Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 5
tafi. Bayan sun je can police station din, sai da suka ci uban duka, amma sun kasa bayyana inda Sadik ya ke. Sai Alhaji ya ce "A hada da Ibrahim a tsare, har sai sa inda aka ga Sadik sannan za'a sake shi." Habawa, Ibrahim ya dinga rokon Alhaji akan ya yi hakuri ya kyale shi zai tafi neman Sadik din da kansa." Amma ina, Alhaji ya ce "Ina, sam ba za ta yiwu ba." ya dubi wani sajen Kabir yace "Yalla6ai,a kama shi mana, me ake jira da shi.?" Su ka damkeshi suka ja shi. Yana ta rokon Alhaji ya yi masa hakuri a kyale shi." Alhaji ya ce "ban haifi dan iska ba, amma idan mutum ya ce zai mai da kansa zai ga ba dai-dai ba." Yana gama fadar haka ya shige motarsa ya nufi gida, zuciyarsa cike da bacin ran abinda su Ibrahim da Mahaifiyarsa suka yi masa. Yana zuwa gida, ya sami Mami tana zaune bisa 46 kujerar falo ta tayi tagumi. Tana ganin Alhaji a fusace ta mike cikin fargaba ta ce "Alhaji ya ya aka yi.?" ya се "Ban sa ni ba, ke in kina da hankali ma kya tambayc ni abinda ake ciki.? To bari ma in gaya miki. "Na sa an tsare IBrahim, domin ba'a ga Sadik ba." ta fora hannu a ka cikin razana ta ce "Alhaji ka sa aka tsare 1Brahim, dan kane fa na cikin ka.?" ya cc "Kema in ba ki yi a hankali ba sai kin bishi, shashasha kawai mara tunani. Ya ya za'ai ki bata min dan, na san duk wannan abin da ya yi ke kika sanya shi, ga shi nan kin jawo masa abin da bai zata ba. Kuma kema sai na hukunta ki, domin ya zama darasi a gaba, domin kar ki sake gigin yi min makamancin wannan." yana gama fadin haka ya sa hannu a aljihu ya ciro wata peper ya fara rubutu a jiki. bayan ya gama ya mika ma ta ya ce "Ga shi nan ki je gida, sai na ne me ki." ta karba a sanyaye tana dubawa, tana ganin saki daya ne, sai ta dora hannu a ka ta fara kururuwa. Ya ce "A'a. kin ga ma za ki fice kar ki tara min mutane a gida, ki sa a zargeni da laifin duka. Alhali ba hali na bane." Gaba daya ma gidan ya bar ma ta, ya fice abinsa da ya ga ta dame shi da ban hakuri, ya ce "In ta gaji ta fice, shi dai kar ya dawo ya same ta, in ba haka ba kuwa zata fuskanci wulakanci.Haka ta hada kayanta tayi tafiyarta, zuciyarta cike da da na sa nin abinda ta aikata, a lokacin da da na sanin bata da wanin amfanin yinta. 47 Yanzu Sadik yana iya tattakawa so sai, kuma yana iya magana so sai, ma'ana muryarsa ta bude so sai, sakamakon wani magani da wannan maharbi ya ba shi. Har ya fara samun sauki, har dan fita muke yi ni da Sadik muna zaga dajin, dan kusa-kusa muke zuwa, mu samu 'ya'yan itatuwa mu wanke mu ci. Wata runa, minje mun sami 'ya'yan itatuwa kamar yadda muka saba, sai muka zauna hira, na ce da Sadik "Yaushe ne zamu koma gida ne.?" ya ce "Sai sanda wannan tsoo ya ce mu ta fi, kin san shi zai nuna mana hanya.?" Na ce "Shi kenan." Ya ce "Wallahi har bana son komawa.?" Na ce "Saboda mai Sadik." "Iya abinda Ibrahim ya ke min ya isa, ko kin san cewa "Shine sanadin bari na gida kuwa.?" Na dafe Kirjina na ce "Ban fahimce ka ba.?" ya ce "Wallahi wata rana ina zaune ina hutawa, ya zo ya ce "Wai Alhaji ya aike shi, kuma ya ce na raka shi." ni kuma da na ji Alhaji ne ya aike shi kuma har ya ce ya zo ya same ni na raka shi. sai kawai na tashi na ce muje. A she shi akwai abinda ya kula a zuciyarsa, shine fa ya kaini wani daji, da farko ma ba nan suka kawo ni ba, daga bayane su suka mai da ni nan gidan da kika zo kika sa meni, domin suna ganin asirin sune zai tonu, oho. Shine fa suka shiga gana min azaba iri-iri. Wallahi Hamdiyya ban zaci za su barni da rai ba, kuma fa duk a kanki ne fa." Na share hawayen da ya zubo min, na ce "Ba yadda bai yi da ni ba, akan na yarda ya aure ni, ni kuma naki. Wallahi Sadik, ko dai-dai da sakwan daya bana Kaunar Ibrahim, 48 ko ganin sa ma na tsani nayi, ni fa wallahi in muka koma gida ba zan kara zama a gidan su ba, gidan mu zan koma." Ya cc "A'a." na ce A'a na mec.?" ya ce "Ki yi zamanki, a yanzu an gane sbarrin su, Alhaji ma ba zai bari ba, na san ma zai sa idlo akan mu yanzu." Na ce "Haka ne, amma ni gara in koma gida, in ma auren ne a auro ni a gidan mu yafi dazaja." ya yi murmushi "Ai ni duk inda kike mai daraja ce ke a gurina, domin irin Kaunar da na ke miki ba zan iya fadar ta ba a baki. Mun jima muna hirı, sannan Ya ce "Ya tashi muje mu samo kwa-kwa." na ce "Kai Sadik, na gaji." Ya се "To shi kenan, mu koma gida." na ce "A'a muje din." ya ce "A'a tun da kin gaji, nima na hakura." na ce "To shi kenan, sai mujc." ya yi dariya "Shi kenan, duk abinda kika ce shi za'ayi." Na ina gama fadar haka naja hannun shi muka tafi can ciki daji, muna ta samo kwa-kwar da ta faffado kasa, muna fasawa muna ci, muna shanyc ruwan cikin ta, sai da muka koshi sannan muka kama hanyar kornmawa. Sai na hango watka bishiyar lemon zaki, nace "La-la-la, Sadik kaga wata bishiyar lemon zaki a can." ya duba ya gano sai ya ee "Tsaya a nan in je in debo, domin gurin ya faye surkukı so sai." na ce "A'a sai dai mu tafi tare." ya ce "To shi kenan, amma sai dai ki tsaya daga baya, ni kuma in tsınko." na ce "Na yarda." muka rankaya, muna zuwa sai Sadik ya dinga tsiko mana, ni kuma ina tara mana. Sai na hango wasu manya-manya nunannu,na tashi zumbur domin in tsuko su. Sadik ya ce "Ke da na ce ki tsaya a sarari,me ya kawo ki nan.?" na ce "Wasu na gani nunannu." ya ce "Bari in zaga, akwai kaya za ki soke hannu." 49 na ce "Don Allah so na ke in dan tsikowar." ya ce "To ga shi nan, sai ki tsinka." na mika hannuna zan tsinka, shima ya tsaya yana kallo na yana cewa "In fa kika soke da kaya kar ki yi min kuka.............." Kawai sai naga ya sa hannusa da karfi ya tare wani abu, ya yin da naji sautin bugun wani abu. babu kafa a hannun nasa ya fisgeni baya da iya karfinsa, na fada can bayansa baki abude, ina mamakin mai nayi kuma.?" Sai ya juyo yana rintse ido gami da cije baki, ya ce "Mu bar gurin nan Hamdiyya." na tsaya ina masa kallon rashin fahimta. ya ce cikin tsawa "Mu bar gurin nan mana na ce miki!!!." Ban san lokacin da na fita da gudu ba, ya biyo bayana, muka dafo aguje. Sai da muka fito sarari sai naga Sadik ya fadı,-ya yin da wani katon dankareren miciji ya nannade masa kafa.Nan take na nayi tunanin shine dalilin faduwar tasa. Na dawo da baya na tsaya ina ganin yadda suke ta faman kokawa da Sadik. Allah ya baiwa Sadik sa'a ya damke kansa, ya tattara karfinsa ya karya, sannan ya zubar da shi. Ya mike ya nufo gurina, sai na ga yana layi kamar dan giya. Cikin karaji na ce "Innalillahi wa'innalillahi raju'un, Sadik ya cije ka.?" Ina ba magana,kif ya kife a gabana. na yi wani ihu da sai da dajin ya amsa kuwwa, na cakumi Sadik na juya shi, idonsa babu baki sai fari tas! zatona Sadik ya mutu,na sa ke kwala kara, gami gurin ya dinga juyawa dani. Kif nima na kife kan Sadik. Nima daga nan ban san meye ya biyobaya ba. A hankali na bude idona, ya yin da na ji sanyin wani a bu ya bigi fuskata, na dan juya kaina. Sai na ga Sadik a waje daya daga shi sai gajeren wando. Maharbin 50 nan na shafa masa wani abu a jiki. na yi wuf! na mike na dubi Sadik amma ba rai. Na ce da Maharbin nan "Ya mutu?." ya ce "A'a bai mutu ba, wuyta ce kawai." N ayi a jiyar zuciya n ace "Zai warke kuma.?" ya ce "Zai warke, yanzu ma kuwa." Sai na ji wani sanyin dadi ya kwarara a raina. na ce "Alihamdulillah." daga can sai naji Sadik yana atishawa,sannan sai ya kuma motsa kafa, ya dan bude idonsa a hankali, ya bude baki le66ansa suka motsa ya fiddaharafin magana, amma ban fahimci abinda ya ce ba. Sai da ga can na dan matsa kusa da shi, na kasa kunnena a bakinsa, sai naji yana kirana "Hamdiyya! Hamdiyya!! Hamdiyya!!!" na ce, a dai-dai kunnensa a hankali "Na'am. Sadik. Ina tare da kai." wuf ya bude ido yana kokarin ta shi, amma ya kasa, na ruke shi ya tashi na jingina shi da jikin dakin na ce "Sadik sannu, ya ya jikin.?" ya gyada kai kawai. Na dubi Maharbin nan dake murza mai magani a koko na ce "Bai yi magana ba." ya yi murmushi Zai yi ne." n ace "To." Ya daura masa maganin, bai dade ba ya fara aman wani bakin abu mai kama da karan wari. Na cc da Baba Maharbi "Wannan kuma meye.?" ya ce "dafin miciji ne,ai har guri uku ya sare shi." Na ce "Kaga fasa kan farko ni ya yi niya, sai Sadik ya kare da hannunsa." ya ce "A'a, daman ba ke ya yi niya ba, domin da ke ya yi niya da ba zai bari har Sadik din ma ya gan shi ba." na ce "Au miciji baya saran mata ne.?" ya yi murmushi ya ce "Ko jinjiri ma in akwai tsautsayi ma yana saransa." na ce "To saboda mai ni bai taba ni ba.?" Ya ce "A to kinga ba ki sha wahala ba ke kadai ba shima sai ya dandana ko." Ina jin ya fadi haka sai na yi murmushi, 51 domin duk ban fahimci abinda ya ke nufi ba, a zatona zolayata kawai yake yi, domin na fuskanci mai son raha nc. Sadik na gama aman wannan, sai na ga ya fara dawowa hayyacinsa. Na yi masa sannu ya amsa idanuwansa cike da hawaye, ya ce "Hamdiyya ina ce ke wani bau bai same ki ba.?" Na ce "Ba abinda ya same ni." ya ce "Alihamdulillah, daman ke na ke ta tunani, domin ka macece." baba Maharbi ya fita ya barmu. Na ce "Sadik gaskiya ka yiwa nutumin nan magana ya samu a hanyar da zata sada mu da bakin titi mu tafi gida, domin kar mu rasa wani daga cikin mu a cikin dajin nan, ni fa hankalina ya gama tashi da gurin nan fa." Ya ce "Ko mai kika ga ya sami bawa, to mukaddari ne daga Allah." na ce "Duk da haka bana son zaman nan din, haka kawai ga mutane can a gari, sai mu dawo daji da zama.?" Ya cc "Ai dole ce ta kawo mu, amma zan yi masa maganar in ya shigo, gara ya mai da mu gida ko kuma ya samu a hanya, na san yanzu hankalin kowa ya ta shi, musamman na rashin ki. domin ni kila ma an manta da ta tawa da ya ke ni dadaddene, sai ke sabuwar tafiya. Da baba Maharbin nan ya zo muka yi masa magana muka ce Ya samu a hanya za mu tafi." Sai ya ce "To babu laifi, mu bari sai gobe, shi zai kai mu titi da kansa." Mukai ta yi masa godiya, shima har da hawayc, wai baya son rabuwa da mu. Da gari ya waye ya ce "Mu shirya." To dama ba wani abu zamu dauka ba, sai dai mu da kayan jikin mu, wanda ni nawa a yayyage suke, ga kaina ba ko dankwali, kuma ga shi gashina a cukurkude na zama 52 kamar wata mahaukaciya. Na cc "Ka wai mu tafi, mai muka dauka zamu ajiye." Sadik ya dubi rigar jikina ya ce "Gaskiya Hamdiyya ba za ki shiga gari da wannan kayan ba." Na ce "To ya ya zanyi.? kasan dai kayan da na zo da su na watsar da su a dajin nan. Ni yanzu ma ba zan iya ccwa ga inda na yar da su ba ma." Ya ciro rigarsa ta jeans, da ya ke iri daya ce da wandon jikinsa ya ce In sa rigar, in ya inyi dan kwali da tawa yagaggiyar rigata." na ce "TO kai kuma fa." Ya сс "Ai ni akwai t.shirt a jikina, na iya tafiya haka, duk da dai kayan sun yi datti." Na ce "Shi kenan mu tafi." muka ce da Baba Maharbi "To mu tafi." ya dubi Sadik ya ce "Sarkin kishi lallai akwai aiki a gabanka." Bamu fahimci abinda ya ke nufi ba. Muka yi dariya, na ce "A"a. to ya kamata ai ka yi masa fada dai." ya ce "Ya yi wa kansa fada dai.Domin na fuskanci akwai LUGUDEN KAUNA a kanki,in ba haka ba kuwa ya sha kaunar zuci." Muka sa ke yin dariya, domin duk bamu san mai yake nufi ba. Na ce da shi "Haba wai kai baka da aure ne." ya ce "Haba. aure kai, ni nine ma kuwa mai aure, nima tawa matar jira nake su gama nasu LUGUDEN KAUNAR а kanta, sannan in yi nawa, kun san manya-manya maganin kanana-Kanana, namu daban ne, in muka sa kai kuma sai hakuri." Muka ce "Haka ne kam Baba." Na ce "Wallahi Baba sai naga daman kamar tare muke da kai, ka san komai game da labarin mu." ya yi murmushi ya ce "Ai a hirar da na kanji kuna yi a nan nake fuskantar wasu abubuwa." A hankali muna tafe, in mun gaji sai mu huta, a haka har muka kai bakin titi, tun kusan karfe biyu muke 53 tsaye a titi, har karfe hudu da rabi bamu samu inota ba, domin duk motar da muka tsayar bata tsaya wa. Da Baba maharbi ya gahaka sai ya ce "To shi zai koma, kar dare ya yi masa a hanya, domin abai taho da makami ba." Maka ce masa "To." muka yi masa godiya so sai, muka yi sallama ya wuce, mu kuma muka tsaya a nan mina jiran mota. Bacewar Baba ke da wuya, sai ga wata mota kirar marsandi sabuwa dau, sai sheki ta ke yi, muka ringa daga ma ta hannu. Muka yi sa'a kuwa ta tsaya. Direban ya leko ya ce "Ku shigo muje, ba kano za ku je ba." Maka cc "Eh. Kano zamu je." "To ku shigo mu tafi." Muka shiga muna mamakin ganin yasan inda zamu dosa. Sanda muka shiga misalin biyar na yamma ne, amma abin mamaki kafin shida munje gida. Ku duba ku ga tsakanin Tagina da Kano, wannan abu ba karamin mamaki y abamu ba. Amma muka ja bakin mu muka tsuke. To ashe abin mamaki yana gaba, domin muna zuwa Kano hanyar Norman Sland ya nufa da mu. Bai zame a ko ina ba sai a kofar Gidan Alhaji. Cikin dumbin mamaki Sadik ya ce "Au dama ka san mu ne.?" Ya ce "I mana. tsiyata da ku mantuwa, yanzu har kunmanta ni.?" Sadik ya ce "Wallahi ni dai ban gane ka ba." ya yi dariya ya dube ni ya ce "Ke ma fa ba ki shaidani ba ko.?" Na ce "Uhm Sadik ma bai sanka ba bare ma ni.?" ya ce "Lallai sannnun ku, to ku fita ni zan koma." Muka dage akan sai ya sanar da mu ko wanene shi, domin kar a gaba mu kara haduwa kaga kamar wulakantaka muka yi." Ya ce "A'a. ni ba komai, ni ba zan manta ku ba." Mu ka ce "To barimu karbo ma ka 54 kudin motarka a gida." Ya ce "Ni kyauta na kawo ku, domin ba haya na ke yi ba." Ya yi baya abinsa,ba tare da ya sa ke saurarar muba, ya yi gaba ya bar mu nan a tsaye muna mamkin wannan abu. Nusaiba ce tsaye da wani saurayin ta ya zo zance, ta rako shi zai tafi gida, sai ta ga mun turo kofa mun shigo. Ai ko muna yin ido biyu da ita, ta zabga wani uban ihu, tay cikin gida da gudu, ta mance da saurayin. Ta yi dakin Alhaji, shima yana shirin tafiya masallaci, suka yi karo da shi a bakin kofasa. Ta ce cikin tsananin kidima da murna da karaji. "Alhaji ga Yaya Sadik da Hamdiyya nan!!!!!!." Alhaji dake jan carbi bai san inda carbin ya kubce masa ba, ya tsinko da gudu yana fadin "Suna ina!!!!" tuni mu kuma mun karaso ciki. Mu ka yi tozali da Alhaji, yana ganin mu ya bude hannu cikin tsananin farin ciki, muka fada jikinsa ya rungumemu yana ta faman murna. Muka shiga ciki, Alhaji ya ce "A kawo mana ruwa da abinci. Nan dai Alhaji a gida ya yi sallah bai je masalllaci ba, Carbin sa ma sai Nusaiba ce ta tsinto masa. Ya yi wa Allah godiya iya son rai, sannan ya ce "Mu jemuyi wanka mu nutsu tukunna da safe ma bashi labarin ko mai nene tukunna. Na shiga bandaki na fesa wanka gami da wanke dankararren curarren kaina, na yi sallah na shafa mai,kana na sauya kaya na masu kyan gaske. Sai ga shi na dawo Hamdiyya sak!na nade gashin kaina na daure shi da ribom. Na fito na sami Nusaiba a falo, na ce "Ina Mami.?" ta ce "Uhm ke dai zauna, sai dai goben kyaji 55 komai. Muna zaune muna taba 'yar hira na yaushe gamo, sai ga Sadik nan ya shiryo tsaf, in ka ganshi ba za ka ce mune muka dawo dazu ba, tanıkar daman can a gida mukc, sai dai rama gata nan kam. Da gari ya waye, Alhaji ya tara mu, bayan mun karya ya sanar damu abinda ke faruwa game da Ibrahim da Mami da irin bukuncin da ya ſaukar musu, sannan ya tambaye mu abinda ya faru da yadda aka yi, muka gamu. Sadik ya fada masa labarin sa,sannan ya sanar masa cewa "Duk ya san Ibrahim ne ya shirya masa haka,sabida kaunar da ya ke yiwa yarinyar nan Hamdiyya......" ya ci gaba da cewa amma yanzu duk wata batun kauna da ya ke ma ta ta kau, domin kuwa duk wannan sai da ran da Hamdiyya ta yi a kan Sadik saboda ceton ran Sadik, hakan shine ya nuna mana matsanaiciyar kaunar da ke tsakanin su." nan muke tambayarsa Mami.? ya ke cewa "Ai dalilin wannnan abu da suka yi w Sadik ya sashi ya yi ma ta sakin jan kunne. Sai da Alhaji ya tara 'yan uwan Mami, ya kira Dagaci, ya kira su Inna da Baba Tasallah, ya hada 'yan uwa kaf, sannan ya bayyana musu abinda ke faruwa, domin da basu da labarin komai, a zaton su dai bata ne Allah ya kawo. To ga sanadi abinda ya sa ya sanar da su, kuma shi baya son rashin gaskiya, ba kuma ya san goyon rashin gaskiya, yanzu ma zancen nan da akc yi Ibarahim yana can tsare a hannun 'yan sanda, domin ya ce "Kar a sak e shi har sai sun bayyana inda Sadik da Hamdiyya su ke." Nan da nan Dagaci ya tashi da fada ya ce "Amma kuwa Alhaji ba ka kyauta ba, ta ya ya za ka sa a tsare yaro, baka san kuruciya banc.? Ai rashin 56 bali irin na yara maza, ka sa a sake shi ya dawo gida. Wannan aikin banza kenan." Alhaji ya ce "Toban ki ta taka ba, amma ai ya kamata a ja masa kunne, domin bai isa ya kawo karan tsaye a zumuncin mu ba, haka ya taso ya ga muna zumun cin mu ba, in dai yace haka zai yi to ba dai a gidan nan ba, sai dai ya nemi wani gidan uban, amma ba dai nan ba." Dagaci ya ce "To ai ya horu, ba zai sake ba, ayi afuwa." Sadik ya ce "Baba Mami ma fa tana gida, ya kamata a ce ya dawo da ita." Dakaci ya ce ita kuma ai ba sakinta ya kamata kayi ba, sai ka tsawatar ama ta, in taki ji ne za ka dau kwakkwaran mataki." Nan dai Dakaci yasa yaje yasa aka saki Ibrahim, su kuma wadancen ya ce A kyale su sai ya waiwaye su in ya nutsu." ya kuma je gidan su Mami ya taho da ita, akan yarjejeniyar in ta kuma ko makamancin wannan ne to bayan ya sake ta sai ya sa an daure ta. Sannan ta yarda da sahardain,suka taho. Suna zuwa gida, Ibrahim ya yi tozali da Sadik, sai ya fashe da kuka, yana neman gafararsa. Ta ke Sadik ya gafar ta masa, sannan ya baiwa Dakaci hakuri, shima ya yafe masa, duk da dai yana nemi gafarar kowa a wajen nan. Sannan ya nemi ta mahaifinsa, shima ya yafe masa. "Amma in ya kara ba zai ga da kyau ba, haka dai guri ya yi tsit! Sannan Alhaji da kansa ya labarta musu irin wahalhalun da muka sha da Sadik a wannan tafiya, ya kuma ya ce "A cikin su waye ya kama ta ya auri Hamdiyya ta aura tsakanin Sadik da Ibrahim.?" Ta ke aka hada baki a ka ce "Sadik ya kamata ta aura!!!." Nan murna ta kamamu, amma muka boye murnar, gudun kar a agane, sai aga rashin kunyar mu kuma gashi da manya 57 a wajen. Nan Alhaji ya nemi aure a wajen Dakaci, da yake ba maza a 6angare na, sai mijin Ba ba, shi kuma bai zo ba, sai aka wakilta Dakaci, domin shi Alhaji daman shine waliyin Sadik. Dakaci ya amince, aka sa ranar daurin aure. Kowa ya watse ya tafi yana farin ciki da abinda ya faru a wannan rana. Daga sannan na zama 'yar lele a wajen Mami, ta dauke ni tamkar Nusaiba 'yarta, shi kuwa Sadik shima hakannc. Da ranar daurin aure ta zo, aka yi gagarumin daurin aure, aka sha shagalin biki, wanda ba'a taba yin kamar sa ba a dangin su Sadik. Gidan da Alhaji ya bayar a ka ginawa Sadik da Ibrahim biyu iri daya, kusa-da -kusa shine gidan da aka kaini. Alhaji shine ya yi komai na game da kayan daki, to daman gidan ba abinda ba'a sa ba a ciki. Gidan kam ya hadu so sai, ba abinda ba'a saba a ciki. A nan gidan Aunty muka sha shagalin biki, amma a can kauyen mu aka dauko amarya. Kun san kauye da tsaraba, wai a dauki yarinya a gidan su ya fi mutunci, To nima nayi farin ciki da wannann lokacin da aka kaini gidan Sadik, na yi mamakin irin dumbin dukiyar da ya kashe, domin sai da na dinga tunanin ko dai mafarki na kc yi ne.?" Domin abiun ya so ya firgita ni, nan dai ya kai amarya suka gama shewe-shewen şu da gude-guden su suka tafi suka barni ni takk a cikin gidan, ba yadda aban yi da su Haulatu da Safiyya ba akan su zauna amma su ka ki kememe. Ita kuwa Nusaiba cewa ta yi In ta zauna yaya zai ce ta yi rashin kunya in sun zo siyen 58 baki. Haka na kyale su ba'a san raina ba suka tafi. bayan sun fan jima da tafiya, sai ga gayyar angwayc nan sun dumfaro, na yi saurin lullube jikina duk da Katon mayafi, na zauna nayi shiru d ni, kaina a sunkuye, suka shigo suka gama barkwancin su, Rarshe suka yi addu'ar Allah ya bada zuri'a ta gari, suka tafi. Ya yin da shi kuma ya yi musu rakiya. Jim kadan ya dawo ya same ni a zaune, shima ya sami guri ya zauna ya dube ni ya yi murmushi ya ce "Amarsu ta ango mai dadin mai dadin tuwo da miya." na yi dan murmushi na ce "Uhin." ya ce "Ya ya hidimar biki.?" na ce "Alihamdulillah." ya ce "kai munasha kacaniya, wallahi tunda aka fara bikin nan ban zauna ba." Na ce "Ai nima haka." Ya ce "To an dai gama komai ko. ya yi kyau,mun godewa Allah,yanzu sai mu tashi muyo alwala mu gabatar da nafula ta godiya da farin cikin wannann rana da Allah ya nuna mana." Na ce "Haka ne." Bayan mun idar da sallah, ya fara mana da tsarabar da suka zo da ita domin mu ci. Muka zauna muka ci muka sha. Bayan mun gama na kwashe kayan, muka je muka yi wo brush, muka dawo muka zauna muka fara hira, da yake dare bai yi ba so sai. Can Sadik ya dube ni ya ce "Hamdiyya Allah ya cika mana burin mu." Na yi murmushi na ce "Hakika." ya ce "Gaskiya abinda kika yimin har in koma gamahaliccina ba zan taba mance shi ba, bani da abin da zan saka miki da shi...... Na katse shi ta hanyar cewa "A'a kana da shi." Cikın doki ya сe "Menene shi, fade shi ko meye shi in ba ki in har ina da shi. Na ce "Ai ba komai bane ilah kishiya, domin na san ko badade, ko ba jima sai ka karo aure, kaga kuwa ai ka 59 yimin kyakkyawan sakamako." Ya yi murmushi ya lakuci hancina ya ce "Kin ganki, ba ki da dama.?" na ce "Ai sanin halin ku na yi na maza." Ya ce "Ya ya akai kika sa ni.?" na ce "Ai halinku ba boyayc bane, kowa ya san shi, kuma in kun kai dubu halin ku daya ne." ya ce "Na alheri ba.? Ai kuma matan haka kuke, ku waye ma ya kaiku halin tsiya." Na ce "Uhm. Yanzu fa ka gama yabona, amma tun kafin a je ko ina ka far kushe mata" "Ai wannan hali na ku sai dai a ganki da shi a kyale." "A'a banda sharri, domin mu ba mu da wani hali sai na alheri.?" Na yi dariya "Haka ne yabon kai." Ya ce "A'a. ba yabo kai bane." na ce "A'a to. ni dai maganar kishiya babu ita." ya yi dariya ya

Chapter 4 of 5