Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 4
har dai ka ga ji da zaman jiranta ka tafi. 34 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Su kuma har lokacin suna takure waje daya suna kallon yanda ake shigowa da kulolin abinci da ruwa da lemuka kala-kala, duk kuma abin da aka kawo Asabe zata shio musu da shi amman kananun kannensu ne kadai ke iya ci, dominsu kowani lokuta suna wuce wa ne ta shin hankalinsu na daduwa saboda karfe biyar da rabi ne dai dai a ka sa lokacin da za a dauki amarya. Kamar yanda Hansa'u bata iya cin wani abu ba, haka Asiya da Umaima. Asiya ke ta kokarin tunasar da Hansa'u yin addu'o'in tare da zayyana mata wata hikima ta musamman da ta gano wadda take 35 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ganin zata taimaka mata wajen gujwar kamuwa da wannan cutar, dukkaninsu zuciyarsu ta nutsu da shawarar Asiya wannan su samun 'yar nutsuwa amma gabansu bai dana dukamketoku ba, har zuwa lokacin 'yan daukar amarya suka zo, sun dunkule kansu waje guda suka dinga wani irin kuka mai ban tauşayi, da kyar aka banbare Hansa'ų daga jikinsu, ji su ke yi kamar wadda za a kai kabari ba wadda ta samu karfin gwiwar rakiyar amarya Daga Asabe sai kawayenta da suka yi ragowa suka tafi kai amarya. 36 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Basu fi minti goma da tafiya ba Lawan ya shigo ya taddasu a daki. "Au zama ku kai a daki ba za ku fito ku gyara gidan ba". Lokacin da uwarku tana nan kuna barin ta yi cangal a cikin gida wato yanzu kuna son ku nuna ba ita ta haife ku ba shi yasa ku ka makale a daki tun safe. Haka suka ta shi duk jikinsu ba kwari daya ta hada wanke wanke tana yi daya kuma na shara. Nan da nan suka kammala sallamar Asabe suka ji a lokacin duk suna zaune a tsakar gida kowacce ta yi tagumi Asabe ke 37 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 cewa "Kai masha Allah wannan ai abin ku yi mata murna ne ba bakin ciki ba, kun ga daular duniya kuwa a gidan 'yar uwarku Hansa'u. Ai duk wata 'ya mace ta gidan miji ce kuma wata rana 'ya'yan gidan wasu ne Allah ya baku ya tata kawai addu'ar da za ku yi kenan" Ta shiga daki tana ta kakkabin zancen su kuwa Uzirin rashin sani kawai su ke yi mata, amma ba waddda ta ji wani sanyi a kan daular duniya da ta ke ciki fada domin rayuwar 'yar uwarsu yafiye musu koma me za su samu tare da ita. 38 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Lokacin da Aminu ke wanki a kofar gidan ya dinga ganin jeran gwanon motoci 'yan kawo amarya nata shigowa cikin gidan ya tsaya cak ya na zancen zuci kar dai babar yarinyar bata yarda da gaskiyar da na fada mata ba, ta kawo 'yarta". Uzaifa da.. yake zaune akan farar kujerar yana karatun nes magzine shima ya dago cike da mamaki. "Wai me ya ke faruwa a gidan nan?" Ya dubi Aminu. "Ga shi nan kuwa kana gani aure ya y1 وو. 39 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Uzaifa ya ce "To Allah ya kyauta ya ci gaba da karatunsa Karshe ma da ya ji hayaniyar mata na damunsa sai ya nade kujrarsa ya koma dakinsa, amma tunanin ya hana zuciyarsa ci gaba da karatu, to wannan bawan Allah mantawa yake yi da lalurar da yake tare da da ita,- shi ma yana daga cikin jahilan mutanen da basu yarda akwai kwayar cutar ba ne, suna dauka talauci ne kadai cutar tunda shi ga shi har yanzu bata tagayyara shi ba, amma laifin iyayen da suke ba shi 'ya'yansu ne saboda kwadayin abin duniya yafi yawa me rabon shan duka ai baya jin bari. 40 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Da wannan ya rufe shafin tunaninsa ya mike dan gabatr da alwalar sallar magariba duk jama'ar da suka yiwa Hansa'u rakiya sun watse jin gidan take yi shiru kamar ba wani mai numfashi a cikinsa, sai kukan tsintsaye da wani irin tausashen kamshi da yake ta shiga hancinta. Dama tuni ta zame jikinta daga kan gadon da suka yi mata mai sauki tun ma kafin su gama barin gidan gani take yi zata iya daukar ciwon ma a duk abin da ta taba a gidan ta bude idanuwanta don gabatar da kudirin da yake ranta. Dakin ya hadu fiye da zatonta kayan gado ne 'yan kasar turkeye Hadiza Ado Yalwa Garari 2 sai kyalli suke yi kamar madubi dakin ya na da girman gaske an ajiye komai bisa tsari gado da wadrop madubi, sai dan karamin firji abakin gadon paintin dakin da tayels din farare ne, tas pantin kayan gidon shi ma fari ne da ruwan toka. Zanen da yake shimfide a kan gadon fari ne tas me adon furanne. Standard A.C nata ba da sanyi da wani irin ni'ima kamshi. A iya rayuwar Hansa'u bata taba shiga kayataccen wuri kamar wannan ba, amma zamanta a gidansu ya fiye mata: wannan zama na mintinan a nan.. 42 21 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Jakarta ta bude ta dauko kwado me hde da 'yan makullaye da Asiya ta bata ta nufi bakin kofa ta duba kofar ta gogaggen katako ne tana kyalli kamar madubi gabanta da bayanta bata ga in da zata sakala kwaďo ba, gwiwowyinta suk ayi sanyi. Hankalinta ya ta shi ya yin da ta soma jin shigowar mota cikin gidan ta tabbatar Alhaji Ahuta ne ta soma zagaye dakin tana tunanin in da ya dace ta shiga ta boye kanta, kamar ance ga shi kawai sai ta hango mukallin a kan window dakin da sauri ta nufi wajan ta dauko mukullin ya yin da ta ke jin takun tafiyasa, na dada karatowa 43 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ta dinga gwada mukullayen can ta ga daya ya ruf ta murda ta ji ta rufo sosai a lokacin ya soma kwankwasa kofar ta jingina bayanta jikin kofar ta sauke numfashi amma har lokacin zuciyarta bata daina bugawa da sauri ba, "Hansa'u bude kofa ni ne Alhaji bude". Ya fada ganin ya nata bugu shiru. Ya dan yi murmushi ya yin da zuciyarsa ke tunsar da shi dama irin wadannan yaran ba a rasa tsoron namiji a ransu, me yiwuwa ta rufe ne saboda tsoron daren farko. Ya juya yana murmushi "Lallai wannan karon ma 'yar 44 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 shela ya samu za a jima yana amfanar kuruciyarta. Ya ji yarinyar ta skae shiga ransa ya na da tabbacin ko yunwa ma zata fito da ita kafin wayewar gari don haka ya koma falonsa ya zauna ya kunna kallo ya cire babbar rigarsa ya. dauko gasasshiyar kaza daya da lemon kwali ya soma ci cikin kvanciyar hankali. Yana zuba idon jin motsinta amma shiru har dare ya yi nisa ya gaji ya koma dakinsa ya kwantar surar yarinyar na yi masa gezau har cikin barcinsa. Haka Hansa'u ta kasa rintsawa saboda tsananin tsoro a iya tsahon 45 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 rayuwarta bata taba kwana ita daya ba, a dakin ba tare da 'yan uwanta ba, ga azababbiyar yunwa da ta hana mata sukuni irin wadda bata taba ji ba, gabanin sallar asuba juriyarta ta kore ta yi tunanin fitowa ta dudduba ko za ta dace da abub da za ta saka a cikinta. Ta bude kofar a hankali sannan ta leko ba alamar akwai mutum a falon a hankali ta fito da sanda tun kafin ta gama fitowa kamshin naman ya cika mata hanci tana fitowa kuwa ta samu ldar a ajiye akan tebur ga wanda ya ci ya rage a filet ledar ta dauka cak ta juya dakin da sauri tasa 46 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 mukulli ta sake rufewa ta na budewa ta na hamdala ga sarki Allah Kazace guda da biredi da lemon kwali a cikin ledar lallai yunwa bata da hankali bare Hansa'u da ta yi kusan wuni biyu ba komai a cikinta sai ruwa. Hannu baka hannu kwarya ta soma cin naman. Ba ta jima da soma ci ba kuma a mai ya dinga ta so mata ta tafi bandakin cikin dakin da gudun a nan ta dinga amayo duk abin da ta ci sannan ta yi alwala domin har an fara kiraye kirayen sallar asuba, ta na idar da sallah wani irin bacci ya yi awon gaba da ita. 47 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Lokacin da Alhaji Ahuta ya fito daga dakinsa bai yi mamakin ganin ta dauki ledar Naman ba domin ya san dole yunwa ta addabeta ya yi murmushi sannan ya nufi kofar dakinta ya dan kwankwasa kusan sau uku bai ji ta bude ba, a zahiri ma bata ko ji shi ba, saboda baccinta da ya nisa. Har ya game dukkan abin da yake yi ya fita ya dai lekata ta window ya kuma hangeta a kan sallaya tana barci ya yi murmushi "Haba 'yan mata haka ake yi eye amma na san yanda zan bullo miki" Ya fada asarari ya yin da yake kare mata kallo Aminu da ya tảho +8 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 karbar jakarsa ya na jin furucin nasa ya sunkuyar da kai yana gaishe shi. ya amsa da murmushi ya mika masa wani mukulli "Kа wanke wancan farar motar". "Yanzun nan dai Uzaifa da ita zai fita yau kada ka 6ata masa lokaci da safe nan zai fita" Aminu ya karbe mukullin "Yanzun nan z aa wanke Alhaji. Ya kara shi har bakin motar ya raka shi sannan ya dawo yana wanke motar yana tunanin halin rashin tausayi irin na Alhaji Ahuta. Shi dai ya ji dadin kawai ba ruwansa da matsalar da yake saka 'ya'yan mutane a ciki. Hansa'u 49 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 bata farka ba har misalin karfe daya da rabi na rana, ita kanta bata san ta yi barci me tsayi haka ba, yanda ta ji anata kiraye kirayen sallar azahar abin ya bata mamaki da sauri ta shiga bandaki wanka ta soma yi sannan ta yi alwala duk son ta sami karfin jikinta ne. Ji- ta ke. yi kamar iska zata dauke ta da kyar ta iya idar da sallah ta gane abu mai dumi take son sawa a cikinta to kuma kafin ta ci wani abu in ba haka ba zata iya amai. Ta murda kofar dakin a hankali sai ta ji kamar ana motsi a falo don haka ta tsaya tana ssauraran abin da ke faruwa muryar wani namiji ta ji yana rera wakar 50 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 jinin jikina ta bude a hankali ta leka wani saurayi ta hango wankan tarwada da mofar a hannunsa ya na ta goge tayal yana wakensa cikin kwanciyar hankali. Sannan ta samu karfin gwiwar bude kofar ta dai san ko Alhaji Na wajan ba zai iya haike mata a gaban wannan saurayin ba. Aminu yana tsaka da aiki yaga an bude kofa an fito cak ya tsaya ya bita da kallo kamar yanda ya. zata Faramar yarinyace sosai kuma yar wannan matar domin tsananin kama da suka yi. Ganin ya tsaya yana kallonta ya sa ta ce masa "Sannu da aiki"! Yawwa 51 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ya amsa mata da sauri har muryarsa na sarkewa ya ci gaba da binta da kallo kai jama'a yanzu Alhaji me zai diba a jikin wannan baiwar Allah kankanuwar yarinya wani irin tausayinta ji yana shigarta hade da mamaki yanda a ka yi mahaifiyarta ta yi watsi da gaskiyar da ta zo nema ya kuma gaya mata ta yarda ta kawo 'yarta wannan gidan. Hansa'u da ta wuce shi ta yi sa'a kofar da ta nufa kichin ne ita ma ta nufe ta ne don ganin ita ce abude ita dai a jikin hoto ta taba ganin irin wannan kichin din don haka babu yanda z aa yi ta iya dafa koda ruwan zafi a cikinsa duk 52 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 kowa da kayan shaye manya manyan gwangwanayen madara da ta yi tozali da su a kichin din ta tsaya cak tana kalle kalle har Aminu ya shigo da moffer а hannunsa da alama kiching din ma goge shi zai yi. Yanda ya ga tana tsaye ya san tana da wata bukatar-ne ya. се "Akwai abin da ki ke bukata ne?" Ta dan yi murmushi "Ruwan zafi na ke son dorawa amman ban iya kunna wannan abin naku ba". Shi ma sai ya yi murmushi hade da sakin moper hannunsa ya nufi gurin gas din "Zo ki ga ni". 53 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ya murda ya kuna sannan ya kuma murdawa ya kashe ya ce kin 66 gane yanda ake yi". Sannan ta kunna ita ma ya dauko kettle din dafa shayi, ya се in ma ruwan zafi ki ke so idan ki ka jona kettle din nan a socket mintina kadan zai tafasa kin ga sai ki yi abin da ki ke so ya nuna mata wajen kayan abinci sannan ya ci gaba da aikinsa. Ta koma dakinta ta dauko ragowar namannan ta zuba masa maggi ta soya abinta domin ita gashin bai mata dadi ba. Lokacin da ta fita tuni Aminu ya fiya gama aikinsa, ta raba komai biyu ta hanyar da ta ya fita 54 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 tana waiwaye in da zata ganshi tana karewa gidan kallo. Fadar kyawun harabar gidan ma kadai bata baki ne, can ta hango shi cikin rumfar da ake aje motoci ta dinga daga masa hannu har ya gane kiransa take yi. Sannan ta се "Yaya ne mene sunanka". Ya ce "Aminu" ta yi murmushi "Ba zan iya çe maka Aminu ba zan dai ce maka Yaya Aminu". "To na gode kanwata Ya ji dadin karramashin da ta yi sai yake jin kamar kanwarsa ce ta jini". Ta shiga dakinta ta kulle kanta sannan tasha tea da bread 55 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 da naman da ta soya ta koshi har ta rage na anjima, sai kuma kewar gida da yan uwanta ta dame ta. Addu'ar ta Allah ya kawo sanadin da zata bar gidan nan batare da wani abu ya same ta ba, lokaci lokaci tana sharar kwalla ita kam bata san wani irin uba ne da su ba, ta na kallon dan Baba a cikin idanuwanta yana kuka yana tambayar me ya faru? Babansu na tura shi, ta rintse idanuwanta wasu kwallah me zafi ta zilalo ko za a kai Hansa'u gobe ta mutu sai an kaita gidan Alhaji Ahmad Ahuta. Lalatattun 56 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 'ya'yanki marasa tarbiya to me mugun hali aniyarki ta biki". Munanan kalaman babansu ke nan akansu da mahaifiyarsu suka dinga amsa kuwwa cikin kunnuwanta, kwakwalwarta ta daketa shigar da tsanarsa cikin zuciyarta da ke dada tafasa ta dinga daukar zafin da ya mika sakonnin cikin hanyoyin sadarwa jikinta, nan da nan jikinta ya dauki zafi iskar da ta ke kadawa tana shiga cikin jikinta ta zame mai tsananin sanyi wani irin yanayi ne ya dinga shigarta me kama da zazzabi ta takre waje guda 57 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 amma bata jin kasalar da zata iya kwanciya. Ta dinga jiyo motsi a falo a kai a kai. Bata iya yunkurin tashi ta boye kanta ba, to ko ta gudu ta dogara ne da kulle dakin da ta yi duk da hakan bai hana gabanta ci gaba da faduwa ba. Can ta ji ana kwankwasa mata kofa zubawa kofar ido ta yi kawai tana sake takure jikinta, har mai bugun ya gaji ya daina. Can kuma sai ta ji muryar Aminu a bakin windo yana cewa "Kanwata ga abinciki nan a bakin kofa ni zan tafi gida sai gobe in Allah ya kai mu". 58 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Muryarta a dashe ta ce "To na gode yaya Allah ya tashe mu lafiya ya ce ameen". Tana jiyo takun tafiyarsa ya na 'yan wake wakensa. Тa tabbata ke nan ita kadai ce a gidan nan. Ta sauke ajiyar zuciya sannan ta mike ta bude Kofa. Foodflasks ta gani da plates ta dauka ta bude jlollof din taliya ce da ta sha busasshen kifi sai kamshin species ne kadai ke ta shi. Cikin zuciyarta tana raya wai Aminu ne ya yi wannan girkin ko me. 59 Hadiza Adö Yalwa Garari 2 Kamar yanda Alhaji Ahuta yai ta bugun kofar ta ji ya kama yau har cikin talatainin dare kuma duk Hansa'u na jin shi ta yi shiru sai dai lamarin na yau ya tunzura zuciyarsa ya fahimci cewa yarinyar nan zata iya zamowa me taurin kai don haka ya dace ya dauki mataki a kanta ya dinga jero tsaki lokaci zuwa lokaci da haka har bacci ya dauke shi. Washe gari bai bi ta kanta ba lokacin da ya shirya har ya tafi daga gidan, ya dai kudurta a ransa cewa da zarar ya dawo yau 60 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 din nan zai sauke mata duk abin da yake kanta. A yau Huzaifa baya fita da wuri kuma ga al'adarsa in har yana gida da kansa yake shiryawa kansa break fast sai dai Aminu ke ta ya shi wasu abubuwa. Lokata da dama tare suke girki in har yana gida, domin sun saba da zama su kadai a gidan kuma baya son cin abincin sayarwa. A yau ma ya fito kitchin din sanye da kayan bacci Amin ke fearar dankali yana wake61 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 wakinsa shi kuma ya na wanke kaza. Hansa'u tunda ta ji motsin Aminu a kitchin ta ji tana sha'awar fitowa ita ma ko dan ta dafa abin da za ta cі. Ta na sanye da doguwar rigar atamfa wadda aka hada dinkinta da yadin satin wanda tun sallar bara waccen Ummansu ta yi musu tare da su Umaima rigar har ta dan dage mata bayan laushin da kodau din da ta yi, duk yawan kayan da Alhaji Ahuta ya zuba mata alefe da wanda yake kawowa dinki 62 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 amma bata taba sha'awar saka kayan ba. Wadda aka kawota da itama Asabace ta takura mata ta saka, har kuka ta yi saboda takaicinsa saka kayan. Ta shiga kitchin din da sallama ganin Huzaifa a tsaye yasa ta tsaya cak ta kasa karasowa ciki, ta kuma kasa komawa, ba ta taba tsammanin Aminu shi da wani ne a ktchin din ba. "Kanwata shigo mana mi ki ke so?" Ba ta ba shi amsa ba sai ta soma gaishe shi ya amsa sannan 63 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ta gaida Uzaifa ba amsa ba ya dai juyo ya yi mata wani irin kallo sannan ya maida kansa ya ja tsaki da ya bayyana asarari ya ci gaba da abin da yake yi wai dubi irin yaran da Alhaji yake aurowa a cikin gidan nan irin yaran da ko matsayin 'yan aiki basu ishe mu Ya fada a cikin zuciyarsa sannan ya sake jan bayanannen tsaki. Yadda Huzaifa ya yi mata da yanda ta ga yanayinsa lallai ta fahimci me matsayi ne a gidan. Ba don ma ta san Alhaji Ahuta bai taba haihuwa ba da sai ta ce dansa ne sai ta ji ciwon abin da ya yi mata. 64 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Aminu da ya ji rashin dadi har 'yar kunya ta kama shi sai ya ce "Babban yaya kenan Uzaifa bai fiya zama a gida ba". Ta dan yi murmushi. "Me zan ta ya ku da shi yaya Aminu, ban saba da zama ba aiki 66 ba duk sai na ji wani iri -Aminu ya yi dariyar yake yanasatar kallon Uzaifa yaga yanayin da zai nuna domin ya san halinsa da muguwar kyama ba kowa yake yarda ya taba masa abin da zai ci ba, ya kowayi sa'a yana aika masa da harara ya ce "Ki je ki zauna kanwata hutu ne ya zo miki kin ga kuwa dole ki huta" 65 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Hansa'u ta yi murmushi kawai don ta kula da irin amsar da Uzaifa ke bawa Aminu da ido ta juya zuwa nata dakin maimakon yin abin da ta fito yi dafa ruwan tea. Bayan sun gama Aminu na zuba na Hansa'u Uzaifa ya dube shi "Baka dibi naka ba wannan kuma na waye?" وو" Na amarya mana" "Wai kai ina ruwanka da. yarinyar nan wanda ya ajiyeta bai bata abincin ba sai mu ne za mu dafa ta ci" Aminu ya e "Sorry oga ga ni na yi muntsare mata in da zata 66 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 dafa bai kamata kuma mu dafa mu hanata ba". Uzaifa ya ja dógon tsaki "Kai dai mugun shisshige ne wallahi da kai" Ya fada ya yin da yake fita daga kitchin zuwa na shi dakin. Aminu ya ajiye mata a bakin "Kofarta sannan ya koma kichin ya dauki na shi ya wuce can kam bancin a harabar gidan ya zauna zuciyarsa cike da tausayin Hansa'u yarinya kamila mai sanyin hali tana gama yin break fast ta shigo kitching din a nan ta debo tukuwane da filet din da aka bata duka ta wanke tana 67 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 share kitchin din Aminu ya shigo ya tarar ma ta gama aikin da ya zo yi ya ce "Na gode aiki na ne ai". Ya ce "Kin ga Uzaifa don yau ka da ki dauke shi wani iri yana da saukin hali sosai, shi son girmansa ne matsalarsa". T dan yi murmushi ta gane Aminu yana gani kamar ta damu ne da abin da ya yi mata ta се "Ai dan manya ne yaya Aminu dole ya so girma ba wata damuwa". Ya ace "Gaskiya ne 96 wannan. 68 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Shiru ya ratsa na wani lokaci Aminu ya ce "Kwanaki wata mata ta taбa zúwa makotan gidan nan don binciken aure sai na ke ganin kamar mahaifiyarki ce saboda tsabar kamar da ku ke yi. Hansa'u ta dago kai cike da mamaki nan da nan idanuwanta suka kawo kwalla muryarta a sarke ta ce "Eh Ummanmu ce ashe kana nan lokacin da ta zo". Ya yi murmushi ni ne ma nan wanda ya fada. mata gaskiyar al'amarin amma na yi mamaki da na ga an kawo ki gidan nan". 69 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ya gabatar mata da tambayar da take cik ransa. Idanuwanta suka ci gaba da zubo da kwalla cikin rawar murya ta ce "Ummanmu bata nan ne" Daga nan ta juya da sauri ta koma dakinmta. Ya bi ta da kallo har ta 6сасе masa da ga ni Ummanmu bata nan ne ya nanata kalmar a sarari hade da, bude hannuwansa na rashin sanin fadar maganarta. Haka kawai ya ji yana son shiga al'amuran yarinyar yana son taimaketa don yà kula da 70 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 matakin da ta dauka, ba abin dogaro ba ne, to amma me ye abin yi. Tunanin da yai ta damunsa ke nan har ya bijiro mata da tambayar da ya san ta girgiza zuciyarsa. Ta dora kanta a kan gwiwarta ta sakale hannuwanta jikin kafafuwanta kuka ta ke mai sauti har da shessheka. Ba ta da juriyar duk lokacin da ta tuno Ummansu da 'yan uwanta tana jin ukuba a rashinsu. Sam ta manta ba ta rufo kofar ba har ta ji diran motar 71 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Alhaji bata motsa daga in da take ba ba zato sai ji ta yi an murda kofa an shigo. Af irgice ta dago sai kuma ta mike a razane don ganin Alhaji a tsaye a gabanta, ta fara tsalle tana zagaye dakin tana cewa don Alla don Allah". Ya ce "Lafiya me ya faru? Nutsu ki min magana me ya firgita ki me ya faru?"" Ba ta tsaya saurarensa ba ta fito da gudu ta samu dan wani sako bayan kujera ta labe har ya zo ya shige bai ganta ba ta na ji yana waya yana cewa. "Ka da ku bar yarinyar nan ta fita daga 72 Hadiza Ado Yaiwa Garari 2 gidan nan" da alama da masu gadi ya ke dama abin da tai zato ke nan shi ya sa bata yi yunkurin fita ba. Ta na ji ya yi mata nisa ta mike da sauri ta nufi cikin dakin ta rufe kofar da sauri, sannan ta jingina bayanta da jikin kofa tana mai da numfashi. Daga Aminu har masu gadi sun tabbatar masa cewa ba ta fito daga falo ba sannan ya tabbatar da cewa boyar masa ta yi, ba karamin haushi ta ba shi ba ya kum ayi alkawarin fita daga sabgarta na zuwa wani dan lokaci da yake ganin zata fada 73 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 tarkonsa wanda bata isa ta fita daga ciki ba Washe gari ya shiya tafiya Abuja shi da Uzaifa wanda za ta dauke su twason sati guda. A bakin Aminu l hi labarin tafiyar Alhaji. Ta yi farin ciki sosai ta sake har ta kan iya fitowa falo su yi kallo ita da Aminu. Ta ko yi girkuna irin na zamani kala kala a wajen Aminu, har tana mamakinsa kamar ba namiji ba yanda ya kware sosai ta sami rangwamin damuwa matuka. Σ 7+ ४ Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Ranar da Alhaji ya cika sati daya cif ya kama ranar lahadi ne. Tunda yamma ake tafka ruwa kamar da bakin kwarya har zuwa karfe tara na dare tun tana tsaye a bakin window tana kallon yanda ruwa ya ke sauka har ta gaji da tsayiwa. Misalin karfe takwas da 'yan mintina ta yi sallarta ta isha'i tana cikin karanta littafinta na addu'o'i bacci barawo ya dauke ta. Har bata ji diran motar Alhaji ba wanda tun bayan sallar la'asar ya sauka a garin amma saboda a yanayin ruwan sama da 75 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ake yi basu samu karasowa ba sai yanzu. Ya shigo falon da sauri duk yanda yake kaucewa dukan ruwa sai da babbar rigarsa ta jika tun daga bakin kofa ya cire ta har lokacin ya na jin saukar ruwa yana murmushi yana yi ne wannan da duk haukan "da yarinyar nan za ta yi ba wanda zai ji ciki har da Uzaifa da yake jin nauyinsa kamar dan cikinsa, kuma shi ne da kansa mafi kusanci da su wanda bayan kofarsa ta waje akwai wata kofar da zata iya sadaka da dakinsa a cikin falon wanda ko 76 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 kiransa yake son yi ba sai ya zagaya ba haka shi ma idan yana son shigowa ba sai ya yi wahalar zagayowa ba. Sai dai ba kasafai Uzaifa ke amfani da kofar ba, amma da an yi wata kwarafniya me karfi Uzaifa zai iya ji Wannan danyar yarinyar kuwa ya san zata iya yi masa kwaroroto kafin ya samu ya cimma manufarsa a kanta. Jallabiya mai gajeran hannu kawai ya saka ya fito daga dakinsa hannunsa dauke da mukullayen gidan gaba daya wanda a ciki ya gama gane na 77 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 dakin Hansa'u dama nemansu ya yi ya rasa tun farko. Ya kuma so ya bita ta lallami shi yasa bai matsa da binciken su ba. Yan da ya ga tsarinta shi ya tilasta masa nemo su domin ya yi gaggawar biyan bukatar ransa ya ajiye mata taurin kai. A hankali ya zura mukullin ya bude kofar yanda ya hangota tana barci ya kidima shi jikinsa har rawa ya ke yi, ya dinga tafiya ciki sanda har ya isa inda ta ke a kasa kan darduma akwance tana sanye da doguwar riga mai santsin jiki ruwan hoda 78 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ta bayyana matukar kuruciyarta dan kwalin ta ya zame kitsonta shiku ya tattare a tsakiya kai ta saka ba ta daure jelolin ba. Ta yi haske fiye da sanda ya santa fatar jikinta ta yi wani irin laushi da bayyana hutu ya kasa hakura yanda zuciyarsa ke wassafo masa abubuwa a tare da ita maganadison ya ci gaba da tsarin figarshi gareta ya kai hannunsa kan abin da yafi daukar hankalinsa. Kamar wadda wutar lantarki ta ja haka ta farka a tsorace sai dai rikon da ya yi mata ya zarce wanda zata zille masa hankalinta 79 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 ya kai karshe wajen ta shi ĝi ta yi kamar ya soma zuba mata cutar jikinsa ne. Ya so ma magana. cikin muryar rada rada "Ki kwantar da hankalinki ni fa mijinki ki ne ki saki jiki da ni duk abin da ki ke zan ba ki gida ne, ko mota ko yawon... Wani karfi ta ji ya zó mata ya yin da shi kuma kasala ke raunata karfinsa ta hankade shi daga gare ta ta nufi kofar fita tana budewa ta ga ta budexta fito bata ma san in da takedje fa Kafarta ba. 0א Hadiza Ado Yalwa Garari 2 Har sai da ta fito ta samu wani sako da ba shi da yalwal haske shukokin sun sa ya dan yi duhu ta rakube a wajan ta na hakin gajiya domin ta san in har ta sake ta kai kanta bakin get din gidan maigadi ba zai barta ta fita ba, koma dole ya mika ta wajansa. Har yanzu ana yayyafi a garin iskar ruwa ma sanyi na kadawa ko ina, sanyi ne da ke gigita mutum nan da nan ta soma rawar sanyi har hakoranta na hadawa da juna. Alhaji Ahuta kuwa da ya fito bai ganta ba ya ja tsaki ya koma 81 Hadiza Ado Yalwa Garari 2 dakinsa shi kam ya gama gajiya da wannan lamarin na

Chapter 2 of 4