Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 3
babu. Ta nan ta gudu a tunaninsa. Amma ba haka abin yake ba!Tun daren da aka kulle ta aljanin ya dauke ta, shi ya fasa silin din don ya bar wa Malam Iro shaidar kulle ta da aka yi ba shi ne mafitar hana ta yawon da ya assasa mata ba. A daren Fauziyya ta samu kanta cikin gararamba ba tare da ta san inda kanta yake ba, saboda a lokacin aljanin ba ya tare da ita, shi da ma burinsa kawai ya fito da ita ya sa ta yin yawo ba madosa. Tun da Fauziyya ta taso a rayuwarta ba ta san wani abu wai jin dadi ba, koyaushe cikin kuncin rayuwa ta ke, wannan yana damunta matuka, musamman yawan zamanta a gurin 73 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR najasa, tana takura ainun, don dai babu yadda za ta yi ne. Da ta samu lafiya na tsayin shekara har kiba ta yi saboda kwanciyar hankali, amma tun bayan dawowar matsalarta ta fige, ta rame, ta kasance cikin kuncin da ya fi na da muni. Idan Fauziyya za ta zagaye fadin garin Katsina tana yawo ba ta jin za ta iya zama na minti biyar da sunan za ta huta, saboda koyaushe tana jin sha'awar ta yi ta tafiya, diddigenta a hanya suke, kuma a cikin duhuwa. Sai dai ta kan samu kanta cikin raunin gajiya, amma zuciyarta ba ta ba ta shawarar ta zauna ta hutan. Na san za ka ce ba ta taba haduwa da jami'an tsaro ba? Sun sha ganinta, amma suna yi mata kallon mahaukaciya tuburan, 74 SUNANMU DAYA-2 VAJNOOR saboda yadda ta ke shiga duhuwaba tarc da tana jin tsoron wani abu ba, musamman kowa ya san yadda shukoki suka yi yawa a gefen gari A King paradisc hotel da ta biyo a duhuwar ma ta ke bi, maimakon ta bi siririyar hanyar da akc amfani da ita,mutanc masu tafiyar Kasa, babura, ko motoci, amma ita sai ta yanki daji ba ruwanta. A wannanranaamummunan al'amarin ya faru da Fauziyya, misalin karfe uku da mintocitna dare ta biyo hanyar da akc amfani da ita,da yake ranar ana ajon wwata kilaki sa Hirji, wannan ya sa king paradisc ba ta yi cikar dangon da aka saba yi ba, tun kusan karfe daya ma sawu ya fara daukowa. Fauziyya na tafe cikinrangajin tafiya, wani matashi da ya fito daga king 75 SUNANMU DAYA-2 VAJNOOR paradisc cikin motarsa Toyota fara mai lambar Mashi ya zo gurinta a tunaninsa tana cikin karuwan da ke baza hajarsu a gurin. Ya kashe motar bayan ya dallare mata fuska da hasken fitilar motar. Ya isa gurinta yana yi mata magana, ta yi masa shiru ta ci gaba da tafiya. Bai yi wata-wata ba, kawai sai ya rungumcta a kirjinsa, ita kuma ta wanka masa mari dolc ya sake ta yana kallonta galala. Yayin da ta ci gaba da tafiya ya kasa jurcwa ya kai mata cafka a karo na biyu. Nan ma ta wanka masa wani marin, abin da ya sa ya kasa kai zuciya ncsa kcnan, yana ganin a matsayinsa na babban yaro ya za a yi karuwa kamar wannan ficikar ta marc shi har sau biyu? Wayc ubanta a kasar nan? 76 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR Kawai zuciya ta ja jagorance shi sakarwa shaidan linzamin zuciyarsa ya shige motarsa ya murjc ta. Sanadin kenan, ko shurawa ba ta kara yi a gurin ba, ajali ya riske ta ta sanadin zafin zuciyarsa da ya biyc wa ya aikata danyen hukuncin da ya zamo tarin nadama". Labiba na zuwa daidai nan a labarinta sai ta rufe bakinta tana kallon Abidu wanda tuni gumi ya gama jikc shi sharkaf. Та сс, "Duk wanda zai ba ka wannan labarin, ai ka san ya wuce duk inda ka kc tunani. Na san yanzu ka fahimcc wacc ce Fauziyya, da wanda ya kashe ta". Shiru Abodu ya yi yana ambato. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un די SUNANAM DYE VANOWOR A cikin zuciyarsa, tabbas wannan labari da Labiba ta ba shi ya kidima shi, kuma ya yarda HAKKI NA BIBIYA! Kafin ya yi magana Labiba ta ci gaba da cewas "Ba wasu ba ne bayin Allah da suka tsayu da taimakkon Fauziyya ba face ni da Abid. Mun kasance eikin tsananin jimami yayin da muka samu labarin mutuwar Fauziyya, to amma ba mu da yadda za mu yi tunda Ubangiji ya fi mu sonta, kuma Shi ya ara mana lokaci har muka taimake ta a baya. Bayan mun dawo daga dogon zangon da muka yi ne muka bibiyi sanadin mutuwar tata, duk abin da ya faru tsakaninku ya bayyana a gare mu, Kuskure daya aka samu Abidu, lokacin da ka aikata wannan danyen aiki khtESΓΠ SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR babu wanda ya ganka sai Ubangijin da Ya chalicce ka, kamanta da Shiyana ganinka, da ka tabbatar mutuwar tata sai ka janye gawar tata yadda za ka samu hanya ka tafi, abinka ba ruwanka baine da yi mata gatancin sada ta da wadanda za su suturce ta su kai ta makwancinta. 02.Amma saboda wannan shi ne karo na farkó da ka taba yin kisan rai, sai zuciyarka ta kasa zamaslafiya, daga lokacin ne ka daima nyawon dare, ка tuna?' m u olob ad sd sy sn sl Nan ma ba ta jira cewarsa ba, ta ci gaba.s Tewntiel sb silk 2 sd ide "Damuwar da ka shiga ita ta sa ka tuba daga rayuwar barikin da kakc yi a boycomahaifanka ba su sáni rbat wanda shi ma mahaifin naka yanadda tasa matsalar sidansth. takaswrawasb wajen rugujcwar rayuwaryalyansa. Wato ya 79 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR kasance mutum mai tsinuwa da cire albarka ga wanda ya 6ata maimakon ya yi masa addu'ar shiriya kamar yadda Ma'aiki (S.A.W) ya fada mana a ingantaccen hadisi, Ka fadi alkhairi ko ka yi shiri. Da yake ba labarin mahaifinka zan ba ka ba, wannan matsalarsa ce, ina so ka sani shi ma ya taka rawar da yanzu yake nadamar duk 'ya'yansa babu na gari, to in bacin abinsa, ka tsine wa wanda ya 6ata ba dole shi ma ya batar da naka ba idan ya samu sararin tunda shi ba ka san illar da tsinuwar taka ta janyo masa ba. Bayan ka daina yawon darc wanda kakc tunanin ka yi tsarkakkiyar tuba, ka binnc abin da ka aikata ba tare da ka sanar da kowa ba ballantana a je ga maganar yanke maka hukunci. 80 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR Bari na kawo maka wata fatawa, ko kuma na ce ingantaccen hadiso da ke magana akan abin da ka aikata da hukuncinsa. 'An karbo daga Abi Bakar dan Muhammadu, dan Umar, dan Hazami, daga babansa, daga kakansa Allah ya yarda da su, 'Hakika Annabi (S.A.W) ya rubuta zuwa ga mutanen Yaman, sai ya ambaci hadisin a cikinsa cewa, 'Wanda ya nemi mumini da kisa ga kuma hujja za a rama, sai idan waliyansa suka yarda wa wanda aka kashc, kuma hakika a cikin rai akwai diyya, da rakuma dari, a cikin hukuncin hanci, idan aka aibata halittarsa, akwai diyya a game da ido biyu, akwai diyya a game da zakari, akwai diyya a game da fatar baki biyu, akwai diyya a game da zakari, akwai diyya a game da gwaiwa biyu, akwai 81 SUNANMU DAYA-2 AJNOOR diyya a gamc da tsatso, akwai sulusi diyya a gamc da jaifa, akwai sulusin diyya a game da munakkila, akwai rakuma goma a game da hakora, akwa rakuma biyar a game da mudiha, akwaj rakuma biyar kuma ana kashe namiji idan ya kashe macc. Amma game da masu amfani da dinari akwai dinan dubu". (Abu Dawuda ya ruwaito shi cikin Mursal, kuma da Nisa'i da dan Khuzaima da dan Jamd da dan Hibban da Ahmad suka fitar da shi, kuma sun yi sabani cikin ingancinsa). Duba da wannan ingantaccen hadisin ya sa muka ga dacewar shiga cikin lamarinka don mu haska maka idan ka zamo mai kwadayin kyakkyawan sakamako, to ka yi cikakkiyar tuba ta ba wa shari'a dama a fidda hakkin rai da ka yi da kisan 82 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR ganganci kamar yadda wani ingantaccen hadisin yake fada. 'Diyya ita ce hakika talatin da kuma jaza'a talati, da kuma khalifa arba'in, wacce a cikin cikinta akwai 'ya'yanta". (Hadisin Hasanun ne). Abu na farko da muka fara duba a tare da kai Abidu shi ne, ka kasance masanin ilimin addini, amma saboda kwadayin da kyallin zaman duniya ke maka yawo a zuciya ya sa kana son 6ata lahirarka, sai Abid ya kawo shawarar yadda za mu dinga haska maka cewa, abin nan fa da ka yi tuna ka binne, dole akwai diyya a tare da kai. Kun hadu da Abid a masallaci kana tunanin ka taba ganinsa, sam ba ka sanshi ba, hikimar dai jan hankalinka ya sa aka yi maka wannan tsarin yadda za ku hadu. 83 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR 1 1 1 A abin da ya yi na canko aya da surar da kake karantawa a cikin zuciyarka, da kuma kin fitowarsa yayin da masu hidimtawa masallacin suka shigo sun isa su tabbatar maka shi din ba mutum ba ne. A ranar ya sake bayyana a gare ka a wajen gidan Amadi Kurfi yana shaye. shaye, wai a nan ana nuna maka mutum a fuska ba mutum ba ne, wato ka ga kai duk wanda zai ganka a masallaci yana kyautata maka zato, to a bayan idon wasu kuma za ka iya kauce hanya kamar yadda Abid ya nuna maka. Maimakon ku yi haduwa ta uku da Abid, sai muka hadu da kai a shagon Shehu Boss, wanda tun fil'azal cinikayya kan hada mu idan za mu yi wa marayun Allah (Mutane) sadaka, na ba ka labarin wata soyayya mai ban 84 - SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR al'ajabi a shagon. Kai da jin labarin soyayyar ai ka san idan dai ba irin labarun hikayoyin din nan ba da ake kirkira to zai kasance a mafarki, don ko mu a jinsinmu ba ma irin wannan soyayyar ta sadaukar da rai har a fita haddin addini, wato kadaituwa irin lokacin da na ce maka Abid da Sumayyah na yi. Hikimar ba ka labarin nan ma a kuma jan hankalinka, ka gane wani kulli idan aka yi shi zai yi wahala a warware shi cikin sassaukar hanjya. Duk abin da muka yi a gare ka babu zalunci, illa taimako da muka yi maka, ka sauke nauyin hakkin da ke tare da kai tun kafin guri ya kure maka, ka rasa hanyar tuba. Haduwar Abid da Salman abokinka a Kaduna, ba ta nufin komai 85 ANOXA 1 1 SENANME DAYA-2 illa ana so Salman ya kawo ma labarin da zai rikitar da kai, wata kila iya tsinkaye da abin da ake so ka fasa Amma haduwarsa da Nazeert nufin kulla wani zaren da za a hask maka wani abu na cewar, ba SUNANKU DAYA ne kadai ab mamaki ba, a'a dalil KAMANNUNKU DAYA. Na farko ba ka san sun hadu har sun tattauna za su sake haduwa? Luna Hotel don a tunatar da kai yawo daren da ka yi har ka aikata laifin kisan bayan kun gama wayar da Nazcer, Abi ya bayyana a gare shi da nufin kai di ne, ya kuma ba shi hakuri. Kafin ka iso Luna din har sun rab kowa ya kama gabansa, don haka da ka zo ba ka tarar da Nazeer ba, shi kuma tunda ya san kun hadu a darco shi ya s 86 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR da ka je washegari ya ga ka raina masa hankali. A washegarin ranar mun hadu da kai gurin karbar dinki, haduwa ta biyu ni da kai, tun a lokacin na so jan hankalinka don na fara kyankyasa maka abin da ka binne yana ta yaduwa da mugunya a rayuwarka, amma sai ka kawar da gabar da na kamo da nuna min daukar zafinka, wanda da ma na san duk abin da ka aikata can bayan dokin zuciya ne, don ka kasance mara sassaucin zuciya ta wajen sanyaya lamuran da ga66an jikinka za su aiwatar. Saboda haka ni ma sai na shashantar da lamarin muka yi hira kawai muka rabu. Kamar yadda ka sani kai din mai laifi ne ta kowanne 6angarc, sai muka 87 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR 1 ga yuwuwar gwara mu fidda wa mahaifanka jin idan babu kai za su samu nakasu ta bangaren soyayyar da suke maka, saboda ko da hukuncin kisa zai 1 hau kanka abin ya zo musu da sauki ba kamar yadda mahaifan naka suke matukar girmama kaunarka har sukan dauke ka da girman daraja fiye da sauran yaransu. Wannan ya sa Abid ya yi shigar Alhaji Sani Kafinta ya je wa mahaifinka da labarin ya ganka ka shawo barąsa! Eh ai ka sha barasar, amma ka dąina. Hakan ba yana nufin an zalunce ka ba a wajenmu illa yadda na fada maka za a cire maka tsammatar ci gaba da rayuwa a gurin mahaifanka. Koda yake daga baya akwai wasu shehunan Malamai da suka kalubalance mu a kan abin da muka yi ba taimako ba 88 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR nc, zalunci ne, sai dai duk da haka ya zamo darasi ga shi mahaifin naka mai aibata 'ya'yan al'umma. "An karbo daga Aishatu Allah ya yarda da ita ta ce, "Lallai Manzon Allah (S.A.W) ya ce' 'Shin ana yin ceton haddi, daga haddodin Allah?' Ya tashi ya yi huduba ya ce, 'Ya ku mutane an halaka wadanda suke kafin ku, domin sun kasance idan wani daga cikinsu mai daukaka ya yi sata sai su bar shi, idan wani daga cikinsu mai rauni ya yi sata sai su tsaida masa haddi". (Bukhari da Muslim suka ruwaito shu). Je ka a nan mun yi kuskure, ai mu ma ababen halitta ne, dole a same mu da kuskuren, kuma muna neman afuwarka a wannan gabar! Sai maganar dattijo mai 'ya, wadda ake tuhumar ka yi mata ciki, shi ma an 89 1 1 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR kawo shi ne don a rikitar maka da tunam ka tuna da wancan hakkin. Bayan su kuma an kawo Naz da Abdulmalik abokanka mам tuhumarka da laifin kisan rai. Idan k nutsu tsaf za ka gane, suna so ne ka amsa laifin ka yi kisan kai cikin ganganci, amma ka ki amsawa, wata kila don kana ganin sun biyo maka da kashe wasu mutanen ne maimakonr daya tal da ka ke ganin bai kai daraja ka yi asarar naka ran dominsa ba. Da ka koma gida ka samu labaris zuwan Nazeer, tun a nan ya kamata ka gane wadancan da ka fara haduwa da jinnu ne, tunda ga shi an sanar da kai Nazeer din ya fi awa biyu a gidan yana jiranka. Sannan ka tarar da I.D card dinka a inda ka ajiye shi a cikin dakinka 90 SUNANMU DAMA-2 NAJNOOR amma duk wannan baiisa ka yi wani abu a kai na abin da ake haska maka ba Mu dawo fangare Rukayyah wadda ka gansu da Abid, ka zo gidansu ta fito kuka yi magana ta ce tas rabun da kai a kan ka dauke ta kana neman 6ata: mata rayuwa. Ba asalim Rukayyan ka ba cс,. saboda mun san darajar mutumei, kuma mun karbi wancan gyaran da aka yi mana na kuskurc, don haka muka guji aibataka a gidan ko da kuwa ba ka da rabon aurenta! Sam Rukayyah ta asali ba ta da masaniyar abin da ya faru daga haduwarku a kofar Marusa zuwa lokacin da ka aika kiranta. Wannan shi ne abin da ya kawo ni gare ka, na kuma sanar da kai abin da ka binnc. 91 1 1 SUNANME DAYA-2 NAJNOOR Muna neman afuwarka ka yafe mana kuskuren da muka yi maka. Sannan muna tunasar da kai, duk abin da ya faru tsakaninmu da kai fadakarwa ce ga al'umma, domin akwai icri-irinka da sukan aikata laifin kisan kai cikin ganganci, amma su binnc ba tarc da sun bayyana ba, saboda kawai kwadayin zaman duniya, ba sa ko tunanin yanzu, anjima, gobe ko jibi za su iya mutuwa. Misali kamar kai in bacin mun san lamarin Fauziyya wanda uwarta ta ja mata da ba mu shiga lamarinka ba, wata kila da haka za ka karc rayuwarka ba tarc da ka bada damar fitar da hakkin rai a garc ka ba. Da wannan nakc maka fitan alkhairi Abidu, ko ka kai kanka ga hukuma a fitar da hakkin rai a jikinka, SUNANMUDAYA-2 NAJNOOR ko kuma ka zauna da hakkin. Sai dai ka sani, ko ba ka samu irinmu ba masu son gyara al'umma ba, za ka iya haduwa da jafa'i kala-kala don ahkkin rai ba Karamar musiba ba ce ga wanda alhakin fitarsa ya rataya a kansa. Wasu za ka riske su cikin kuncin rayuwa koyaushe. Wasu kuma duk zafin neman da suke ba ya amfana musu komai. Wasu cuta ake jarabtarsu da ita, ka ga dai sun kar wani don su su sake, amma ciwo ya hana sakewar. To a irin wannan mcne ne riba? Ва gwanda mutum ya tsaya da gaskiyarsa ba, don ya kwadaitu da kyakkyawan sakamako ba?" Idanun Abidu sha6c-sha6c da hawaye ya dago kai, murya a raunane ya cc. 93 SUNANMU DAYA-2 AJNOOR "Wallahi na gode da wannan taimako da kuka yi min, na kuma yafe muku duk abin da kuka yi min bisa kuskure. Tun daga yanzu ma ina mai yi miki albishir zan kai kaina ga hukuma cikin biyu a yi daya, ko dai na biya diyyar rai da dukiya, ko kuma a kashe ni duk yadda ya samu zan yi farin ciki, muddin zan gyara kurena zuwa lahirata". Labiba ta yi murmushi, ta cc. "Na ji dadi sosai Abidu: da ka fahimci rayuwa. Ina kuma sanar da kai zan yi kokarin hada ka da mahaifin Fauziyya wanda har yanzu yake kukan mutuwarta. Saboda bayan ka barta a inda ka murje ta da mota, hukumar 'yan sanda suka tsinci gawarta suka yi sanarwa, har 94 a At a Su aj a Ka Ka SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR shi Malam Iro ya samu labari ya je ya karbi gawar tata yana mai kokawa da ta mutu a cikin gurbatacciyar rayuwa. Daga baya ne na yi shigar bil'adama kamar yanzu, na je na yi masa gamsasshen bayani game da lalurar Fauziyya a matsayina na aminiyarta, na nuna masa ma ai a gidanmu ta ke zuwa duk lokacin da ba ta gidansa, sai ranar da lalurin zai faru ne ma ciwon nata ya taso ta fita. Na yi masa kuma alkawarin zan taya shi addu'ar Allah ya bayyana wanda ya yi kisan, don na fada masa akwai wanda nake zargin shi ya aikata hakan a gare ta". Abidu ya goge hawayen da ke idanunsa, ya ce. "Idan ba damuwa Labiba ki hada ni da shi mahaifin Fauziyyan a yau din 95 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR nan don na yi alkawarin ba za a kwana ba sai na kai kaina ga hukuma". Labiba ta tsura masa idanu, lokaci guda tsananin tausayinsa ya shige ta, ta ce. "Ba damuwa don wannan, sai dai ka san me?" Ya girgiza kai ba tare da ya yi magana ba. Ta ce, "Kafin ka damka kanka ga hukuma, zan yi maka wani taimako na gyara tsakaninka da mahaifinka, gudun kada idan ya ji wannan labarin ya yanke maka BAHAGON HUKUNCI, ma'ana ka yi tuban da kake neman rahamar Ubangiji, amma ka rabu da shi yana mai tsananta fushi da kai, wanda mu ne sanadi". Ya ce, "Idan kin yi hakan ma kin taimake ni, kuma zan ji dadi, ko da 96 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR hukuncin kisan ya tabbata a gare ni na san zan samu addu'arsa". Suka yi shiru su duka, kan Labiba nakasa tausayin Abidu na kara shigarta, shi kuma yana ji a ransa kamar ya fi kowa sa'ar rayuwa, tunda har yau aka tono masa abin da ya binne har aka nuna masa hanyar tuba ta gaskiya ba irin wadda ya yi ba. Lallai wannan ya fi komai dadi a gare shi, ba ya kaico don hukuncin kisa ya hau kansa! BAYAN SHEKARU SHA SHIDA Alhaji Abidu Nasir Barhim yana zaune a katoton falonsa da ya gama haduwa da kayan more rayuwa, Hajiya Rukayyah tana daga gefensa dauke da turtsetsen cikinta haihuwa yau ko gobc. 97 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR Muhammad dan shekaru goma ya shigo falon rikc da hannun wani yaro wanda shi ma ba zai wucc shekaru goman ba. Sun taso ne daga makaranta. Alhaji Abidu ya dubi Muhammad da murmushi a fuskarsa ya ce. "Muhammad ina ka samo aboki?" Muhammad ya sake riko hannun abokin nasa yana dariya ya ce. "Daddy dan makarantarmu ne wanda na ke fada maka SUNANMU DAYA da shi". Da sauri Alhaji Abidu ya dubi Hajiya Rukayyah kamar yana son tuhumarta wani abu, amma sai ya basar ya maida duban nasa ga Muhammad ya ce. "Shi ma sunansa Muhammad a kenan?" Muhammad ya kada kai, ya сc. 98 Sa SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR "Eh Daddy, sunansa Muhammad Abid Nasir!" Gaban Alhaji Abidu ya sake faduwa, ya tsura wa yaron idanu, yana tuna abubuwan da suka faru da shi can baya, wato lokacin da ya 6oye laifin da ya aikata. Wanda bayan ya kai kansa kotu, kuma Labiba ta gayyato Malam Iro mahaifin Fauziyya, tun kafin a yi zaman kotun ma Malam Iro ya ce shi kam ya yafe wa Abidu abin da ya aikata, yana fatan hakan ya zamo darasi ga na 'yan baya. A lokacin da kotun ta zauna kuma aka yanke wa Abidu adadin abin da zai biya diyya kamar yadda shari'a ta tanada, sannan aka umarce shi yin azumi sittin na kaffara. Tun daga lokacin ya samu kwanciyar hankali, komai ya kwaranye, 99 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR har shi kansa mahaifin nasa sai da ya yi sanyi lokacin da ya ji abin da ya faru da Abidun, har ya huce da fushin da yake da shi, mafarin kenan ya shiga cikin lamarinsa har aka sanya ranar aurensa da Rukayyah, lokaci kuma na yi aka yi auren. Yanzu shekarunsu goma sha biyar kenan, suna da 'ya'ya hudu, Labiba ita ce babba, wadda suka yi wa aljana Labiba takwara, sannan aka haifi Muhammad, sai Aliyu da Nafi'u. Yanzu kuma ga cikin na biyar a jikin Hajiya Rukayyah. Alhaji Abidu ya sauke gwauron numfashi, cikin kada kai ya mike tsaye a cikin zuciyarsa yana maimaita kalmar. "SUNANMU DAYA”. MASHA ALLAH 100 AgV SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR Abin da muka yi kuskure Allah ya yafe mana, wanda muka yi daidai Ya hada mu a ladar. IYAYEN YUSUF Nura Sada Nasimat Kt Da Naja'atu Haruna Sale Ke muku fatan alkhairi. SAKO Tabbas Ubangiji shi Ya sanya dan Adam ya zamo khalifansa a ban kasa don haka koyaushe bawa ya riki gaskiya tare da kyakkyawar rayuwa. Ka zama mai SADAUKARWA wajen neman bautar Allah, kar ka sanya wasu-wasi ballantana kayi tunanin INA HUJJAR TA KE? Don kar ka shiga WUTAR DAJ darrada karsheka 1011 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR BAHAGON HUKUNCI, amma fa RASHIN JINI bai sa a gano SUNANMU DAYA ba don rayuwa yanzu ta zamo KAZA DA HATSI. Daga alkalamin. Aminu Malami Muhd KADAN DAGA WUYAR SABО Та сс, "Wallahi Abba ne ya kori Yaya Murtala". Das! Na ji gabana ya fadi, gaskiya ban so hukuncin da Abba ya yanke masa ba, sai na ji da ma na ce eh a kan maganar da ya fada. Ban ankara ba na ji hawaye na bin kumatuna, Asma'u ta се. "Aunty kukan me kikc yi ne? Na dauka abin da Abba ya yi daidai ne? Idan 102 SUNANMU DAYA-2 NAJNOOR kika tuna cin mutumcin da ya yi miki... To me ye naki na zubar da hawayenki a banza?" Na jawo hankici Na sharc hawaycn da ke bin kumatuna, na ce da ita. "Kada ki damu Asma'u, ba wai na ji zafin abin da Abba ya yi masa ba nc, kawai na ji ya ba ni tausayi". Daga nan hirar ta tsinkc, inda Asma'u ta tashi ta bar ni a falon. Darc ya yi shiru ban ji aikc na zo inji Isma'il ba, har misalin tara na dare, saboda haka hankalina ya matukar tashi, na sa hannu na janyo wayata na duba asusun, ko Kwandala babu sai wasu kobbai. Na ja dogon tsaki, ko me Isnar yake nufi nc, ko ya yi fushi nc? Ban san lokacin da bacci ya dauke ni ba, misalin karfe sha biyu da rabi da minti biyu sai ga wani yaro ya shigo gidan ya 103 SU NANMU DAYA-2 NAJNOOR kawo takarda wai in ji wani ya ce a kawo min. Na kara cikin zumudi, don na san ba ta wuce ta Isma'il. Na bude don na karanta, sai na ga rubutun kamar ba nasa ba, amma haka nan na daurc na soma karantawa. Kin ga Fatima, ni fa ba karamin yaro ba nc bare ki ba shi alcwa a baki, ko kin dauka ban dauki haske a kan abin da ke tsakaninki da Murtala ba? to ki sani ki kuma dada sani, tuni na soma bincike a kan al'amuranki. MARYAM HASHIM. ALIYU WAMAKO tul Littattafan marubuciyar:- RASHIN JINI SADAUKARW INA HUJJAR TAKE! KAZADA HATSI WUTAR DAJI. SUNANMU DAYA BAHAGON HUKNCI DAJL.s F ancy Printing & Publishing Co S/Unguwa, K/Dorawa, Katsina. 07027048439, 08131994808, 08095052216 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 3 of 3