ba tare da na sa ni ba, sai da na kai
cikin wasu sarke-sarken bishiyoyi sa reshina, sannan na
yanke shawarar na juya na dawo baya, domin kuwa
babu hanya. Allaha ya taimake ni na gani tunda wuri,
juyawar da zanyi ni ban sa ni ba ashe akwai wata
dankareriyar katuwar mesa saman gurin da nake, kawai
sai naji wata irin kara shuu! sai ra fado min a jiki ta
nannade ni, gata katuwar gaske, tayi wata irin haniniya
kamar kukan katon bijimin sa, ban san sa'adda na kwalla
kara ba, gami da kiran "Wayyo Allah! na shiga uku."
tsananin nauyinta tane ya kaini kasa, daman ita haka
take so kenan, ta sami damar da zata karyamin
kasusuwa ta hadiye ni. Nayi lamo dani ina karanta
kalmar shahada, domin na debe tsammani ga rayuwa ta.
Ta bude bakinta ta dai-daici kaina zata saka kaina
a bakinta ta hadiye, ni kuma na rufe idona ina ta faman
salati, domin nasan tawa ta kare, daman karar kwanace
ta kawo ni dajin nan...." tunanin ya katse sakamakon
wani abu da naji ya fashe fus! naji kuma wani danshi
mai dumi ya jikani, naji duk dabaibayeni da mesar tayi
duk jikinta ya sa ki, ta warwareni, nayi firgigit na bude
idona da saurinka, nayi yunkurin tashi, sai naji nauyi,
duk abin nan ban lura da kan mesar ba, sai jini da na
gani a jikina. ya bani mamaki ya yin da na mike nayi
32
0
A
arba da kan mesar can waje daya ya dagargaje saboda
tsabar wahala har ya fita daga uwar jikin, na kwallah
wata uwar razananniyar kara na fita da gudu, ba koma ta
kan kayana ba, wato jakar da ruwan nan na barsu,
bukatata dai in bar gurin, domin abuda ya kashe mesar
nan hakika ganinsa ba zai yi min kyau ba, duk da cewa
bana debe tsammamin gudun da nake yi zai sa na tsira
daga wannnan abu, to amma gara ya kasheni bisa
kokarina na tsira da rayuwata.
Bani na daina wannan uban gudu ba sai da na kai
kimanin minti goma sha biyar saboda tsananin razana,
wannan ya nuna min kenan ba karamin nisa nayi da
gurin ba. Sai da na sami sarari sannan na zauna na huta
ina ta faman haki kamar raina zai fita, bakina ya bushe,
makogwarona na ta suya, ga wahala da jikaga, ga kuma
kayan jikina duk sunyi faca-faca da jinin wannan mesar,
abin dai ba kyan gani. na dade a zaune kafin in tashi,
lokacin sha biyu ta kusa, na tashi na yi mika gami da
hamma, na dudduba ko ina, ba alamar ruwa a kusa, dan
haka na dada nausawa can yamma ina tafiya, kafata ba
ko takalmi, daman na zubar na zubar, in ma ba wauta
irin tawa ba, mai ya kaini saka takalmi mai tsini da zan
shiga daji har da wani kashe dauri, to dankwalin atamfar
tawa ma acan na baro shi, daga ni sai riga da zani, kaina
babu dankwali, gashi babu kitso, tunda ban dade da
zuwa saloon ba wannan tafiyar ta sameni.
Har yanzu dai zuciyata bata karaya ba, tafiya
kawai na ke, ban san inda za ni ba, can sai na hangi wani
guri, bisa alama akwai danshi a gurin, domin na hangi
tsuntsaye na ta shawagi a sama, kuma gurin yana
33
yanayin da hazo-hazo alamace ta akwai kogi a nan ko
wani ruwa na kwarara. Nan na himmantu akan tafiya ta,
domin na matsu na Karasa gurin na ga ruwa na sh,
domin har ishirwa tagama galabaitar da ni, ba ni na isa
gurin ba sai misalin karfe biyu da rabi, tuni kafata ta
fara sabawa da tafiya, nayi sa'a ba komai a gurin, wani
katon ruwa ne a gurin, yana kwance damkam! ga
tsuntsaye na ta faman kai da komowa a gurin. na karasa
dab da gabar ruwa duk chakwa-kwali da sawayen
namun daji, hakanne ya sa ni tunanin ko akwai namun
daji a gurin ta, amma na yi mamakin rashin ganin
dabbobi ko daya a gurin, nan dai na nemi gurin takawa
mai dan tsananin domin kar na kabe tabo, na hangi wani
dan tudu mai wasu irin kusassari kamar kaya-kaya dago
na dan taka gudun kar na cace na sunkuya na fara debo
ruwan ina sha da tafin hannuna, na ji in da na taka din
ya danyi motsi, nayi zaton kasar gurin ce ta sha ruwa, na
yi nufin na sauka kar ta rozaye dani, babu zato babu
tsammani sai naji wanı irin gurnani da ban fahimci meye
ba, kuma ban gane daga ina ake yinsa ba, na mike tsaye
ina hangawa, domin kar na koma muyi kicibus da abin
da ya ke gurnanin, daga can sai na jiyo gurnanin yana
kara kusantar inda na ke. Yo dubawar da zanyi sai na
hango wasu garken zakuna manya-manyan gaske sun
nufo inda nake, suna ta faman sunsune-sunsune, ga
alama kamshina ma su ka jiyo, bayan sun taho shan
ruwa. Nan fa na rude, nayi tunanin ina ma mesar nan ce
ta kashe ni tun a gurin da ya fiye min sauki, domin babu
ko shakka zakunannan watanda za su yi da namana, ba
zan ma wadace su ba, domin ina zaton gaba ki daya
34
T1
aa
2
akaап1
aIVA
a
a1נו
family din su suka hadu suka taho shan ruwa...." Ban
gama tunanin da na ke yi ba, sai na ga gurin da na ke
tsayc ya yi wani irin juyi ya fada ruwa.Shu!!! yana
yanka ruwa kamar jirgin ruwa. sai da na dade ina saita
kaina sannan na gane ashc akan wani narkeke kadane
mai mutukar girman gaske, idansa jawur ko wanne daya
ya yi dunkulen hannuna, wannan fa shine gaba kura
baya ga damisa, ni dai na zuba ido ina ga inda zai
kaini, domin nasan dai in har kadan ya kama mutum to
cikin ruwa yake danna shi, su hadu da 'yan uwanshi asha
walima, to wannan kadan sai na ga ya nufi bakin gaba
dani, hakanne ya sa ni tunanin ko baya so 'yan uwansa
su taya shi ci, sai ya yi gaba abinsa. Sai da yaje bakin
gaba sannan ya watsa ni waje, ya koma ya dulmiye a
ruwa, daga nan ban sakc jin ko duriyar sa ba. Su kuwa
garken zakunan nan ban san yaddka suka kare ba da su
ka rasa ni ba.
Na jima ina jin jiki saboda jifan da kadan nan ya yi
da ni. Na mike da kyar na tashi jikina na ta faman
tsuma, duk kuwa da cewa na dan fara sabawa da wahala
yunwa, kishirwa da sauran makamatan irin su. Bayan na
huta na tashi domin na ci gaba da tafiya, jikina duk ya
mutu, ina ta tunanin abinda naje nema, wato Sadik.
"Anya kuwa Sadik yana da rai kuwa, in kuwa yana da
rai to shiko zaman me ya ke yi a wannan bakin dajin.?
Au cewa fa aka yi kama shi aka yi aka kulle." To kuma
ai ni ban ga alamar ma zan sami wani gida anan ba." na
kauda wannan tunani da tambayoyi mara sa amsa da na
ke ta jero wa kaina, na ci gaba da tafiya ta kawai. Sai da
na yi nisa so sai da bakin ruwan nan ya zama na bana
35
hango sht, sat na iske wasu bushiyoyin kwa-kwn ta
ruwa, ga wasu nan sun fado Rasa, sun fhr fashe, na
zauna na dauka ina ta barewa ina shanye ruwan cikin su
ina cin kwakwar Sai da na Roshi NO ani sannan na tashi
na ci gaba da taflyata. Ina cikin tafiya sai na ji ta sama
wata aska shuu! ta jefar da ni wje daya, daga kan nan
nawa sai naga wata Ratuwar mikiya, tana neman ta
kuma kawo min sura, na goce a dai-dai sanda ta kawo
surar ta watci kasa, ta sa ke dawowa kaina, ta nufi t
cire min ido. da na fahimci nufin ta kenan, sai na ringa
kare idanuwa na da hannuwana, hakanne yasa duk ta
yayyaga min kayana da faratanta masu kama da reza,
duk kuma ta yayyaku sheni, jikina ya yi jona-jina, har na
fara galabaita, na kasa karo kaina, nayi shane-shame a
kasa, havnayena bisa idanuwa na, domin ka da ta kwaRule min idanuwana. Ta taso da saurinta da niyar ta cake
ni, sai na ji wani irin bugu can nesa da ni, ji kake wani
jif!" na yi saurin ta shi in ga menene kuma, sai na ga
mikiyar can gefe daya kwance ba rai, daga nan sai naga
wuta ta kama jikinta. Mikiyar nan ta kone kurmus. Ai
nan na mike cikin gigitacciyar razana na runtuma a guje,
na Rara nutsatsa can ciki, sai da na gaji da gudu sannan
na zauna na huta, nayi tagumi ina ta faman tunanin anya
kuwa zan iya abinda ya kawo ni kuwa.? a gaskiya na
tafka mummunar wauta ta shigowa dajin nan, domin
wani mafarkin ba gaskiya bane." Daga nan na fara
tunanin abubuwan da suke faruwa dani a dajin, na fara
tunanin anya kuwa ba wani abu da yake taimaka min,
amma ban fahimci ko meye ba.?" Na kauda wannan
tunani da cewa "Allah ne mai taimawa bayinsa domin da
36
yar darsa ake yin komai." Ina gama yin wannan tunani na tashi dan ci gaba da tafiyar da ban san inda zan nufa ba.
a
Ina cikin tafiyata sai na dinga hangen kamar mutum a zaune a gindin wata bishiya. nan na kara azama domin ganin ko mutum ne na sami abokin hira, domin rabona da aganin mutum tun da na fita daga mota, har na debe tsammamin ganin wani kuma, ina isa dab da gurin sai na gano bafulatanar mata zaune, jikinta sanye da kayan fulani,amma ba komai a hannunta sai wata 'yar butar ruwa. Na yi ma ta sallama, ta amsa min cikin fara'a. Na cc "Dan Allah ki taimakeni da ruwa zan sha." ta ce "To ai ba wani abu, ungo, ta miko min ruwan da ya ke hannunta. na karba, domin ni duk zuciyata ta dake daga duk wani abin tsoro da zan gani. Sai da na sha wannan ruwa na koshi, sannan na mika ma ta ina ta faman yi ma ta godiya, na ce "Bari in dan huta a
nan sannan na ci gaba da tafiya." na zauna a kusa da ita. Ta ce "Ba kya bukatar wani abinci ne, ko da 'ya'yan itatuwa.?" Na ce "Ina bukata, to amma ban san su ba shi ya sa ban ci ba; ko ban sa ni ba ko ba'a cin su, iya ka wadanda na sa ni nake ci in na samu.." Daga nan ta tashi ta nuna min irin wadanda ake ci, na tsaya ina kallonta ina mamkin ta. "Ji bi mace ita kadai a bakin daji nan amma ko alamar tsorata babu a tare da ita, can nace da ita "A nan kike da żama.".
"Ke dai kyale ni inda kika ganni." ta ce da ni. na ja bakina na tsuke na zuba ma ta ido ina kallon ikon Allah. Daga can sai naji barci yana neman kamani. Nan na kishingida, abinka da gajiyayyiya, ai nan take barci ya
37
yi awon gaba da ni, daga nan ban san abinda ya faru ba.
Acan gida kuwa, tunda gari ya waye Mami ta ga
shiru ban fito neman abin karyawa ba, sai ta shiga dakin
domin taga ko lafiya.? Tana shiga taga wayam! sai ta
zaci fita nayi, dan haka bata damu ba a wannan lokaci,
sai da taga har goma na safe ban dawo ba, sannan ta
gayawa Ibrahim, shima a wannan lokaci hankalinsa bai
ta shi ba, domin babu zato sai ya dauka ko gidan Aunty
naje, shima ya tafi domin ya ganni hankalinsa ya
kwanta. Yana zuwa tace Ai na jima rabona da gidan ta,
sai dai in kauye na tafi." Bai dawo gida ba yana yi ma ta
sallama, ya nufi can kauyen domin yaga ko naje can, da
isar sa suka karbe shi bannu bibbiyu. Ciki fara'a Inna ta
ke tambayarsa muna nan lafiya ince ko.?" ya ce "Inna ai
ita na zo nema, domin tun da safe ba mu ganta ba, shine
muke tunanin ko tazo nan." Inna fa hankalinta ya ta shi,
tace a je gari zanzari a gani ko najc. Nan take ya tashi ya
tafi garin gidan Baba Tasallah. Ya je nan ma bana nan,
ko gidan Dakaci bai je ba ya dawo ya sanar da Baba,
sannan yace "Da Allah abi gida jen 'yan uwa ko tana
can." Inna tace "Ni da kaina ma zanje." Daga nan ya
yiwa Inna sallama ya komo gida, aka yi ta yawon
nemana, amma shiru, hankalin Alhaji da Ibrahim fa ya
yi mummunar ta shi, su ka fara bada cigiya ta a cikin
kafofin yada labarai. Shiru abu yau har kusan kwana
hudu babu wani amo balle labari. Daga nan Alhaji ya
shiga yiwa Ibrahim fada da cewa "Duk wannan abu kai
ka jawo shi, domin na fuskanci yarinyar nan ba sonka
38
takc ba, kai ka matsa ma ta ta ce tana sonka, abinda ya
sa ta gudu shine dan ta ga babu yadda za ta yi ne. Imma
ta cc bata kaunarka ba kyalcta za ka yi ba, na fuskan ci
kai ba yaron kirki banc, ga shi ka janyo lissafin mutane
ya jagwal-gwale, to yanzu ya ya zanyi da iyaycn
yarinyar nan.?" Ibrahim ya yi shiru, ransa a bace ya сe
"Wai ni Alhaji da za'a dinga yi min fada ni ne na ce ta
tafine!.? ba za ka kyale mutum ya ji da abinda ya dame
shi ba, sai ka yi ta yi masa fada haka kawai..."
"To waye ya jawo.?" Alhaji ya tambaye shi cikin bacin
rai. ya ci gaba da cewa "Ai kai ka jawo, fada kuma dole
a yi ma ka shi....." Ibrahim ya ta shi ya tafi yana
gunagunai. Shima Alhaji ya fice zuciyarsa cike da bacin
rai yana fadin "Da ma ya sa ni ya rabu da yarinyar nan
ta tafi gidan iyayenta tayi zamanta, yanzu irin wannan
me gari ya waya.
Ita kanta Mami abin ya daure ma ta kai, ta samu
Ibrahim ta ce ma sa "Ibrahim kar fa asirin mu ya tonu,
ko aikawa zan yi a kwanto mana Abubakar Sadik, da ya
ke yarone mai hakuri mu ba shi hakuri domin kar ya
bayyana komai, in ya so sai ya nemo Hamdiyya, in
kuma an samu labarin ya dawo, ita ma sai ta dawo.."
Ibrahim ya ce "Tab di jam! Mami kenan, wallahi komai
za'a baiwa Sadik sai ya bayyana, domin yana shan
wahala, na ma fa ce su dauke shi gaba daya ma daga
nan su mai da shi dajin nan da yake tsakanin Tagina da
Birin Gwari a cikin wani gida da yake cikin kungurmin
daji.." Ta dafe kirji "Haka aka ce kayi.? haba Ibrahim,
mai ya sa kake haka, kar ka manta fa dan uwanka ne fa,
ya ya zaka sa ayi ta gana masa azaba, ni dai ban saka ka
39
ahh
abma hahe Thwalh i
han tate that IT DE VE
ব। কথি
suke waga a firge Ahя hakun Kol
Lallar Ya kara so a w
kuycrun falon ya лша, уа dor Marn aaide
Fokarn neman yrwur baknta NA Sabodt tsah
sanarn fingici da te ye or "Ragva Lбя
sammutn kina da wanma hahn na k ba sa
yu Kn бoyс halayvar ka mara kva km o
da min kyvа dan tsagata ya had ye ywm ha
oika, daga bisa un yva ci gaba da crwa "Tanda nake da ke
han taba una za ko sa ni a ma wannan bs sa
vanza Wae dama kece mmol abaisim Satam
Sadif ko keda danki, t0 Handryva ma kune kukа ут
sanadin Satanta don haka san ki ncamo ta" Науa
Mami ta dafe kirji "Alhaji walahi bam na Satar da ita
ba Ya katseta Yi min sbira mara otunci, wailahi
sai kin ffo m da ita" Ya dubi brabin, "Kai kum
wallahi Allah kaga dan jinn jane to sai ma bukuntaka
dai-dan da larfin da kzyi.. Ina son ma za ka sanar da n
mda ka kzi Abubakar.7 Cikin tsanann nadama уа сс,
Ya can ckia gr min da..jin
Ta gima ya karasa batunsa muryarsa na rawa
dim?
"Oh. can kka kai shi ko.? 10 mai kayi masa a can
"Wallahi ban yi masa komai ba, yana can dai a
tsarc?
40
"Zamu je da kai a taho da shi, amma Ibrahim ka
bani kunya, kuma ka bata rawar ka de tsalle kuma ka
bata wayon ka, ban taba yin tsammanin haka kake ba ai
yau, amma kowa ya yi da kyau, zai ga mai kyaı, kun.a
abinda ka shika shi za ka girba.." ibrahim ya dur kusa ya
kama kafar Alhaji yana kuka yana rokonsa gafara yana
cewa, "Wallahi ya daina, ba zai kara ba, warınan ma
tsautsayi ne." Alhaji ya ce "Kai jama'a, Hajiya kin cuce
mu, wallahi kece kika bata min yara, shi kenan da
namiji, amma kina neman samin shi a wani hali ko.?" Ta
share hawaye ta cc "Alhaji, wallahi duk abinda ka gani
ya baru, ba laifina bane. Laifina daya dai da na biye
masa, duk abinda ya ce bana kwabarsa..."
"Ai ina jin hirar da kuke yi, za ki bakantawa wani
domin ki farantawa naki. Hum walllahi Hajiya Lami kin
cucc ni, yanzu dare ya riga ya yi, amma gobe in Allah ya
so zamu je a taho da shi. Ni yanzu ma da wacce fuskar
zan kalli yaron nan da kuma ubansa Dakaci...?" Ya
tashi ransa a bace ya fice, yana tunanin abinda yake
wakana.
***
Tun da barci ya share ni a gurin wannan
bafulatanar, ban iashi farkawa ba sai a kofar wani gida a
ciki dokar dajin nan. Na mike ina mai mutukar mamakin
abinda ya kawoni nan, domin ni dai na san ba anan na
kwanta ba. Ta ke na tuna da wannan mata Bafulatana, na
dudduba ban ganta ba, na fara tunanin ba mutum ba ce
oho, na ce a raina "Ko ma dai nanne gidan da Sadik ya
ke.?" domin a mafarkin da na yi ance a nan dajin yake.
41
Nan ta ta ke naji wani irin gwiwa yazo min gami da Karfi. Na dubi jikina, duk kayana sun yayyage, sun yi wani bakikkirin, kaina ya cukurkude na zama kamar mahaukaciya, da da kitso ne ma da abin ya fi sauki, to
amma a tsefe ya ke. Na mike cikin sanyin jiki na nufi kofar gidan, ina turawa sai na ji ta bude, na yi karambanin cusa kaina a cikinsa, na samu ashe ba tsakar
gida, dakuna ne kawai da wani katon falo a tsakiyar Sakunan, na samu wsu mutane masu kama da 'yan fashi
a kwakwkwance sun sa ki baki suna ta munshari, sai na
yi tunanin sune na gani rike da Sadik a mafarki na. Na
farko na shiga cikin da karfin zuciya ina duddubawa, sai
na bude wani daki, na tarar da wani mutum a daudaure,
a haka dai fari ne, amma yanayin wahala da datti sun sa
shi ya koma baki, gashi duk ya rufe masa fuska. Sam
ban gane ko waye ba, har zan rufe kofar sai na ji ana
kirana a hankali ana cewa "Hamdiyya, zo ki kwance ni,
Hamdiyya kar ki koma nine Sadik din ki ki zo ki
kwance ni." ta ke na ji jikina ya yi wani yarrr! na shiga
dakin da sauri na, na fara kwance shi, sannan na girgiza
shi na ce "Sadik kai ne ka dawo haka.?" Ya ce cikin da
she war murya, "kiyi sauri ki kwance ni, mu fita daga
gidan nan, domin naji lokacin da Ibrahim ya yi wo
musu waya tunda safe ya ce su kashe ni.!" Na bude baki
gami da zare idanu, na yi ma za na kwance shi, na kamo
hannunsa muka fito. To fa, ashe baya iya taka kafar,
dole tasa na yi masa jagora, ta hanyar jin gina shi a jikin
da na yi, muka fito muka fara tafiya yana ta dingisawa,
sai da muka bar gidan, sannan na lura da raunikan da ke
jikinsa. Take na fashe da kuka. Muryarsa bata fita so sai
42
ya ce "ki yi a hankali, kar su jiyo mu, muyi mu bar gidan
nan. Na ce "To." muka nausa gabas. ya cc "Mu yi kudu,
domin in muka mike hanya za su biyo sawun mu, su
same mu su hallaka mu, kuma muyi azama ba hutawa."
na ce "To." muka dinga tafiya baji-ba-gani, sai da muka
sami awa uku muna tafiya, sannan muka dan zauna
muna hutawa, duk da haka zuciyar Sadik bata amince da
mu zauna ba, ni na matsa masa mu zauna, domin na gaji.
Ba mu yi awa guda da zama ba, sai ga wani
maharbi a tsaye akan mu. Na dube shi a razane na ce
"Lafiya malam.?" ya ce "Mai kuke yi a nan.?" na ce "Ва
komai, muna hutawa.?" ya ce "To ma za ku tashi ku tafi,
domin yanzun nan na ga wata motar 'yan sanda da wasu
mutane a ciki sun yi hanyar wani gida da ke cikin dajin
nan.".Habawa, ba shiri muka muka tashi muka nutsatsa
tare da maharbin nan, muka dinga tafiya maharbin yana
taimakawa Sadik, ta hanyar sakale shi da hannayensa
kamar yadda na yi masa a farko. Muka dinga tafiya,
bamu zauna a ko ina ba sai wani dan gida na itatuwa. A
she a nan maharbin nan yake da zama, ya kaimu har
cikin gidan, muka zazzauna, ya kawo mana ruwa da
gashashshen nama, muka dinga ci, sai da muka koshi
muka sha ruwa, sannan hankalin mu ya komo jikin mu.
Sai da maharbin nan ya fuskanci mun nutsu,
sannan ya fara tambayar mu inda muka je a cikin
wannann kungurmin daji da kuma abinda ya kawo
mu.?" Sadik muryarsa bata fita so sai ya bada labari,
nima na bada labarin 6atan da Sadik ya yi da nemansa
da aka yi ta yi, da kuma mafarkin da na yi, game da
shida tahowar da na yi da wahalhalun da na sha, da
43
hadarurrukan da na haye, duk na fada musu. ka wai sai
na aga Sadik yana hawaye, ya ce cikin sanyayyiyar
murya "Ba wani ne ya jawo mana wannan masifa ba,
duk Ibrahim ne, be irin ukubar da ban gani ba, Allah ne
ma ya yi da sauran kwanana a gaba, domin na debe
tsammmani da rayuwa, yanzu ba zan iya ba dda labari
ba, amma nan da kwana biyu zan baku labarin halin da
na samu kaina har na galabaita haka.
Maharbin nan ya shi ya yi wa Sadik gyaran fuska,
sai a sannan na ga yanda Sadik ya rame, sai kace wanda
yka yi cuta. kai wannan abin tausayi da yawa ya ke, na
dube shi na ce "Sadik yanzu kaine ka daw3o haka.?" ya
ce "Ninc, wuya meye bata sawa.?" na ce "Haka ne kam."
Nan muka yi ta yin hira har dare ya kawo kai, Nan
maharbin nan ya kawo mana gashashshen naman zabin
daji mai dumi, muka ci muka sha, muka koshi. Sannan
muka zauna a 'yar bukkar nan ta maharbin nan muna
bira har shi, ba abinda ya damemu, sai hira muke kamar
wadanda suke a cikin gidan su, idon mu ya rufe da ganin
juna, sai muka manta muna cikin daji, na ce "Kai muna
ta hira kamar ba a daji muke ba, kar fa wasu miyagun su
far mana, bayn mun sa ki jiki." Sai maharbin nan ya yi
dariya ya ce "Ain nan ko tsun-tsu sai na ga dama zai
gifta ta wajcn nan." ba mu yi mamakin jin haka ba,
domin ba mu san irin shirinsa ba. Nan dai muka yi ta
hira, har barci ya dauke mu. ya yinda maharbin ya cе
"Zai fita, shi a waje ma zai kwana.
44
***
Al'amarin su Alhaji kuwa, da gari ya waye, sai ya
je ya sanar da 'yan sanda abinda ya ke faruwa, ya се
kuma a bashin 'yan sanda su tafi domin taho da Sadik.
Haka kuwa aka yi, suka ba shi 'yan sanda mota guda da
kayan aiki, aka dunguma zuwa dajin, da Ibrahim aka tafi
da Alhaji, suka nausa. Ibrahim shine mai nuna musu
hanya, aka yi sa'a ba wani bata lokaci suka je gidan, da
isar su, tun daga nesa suka kashe motar, suka dinga
sanda. Har sai da suka je bakin kofar gidan, sannan suka
shiga bayan sun gama shirin ko ta kwana. Suna shiga
ciki, suka gansu a kwakwkwance shame-shame suna ta
faman sharar barci har da munshari kamar wadanda aka
baiwa maganin barci. Su kansu 'yan sandan sai da abin
ya basu dariya, domin basu dauki abin da mutukar sauki
haka ba. Ta ke suka sassaka musu ankwa, sannan suka
shiga gabgabza musu mari, domin su tashi daga nannau
yan barcin da su ke yi mai kama da na mutuwa. Su nuna
musu inda suka tsare Sadik." a gigice suka farka, suka
dubi 'yan sandan cikin mamaki, suka yi waura-wura da
su. sai daya daga cikin su ya fara kwarmaton cewa
"Wallahi mu ba 'yan fashi bane, oga Ibrahim ne ya kawo
musu wani aiki ya kawo mu nan, Sai wani daga cikin
'yan sandan ya ce "Ai dama ba ance ku 'yan fashi bane, a
bisa laifin ku aka kamaku. Ina Sadak din.?" Suka nuna
dakin da yake. Ta ke biyu daga cikin 'yan sandan suka
isa dakin da bindugogi a hannunsu, suka dudduba babu
kowa a dakin sai igiyoyi da dan tarkacen da ba'a rasa ba,
ga takalmi da agogo wanda ake zaton na Sadik ne. Suka
kwashe suka fice, suka tasa sauran a gaba, suka nufi
45
inda 'yan uwansu suke. Suka sami Alhaji suka gaya
masa basu sami Sadik din ba. Amma dai ga takalmansa
nan da agogonsa." Alhaji ya karba ya duba ya сe "Hakika na sa ne, to ina ya kc.?" Su ka ce "Wallahi su
dai ba su san inda ya yi ba..." Alhaji ya daka musu tsawa
ya ce "Ina kuka kai min Sadik, ko kun kasheshine.?" Su
ka ce "Ba su kashe shi ba, su kafin su yi wannan barci
ma sai da suka sa ke lekawa domin su ganshi, kuma sun
ganshi a sannan din." Nan aka shiga caje gidan, an caje
gidan nan tsaf amma babu Sadik babu alamarsa. Alhaji
ya ce "Shi kenan, yanzu abinda za su yi shine, su je can
police station din su kai wadanda aka kama su fara
tuhumar su tukunna." Duk suka dunguma suka shiga
cikinmota suka