ki gani, yanzu za ki fađa, ya yi wuf ya saka
mukulli ya kulle dakin, ya zarc ya sa ka a aljihun
wandonsa na jeans, ya koma ya zauna ya ce "In Mam ko Alhaji in wani ya zo zance kince ba za ki fita badaga
dakin nan kinzo kenan tunda aka sa bikin mu ya yi nisa har tsahon wata guda." Na cc, "Shi akansa Alhajin ya
san ba zan ce haka ba."
"Kar ki cika baki, ahannuna kikc.'
27
"Ko ma amc na ke baka isa kayi min abinda Allah
bai yimin ba." na ce da shi.
"Au ni kike gaya wa wannan maganar, zan yi
maganin ki yanzun nan."
"Ni dai kawai ka tashi ka bude min kofa in fita."
na ce masa.
"To ko yanzu aikin kin taya ni hira....." na katse
shi. "Ni dai na ce ka bude min ko."
ya je ya bude min yana dariya gami da cęwa "То
sai na zo hira ko.?" Na ce "kaji da shi, anayi tafiyata
daki ina ta tunanin wadda zata fishsheni.
Dare ya raba, ya yinda na farka daga nannauyan
barcin da nake, tunanin mafarkin da na yi, amsa kuwwar
kalaman mai maganar yana ta dawo min cikin kunnena
kamar ido biyu na ji su. "Ma za kiyi ki taimakawa Sadik
din ki kafin ya hallaka, yana can a dajinan dake tsakanin
Tagina da Birnin Gwari, in kinje ki sa fuskarki yamma,
ki shiga dajin zan dinga nusar da ke hanya, in kin tashi
daga barcin kiyi azama ki fita daga gidan karki gaya wa
kowa, ki taimaki Sadik, domin yana cikin mawuyacin
hali." Wuf! na mike ina kiran Iannalilahi wa'innalillahi
raju'un. mai yake shirin faruwa kuma.? Wane irin
mafrkine wannan kuma.? Wane hąli Sadik ya ke ciki.?
Duk wadannan tambayoyi ne da bani da amsar su. Nan
ta ke na yiwo alwala na yi sallah raka'a biyu, na yi
addu'ar Allah ya sa mafarki nan ya zamemin alheri,
domin abin nan ya tsoratani, bayan na idarne na koma
na kwanta, amma fa barcin bai yuwu ba, a haka har gari
ya waye idona biyu ina tunanin wannan mafarki.
Kashe gari, tun da sanyin safe na tashi bayan na yi
28
sallah na zauna ina tunanin mafarkin da nayi, tunanin
wannan mafarki da nayi. na yi tunanin ko in watsar da
shi domin abin ya fayc tsoratanni, wata zuciyar ta kara
ta ce, "Anya cewa fa aka yi ki tashi da safe, gwara ki tafi
din,. in ma ajalin ki ne haka Allah ya so, da wannann
auren ma ba gwara kiyi tafiyar ki ba!." na daga kaina na
dubi agogo biyar da rabi. na ce "To yanzu zan tafi
wannan tafiya tawa, Allah ya sa alkairi a cikinta." na
tashi na nemi hijabi na na sa ka, na dan hada kayana a
karamar jaka, na sami wata 'yar roba na dura ruwa,
sannan na dauki jakar, sai da na faki ido sannan na fice
abina, ba wanda ya gannni, na kama hanyar tasha, na ko
sami motar da zata yi lodin legas zata bi ta tagina da
birniņ Gwari, na shiga, bayan na biya kudin motar
sannan na shiga na zauna, da aka gama lodi, mota ta dau
hanya, muka dinga tafiya ba ji ba gani, masu hira nayi,
masu shiru nayi, masun gyangyadi na yi, masu barci na
yi, ni ko idona kuru ina tunanin abinda yake wakana,
hakika mafarkina da akwai kamshin gaskiya a cikinsa,
domin zuciyata na dada karfafamin gwiwa cewa zan
samu abinda na ke nema. to ma ji dai ma gani, wai an
binne tsohuwa da ranta.
A farkon dajin na ce zan sauka, mutanen cikin
motar suka hauni da banbamin fada. "Ke kuwa wannann
yarinya me a sameki haka.? kina da hankali kuwa, za ki
ce a wannan dajin za ki sauka, dajin da yake da miyagun
kwari da namun daji da kuma gagaruman 'yan fashi.?"
wasu suka ce "Ko dai makuwa ki ka yi ba ki san inda za
ki sauka bane.? Ga garuruwa mun wuce, amma kice wai
a nan za ki sauka.?" Na kalle su na yi murmushin karfin
29
hali na ce, "To wai ku meye na ku a cikin wannan lamari
ne.? nan din na yi niyar sauka." Na dubi karen motar.
"Malam ka yiwa direban magana ya tsaya ka bude min
tunda na shigoi, ai na gaya maka inda zan sauka, kuma
ka amsa min ka dauko ni, to yanzu idan ka wuce da ni
ina za ka kaini." ya daki kofa gami da cewa. "Akwai
mai sauka." Dareba ya ja ya tsaya, wani tsoho da da
muke tare da shi a kujera daya da bai magana ba tun
sa'inda mutane ke ta faman batun, ya ce da kwandastan
"Da Allah yaro yi ma za ka bude ma ta ta fita, nan ba
gurin tsaya wa bane." Kwandastan ya bude min na
dauko jakata na fito na ce, "Na barku lafiya." ya yin da
wasu suka amsa,wasu kuwa cewa su ka yi "Ni kunga
yarinya kamar nutsatsiya, amma kila yarinyar 'yan fashi
ce tacje gari ta yi musu siyayya ta dawo." Na yi dariya
kawai, na suri jakata ya yinda su kuwa suka ja motarsu
su ka yi gaba.
Na tsaya na kalli kudu da arewa, gabasa da
yamma, babu kowa a dajin nan sai ni daya kwal! nace a
raina "To yamma aka ce in yi, yanzu gashi na kasa gane
yammar tunda kaina ya juye, na dubi agogon hannuna
sha biyu saura minti goma, na ce "Kai amma mai motar
nan yana zuga gudu, har mun zo.? na tsaya saitin rana
nace zan gane yamma, ta hanyar ganin inda ranata dosa,
take kuwa na fahimci yamma, na sa kai kawai cikin daji
zuciyata a dake.
Tafiya kawai nake yi ba tare da na san inda za ni
ba, tun sa'adda na sauka har yamma ligis ina tafiya ban
gamu da komai ba, sai dai gajiya, domin rashin sabo da
tafiyar, na dinga wuce kwazazzabai da bishiyoyi. Na
30
ciro wani fanke da na zauna a gindin wata bishiya na
siya a kan wata yarinya tun a tasha, na fara ci, domi
yunwa ta soma addabata, na dauki ruwan da na duro a
butar roba wata 'yar jarkar nono babba, na sha ruwan,
sannan naji dama-dama, na dauki kayana na kara gaba,
ko kadan babu alamar wata hanya da mutane suke bi, ni
dai kawai duk inda na ga sarari sai inbi, in kuma naga
guri ya yi sarkakiya da yawa sai na kewaya, haka nayi ta
tafioya har magariba ta gabato, na sami wata bishiya
wadda bata da girma so sai, na haye na bar kayana a
kasa, nayi zamana. Da haka darc ya yi, dajin ya yi tsit
babu wani motsi komai, sai wani irin matsanaicin duhu,
wanda ko tafin hannunka baka gani. Haka nayi zamana
dan gwargwar akan bishiya nan, idona kuri har gari ya
waye, na duro na fara neman inda ruwa yake inyi
alwala. na nema babu, sannan na tuna da taimama, nayi,
na gabatar da sallah, na ci gaba da tafiya, hantsi na
dagawa na fara jin wata irin yuwa, na rasa yadda zanyi,
sai ruwan nan da ya dan rage min nake kurba, da kadankaďan, a haka har naje wani wajc inda na sami gwandar
daji, da yake na saba da su tun a kauyen mu, na fara sha,
ga shi na yi sa'arta manya-manya da yake ba mai zuwa
ya diba dajine, sai da naji na koshi, sannan na dauki
hanya, kuma sai na dinga jin barci da kasala tana dauka
ta, domin na koshi, in banda kwanciya ba abinda nake
so, don haka sai na fara hangen inda zan dan kwanta in
huta, gashi dama jiya ko rintsawa ban yi ba. na ko yi
sa'ar samun wani guri a gindin wata bishiyar dorav'a
mai yawan ganye babu ciyawa da yawa, na nufi gurin na
dan tatare gurin da zan kwanta, da yake ba damuna
31
bace, du ciyawar ta bushe, na ciro zani a jakata na
shimfida na kwanta, tun ina lumshe ido inyi sauri na
budes har barci mai nauyi ya dauke ni, bani na tashi ba
sai da azuhur,nayi saurin mikewa nayi taimama nayi
sallah, sannan naci gaba da tafiya abuna.
Ina cikin tafiya, sai nabi ta wata hanya da baza ta
fiddani sarari ba,