Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 4
yarinyar nan ba ma zai iya jurewa wannan tsallen bataken ba, ya zama dole ya hadata da ubanta duk ma wacce za a yi a yi domin hakurinsa ya kai bango. Ya juya ya koma nasa dakin Uzaifa yana kwance a dakinsa ya lulluba da bargo mai taushi yana chart da abokinsa a waya ya dinga jin wani irin sauti numfarfashi da shissheka ya soma nazarin daga inda yake jiyo wa wajan window sane na waje sannan ya mike yana 82 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 nazarin to mutum ne a wajen ko wata dabbarce. Cikin wannan ruwan da fargaba ya isa wajan sannan ya kunna fitilar wayarsa wani dogon tsaki yaja yayin da ya haske fuskarta da fitilar wayarsa duk da ta sa bayan hannuwanta biyu ta rufe fuskarta saboda kashewar da haske ya yi wa idonta hakan bai hana shi gane ko wacece ba saboda kayan taба gani a jikinta yanzuma su ne a jilkinta ga yanayin girmanta "Ke me ki ke yi a nan?" Ta sauke hanmnta da ba muryar da ta yi tsammanin ba ce 83 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ita ma ta gane shi bakinta na rawa ta ce "Uhm! Uhm koface ta ki buduwa" "Ba sai ki yi magana daga ciki a bude miki ba". "Na yi ba'a bude ba, mu je bai saurareta ba ya yi gaba tana binsa a baya har zuwa kofar dakinsa. Kofar da zata sadaka da falo ya budemata sannan ya kirata Zo ki shiga ta nan. Ta dai bi zabin sane saboda gigicewa da sanyin ya sa ta yi badon ta san in da yake nufi ta shiga ba, sai da ta shiga ne ma ta gane a babban falon take sannan 84 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ta yi saurin shiga dakinta da ta ga har lokacin dakin abude ma yake. A wannan rayuwar sadaukarwa da Alhaji kai shi ne kawai mafita a cikinta domin yanzu ta gama saduda matukar kadai take gani tafi dacewa da ita. Shine dalilin da yasa ta kasa rufe kofarta ta kudunduna har lokacin tana rawar sanyi kwallah na zuba daga idonta nan da nan zazzabi me zafi ya rufe ta addu'arta Allah ya sa zazzabin ya zamo ajalinta ta huta da wannan zulumin rayuwa. Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ** Lawan ya yi shirin fita tsaf yana saka hula asabe ta tsaya a bakin kofar dakin ganin yana shirin fita ya sa tacewa "Na gaya maka fa shinkafarmu ta kare, kuma wannan kudin ma da ka baya ba fa za su isa cefane ba". "To ai shi yas ana baki dari biyar din ki siyi duk abin da za ki " siya a ciki. A cikin naira dari biyar din zan sai shinkafa na sai kayan miya, na sai magi da mai to wallahi da sake domin sam ba zai isa ba." 86 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 "Wai ke wane irin rashin hankali so ki yi ina ki ka kai shinkafar buhu guda ko sati bata yi ba, kun zo kina so ki mai da niw ani marar hankali. Asabe bata san lokacin da ta lailayo wani ashar ta maka ba "Mai kake nufi da abin da ka fada, ka dai san ba daga gidan tsiya na fito ba bare ka се gidanmu na kai. Shinkafar da ke kawo a ka yi abincin wuni biki sannan muka ci gaba da ci har kawo wannan lokacin, in ba ka ce min sambarka ba aikwa ba zaka kushe min ba" 87 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ya ce "Sambarka cuta da ha'inci". Ya yi ficewarsa ya barta tana ta sababi. In bayan kar ace da ga yin aurenta ta fara korafi da sai ta kai kararsa gurin manya, domin dai ita ba za ta laminci zargi da cin mutumci ba. Duk abin da yake faruwa a kunne Asiya da Umaima ya yin da suke shirin tafiya makaranta domin duka duka karfe bakwai ne na safe. Ta na ta wannan mitar a tsakar ida suka gama shiri su kai mata sallama sun fito suna tattauna abinda yafi damunsu 88 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 rashin sanin halin da 'yar uwarsu Hansa'u ta ke ciki sun damu kwarai har suka nuńa sha'awarsu ta son zuwa gidan. Su ka gayawa Asabe amma daren jiya take gaya musu abin da Babansu ya fada da tai masa magana, wato gargadin mijin Hansa'u a kan cewa to shi fa baya son ana masa zirga zirga a gida, idan ta kwana biyu da kansa وو zai kawota gidan ta gansu". Su dai wannan hukuncin bai musu dadi ba. Tun jiya suke tunanin yanda za su bi a zancen da Asabe ta yi musu suje gidan, suna kewar Hansa'u matukar kewa Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Sun yanke shawarar idan sun taso daga makaranta za su taka da kafafuwansu su bi kwatance, har gidan Hansa'un don su ganaota. Hakan kuwace ta faru domin suna ganin in har suka bari suka koma gida toh basu da wani lokaci na kansu da zasu iya fitowa batare da Asabe ta sani ba, haka su kaita tafiya har suka zo kofar gidan sai dai da ganin tsarin gidan ma kadai ya kada hantar cikinsu, suka fara tunanin ta ina ya dace su bi domin su samu su shiga. Sun tura kofar gate din a rufe take gam gam. 90 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Asiya ce ta dubi Umaima "To ko mu kwankwasa?" Ba ta ce mata komai ba, sai ma ita din da ta soma kwankwasa wa. Maigadi ne ya leko ta wata 'yar kofa "Kai yaya what 99 happen". "Da ganinsa ma ba bahaushe ba ne suka kasa ba shi amsar tambayarsa, har sake nanata musu da gurbatacciyar hausarsa ya yi "Me ku ke so?" Su ka yi shiru suna kallon juna. Asiyace tai karfin halin cewa "Wajen Hansa'u muka zo". "Waye Hansa'u anan?" 91 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Umaima ta ce "Amarya ta nan gidan ta Alhaji". Maigadi ya rufe 'yar karamar kofarsa "Kai ku tafi Alhaji bai ce wani zai shigo ba" Sun ji rufe kofar tasa kamar saukar aradu a tsakiyar kansu. Ga koshi ga kwanan yunwa basu sha wahala wajan gane gidan ba amma shiga gidan ya gagare su. Haka suka zauna kan wani tudu cike da sarewa ga yunwa ga gajiya. Daga karshe dole suka ta shi suka koma gida. 92 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Duk yanda Lawai ya za ci samun sauki daga Alhaji Ahuta lamarin na neman canza tunaninsa domin 'yar kyautar da ya ke yi masa ta bajinta, tun da Hansa'u ta tare ya make hannunsa, ko haduwa suka yi da shi gaisuwace kawai ke shiga tsakaninsu. A cikin kwanakin ma sai ya bijiro masa da wani al'amari da ya girgiza shi wai su ta shi daga wannan gidan su sami wani su kama, shi zai biya kudin shekara, wannan gidan da suke ciki ya na so ya gyara musu shi sosai ya dora musu bene. 93 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Hankalin Lawai ya ta shi kwarai domin ya shiga tunanin cewa anya kuwa Alhaji ba yaudararsu yake son ya yi ba ya tashe su daga wannan gidan. Sai dai dole ta sa ya amsa da toh, tunda ba shi da hujjar jayayya da shi a kan abinsa. Tun dare yake tunanin hanyar da ya kamata ya bi ya fadawa Asabe maganar tashinsu ya rasa, domin ya kula da Asabe kwata kwata ba ta son babu, ba kuma ta yarda da kaddara ba, ba kuma ta da hakuri bare lamuni. Tun da ya yi mata karyar cewa gidansa ne bai san hukuncin 94 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 da za ta dauka ba, idan ta ji dama gidan sirikin sane. Yana tsaka da wannan tunanin ya dinga jin ana buga kofar gidan bam ban kamar za а 6allah. A fusace ya mike ya na cewa wai waye ne zai ballan kofa. Asabe na ceaw Je ka dai ka ga ni wannan irin bugun haka da sassafe, sai kace name bin ba shi". Yana budewa ya yi tozali da Alhaji Ahuta. Gabansa ya yi wata irin faduwa domin ganin yanda fuskarsa ta nuna tsananin 6acin Hadiza Ado Yalwa Garari 2 rai, ya mika mas ahannu suka gaisa. "Karar yarinyar nan na kawo Lawa don na ga ji da rashin da'a da tarbiya da take nuna min, ka ga dai kaunace tasa na tsallake mata da yawa na zo na nemi auranta, amman ace yarinyar nan na guduna kamar kare, tunda na auri yarinyar nan fa ko inuwa daya ba mu taba zama ba, bare wata magana ko wani biyayyar aure a tsakaninmu" "Subhanallahi" in ji Lawai ya soma ba shi hakuri "Kuruciya ke damunta alhaji amma ai ba ace 96 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 bata kaunarka ba bari na sa ko hula ta na je gidan na same ta" Alhaji na hucin bacin rai ya ce "To in hakan zai yiwu da dai yafi, domini ni shawarar da na yanke da ba mai dadi bace" Kalaman hakuri dai ya ci gaba da ba shi ya shiga gidan da sauri Asabe na tambayar abin da ya faru. "yar banzan yarinyar nan mana Hansa'u ashe halin banz atake gwada Alhaji aka kaita gidan". Asabe ta ce "Amma kamar ba zata aikata ba sai dai ina zargin 'yan uwann na nata kamar suna 97 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 satar jiki suna zuwa gidanta dan rannan daga zuwa makaranta basu dawo ba sai la'asar". Ya dora hularsa a kansa "Koma me suke kullawa dai dai na ke da su zan yi maganinsu bari dai na dawo". Duk abin da ake syi su Asiya na ji sai dai jikinsu ya yi sanyi da yanda aka yi Asabe ta gane sun je wajen Hansa'u kuma babansu ya ce zai dauki mataki a kansu, shin wani mataki zai dauka?" kowani mataki zai dauka ma sun san ba wanda zai musu dadi ba ne, domin sun fi kowa sanin halin mahaifinsu bai furta ba ma yana 98 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 daukar mummunan mataki bare ya furta". Haka suka fito suka tafi makaranta zuciyarsu cike da wasuwasi da fargaba. Zazzabi da ya hana Hansa'u rintsawa tun cikin dare har yanzu yana nan a jikinta musamman kanda da yake tsananin ciwo wanda da kyar take iya bude idanuwanta ta na ji a ka turo kofar aka shigo ta kasa bude idonta sai jin muryar Babansu ta yi a kanta ya na cewa. "To mutuniyar banza kin dauka wanda ki ka raina dinne shi 99 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 yasa kina jin ana yin sallama ki ka yi wa mutane banza" A firgice ta mike ta ja jikinta zuwa jikin gado. "Wato zuwa ki ka yi ki mike kafa ki rashin mutuncin da ki ka ga dama, wannan ba mijinki ba ne da ba zai ce miki ki yi ki yi ba, ki bari ki bari ba, har ki ke yi masa wani guje gujen banza da wofi" Ya dinga fada ta inda ya ke shiga ba ta nan yake fita ba, har ya soma kokarin dukanta Alhaji ya rike shi yana ba shi hakuri ya ce ai ma da laifinka da ba ka sa igiya ka daure ta iyalinka ce fa, kana iya yin duk yanda ka so da 100 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ita, lallashinta da ta ga kana yi ne yas atake maka abin da taga dama". Ameenu da yake girki a kitching duk hayaniyar da Lawai ya ke yi yana ji don haka ya fahimci duk abin da yake faruwa ya kuma tabbatar da cewa mahaifin Hansa'u ne. Kalamansa na karshe ne suka girgiza shi har ya kasa ci gaba da tsayuwar da yake yi, ya zauna ya rike kansa da hannu biyu. Hatta Huzaifa da yake bacci a dakinsa fadan Lawai ya farkar da shi daga bacci domin shi Lawai mutanne da bai iya magana 101 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 a hankali ba, gidan ya yi shiru muryarsa kawai ake ji. Hüzaifa ya ja dogon tsaki, ya mike zaune a tsakiyar gadonsa wai wane irin mutanene Alhaji ya yayibo mana ne baccin safen ma ace... Kalaman Lawai na Karshe su ka sa ya kasa karasa abin da yake son fada. Ya mike tsaye zuciyarsa ya ji tana son ganin wannan wane irin uba ne. Yana shiga kitchin din ya tarar da Aminu dafe da kai Kwallah na disa a idanuwansa. A iya zaman da ya yi da Aminu bai taba ganin hawayen 102 Hadiza Ado Yalwa Garari.2 saba irin yau, da hanzari ya Karasa inda yake ya dafa kafadarsa "Aminu me yasa ka kuka haka?" me ya şame ka?" Aminu ya dago tausayi ne Oga, wallahi tausayin yarinyar nan na ke ji”. Huzaifa ya dauke hannunsa daga kan kafadarsa yana 'yar gajeriyar dariya "To wai Aminu ko son yarinyar nan ka ke ne, ka damu da yarinyar nan, damuwar da ko danginta ba na jin sun damu da ita" Aminu ya dan yi murmushi yana share kwalla "In so ta in yi ya ya da ita oga tana matar aure 103 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 kuma in ma ba haka ba, kai ka san ina da wadda zan aura, kawai dai tausayinta ne tausayin irin na wanda ko wani mai kanwa ko 'ya ko kuma duk ma wat anasaba ta diya mace mai rauni zai ji shi a ransa. Daga nan ya dinga zayyanewa Huzaifa abinda ya sa ni game da ita tun daga zuwan mahaifiyarta binciken aure kawo yanzu zuwan mahaifinta. Ko rakiyar da Alhaji ya so ya yiwa Lawai dakatar da shi Lawai din ya yi ya ce ya yi zamans a dakin matar. 104 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ya kuma ci gaba da ba shi hakuri shi ma din tsayawa ya yi Lawai yà fita ya rufe kofa bugun rufewar kofar ya yi dai dai da bugun zuciyar Hansa'u, duk dai ta saddaka komai a yanzu dole ta bawa Alhaji kanta ba zata iya yi masa musu ba. Yanda Lawai ya fito a fusace ya na suratai yasa daga Uzaifa har Aminu binsa da kallo ta tagar kitchin din, har ya bace musu da gani Uzaifa ya girgiza kai "Yanzu kam ya fahimci irin abin da Aminu ya ke ji game da yarinyar lalle ne abar tausayi ce ya zama kuma dole zuciyar imani ta 105 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 tausaya mata domin bai taba ji ko ganin Uba irin wannan ba. Shi kam Da bai ji wani abubuwan da kunnensa ba da zai iya musantawa in fada masa a ka yi. Daga shi har Aminu sai da suka razana suka kuma kalli juna lokaci daya ya yin da suka ji Karar buga kofar da Alhaji Ahuta ya yiwa dakin Hansa'u sai dai babu. wanda ya iya furta kowace kalma a cikinsu kowannensu da abin da yake ayyanawa a ransa. Tunda Lawai ya shiga gidan ya shiga zaynawa Asabe abubuwan da yake faruwa. 106 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Sai da Asabe ta gama sauraransa tsaf sannan ta се "Amman Lawai da bari ka yi na je na same ta na tambayeta ko akwai wata matsalar na kuma lallashe ta ka ga har yanzu fa ita yarinyace". A harzuke ya ce "Ita din wa da za a lallasheta, ita ta haife ni ko ni na haife ta, kuma ko da ta ke yarinya ai ba dabba bace dole ta san mai kyautata mata, cikin yan kwanakin nan ba ki ga yanda yarinyar ta canza ba ta yi bulbul ta yi jawur da ita, idan borin nata bana iskanci ba ne na kuruciyane ta yaya zata iya mike kafa a 107 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 gidansa ta dinga cin mai kyau tana shan mai kyau bata guje abin hannunsa ba sai shi. ni na san daga in da matsalar take kuma zan yi maganinta, wannan munafukar yayar ta su mai halin uwarta Asiya ita take zugata, tun da ki ka fada min tana zuwa gidanta hankalina bai kwanta ba. Ranar ko fita bai yi ba har sai da su Asiya suka dawo, daga ita har Umaima ba wadda ta cire kayan makaranta, ya rufe gida, ya fito da bulala, dukkansu sai da ya zane su tsaf, sannan ya ce daga yau sai yau kar ya kara ganin wata ta fita daga gidan nan da 108 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Nufin zuwa wata makaranta wadda ake fakewa da ita atafi yawon banza, hankalin Asiya ya tashi wadda kwanaki yarage suyi jara bawar Cikin muryar kuka tace baba dan Allah kayi hakuri kwanaki yarage nagama karatuna, ya ce tayi saurin shan gabansa tana rike bulalar tana cewa dukan ya'isa haka, shikuwa jikinsa har tsumo yake yake nizan fadi magana kina mayar min da magana banda rashin sanin ciwon kai yaushe dibga dibga daku zaku dinga diban jiki kuna yawo a gari, da sunan zuwa makaranta bakin jini ye hana kowa yace jana sonku, yar uwar taku data samu miyi kukeso kuje ku kasowa aure dule ku zauna min agida ku zamemin yen iskan gari, toh ninan mahaifinku kada nasake ganin wata tafita da niyyar zuwa makaranta, in kuma allurai waddah takeson bujirewar umernina kamar yanda uwarku tomma a shirye naknadauki matakin dana dauka akanta akanku 109 Hadiza Ado Yałwa Garari 2 Ita kanta Asabe bata tsammacin wannan hukunci mai tsananin daga gare shi ba,ta dinga ba shi hakuri ammah ina kamar harzuka shi take yi fadi yake wannan In ma ban hanata zuwa gidan Hansa'u ba ai yawo bin maza zata dinga yi kar ta janyo min abun fada gwarama su su zauńa a gidan, makarantar na soke ta, kuma ban ce ki bawa wats higiyar abincina yau ba, gobe ma sa kara fita batare da sun nemi izinina ba. Sai da ya gama bambaminsa da fadar munanan kalamansa sannan ya ji sanyi har ya fita. 110 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Dukkansu kuka suke har da shassheka shi ke nan yawargaza burin mahaifiyarsu, da ta sha wahala a kan karatunsu, ko dama bai hana a basu abinci ba ba ma jin. yunwa a cikinsusu domin bakin ciki da takaici ya gama cika musu ciki. Asabe da kanta ta shigo > dakinta da abincin da ta zubo musu ta soma lallashinsu "Kun san halin mahaifinku bai kamata ku sawa kanku kunci haka ku kwantar da hankalinku zan lallashe shi da sannu har ya hakura ya barku ku yi karatu". 111 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Asiya har ita din ma haushinta ta soma ji ta san dai da bata fada masa ba bata da masaniya a kan dadewar da su ka yi rannan basu dawo ba, sannan in har ta san halinsa ta kuma yar da su sun sanshi to h da bata furta cewa zata lallashe shi ba, domin Lawai mutumne da baya jin lallashi ba kuma ya jin shawara kuma ya jin shawara kuma ba shi da hakuri sannan ya jima ya na adawa da maganar makarantarsu. ** Bayan Alhaji Ahuta ya rufe kofar ya nufi Inda Hansa'u ke tatakure tana makyarkyata ga 112 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 zafin zazzabi da zafin zuciya kwalla kadai ke zuba a gefan idanuwanta, duk da yanda gabanta ke ta faduwa ganin Alhaji ya nufota bai sa ta wani yunkuri na gudu wa ba, idanuwanta kawai ta mayar ta rufe ko don ta samu saukin bugun žuicya har ya kara so daf da ita, ya zauna a gefanta, ya kai hannu ya rike hannunta. "Ki kwantar da hankalinki mana Hansa'u ni ba jahili bane ba zan yi miki abin da mahaifinki ya umarce ni da na yi miki ba zan fi so mu fahimci juna, ki mai da ni cikakken mijinki amma kin sawa 113 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 kanki tsoro da damuwa, ga shi har ya haddasa miki zazzabi" Ya kai hannun ya taba gefan wuyanta. "Kai wannan zafin jikin ya yi yawa?" Ya fada cikin damuwa bana yanzu ba ne, tun yaushe ne baki da lafiya haka?" Bata ba shi amsa ba sai dai ta bude idanunta da suke cike taf da hawaye sannan bugun zuciyarta da rawar jikin da take yi ya dan ragu. Hannunsa ya saka a aljihu ya zaro wayarsa Likita ya kira ta na ji yana yi masa bayanin zazzabi 114 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ne mai zafi bata san abin da likitan ya ce ba ta dai ji yana cewa ba damuwa. Sannan ya fita ta sauke wata nannauyar ajiyar zuciya tana share ragowar kwallah. A kichin ya samu Aminu da Uzaifa ya ce da Amun ka sanarwa yarinyar nan wani abinci da sauri likita zai ganta, sannan ya dubi Uzaifa da ya dauke kansa tun daga shigowarsa kichin din. Ya dai yarona ba wata 99 damuwa na ganka a nan" "Babu" Ya ba shi amsa a takaice ya yi kamar ya sake yi masa wata 115 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 tambayar ganin yanayinsa kamar baya son magana yasa ya yi shiru don ya san miskilancin Uzaifa ba lallai ne ya ba shi amsa ba, tunda ya fara da takaita masa. Nan da nan Aminu ya hada mata kayan tea a tray ya dura da doyar da Uzaifa ke soyawa kansa. Ya kwankwasa kofar sannan ya murda ya shiga da sallama. Ya hango ta can kurya a kwance ya sauke ajiyar zuciya "Kanwata ashe baki ji dadi ba, shi yasa yau na ji ki shiru Allah ya sauwake ya sa kaffara" Duk yadda take jin jikinta ganin Aminu yasa ta dan ji sanyi 116 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 har ta yi murmushi domin shi mutum ne mai barkwance ko da yaushe ba ya raba fuskarsa da murmushi. Amin ta amsa cikin sanyin murya ta shi ki ci abin da ya samu, kanwata kada yunwa ta illata ki". juya. Yana gama fadin hakan ya وو "Na gode yaya Aminu" Ta yi furucin duk da bai ji ma abin da ta ce ba ya yi murmushi domin ya gama fahimtar babu abin da ya faru a tsakaninta da Alhaji. Hadiza Ado Yalwa Likita Garari 2 dubata ya gama sannan ya dauki jininta dan yi mata gwajin MF dama JP. Wunin ranar Alhaji bai fita ba sai bayan sallar la'asar, tunda ya shiga Hansa'u ta rufe idonta da nufin barci take yi ya zauna a gefanta ya zuba mata ido sosai ya ji son yarinyar na shiga bargon da jijiyar jikinsa ya tabbatar kalmar rabuwa da ita ko da ya furta to yaudarar kai ne domin ba žai taba iyawa ba. Duk abin da take so zai yi iya iyawarsa na ganin ta amince masa ya na jin a jikinsa kamar ita ce maganin cutarsa. 118 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ba zai taba yarda da ya yi wasa da rayuwarta ba, ba zai bari lafiyarta ta tabu ba. ya shafa gefan fuskarta me bayyana karar da kuruciyarta sannan ya yi ajiyar zuciya yana yabawa kansa sa'ar da ya yi. Ko lokacin da ya soma ganinta bai ga kyau a tare d aita ba kamar yanzu. Shi kuruciyarta kadai ya hanga. Ya mike tsaye akwai bukatar ya fita wajen da za a dauke masa abin da ke addabarsa saboda kasancewa da yarinyar nasa ya shiga wani hali shi kuma ya fi son binta a hankali. 119 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ya mike ya gyara mata bargon da ya dan zame mata sannan ya kara mata karfin AC ya ja mata kofa ya fita.ya kira yarinyarsa Janifer ta tabbatar masa da tana nan cikin Ni'ima Hotel can ya nufa to amma me?" Duk yanda yake ganin kuruciyarta yau din ma sai yaga ta yi masa tsufa hoton fuskar Hansa'u kadai yake gani dama wasu abubuwan natare da ita da baima ganewa idanuwansa su ba, suka kuma zamo burin ganinsa. Sai ya kasance ba shi da walwala har jenifa ta fahimci hakan yace baya jin dadin jikinsa 120 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 komai ya ji ya fice masa daga ransa dole ya bar hotel din da ya so ya kwana a can. Ya tsaya a wani Bekiry ya jido kayan snacks da ice cream caculate da sauran tarkacen kayan zaki yana rayawa a ransa yara sai kayan zaki. Haka ya tsaya a wani boutique riguna da dogayen wandona masu bayyanar da surar jiki ya zaba kaloli masu daukar hankali kayan da suka fi daukar hankalinsa ke nan a jikin mace shi yasa ya fi son hulda da yaran kabilu ba hausa ba su matsalarsu kawai duk yarinyar daka taba sai 121 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ka ga ta san maza shi yasa bai taba sha'awar aurensu ba. Lokacin da Hansa'u ta ji fitarsa ta samu karfin jiki domin babu żazzabi a jikinta tunda ta sha magungunanta, saboda haka ta shiga wanka ta shirya cikin doguwar riga ta materiyal su ma tun nata ne na gida, ta raba gashinta gida biyu ta daure ta zauna a bakin gado da carbi a hannunta tana karanta addu'ar fita daga cikin wani kunci. Ta dinga karantawa. Ta tabbatar da babu kowa a gidan domin Aminu ma ya yi mata sallama ya tafi gida Uzaifa 122 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ma ta na jin lokacin da ya fita a motarsa, kasan zuciyarta da tunanin mahaifiyar dana kannenta ita kam tana cikin kewarsu tana cikin kishirwa ganinsu. Ta dinga tuna wasu abubuwan da suka yi lokacin da suna tare wani lokacin ta share kwalla wani lokacin kuma ta yi murmushi. Har bata san lokacin da Alhaji ya shigo da mota ba sai jin muryarsa ta yi ya shigo da sallama ta amsa da sanyin murya ya fadada fara'arsa "Yauwa Baby na jiki ya fara warwarewa ki yi hakuri na jima sai da na fita na tuna ba waya a hannunki bare na 123 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 kira ki na ji yaya jikin na ki, hankalina ya kasa kwanciya ban ma gama abin da na ke yi ba, na ji ba zan iya tsayawa ba, ban san halin da ki ke ciki ba". Yana fada yana fito da kayayyakin da ya siyo mata daga leda. Ice cream ya bude ya debo cokali "Bude bakin" Ya kai bakinta ta kau da kai cike da tsananin 6acin rai. Ya dora shi a kan ciyarta "To dauki ki sha tunda kunya ki ke ji, ban da abinki nawa ki ke da ba za a baki a bu a baki ba, ki ke jin kunya". 124 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ya dauki daya robar Ice cream din da ragowar alwowin ya nufi dan karamin firij da yake gefan gadon ya zuba a ciki. "Ga ragowar nan in sun kare ki yi min magana asiyo wasu ki 66 rage jin kunyar nan Haka ya zauna yana ta Iallabata har sai da ya ga ta sha Ice cream din sosai sannan ya kamo hannunta "Ta so mu je mu yi kallo a falo za ki ji dacin jikinki kwanciyar nan ta ishe ki haka, ta dinga jin kamar ta kurma ihu gaba daya ya gama matsa mata sai dai ta yiwa kanta alkawarin yi masa biyayya ko da hakan zai zama 125 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ajalinta, ko don kada ya fadawa babansu da take tsoro shi ma tamkar ajali. Lallai kallon da suke yi a yanzu na debe mata kewa wani lokacin har ta kan dan yi murmushi film din tom and jerre ne kala kala har Alhaji ya fahimci jin dadinta da kallon yawancin abubuwa shi ke fassara mata da hausa kallo na yi mata dadi sosai. Har ya soma hamma ya dubeta "Mu je dakina ki ta ya ni kwana, ko ba wata matsala za ki iya kwanciya ke kadai". "Zan kwanta a dakina" { 126 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ya sake yin hamma ,to " ba damuwa, amma ko da akwai wata matsala ka da ki rufe kofarki,ki barta a bude ba wani abu fa." Ta daga kai kawai. Ya ja gefen kumatunta ya na murmushi ba magana sai daga kai. "Mu kwana lafiya." Ya kwashi wayoyinsa da makullen motarsa ya shiga dakinsa. Ta sauke ajiyar zuciya bayan ya face mata da gani,ita kam duk wani abu da zai kai shi ga fatar jikinta tsananta shiga tashin hankali ya ke yi. Domin tana ji kamar daidai yake da shiga kwayoyin cutar da ke jikinsa cikin nata jikin, shi ya sa ba ta samu kwanciyar hankali ba, sai ta ga ba ya wajen, don ta fuskanci kamar ma da gayya yake yawan taba ta, domin ba ya iya shafe 'yan mintoci ba tare da ya 127 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 riko hannunta ko janyo wani sanadi dfa zai hada jikinta da na sa ba. Duk da ta sakankance ta mika rayuwarta, amma tsoro da fargaba. aya. Kash! mai karatu,a nan zan dasa Shin ina Harira ta nufa? Shin ina labarin ESP Abdul da Jidda matarsa? Duk mu hadu a littafi na uku. Daga mai debe muku kewa Khadija Ado Yalwa(Khadija Adamu Shitu) don yabo ko ba da shawara 09065291030 sai na ji dga gare ku. 128 3 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya

Chapter 3 of 4