ƙare a kwance. Allah shi ne shaida ina zaune da ku da zuciya daya, kaf dinku ina muku kallo tamkar na yaran da na raina da hannuna. Komai zai wuce da yardar Allah. Itama Hajara in sha Allahu mijinta zai zo, Allah ya bata ikon yarda da ƙaddara."
Anti Hafsatu ta share kwalla na tausayin Inna Mairamu, mace mai nunamusu kauna da zuciya ɗaya, ga hakuri da kawar da kai da kuma maida lamarinta gaba ɗaya ga Ubangiji. Kafin Anti Hafsatu ta kai ga cewa wani abu sai ga Hajara ta shigo ta musu tsaye a kai. Wani kallo take watsawa Inna kamar ta ga kashi fuskarnan jage-jage da ruwan hawaye tun bayan Husna ta fesa mata cewa Anti Hafsatu ta fito da su wai za ta yi magana da Innar ta yi saurin fitowa ta laɓe. Komai a cikin kunnenta suka faɗi.
"Ke Hajara wane irin rashin ladabi ne wannan? Mu kika tsayawa a kai haka tamkar wasu sa'anninki?"
Hajara ba ta ko bi ta kan Anti Hafsatu mai wadannan zantukan ba ta ɗora nata zancen.
"Duk abin da ka yiwa ɗan wani a rubuce yake sai an yiwa ɗiyarka. Abin da kike fatan ya kasance a kaina, Mairamu (kamar yanda take kiranta tun farko wanda har ta koyawa Husna) ki sa a ranki har abada ba zai tabbata ba sai dai ki gani akan Sadiya. Zama ba aure, karuwanci, cikin shege duk za ki gani a jikin wannan ɗiyar taki mai kama da zabiya. Aure kuma ko ana ha maza ha mata zan yi shi, ki zuba idanu ki ga ikon Allah. Ƙaryar mutum wallahi!"
"Ke Hajara!" Anti Hafsatu ta mike lokaci guda tana kiranta murya a ɗage, hannu ta ɗaga da niyyar marinta ko me ta tuna sai ta dunƙule ta fasa ta ɓige da nuna ta da yatsa idanunta na fitar da hawayen baƙin ciki. Ita ko Inna Mairamu kanta a ƙasa ta runtse idanu tana ambaton sunan Allah, zafin kalaman da Hajara a yau ke jifan ɗiyarta da shi da mummunan bakin da take yi gareta ya sanya ta kasa jure yin shiru wannan karon ta ɗago kai tana kallonta.
"Hajara kar ki bari Allah ya kama ki da laifin ƙazafi da kuma ƙage. Sadiyar dai da kike aibatawa kin fi ni kusanci da ita don ko yau rabuwar aure zai iya zama dalilin da zan nisanta da ku gaba ɗaya, ita ɗin kuwa babu yanda za ki yi da ita saboda dolenki ce kuna tsatsonki."
"Hajara ba ki da hankali, kin manta wace ce ita kike a wajen mahaifinki? Wallahi ki kiyaye harshenki domin nan gaba zai iya haifarmaki da dana sani marar iyaka. Yau ace Mama na raye an fadamaki za ta ji dadin irin wannan abu da kike aikatawa? Ko kuwa an faɗamaki Husna za ta so ki dinga yiwa Mahaifiyarta irin wannan cin kashin?"
Idanun Hajara har ƙanƙancewa ya yi tsabar bala'i ta dubi yayarta murya a sama ta ce.
"Ki bar kiran Mamana a wannan sha'anin, tana can kwance cikin kabarinta. Alhamdulillah ta rabu da mutane lafiya, uwa uba ta rabu da mijinta lafiya yana mai addu'a da nema mata gafarar Ubangiji. Sannan Alhamdulillah uwata ba ta cutar da rayuwar kowa ba. Husna kuma ita kanta ta fahimci wace ce Babarta Mairamu, ta soma gane ita ke haddasa rashin yiwuwar aurena. A hankali za ta gane komai."
Inna Mairamu zuwa lokacin ma ta kasa ƙara uffan, Anti Hafsatu kuwa zagin Hajara take yi kawai tsabar takaici, abin da ya hana ta kai mata duka bai bwuce dokar da Malam ya sanya musu akan Hajara ba, har Allah ya isa ya yi ga duk wanda ya sa hannu ya taɓa masa ita. Koda dai ba akan Hajara ba kawai, shi tun fil'azal mutum ne da babu wanda ya isa ya dokar masa yara.
"Lallai yau na ƙara yarda ba za ki taɓa sauya hali ba. Wannan rashin hankalin da kike yiwa Inna wallahi muddin ba ki bar yinsa ba sai kin ga sakamakonki a rayuwa. Shashashar banza da wofi wacce ba ta san girma da mutunci Dan Adam ba."
Ita dai Hajara guntun tsaki ta ja ta fice tana banko labulen, Sadiya dake kicin tana ganin ta shige ɗakinsu ta fito a guje ta yi wajen Innarta tana kuka sosai a duniya ta tsani Hajara ba don komai ba sai saboda cin zarafin Innarta wanda nata ya ninka na sauran yan uwan, sukan ma nuna halin ko in kula irin na ƴan boko ga Inna, amma ita kuwa idanunta take murjewa ta ci mutuncinta son rai. Itama Innar nata hawayen ba su bar zuba ba. Anti Hafsatu kuwa hakuri take ta ba Inna kamar harshenta zai tsinke. Har sai da Innar ta dakatar da ita da nuna nata kar ta damu babu wani abu.
A can ɗakin kuwa, Husna ta ji komai da ya wakana zuciyarta ta ɗan yi babu dadi, babu wanda zai so a dinga cin zarafin mahaifiyarsa haka, amma kuma ai a ganinta gaskiya Antinta ta faɗi, duk abin da ka yiwa wani za'a yi wa naka. Har Hajara ta shigo ba ta motsa daga inda take zaune rike da babbar wayarta ƙirar Infinix da Antin ta siyamata wai ta dinga kallo. Akan wayar ma sai da Malam da Inna suka yi faɗa, ba ta ga dalilin da za'a ba Husna waya ba, duka-duka a ganinta yarinyar shekarunta nawa a duniya? Karshe dai da Malam ya yi mata kaca-kaca dole ta zuba idanu, takan yiwa Husna nasiha da nunamata irin hakan da ake mata sam ba gata bane, amma yarinyar sai take ganin kawai Innar ta takura mata ne.
"Anti Hajara."
Cewar Husna fuskarta dauke da tsantsar damuwa, ita har ta rasa ma bayan wa za ta bi, takan ji ciwo idan aka yiwa Inna, kuma takan ji zafin asirin hana aure da aka ce Inna ta yiwa Antinta.
Hajara ta dube ta sai ta ƙara fashewa da kuka ta janyo hannunta cikin nata.
"Momina, meyasa Mairamu ba ta kaunar ta ga nayi aure? Me nayi mata da take fatan na dauwama a gida? Shikenan don uwata ta mutu sai na zama marar gata? Kinga don nace abinda ta yimin za ta gani a kan Sadiya shi ne Anti Hafsatu har kusan dauke ni da mari ta yi. Wato ba ta son a yiwa Sadiya amma idan da ace ke nace a yiwa babu abin da zai dame ta ko? Na fadamaki, saboda kina kaunata shiyasa Mairamu ta fi nunawa Sadiya so sama da ke, hum, ai shikenan. Ki yi addu'a na samu miji na yi aure, wallahi gidana za ki koma."
Husna itama kukan take yi, bilhakki tausayin Antinta take ji, tana kuma jin zafi idan ta tuna wai Mairamu ta fi kaunar Sadiya saboda ita. Ta kuma soma yarda da hakan, kuma Hajara ta ce ba don komai ba ne sai ganin Sadiya kyakkyawa ce za ta yi amfani da ita domin ta zame mata tamkar jari, ita kuwa tunda ba ta da kyawun fuskar Sadiyar, kuma wai Sadiyar sunan mahaifiyar Innar ta ci, ita kuma saboda sunan maman su Hajara ce kuma matar da Babansu ya fi kauna shi ne dalilin da yasa komai ta aikata sai ta ce bai yi ba ta daina.
"Kiyi hakuri Anti, kinji? Nima na fi so kiyi aure na bi ki gidanki. Na gaji da zama tare da Mairamu tunda ba ta kaunata."
Hajara ta murmusa ba tare da ta ce komai ba sai aikin kallon lallen da aka zana mata a hannu don bikin aurenta har ma ya soma gogewa.
©Rufaida Umar.
https://arewabooks.com/book?id=663894ac767a55b1dd421f6a
*Kazar Kwanci free pages 1-5 sun sauka a arewabooks, kuna iya bin link ku sha karatu.*
***
*Kazar Kwanci...*
*Free page*
06
Anti Hafsatu ba ta kuma bi ta kan Hajara ba, abin da ya faru kuma bai sa ta iya zaman jira har Malam ya dawo su gaisa ba, tana yin sallar azahar ta ci abinci ta tattara ta bar gidan. Sadiya kuwa kamar yanda ta saba haka ta zauna tana taya Inna da wanke-wanken kwanukan da suka ɓata na abincin rana, Hajara da Husna ko ta kan abincin ba su bi ba, tana nan tana gyara wurin da ta kammala aikin Husna ta fito yafe da siririn gyale ta shuri takalmanta ta fice daga gidan. Da idanu kawai Sadiya ta bita, can kuma sai ta dawo hannunta riƙe da leda babba sai ɗaya dauke da lemo da ruwa ta shige ɗakin. Ita kuwa Sadiya tana kammalawa ta nufi dakin Innarta, kamar yanda ta bar ta haka ta tarar da ita. Ta zauna fuska dauke da damuwa.
"Haba Inna, don Allah ki bar damun kanki da tunanin abin da ba za ki iya gyara shi ba."
Inna ta sauke ajiyar zuciya ta dube ta.
"Kar ki damu Mamana, ba wannan ke damuna ba, rayuwar Husna nake tausayawa, an ɗauki turbar lalata min tarbiyyarta amma ina ji ina gani ban isa na yi magana ba. Wannan shi ne damuwata."
Sadiya ta sauke ajiyar zuciya.
"Ki cigaba da addu'a Inna. In sha Allahu komai zai yi daidai."
Ta gyadamata kai.
"Allah ya dafamana."
"Amin inna."
***
WAIWAYE...
Malam Sa'ad Shagari ya dubi Mairamu cike da nutsuwa. Ita kuwa kanta na ƙasa tana ɗan murmushi. Shima sai ya tsinci kansa da murmusawar kafin ya soma magana.
"Sai kika yi mamakin gani na ko Mairamu? Ban ji kin tambayi abin da ya kawo ni ba?"
Ba tare da ta dube shi ba ta amsa.
"Ba komai, nasan ko da me ka zo alheri ne ai Malam, ya gida ya kuma ƙarin hakuri? Naji a wurin Malama Fauziyya cewa uwar gidanka Allah ya yi mata rasuwa, Allah ya gafarta mata na so shiga da na dawo na yi maka gaisuwa duk da ya dauki lokaci amma Allah bai nufa, kuma sadda aka yi rasuwar sai nima abin ya zo kan gaɓa, an yi min wata rasuwar a can gida na tafi, yayata da muke uwa daya uba daya, shi ne ma dalilin jimawata ban dawo ba."
"Allahu Akbar, Allah ya gafarta mata."
Mairamu ta amsa da amin, shiru ya ɗan biyo baya kafin ya ɗora.
"Mairamu, koda ban faɗa ba, nasan Malama Fauziyya ba za ta rasa sanar da ke kaɗan daga dalilin da yasa na zo wajenki ba. Amma zuwa da kai ya fi saƙo. Kamar yanda kika sani, Marigayiya matata Hajiya Asma'u, da mahaifina da mahaifinta uwa daya uba daya, hakanan iyayenmu mata su ma auren dangi na zumunci ne ya faru tsakaninsu har suka haife mu. Wanda cikin iko na Allah soyayya ta ƙullu tsakanina da Asma'u tun tana matsayin ɗalibata har Allah ya nufa ita za ta zamo uwa ga ƴaƴana bakwai. Ba zan ɓoyemaki ba, ta kasance mace mafi soyuwa a gareni, bana jin a duniyata na taɓa son wata ɗiya mace irin son da na yiwa Asma'u. Mace mai hakuri da kuma kauda kai, a tsawon shekarun da muka rayu da juna da ita, saɓanin da za ki ga ya haɗa mu sai dai ko irin na harshe da haƙori, kinsan ɗan adam ajizi ne. Lokaci ɗaya cutar annobar amai da gudawa ya zo da ajalinta, ta rasu."
Ya ɗan numfasa, Mairamu ta ɗan dube shi cike da tausayawa, ko daga yanayin fuskarsa da yanda yake magana za ka fahimci cewa har a lokacin yana jin zafin rashinta, ta samu bakinta da furta addu'ar neman rahma gareta. Ya amsa da amin sannan ya ɗora.
"Shekara guda kenan da rasuwarnan, manya sun matsa akan zamana a haka babu aure, nima kuma ban ga amfaninsa ba ko don kare mutuncin kaina da na iyalina. Wannan ta sa na nemi zaɓin Allah kuma cikin ikonSa muka haɗu da Malama Fauziyya ta zo shagona neman wani littafi, anan Allah ya kawo zancenki na ji har a raina zan iya zaman aure da ke, wannan shi ne dalilin da yasa na nemi ta nema min izninki kafin na zo gareki. Ba zan yi maki dole ba Mairamu, zan ba ki lokaci nan da kwanaki uku kiyi tunani zan dawo, idan har kin amince sai na samu magabatanki tunda dai mu yanzu ba yara bane ko? Koda dai na fiki tsufa."
Ya ƙarashe da ƴar dariya itama sai ya ba ta dariyar, ta ɗan murmusa. A haka suka tsaida maganar cewa zai dawo ya ji amsa nan da kwanaki uku.
Bayan kwanaki uku kuwa ya dawo, ya samu kyakkyawar amsa inda a take ta amince da yin fatan alheri a lamarin.
Malam Sa'ad bai yi ƙasa a gwuiwa ba ya ja amininsa Alhaji Abubakar wanda ya kasance shahararren ɗan kasuwa a kwari, suka rankaya wajen ƙanin mahaifin Mairamu wanda ta ke zaune gidansa tun bayan rasuwar iyayenta.
A sati biyu aka kammala komai, aka tsaida ranar daurin aure. Sai a wannan lokacin ne kuma Malam Sa'ad ya tara yaransa kaf domin sanar da su.
Ya dube su, su din ma shi suke kallo, sun riga sun ji labari a wajen ƴan uwa sai dai su na fatan ji daga bakinsa. Ai kuwa yana faɗi, Hajara ta shiga kuka.
"Wayyo Mama, shikenan mutuwa ta raba mu da ke. Yanzu Malam zai ƙara aure. Na tabbata marainiya."
Malam ya bita da kallon tausayawa, Safiyya ma sai da zuciyarta ta karye. Anti Hafsatu kuwa ba ta ce komai ba sai fatan Allah yasa ko wace ce ta maye musu gurbin Mamarsu. Caraf kuwa Mustafa ya karɓe.
"Aa Hafsat, bar wannan magana. Ai babu wata da za ta iya maye gurbin Mama a zuƙatanmu. Malam dai ya yi aurensa kawai, muna mishi fatan zaman lafiya."
"Wannan hakane. Ai babu kamar uwa. Malam Allah ya sanya alheri." Cewar Baba Habu.
Hashimu kuwa babu abin da ya dame shi, kusan shi ya ma fi su halin ko'in kula da irin wadannan al'amuran, a ganinsa mene ne don Abban ya yi aure? Matar dai ai ba zama za su yi da ita ba tunda duka suna da gidajensu sun yi aure. Safiyya ma an saka ranar aurenta an kusa sai ko Hajara auta ƴar sakandire.
Haka dai Malam ya kammala maganarsa ya tashi ya bar su don kukan Safiyya da Hajara na neman karya masa zuciya. Sai da Hashimu ya tsawatar kafin su nutsu su bari.
"Murna kake yi kenan da auren Yaya Hashimu?"
Baba Habu ya tambaya. Hashimu ya ja tsaki.
"Ina ruwana don Malam zai yi aure? A kanmu za ta zauna? Ku mene ne naku ciki? Kuna fa gidajenku, idan ma ba ku so ba, ba za ta taba sanya ku a idanu ba ballantana wani mu'amalar ta haɗa ku da ita? Ni fa da dai ya auri wata cikin dangi gwara wata can bare da ba mu san ta ba."
"Wallahi kuwa, nima haka na gani Yaya, da dai Malam ya kwashi wata a ƴan uwa da suka yi zumunci da Mama, gwara ya yi aurensa daga can waje." Zakari ya furta don shi dagaske ya ma ji dadin auren mahaifin nasu, zamansa haka tausayi yake ba shi koyaushe idan ya dawo gida sai dai ya yi zaman jugum da tunani. Anti Hafsatu ma ta nuna goyon bayanta, karshe mazan suka mike zasu wuce, cikin zolaya Baba Habu ya dubi Safiyya da Hajara.
"Toh, Safiyya gwara ke kin ma kusa barin gidan abinki, ke kuwa Hajara sai ki shirya tarbar sabuwar Mommy. A kuma yi mata biyayya ba ƙaƙƙautawa."
Aikuwa ta ƙara tunzura ta fashe da wani sabon kuka tana fadin ita wallahi ba ta isa ta kirata da sunan Mommy ba. Haka yana dariya ya fice ya bi bayan ƴan uwansa. Anti Hafsatu kuwa ta dubi Hajara wacce kukanta ya soma kai ta bango.
"Malama ki yiwa mutane shiru haka. Wannan ai hauka ne da rashin hankali, shikenan haka zai zauna babu aure? Idan kin ga dama ki yiwa kanki faɗa ki rungumi ƙaddara don auren Malam babu fashi, idan kuwa kin ƙi sai ki zauna ki yi ta fama da ciwon zuciya tunda ba ki isa ki dawo da abin da yake dama can aronsa Allah ya bamu ba."
Wannan ne dalilin shirun Hajara ta miƙe tana kunkuni ta shige ɗakinsu. Safiyya kuwa ta dubi Anti Hafsatu da mamaki.
"Wai Anti Hafsatu ba kya jin zafin da muke ji a zuƙatanmu dangane da wannan lamari?"
Harara Anti Hafsatu ta doka mata tana mai kunce goyon ɗanta Daddy dake bayanta wanda ya ishe ta da kuka.
"Zafin me zan ji? Ku yanzu kun fi kaunar Malam ya dauwama a haka babu aure? Ba kwa la'akari da cewa kuma aure za ku yi ku bar gidan? Ai idan ita Hajara ta yi wannan wautar ke bai kamata ace har da ke ciki ba. Yaya Mustafa ma sun ba ni mamaki don na tabbatar su kansu ba wani murna suke da hakan ba. Amma kar ku manta, muddin kuna kaunar Malam dagaske, toh taya shi son abin da yake so shi ne mafi dacewa a garemu baki daya."
"Tabɗijam! Shikenan ai, ya yi auren amma wallahi nidai babu abin da zai taɓa haɗa ni da matarsa. Har gobe ba da za ta taɓa maye mana babban gurbin da muka rasa ba a rayuwarmu."
"Ku kuka sani. Aure dai babu fashi da yardar Allah." Daga haka ba ta ƙara tankawa ba, karshe ma Safiyya sai ta mike ta nufi dakinsu don su kara jajantawa juna ita da Hajara.
***
Ranar juma'a aka ɗaura auren Mairamu da Malam Sa'ad bayan saukowa daga sallah. Aka bar tariyarta nan da sati daya bisa alfarmar da Malam ya roƙa don ya ƙarasa gyaran gida saboda a satin da ya wuce bai samu aikata komai ba dalilin tashin hankalin da hakan ya haifar a gidan. Inda Hajara da Safiyya suka yi ta faman kuka su Hajara har da kwanciya ciwo yayinda Safiyya ta tayar da iskokai su fa a dole Malam ba zai ƙara aure ba. Sai da babban yayan Malam ya tsawatar kafin su nutsu, dama abin nasu har da zuga inda facalolin Mama da kuma yan uwa suka dinga tada jijiyoyin wuyar ba haka ba. Musamman ma zawarawan da suka saka rai Malam din zai auri daya a cikinsu.
Sai lokacin ya samu sararin fenti. Gidan dakuna biyar ne, daya mai ciki da falo na Malam ne sai ko falle biyu wanda a baya Asma'u ta maida daya daki dayan kuwa falo, sai ko daki daya na yanmatan yaran. Sai shago a waje na samarin gidan. Babu laifi akwai wadataccen tsakar gida har da ɗan shuke-shuke a gefe daya zagaye bangon tsakar wajen da kuma famfo da aka zagaye wajen da tayil inda ake wanke wanke. Gidan ma dai duka tayil ne a ƙasan.
Ranar da Mairamu za ta tare, daga ita sai yan uwanta hudu, matar dan uwan maihaifinta da suke kira Dada sai kuwa yaran Dada mata uku, sai makwaftansu mutum biyu. Kwanansu uku suna kwasar amarcinsu, sai da ta yi sati ko ƙeyar ɗansa ko ɗaya ba ta gani ba, lokacin Zakari ya tafi bautar ƙasa a Yobe. Hajara da Safiyya kuwa sun koma sun tattare can babban gida wurin dangi tsabar baƙin ciki da takaici. Sai da suka yi sati biyu cif kafin su waiwayi gidan. Gani suka yi ma ai dama suka bayar da Mairamu za ta ci karenta ba babbaka a gidan Mahaifinsu, gwara su zo a yi komai a gabansu.
***
Mairamu na zaune ta kammala suyar kifin da Malam ya kawo na miya, sai kawai ganin mutane ta yi sun faɗo kamar an koro su babu ko sallama har sai da ta ɗan razana. Suka yi tsaye cak su na ƙare mata kallo da kuma bin kifin da ke cikin mai yana soyuwa da idanu, sai kuma suka saki dariya gami da cafkewa.
"Wasssh! Babu a house! An samu na bati!" Fadin Safiyya, suka ƙara tuntsirewa da dariya. Ita dai Mairamu kallonsu kawai take, ko ba a faɗa ba ta san wadannan yaran Malam ne don ta ga tangameman hoton family da suka dauka wanda ke manne a falon Malam.
Ta yi kamar ba ta ji furucinsu ba, da ɗan murmushi saman fuskarta ta ce.
"Ah Safiya ku ne tafe? Sannunku da zuwa. Ku shiga ciki."
Suka watsa mata harara, cike da tsiwa Safiya ta ce.
"Ai ba sai kin ce mu shiga daga ciki ba Mairamu tunda gidan ba na uban wani ba ne."
"Atoh." Hajara ta karɓe. Inna Mairamu ta tauna maganar a ranta, ba ta ji zafi sosai da kiranta da sunanta na ainahi da budurwar ta yi ba kamar zagin ubanta da ta yi. Daga haka ta ɗan yi murmushin yaƙe ba ta ƙara cewa uffan ba ta cigaba da aikin dake gabanta. Tana kallo suka faɗa ɗakin da dama mallakinsu ne, a gyare yake tas don Inna Mairamu mace ce da ba ta son ƙazanta da ƙura, hakan yasa duk bayan kwanaki biyu take shiga ta gyara shi, Malam kan ce ta bari tunda babu mai kwana a dakin amma ta nuna masa babu komai ta san watarana za su zo. Ba kuma ta son su tarar da wurin kaca-kaca. Yakan yi murmushi cike da jin dadi, wato dai ta nunawa nasa kulawa.
Shinkafa da miyar kifi ta yi sai kuwa ruwan shayi na Malam wanda ya zame masa jiki sai ya wuni yana sha idan yana gidan. Ganin haka yasa har ƙaton filas dinta na shayi take cikamasa ta sanya masa a mota ya wuce da shi kasuwa.
Ta kai babban farantin da ta shiryawa mijinta abinci zuwa falonsa ta ajiye sannan ta fito da zummar daukar filas na shayi, turus ta tsaya ganin Hajara ta dauki faranti ta zuba shinkafa tili guda ga miya da kifi nasha-nasha a sama. Suna hada ido Hajara ta watsa mata kallon tara saura tana turo baki gami da fadin.
"Ai dai tunda Ubanmu ne ya yi cefanen babu wata da ta isa ta hana mu ci."
Ɗan murmushin da bai kai zuci ba Inna ta yi.
"Hajara kenan, ko ba ki yi haka ba dama ku din nake niyyar ɗibarwa. Sannan eh Babanku ne ya yi cefane, amma kinga tunda ni na girka ina da iko akan tukunyata ko?"
Hajara ta ɗaga kafaɗa.
"Oho dai, ko me za ki ce ba zan fasa abin da nayi niyya a gidan nan. Kema din arzikin ubanmu kike ci, ban da haka ko ƙayar kifi sai ki shekara ma ba ki gani a kwanonki ba!"
Tana kai wa nan ta kaɗa kai ta yi ciki, can kuma ta dawo daidai sadda Inna Mairamu ke kokarin juye ragowar miyar a wani karamin filas dinta, hannu ta kai da zummar ɗaukar ruwan zafin dake cikin filas, caraf Inna ta riƙe hannun gami da ɗauke filas din.
"Wannan dai na mahaifinku ne. Idan sha kike son yi, ki bari idan ya dawo ya yi amfani da shi sauran ki ɗiba."
Hajara na huci take bin Inna da kallo kamar ta tofa sai kawai ta yi ƙwafa ta koma ɗaki.
Sai da aka soma kiraye-kirayen sallar Magriba sannan Malam ya shigo gidan. Inna na bandaki tana alwala, Hajara suka tarbe shi da oyoyo kai kace wasu yara ne ƴan shekaru goma shima ya yi farin ciki da ganinsu duk da daman sai da ya je can babban gida kai musu tsarabar kasuwa ya ƙara lallashinsu akan su dawo gidan ya iske sun ma taho. Da wannan murnar suka karɓi ledojin hannunsa zuwa cikin falonsa. Koda Inna ta fito sai kawai ta yi dakinta sanin da ta yi shima Malam din masallaci zai nufa. Sai bayan ta idar da sallah ne ta dan yi lazimi, ba ta kai ga idarwa ba ta ji Malam na faman kwalamata kira har kafin ta fita ya banko labulen ɗakin nata ya shigo. Suka yi kiciɓus bayan ta shafa addu'ar da ba ta kai ƙarshensa ba kirjinta har dukan tara-tara ya shiga yi domin dagaske dai ta tsorata da wannan kiran.
"Lafiya? Sannu da dawowa." Shi ne abin da ta tsinci bakinta da furtawa lokaci guda. Bai ko amsa ba cikin ɗaure fuska ya hau fada ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba kamar wanda aka jonawa batiri.
"Ni bana son haka, daga dawowar yara har kin fara hana su abinda Ubansu ne ya kawo? Ba ki ba su abinci ba, don kuma sun nuna su na da buƙatar shan ruwan shayina kika ce ai ba su kika dafawa ba? Mairamu duk abin da nake kawowa gidan nan ba nawa ne ni kadai ba, na iyalina ne, bana son haka. Kin jefa zuƙatunsu cikin kewar mahaifiyarsu, wato kin soma nuna gazawarki a