Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ke mummy kin manta hirar da mu kai dake jiya kince insha Allahu sai kin Goya 'ya'yana mummy amma tun su Aunty Saiam basuyi Aure ba kika tafi y mummy y? Kuka suka k'ara fashe dashi kamar ta zuga su banda Saiam da ta rungume kan Hajiya Nafeesa tun dazu ta kura wa jinin dake ta zuba ido ko kifta ido bata yi Suhaima ce ta fara ankara da Alhaji Nazifi dake kwance kamar matacce da sauri ta mik'e tayi wajensa tana " Daddy Daddy Daddy" ko motsi Alhaji Nazifi baiyi ba wani mugun ihu Suhaima ta fasa tana "shikenan mun zama cikakkun marayu Daddy shima ya mutu" Safna da sabida tashin hankali bama tasan babu kaya ajikinta ba da gudu ta tashi tana "AAA Daddy bai mutu ba Suhaima daddy bazai tafi ya barmu ba " Aguje ta nufi band'aki ta d'ebo ruwa ta watsawa Alhaji Nazifi Alhaji Nazifi kuwa yaja wani dogon ajiyar zuciya still bai farka ba wani ruwan Safna ta k'ara watsa mishi ahankali ya k'ara Jan wani numfashin kafin ya bud'e idonsa ahankali ya zubawa Suhaima da Safna ido kamar Wanda bai sansu ba Take maganar Hajiya Nafeesa ya hau amsa kuwaa a kunensa "Alhaji idan wani Abu ya samu yarana wlh bazan tab'a yafe maka ba" Mik'ewa yayi zumbur yana "Nafeeeesa" tare da nufar wajen da take kwance da gudu inda su Suhaima suka bishi abaya aguje Zub'e wa yayi akan gwiwarsa yana kallon jinin dake ta zuba akan tiles Sahiba na kwance a k'afar Hajiya Nafeesa Saiam kuma ta rungume kan Hajiya Nafeesa gam ta kurawa waje d'aya ido Samha kuwa ta rik'e hannun Hajiya Nafeesa tana wani irin kuka kamar ranta zai fita majina sai fitowa yake a hancinta Alhaji Nazifi hawaye ne ya hau gudu a fuskarsa yana " Nafeeeesa karki min haka karki tafi ki barni" Samha had'iye kukanta tayi tana wa Alhaji Nazifi wani irin kallo tana "Daddy kana ina lokacin da b'arayi suka harbi mummy?Daddy kana ina lokacin da mummy take fad'i tashi akan ta hana a keta mana haddi? Daddy wane k'ok'ari kayi Dan kar ayi mana fyad'e? Daddy wane k'ok'ari kayi Dan kar su kashe mummy? Daddy mummy lost her life because of us she sacrifice her life because of us Daddy kana ina hakan duk ya faru? Daddy ayanzu zaka zo kace kar ta tafi ta barka? Daddy ayanzu kake da bakin magana? Daddy agaban idonka aka ringa k'ok'arin yi mana fyad'e Daddy agaban idonka aka harbi mommy sau uku Daddy sai yanzu zaka zo bayan sun tafi ? Sai yanzu zaka yi kuka Daddy? Duk maganar nan da take yi kuka take sosai Alhaji kuwa zuciyarsa ya ringa bugawa da sauri da sauri kansa na juyawa ahankali yakai hannunsa ya ruk'o d'aya hannun Hajiya Nafeesa yana "ki yafemin Nafeesa bazan iya rayuwa babu ke ba Nima biyoki zanyi" daga haka ya rik'e zuciyarsa ahankali ya sulale k'asa Wani mugun ihu Suhaima ta fasa daya tilastawa mak'ota yar rige rigen shigowa Suna sallati Dan tun dazu suke so su shigo so suke b'arayin suyi nisa adai-dai lokacin da 'yan sanda suka k'ara so gidan suma Safna da suhaima da sahiba jijjiga Alhaji Nazifi kawai suke yi suna ihun kar shima ya tafi ya barsu Samha kuwa numfashinta ya ringa fita da sauri da sauri Saiam kuwa tamkar dutse tana nan a kankame da kan Hajiya Nafeesa ta zubawa waje d'aya ido Sallati mata hud'un da suka shigo da mazajensu suka tayi suna kiran Hajiya Nafeesa sai a lokacin Safna ta Ankara ba kaya ajikinta Dan had'a ido tayi da mijin wani mak'ocinsu yana mata kallon kurilla da sauri ta janyo hijabi tasaka A adai-dai lokacin da 'yan sanda uku suka shigo da mace d'aya Da k'yar yan sandan ya tilasta wa matan suyi shiru da su Suhaima Dan su tambayesu duk yanda akayi Alhaji Nazir dake gefen gidansu Alhaji Nazifi ne yafara cewa bari akai Alhaji Nazifi asibiti Dan yana numfashi kad'an kad'an da sauri suka kinkimeshi sukayi waje 'Yan sandan kuwa suka tsugunna a kusa da gawar Hajiya Nafeesa macen ta ringa d'aukar gawan hoto da wajen da jinin ke zuba akan tiles d'in kuka suke kamar ransu zai fita Ahankali macen ta matsa kusa da Saiam Dan tace mata ta sausauta rik'on da tayi wa Hajiya Nafeesa haka sabida ta d'auki fuskarta hoto Kukansu ne ya d'auke gabad'aya a lokacin da Saiam ta aza d'aya hannun ta abakin ta alamar suyi shiru ssshshhssh tace cikin whisper kamar bata San aji mai take cewa "kuyi shiru karku tashi mummy daga bacci bacci take yi ba mutuwa tayi ba uban waye yace mummy ta mutu to duk Wanda yake wa mummy fatan mutuwa shi zai mutu ba mummy ba dan haka Ku matsa karku tasheta Mummy ai baki mutu ba ko? ni nasan bacci kike yi ba gobe kika ce zamuje gidan Aunty khadija ba Ni nasan bazaki mutu ba lah mummy kinga wai kuka suke kin mutu" Wani mugun ihu Safna ta fasa tana tashiga uku ta lalace Aunty Saiam ta haukace su Sahiba kuwa jikinsu ya d'auki rawa suka zubawa Saiam ido dake kwantar da gashin Hajiya Nafeesa 'Yan sandan kuwa hankalinsu ne ya tashi suka hau yimata video still lokacin tana surutu ita kad'ai Samha kuwa zub'ewa tayi ak'asa Dan k'ok'awa take da numfashinta Ahankali aka fara rarrashin Saiam data k'ara rungume kan Hajiya Nafeesa kamar wacce za'a k'wace ta sai surutu take ita kadai tana yiwa Hajiya Nafeesa rad'a a kunne ganin bama tasan suna yi ba yasa suka fara k'ok'arin b'anb'are hannun Saiam daga kan Hajiya Nafeesa data rungume Wani mugun ihu ta ringa yi tana kar su tashi mummynta bacci take ba mutuwa tayi ba su rabu da ita kar su tasar mata mummynta.......... I really felt it wlh Allah ka biya mahaifinmu bukatunsu ka ara musu tsawon rai wayanda suka rasa nasu iyayen Allah ka kai haske kabarinsu alfarmar annabi Muhammad Saw Ina masoyan Sadnaf masu nemanta ido rufe ga contact din Sadnaf nan da Alphabet 0H0CCGCABCE Karku manta ishashen lokacin danake dashi shine Friday Saturday Sunday sauran ranakun sai ahankali amma bance bazaku jini ba incase idan ban poster ba working days sai kumin uziri [2:33PM, 4/7/2018] 鈥�+234 806 462 6766鈥�: 馃寫 馃寫 *B馃叞K'IN D馃叞RE*馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫 *Written by* 馃拝馃拝 *Sadnaf*馃拝馃拝 *A heart touching story* 庐 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS* _莎蓻 蓶啤艐'脓 啤艐俪醿� 蓻艐脓蓻艡脓膮谋艐 艐蓶 蓻蓶懦膯膮脓蓻, 醿撑� 莎蓻 膮俪艦啤 脓啤懦膯骚 蓶 骚蓻膮艡脓 啤蕜 艡蓻膮蓶蓻'艦_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM *#IG PML WRITERS* #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *Page 4* Ihu Saiam ke yi sosai ta kankame kan Hajiya Nafeesa akan kar atasheta bacci take ba mutuwa tayi ba Dak'yar matan suka banbare hannunta daga kan gawan Hajiya Nafeesa Saiam kuwa ta hau birgima a k'asa gwanin ban tausayi Matar Alhaji Nazir mak'ocinsu Alhaji Nazifi ce tafara ankara da halin da Samha take ciki dan kirjinta sama yake sosai Salatin da tayi da k'arfi ne yasa suka juya suka kalli inda Samha ke kwance cikin mawuyacin hali Sahiba hannu ta d'ora aka tana ta shiga ta uku ta lalace Da sauri 'yan sandan suka umarci matan da a saka Samha a mota itama tana buk'atar taimakon gaggawa Mata biyune suka kinkimi Samha sukayi waje da ita inda d'aya daga cikin 'yan sandan ya d'auko wani zani daya gani akan k'ofa ya rufe Hajiya Nafeesa Kafin ya maida hankalinsa kan Safna da Suhaima dake zaune a kusa da gawan Hajiya Nafeesa sai sheshek'a suke suna jiyo muryar Saiam da aka kulle a dressing room tana su bud'e mata ita mummynta bata mutu ba Da k'yar Suhaima ta iya basu labarin duk abinda yafaru d'aya d'an sandan yana recording d'ayan kuma yana rubuta statement d'in bayanan ta K'arfe takwas dai-dai yan uwa da abokanan arziki suka ringa tururuwa cikin gidan suna koke koke familyn Hajiya Nafeesa gabad'aya sai da suka zo ciki kuwa har da mahaifinta da mahaifiyarta Suna shigowa su Suhaima suka fashe da mugun kuka Safna ta mik'e da gudu taje ta rungume hajiyar su Nafeesa Dan tamkar an tsaga k'ara sabida kamaninsu da Hajiya Nafeesa banbanci kawai ita hajiyar su Nafeesa ta tsufa Agaban gawan Hajiya Nafeesa ta tsugunna ahankali ta yaye zanin da aka rufe mata fuska dashi Runtse idonta tayi da k'arfi data ga yanda jini ya wanke fuskarta Fuskarta ta kumbura tayi suntum Girgiza kai kawai take hawaye na gudu a fuskarta ahankali ta maida Zanin ta rufe Ta fara magana cikin wani irin yanayi tana "Nafeesa bazan tab'a yafe wa Wanda ya kasheki ba amatsayina na mahaifiyarki zanta addu'a Allah ya tarwatsa rayuwar Wanda ya kashe ki shi da kwanciyar hankali a duniya sai dai alahira" Kuka take sosai Wanda yasa duk wayanda ke palon kuka Mahaifin Hajiya Nafeesa kuwa yana daga nesa ya kurawa Gawan Hajiya Nafeesa ido jikinsa sai rawa yake yana tuno shekaranjiya da ta zo gida tana ta abubuwa haka kamar na bankwana sau uku ta na fita ta dawo idan suka tambayeta mai ta dawo yi sai tayi murmushi tace ta dawo ne tayi musu Sallama Ashe sallamar k'arshe take musu Ashe tafiyar da ba'a dawowa zatayi Alhaji Mamman fashewa yayi da kuka yana "Ya Allah ka tonawa wadanan azzuluman asiri Allah ka hanasu zaman lafiya a gidan duniya Allah ka wulak'antasu Allah ka dai-daitasu" Kuka Alhaji mamman keyi sosai Ahankali mazan suka fara mik'ewa suna Barin palon dan za'ayiwa Hajiya Nafeesa wanka a suturceta akai ta gidanta na gaskiya Ciki kuwa Saiam gajiya tayi da buga k'ofar ta sulale k'asa tana "Mummy ki tashi kice baki mutu ba baccine ya d'aukeki" Ahaka tayi ta sumbatu tana kuka ak'arshe ta koma tana sauke ajiyar zuciya ahankali wani irin bacci ne yayi awon gaba da ita ko minti biyar batayi da bacci ba tayi mafarki yanda take kwance Hajiya Nafeesa ta bud'e k'ofar d'akin ta shigo fuskarta d'auke da wani irin murmushi exactly kayan data sa ne ajikinta har da hular net d'in Zumbur Saiam ta mik'e tana nunata da hannu tare da cewa "Mummy dama baki mutu ba ni nasan mafarki nake yi ba mutuwa kikayi ba" Murmushin da Hajiya Nafeesa ke yine ya juye zuwa b'acin rai tafara magana tana "Haba Saiam Akan me zaki ringa Min kuka alkawarin da kika d'aukar min kenan kada ki sake ki k'ara zubar min da hawaye mutuwa Riga ce a Wuyan kowa idan lokacin tafiyarka yayi babu makawa sai ka tafi Dan haka nima lokacin tafiyata ne yayi addu'arku kawai nake bukata " Haba Saiam karfa ki manta kece babba ke ya kamata ki ringa kwantar wa da kanenki hankali ki zame musu tamkar uwa Daddynku na cikin wani hali kiringa kwantar masa da hankali ki zama jajirtaciya Dan Allah Saiam idan kun tuna ni kuyimin addu'a kawai karku manta azumin danace Ku rama min" Saiam da sauri tace "to mummy wai yaushe zaki dawo muna bukatarki mummy" Wani murmushi Hajiya Nafeesa tayi daya sata masifar kyau da haske tace "Saiam da kunsan inda zanje ayanzu da baki ce na dawo ba da Baku wahalar da kanku kun zubar da hawayenku ba inda zanje yafiye min inda na Bari sau dubu dan haka kucigaba da min addu'a Saiam kina so inyi fushi dake"? Da sauri Saiam ta girgiza kanta Hajiya Nafeesa tace " to karki k'ara zubar da hawayenki karki k'ara bari kannenki suyi kuka ko daddynku maza tashi ki tafi d'akinku kije kiyimin addu'a kafin akaini makwancina" Duk mafarkin da Saiam tayi baifi cikin minti biyu ba da sallati ta mik'e zumbur tana bin ko ina na d'akin da kallo gani take kamar ma ido biyu Hajiya Nafeesa tazo mata ba mafarki take ba maganganun da Hajiya Nafeesa tayi mata sai amsa kuwaa yake a kunenta Da sauri ta nufi k'ofar ta fara jijjigawa tana cewa a bud'e mata Adai-dai lokacin da aka gama yiwa Hajiya Nafeesa sutura aka sata a tsakiyar d'akin Ganin bugun k'ofar da Saiam take yayi yawa ne yasa Aka je aka bud'e mata k'ofar da sauri ta fito daga d'akin har tana tuntub'e Cak ta tsaya ta kurawa makarar dake tsakiyar d'akin ido an lullub'e Hajiya Nafeesa da farin likkafani Ahankali ta ringa tafiya har sai data k'araso gaban makarar ta tsuguna ahankali wasu siraran hawaye suka zubo mata Da sauri ta d'auke hawayen da bayan hannunta ta runtse idonta cikin dakewa da karyayar zuciya tafara karanta suratul Rahman cikin wani irin rawar murya mai d'auke da kuka aya goma kawai ta iya karantawa tafara jero addu'oi tana yiwa Hajiya Nafeesa Addu'a 'yan d'akin kuwa sai ameen suke cewa Ganin maza sun fara shigowa zasu zo su d'auki gawar Hajiya Nafeesa ne yasa hajiyar su Nafeesa zuwa ta janye Saiam Aikuwa kamar ta zuga su Saiam dasu Safna tuni suka fashe da wani irin kuka suna kallon makarar Hajiya Nafeesa da akayi sama dashi kuka suke sosai suna shikenan mummy ta tafi Duk inda ka kai da taurin zuciya sai ka zubar da hawaye Saiam kamar d'aukewar ruwan Sama tayi sauri ta tsayar da kukan da take ta kamo hannun su Safna gabad'aya tafara goge musu hawaye tana "mummy tace kar mu sake mu zubar mata da hawaye idan ba so muke tayi fushi damu ba tace muringa mata addu'a kawai" Tausayin Saiam ne ya k'ara rufe duk wayanda ke d'akin dan sun d'auka duk zafin mutuwar Hajiya Nafeesa yasa Saiam ta fita hayyacinta bata San mai take cewa ba Fad'ar mutanen da suka sallaci gawan Hajiya Nafeesa b'ata bakine dan sai da aka kashe hanyar da motoci suke wucewa dan inda makabartar yake da dan tazara sosai daga gidansu Hajiya Nafeesa ahaka aka kai Hajiya Nafeesa dubanin mutane na yabon hallayenta na gari banda kananan yara da har dasu aka je binneta suna ta kuka Hajiya mai raba musu alewa duk ranar juma'a ta mutu Idan ka kalli yanda su Saiam suke zaune waje d'aya suna Jan carbi hawaye da majina na zubo musu lokacin da zaka fara hawaye ba sani zakayi ba Bama sa iya amsa gaisuwar da ake musu ciki kuwa har da saurayin Saiam da Safna da zasu Aura suna ganin halin da su Saiam suke ciki sai gashi hawaye ya hau zubo musu sabida adaren da Hajiya Nafeesa zata rasu da suka zo zance suka je suka gaisheta haka kawai ta hau yi musu wa'azi da nasiha tana kan kujera sanye da hijabi da fararen hakoran maccanta sai murmushi take she is very social and civilized dan har ga Allah har suka je gida suna yabon halayenta ashe mutuwa na nan tafe Saiam cikin dakushashiyar muryarta ta kalli Suhaima tana tambayarta inda Samha take da Daddy dan duk abinda akayi basani tayi ba Anan Safna ke ce mata suna asibiti Alhaji Nazir ya kaisu jijjiga kanta kawai tayi ta mik'e aka hau tambayarta ina zata je Cikin muryarta da bata fita tace zata je asibitin ta gano halin da suke ciki dan tamkar yanzu Hajiya Nafeesa ke ce mata ta kwantarwa da Daddynsu Hankali da kanenta Fawazz Saurayinta da sauri ya mik'e yace zai kaita asibitin Saiam ko kallonsa bata yi ba tayi waje kamar iska zai d'auketa .... Nikam sai dai kuyi maneji Allah dak'yar nayi wanan Mutuwa rigar kowa wacce ba cirewa ta d'auki Hajiya Nafeesa jikanta sarki buwayi Hajiya Nafeesa Allah ya jikanki rabbi shi yayi kiranki kullum muna ta tunaninki muna yabon halayarki Ya Allah ya Allah ya gufuru ya Allah ya Allah Ya Allah gafarta mata ya Allah ya Allah馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶馃槶 Allah kasa mucika da kyau da imani [2:34PM, 4/7/2018] 鈥�+234 806 462 6766鈥�: 馃寫 馃寫 *B馃叞K'IN D馃叞RE*馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫馃寫 *Written by* 馃拝馃拝 *Sadnaf*馃拝馃拝 *A heart touching story* 庐 *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS* _莎蓻 蓶啤艐'脓 啤艐俪醿� 蓻艐脓蓻艡脓膮谋艐 艐蓶 蓻蓶懦膯膮脓蓻, 醿撑� 莎蓻 膮俪艦啤 脓啤懦膯骚 蓶 骚蓻膮艡脓 啤蕜 艡蓻膮蓶蓻'艦_ #WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM *#IG PML WRITERS* #https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035 #http://maryamsbello.blogspot.com *sadaukarwa ga dukanin masoyana na zahiri da badini da wayanda na sani da wayanda bansani ba Sadnaf na kaunarku kamar yanda kuke kaunarta ana tare insha Allahu*馃檹馃檹馃檹馃檹馃檹馃檹 Page 5 Ogansu Sai daya gama shek'a ayarsa da linder ya fito ya shirya a cikin manyan kaya kai ahaka idan ka ganshi zaka d'auka mutumin arziki ne Dan har da su hula yasa Yana fitowa daga d'akin su Lion suka mimmik'e har da Akram da kansa ke balain ciwo Hannunsa a sak'ale yake a k'ugun Linder ya sakar musu wani jairin murmushi yana "Killer lion scorpion black Akram Ni zan tafi Port Harcourt wajen iyalina zan dan huta haka kamar na 3weeks kafin mu kuma fita wani operation d'in inda nake tunanin wanan karon kano muka nufa dan akwai wani Alhaji Buba mai gwala gwalai yana da balain kudi ina nan ina monitoring d'insa akwai wata servant d'insu Habiba ita nakeso na jawo jikina in sakar mata kud'i ta bani details d'insu sosai da yanayin gidan immediately ina gama samun Duk wani information akansu zan kiraku Ku fara shirye shiryen daya kamata" "Sanan kafin lokacin idan kuna da wani uzuri zaku iya zuwa kuyi amma kwana uku kawai na Baku dukanku Ku dawo do I make my self clear"? Da sauri dukansu suka gyad'a Kansu suna yes boss Daga haka ogansu yasa kai ya fice daga palon suna take mishi baya still yana rik'e da kugun Linder dan shi zaiyi dropping d'inta a hanya Sai da Killer yasaka mishi brief case d'in kud'inshi abayan boot kafin ya ja da baya Ogansu kuwa yaja katon jeep d'in yabar harabar gidan Ciki suka koma gabad'aya kowanensu yafara shirin tafiya uzurinsa akwai masu zuwa su duba iyayensu irin su Lion da sukayi wa iyayensu karya akan aiki suke a Abuja akwai irinsu black dake da iyali da suma suka shirgawa iyalinsu karya akan suna aiki a abuja Akram ya rigasu shiryawa gabad'aya dan ji yake kamar akan k'aya yake Kallonsu Lion yayi fuskarsa d'auke da murmushi adai dai lokacin da yake rataya jakarsa a kafad'arsa yace " to ni kunga tafiyata zanje naga parent d'ina da siblings d'ina zan kai musu d'an abunda muka samu insha Allahu bazan wuce 3days da boss ya d'ibar mana ba" Dukansu murmushi sukayi dan haka kawai Allah ya had'a jininsu da Akram shiyasa ma koda an fita operation dashi baiyi komai ba basa damuwa Killer ne yace " same here muma zamuje muga namu iyayen akwai kanwata ma da za'ayi bikinta nasan suna nan suna zuba ido dan dani suka dogara Nima zan kai musu abunda ya samu" Murmushi kawai Akram yayi a zuciyarsa yana tausayin halin da suka jefa Kansu sabida talauci yana tausayinsu ranar da asirinsu zai tonu asaka musu ankwa a hannu all they are a doing is for d sake of their family Duk rashin aikin yi ne ya janyo musu fad'awa halaka ciki kuwa har da rasa imaninsu tunda basu d'auki kisan kai abakin komai ba D'aya bayan d'aya ya bisu ya rungume yana ce musu sai sun dawo nan da kwana uku daga haka yasaka kai ya fice daga gidan dayake ji tamkar prison bai zame ko ina ba sai head quarter d'insu na Ss Agajiye ya k'arasa office d'inshi ya dafe kansa dake Sara mishi har yanzu yana jin ihunsu Samha a kunensa ko yaya ya runtse idonsa sai ya hango abubuwan da suka faru a Daren jiya Haka kawai yaji ya tsani kansa yana tuhumar kansa shima da laifin shi awajen kisan Hajiya Nafeesa sai yanzu yake mugun daya sani da ya d'auki mataki tun a lokacin daya sani ya harbesu duka dayaga yanda Hajiya Nafeesa ke fad'i tashi akan ta kare martabar 'ya'yanta idan kuma ya tuna kwanan ta ne ya kare sai ya rage ganin laifinsa ahaka ya zauna wajen minti ashirin kafin ya iya mik'ewa ya Shiga band'akin dake cikin office d'in ya d'aura alwala yazo yayi sallar Azahar yana idarwa ba tare da b'ata lokaci ba ya nufi office d'in ogansu Bayan sun gaigaisa kamar yanda suka saba da tambaye tambaye ogansu ya tambayeshi abubuwa daya k'ara samo musu akan Alhaji Bala Akram jiki Asanyaye ya mik'a masa 'yar k'aramar Camerar dake hannunsa ogansa kuwa ya k'arba a dokance Cikin minti biyar ya had'a camerar da system d'in dake gaban table d'insa Tun daga yanda suka shirya da zasu tafi operation har zuwa yanda suka d'aure mai gadin gidansu Hajiya Nafeesa daya bud'e musu k'ofa tagumi ogansu yayi yana kallon system d'in dake gabanshi jikinsa sai rawa yake yabi ya jike da gumi duk da sanyin Ac dake ratsa office d'ind'in Wani irin kad'awa idonsa yayi ya mik'e jikinsa na wani irin k'yarma "innalillahi wa inna ilaihi rajiun" kawai yake maimaitawa ahankali ya kalli Akram daya dafe kansa da hannu biyu k'walla na zuba a idonsa dan wani irin zafi yake ji a zuciyarsa dayake jiyo sautin kukan Hajiya Nafeesa da su Saiam magana ya fara yi yana "Akram meyesa baka ceci rayuwar matan nan ba meyesa bakayi wani Abu dan kar Alhaji Bala ya harbeta ba tunda nake ganin abubuwa ban tab'a ganin abun tausayi irin wanan ba matan nan tabani tausayi fiye da tunanin mai tunani Alhaji Bala ya Dade yana abubuwa amma this time around his cup is full bama bukatar wani prove ko evidence wayanda muke dasu kawai sun ishemu enough is enough lokaci yayi da ya kamata mutane su San waye Alhaji Bala lokaci yayi daya kamata ace mutane su San irin sana'ar da yake yi" Rawa jikin shi ke yi sosai idonsa jajawur Akram kuwa ko magana ya k'asa yi dan shi kad'ai yasan halin da yake ciki Ni kam waye wanan Alhaji Balan ne toh bari muji waye shi Alhaji Bala haifaffen dan jigawa ne a kauyen kafin Hausa su hud'u iyayensu suka Haifa duka maza sun taso ne a cikin tsananin talauci dak'yar suke cin abincin sau biyu arana tunda Bala ya taso ya taso da masifar San kud'i dan idan ya zauna da mahaifiyarsa Saude haka zai taba ta labarin irin kud'in da zaiyi idan ya girma da abubuwan da zai mata da kanensa sabida mahaifinsu ya Dade da rasuwa ahaka Alhaji Bala ya taso da mugun San kud'i duk da mahaifiyarsu Saude na matuk'ar k'ok'ari dan taga ta sama musu ingantaciyar rayuwa Alhaji Bala na da shekara goma sha biyu ya fara buga buga shine noma shine aikin gini sharar kwata duk wani Abu daya San zai shigo masa da kud'i yinshi kawai yake ahaka rayuwa tayi ta tafiya dak'yar ya gama primary sch a kauyensu inda daga nan ya tattara karatun ya watsar ya cigaba da Neman kud'i yana kula da mahaifiyarsa da kanensa uku Saidu Abubakar da zaidu ahaka Alhaji Bala ya ringa Tara kudin da yake buga buga inda ya Tara wajen dubu biyar a lokacin kudine masu daraja da yawa shawara yayi da mahaifiyarsa Saude da ta tsufa tukuf wanda a zahiri ba tsufan tayi ba tsabagen talauci ya tsufar da ita Shawara ta bashi akan yaje birni ya saro shadodi da atamfuna masu kyau na manya da yara yanda basai aringa wahalar zuwa birni siya ba aikuwa take yabi shawararta dan babu inda ake siyarwa a kauyen Aikuwa cikin sa'a ya saro kayan dan kayan basa sati ake siyesu har da masu kawo mishi kud'i ya hada masu lefe awanan lokacin Watarana yaje birni zai sari kayan an gama loda mishi kayan a mota kenan zai hau yaji ana ta mishi horn abayansa Juyawa yayi yaga wata had'adiyar mota ya had'iyi wani irin yawu dan sai ka isa zaka iya siyan motar kafin ya gama karewa motar kallo aka bud'e k'ofar motar aka fito buhun hannunsa ya wurgar ya tafi da gudu ya rungume abokinsa Ukashat da sukayi primary sch tare Sai da ukashat ya kalleshi daga sama har k'asa kafin yace ya yaganshi haka Shi dai Alhaji Bala baki a sake kawai yake bin ukashat da kallo da kayan jikinsa da motarsa Horn mai motar ya ringa yiwa Alhaji Bala dan yazo su tafi Ukashat kuwa yace yaje ya hau zai biyosu abaya Aikuwa haka akayi har k'ofar gidansu Alhaji Bala Ukashat ya bisu sai da aka gama sauke kayan gabad'aya Sanan Alhaji Bala ya nufi wajen ukashat dake hakimce a cikin motarsa yana yatsina fuska kamar Wanda yaga kashi d'aya barin Alhaji Bala ya bud'e ya shiga ya zubawa ukasha ido yana mamakin yanda akayi yayi kud'i acikin shekara takwas kawai da

Chapter 3 of 13