Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 4
don ku rabu lafiya kin san.... Haba Bebi na fada miki bana sonsa bana Kaunarsa inkuwa na aureshi to ina mai tabbatar miki da cewa mutuwa zanyi don bakin ciki, tai dariya ta ce yanzu Ameerah bakin cikin wani yana iya kashkei? Haushi gami da takaici suka cikan zuciya nace Bebi na gode ai dole kiyimin dariya tunda ke kina zaune gidan mijinki hankali kwance, haba Ameeraha inariga nasan duk abin da kike ciki na kuma gamsu dake sosai ta taso daga inda take ta dawo kusa dani ta dafa kafada ta ta ce yanzu abin da zamu fara yi shine muje wajen Kaka Aisha mu baiyana mata komai da komai mu fahimtar da ita duk yadda lamarin yake idon idan munga ta fahimci abin da muke nufi sai mu roketa da taje wajen Alaramma tai mai bayani kamar yadda mukayi mata, idan kuma muka ga taki fahimta to sai muje da kanmu muyi masa bayani, nace uhn! Bebi kamar ba yau muke tare dake ba kin manta da halin zuriyarmu kuma kinsan nasha gaya miki irin tsatstsauran ra ayinsu sannan kice wai muje gidan Alaramma ai kinsan ma kawai cewa zaiyi suzo jibi a daura auren kowama ya huta, Bebi ta ce to yanzu kamata ya yi mutashi muje wajan shi Sunusin mu lallasheshi ya janye maganar Auren ko ya kika gani? Nayi shiru nasan ku yarda kaina tunhanin sannannn na dago nace da bebi kai bana jin Sunusi duk lallashin da zamuyi masa zai janye wannan abune mai wahalar gaske, ke dai baki sani ba tunda ance sai an gwada akan sannan na kawarai kuma a rashin tayi akan bar araha, dan haka ba zakakiyi saurin yanke hukunci ba zuwa zamuyi mu lallame shi Allah Annabi in kukai haka kila yaji tausayin mu ya janye, to shikenan Bebi si ki bari zuwa jibi ki same ni a gida kinga in na rakoki sai mu wuce wurin sa muji wai nar da yake toya wa tunda in ba haka ba futa yanzu a bune mai wahala, to ai shike nan Ameerah Allah ya kaimu. ******** ********* A washegari ne kuma ina tsakar gida ina yiwa Anti tsintar shinkafa ita Anti tana daki sabili da a yau ma Kaka Aishat tazo suna can suna tattaunawa nasan dai a kaina ne, daga baya ne Anti ta kira ni nayi sallama nashi ga cikin daki, ganin Anti ta kalleni...... cikin barara ta ce bani nake kiran ki ba ga mai kiran ki nan.......Kaka Aishat ta ce Ameerah me yasa kike son ki ta dawa mutane hankali, ki sani ko ni kaine ba'asan raina za'ayi miki auren nan ba, tunda dai ba kya so to amma ya muka iya, ai sai dai hakuri in Allah ya yadda ba za ki bekin ciki ba, na sa kuka ni wallahi ba na sonsa ni dai ku hada ni da kowaye amma ba Sunusi ba, don ba na sonsa ko kadan. To Ameerah wallahi da kaina naje wajen Alaramma amma banyi nasara ba, ba kiji irin fadan da ya yimin ba, wai shi ba za'a mai da shì karamin mutun ba, tun da ba'a son Ameeral ta, ba ta zo duniya ba a kewa Yarinya g ka gama borenta daga baya a zauna lafiya lau cikin kwanciyar hankali. "Ni dai na bashi hakuri, na ta shi na taho, dan hakak ni dai abinda zanjaddada miki bai wuce ki dai yi hakuri ba." Ni kam ban da kuka babu abin dana ke yi, ni kaina bansan a kan me na ke kukan ba, kukan bakin cikina ko na takaici ko kuwa na mamaki abin da Sunusi ya yi min ne. cikin wannan haline Kanin Antina, da muke kira Kewu Aminu ya shigo ya iske mu a haka nan dai nan ya shiga tambayar su... wai meye ta ke kuka.?" ya tambaye su. Kaka Aishat ta ce "A kan dai maganar nan ta aurenta ne da wai ba ta son mijin ka ganta nan rarrashin duniyar nan babu wanda ban yi ba amma ta ki hakura."ya ce "To kuma me nene na rarrashinta ba sai ku kyale ta tayi ta yi ba, in ta gaji za ta dai na...... Na katse su da fadin "Vallahi Kawu tun farko na gaya mu su ni ba na son shi kuma duk tsanani ba zan aure shi ba." Ban san lokacin da ya dira a gabana sai ganinsa kawai na yi har inda na ke ta ke ya fitar da hannu ya shararan mari, ya kuma cigaba da fadin "dan ubanki sa'o inki ne ki ke fada musu wannan maganar da ba ta dace ba, ta shi ki fita ko kiji ba dadi.?" Na mike ina kuka na fita tsakar gida na zauna. A washe gari ne bayan mun shirya ni da Bebi sai muka nufi ioda muke da tabbacin zamu samu Sunusi na nunawa Bebi shagon nasa kinga shagon nan ni dai anan na san shi, domin anan muka taba haduwa da shi, to ni ban sani ba kó nanne ko kuma zuwa ya ke yi cho." Ai kuma a kulle ya ke ba mamaki ya tafi masallaci tun da yau Juma'a an fara tafiya masallaci.?" 18 Na yi shiru dan ni ina ganin kamar ita ke nan damar da nake da ita kuma ta wuce ni shi ke nan yanzu ta wuce ni, yanzu auran dole za'a yi min zan auri wanda ko a mafarki ban san inganshi balle ace yau shi ne mijina. Bebi ta dafa kafadata "Haba Ameerah ke fa halin ki ke nan komai na ki sai kinyi kuka kullum cikin kuka ko gajiya ba kyayi, kiyi hakuri Insha Allah komai zai zo da saukI." Na yi dan murmushi lokacin dana share hawayen da ya batan fuska nace "Ba komai Bebi na gode da kulawarki a gare ni zo mu tafi.?" "Lafiya me kuke nema.?" Aka tambaye mu. Gaba daya muka juyo muka kalle shi wani dan kaukauran saurayi ne wanda zan iya kiransa wankan tarwada ya kara so kusa da mu ya na fadin """"yan mata lafiya ne kuke tsaye anan wajan.?" Na yi saurin waigowa da dan takaitacen murmushi nace "A a ba komai dama munzo neman wani ne wai shi Sunusi to kuma sai muka tarar da shagon a kulle." Ya yi dariya ya ce "Af ku na nufin ku ce kun zo wajan Sunusi ne.?" "Ina fatan dai lafiya.?" Cikin murmushi Bebi ta ce "Lah! ba komai wallahi hala kai abokinsa ne.?" da sauri ya gyada kai yace "Ah! ai in ki kace haka kin takaita don kwa ni ina ganin na zarce aboki sai dai amini." Na kalli Bebi, Bebi ta kalle ni to amma tun kafin mu yi magana sai ya ci gaba da fadin "Idan wani sako ku ke da shi kwa iya gaya min, in ya so in ya dawo sai na fada masa domin rabona da shi, na dan kau da kai na ce "To ba komai in ya dawo ace Amira ce ta zo nemansa ba ta same shi ba.?" ya ce "To shi ke nan insha Allahu da ya dawo zan sanar masa." Shi ke nan mun gode muka fada kusan a jere ni da Bebi. **** **** 19 Bayan saukowa daga masallaci ne aka aiko ana kirana a waje. Na ce "Je ka ka ce ba ta nan." Kai tsaye Antina ta kalle ni "Ki je mana ki ga wanda ya ke kiranki.?" na mike na fita. Na figi mayafi ina kunkuni ba tare da raina ya so ba na taddashi yana tsaye kusa da babur din shi ya na ta faman murmushi ya ce "Malama Ameerah ya gari, ya kuma kuka zo gida dazu, na zo na sami sakon ki a wajen abokina Muftahu, ina fatan lafiya.?" Nayi kokarin sakin fuskata tare da kago murmushin dole na ce "Lafiya lau illa dai kawai na je ne akan wata alfarma da na ke nema.?" "A wajena!?" ya fada yana mai nuna mamakinsa yace "kwarai kuwa."ya ce "To ta me.?" Na ce "Tabbas nasan ka na so na, so sai kuma na riga na fada maka cewar ba zanyi aure ba to amma duk dana fada maka hakan baka hakura ba har ka dauki kudinka ka aika da shi to duk da hakan ba taci ba na san so na ne ya jawo, to sai dai ni a waje na sai aka sami akasi hakan ba zan iya aurarka ba, hakan ne ya sa tun farko na fada maka gaskiya to amma kai ka ki ka gane me ya dace ka yi don haka alfarma da na ke nema ita ce ka yiwa Allah da Manzansa ka Hakurar min wannan masifar ka janye abin daka ke nufi a kaina, wallahi na shiga wani hali na daban dan Allah ka tausaya min kayi hakuri kai ka dai ne wanda zan kaiwa kuka na ka share min hawayena har ga Allah ni ba na son wannan auran.?" ina kuka ina rokonsa. Munfi minti uku ba wanda ya yi magana bayan na gama maganata ni kuwa ban da kuka ba abin dana ke yi ina cewa "Don Allah ka tausaya min ka taimaka min.?" 20 Ya katse ni yace "Ya isa Ameerah share hawayen ki ki kuma saurareni ni kaina ina tausayin kaina ina cewa ina ma Ubanginji bai kaddaro haduwar mu ba ina bakin ciki idan na tuna da wai Ameerah da na ke so na ke kaunar ta fiye da kaina na ke kuma kasa barci saboda tunaninta ita ce bata so na, take wasu siraran hawaye suka soma zirara daga idanun shi ya kuma cigaba da magana cikin raunanniyar murya ki yi hakuri Ameerah na yi imani har abada ba zan daina son ki ba, ki yi hakuri ki dauki wannan a'l'amari а matsayin kaddara garemu kuma ni a kullum cikin yakinin wata rana za ki so ni, ki tai mana addu'a' Allah ya zabar mana abinda ya fi alkhairi a garemu cikin kuka ya ce "Yaya za'ayi kace wata rana zan so ka alhali ni na san ba zan ta ba son ka ba har iyakar rayuwata."ya ce "Zan so ki?" Ya yi murmushi shi ke nan Ameerah ki ta ya ni addu'a ni ma Allah ya cire son ki daga cikin zuciyata shi ko.?" Na daga kai alamar I, ya mike tsaye daga.kan babur din to yanzu sai yaushe Ameerah.?" Nace shi ke nan ina jiranka in ka ji ka daina son nawa ka aiko a karôl kudinka ni ban ce ka kuma zuwa wajena ba na juya na shiga cikin gida na barshi anan. Ina shiga gida na wuce Anti a tsakar gida Can ko kalli inda take ba kai tseye daki na wuce da sniga ta na fada kan gado na bude wani sabon babin kukan. Ban ji shigowar Anti ba, sai kawai ji na yi tai kiran sunanana sanyaye, kunan da ke cikin zuciya ta ta hanani in iya amsa wa Anti, kiranta na ci gaba dai da gunjin kukana. Anti ba ta hakura ba sai ta sake kiran akaro na biyu to wannan karan ma dai ban amsa ba kukan dai na ke yi lalle Ameerah amma kin bani mamaki wato a yau 21 kiyi wayon da zaki nunan ba ni na haife ki ba ko.?" Kin nunan iya kata tunda har nayi kiranki ban samu ko amsawa ba, saboda ba ni na haifeki ba, to amma Ameerah da kinyi tunani da baki yimin haka ba, ko ba komai na rike ki amana. Ta yi waje fuu cikin fushi. "Wa iyazu billahi ban san lokacin da na hanzarta tashi zaune ba, duk da matsanancin tashin hankalin da ke tattare da zuciyata sai na jisu ba komai ba ne akan na yanzu wato abin da anti ta fada game da ni ko kusa ko alama abin ba haka ya ke ba, yaushe zanyi wani yunkuri dan in gwadawa Anti iyakar ta, cewa ni ba ita ta hateni ba duk da irin halaccin da ta nuna min.?" nti ******* ***** ******* Sadiya shine cikakken sunanta kuma kanwace a wajan mahafiya ta uwarsu daya ubansu daya tun lokacin da auran mahaifiyata ya w a lokacir ina yar shekara shida kuma dama yawancir hutuna nafi yin sa ne a gidan Anti don haka matsananciyar shakuwa ta shiga tsakaninmu sai ya zama d dai lokaci da auran mahafiyata ya mutu ya zo dai da da lokacin hutuninu ina gidan Anti don haka iokacin ban sake komawa gida ba hakan ya samo asaline daga wajan mijin Anti saboda shima yana matsayin abba a wajena, ta bangaren kaka Aisha don haka ta tsaye szi na zarce da zama gidan Anti na taso cikin matukar kulawa da samun cikakkiyar tarbiyya saboda macece mai hakuri da zumuci ba ta bambanta tsakanimu da 'ya'yanta haka zalika shi ma mijinta mutunne mai kirki ya na bani kulawa sosai.... Jikina a sanyaye na tashi na nufi wajan Anti na iske ta zaune a tsakar gida tana zaune kan kujera 'yar tsugune ta yi 22 tagumi da hannayenta biyu fuskarta dauke da matsanancin bacin rai. Na tsuguna a gabanta cikin muryar kuka na kira sunanta "Anti na zo ne don na ba ki hakuri saboda yadda na ga ranki ya baci kuma hankalina yai mummunan ta shi saboda jin lafazin bakinki, wallahi Anti ina so ki sani na rike ki uwane tamkar yadda ki ka rikeni 'ya a gare ki kuma harga Allah ba ni da niyyar yin wani abu don janyo bacin rai a gare ki ballantana nayi abin da zai zama na nuna ki ba ke ki ka haife ni ba. To amma Anti game da maganar Sunusi a yadda na ke ji a zuciyata da na aure shi gara rayuwata gaba daya na tsane shi na ki jininsa don haka bana kaunar ganinsh Anti.... Sannan sai kuka ya ci karfina cikin karaji kukan naci gaba da fadin "Don Allah Anti ki taimake ni don bana san Sunusi ba zan iya auran Sunusi ba, Anti duk da ni 'yar nan Anti, babu mai iya sharemin hawaye na sai ke don haka ki taimake ni Anti ki goyi baya na akan a kyale ni da maganar Sunusi.?" Anti ta dago kai cikin matsanancin tausayi ta riko hannayena ga mamakina sai naga hawaye ya soma zuba daga idanuwata cikin raunananniyar murya ta soma fadin "Tun farko Ameerah da da yadda zanyi da nayi don ganin tsatstsauran ra'ayin Alaramma bazan iya dosar wata mai kama da wannan ba to amma ni shawarata mu dukufa da du'a i ina ganin ita ce hanyar samun mafita a garemu.?" **** ***** **** komai ya rincaßemin ga shi duk wanda na je wajansa akan ya taimakamin kowa sai yace da ni in yi hakuri amma babu mai iya cewa Alaramma mai da kudin nan kowa na tsoronsa, wani baban abu da ya fi 2 bani mamaki dai dai da mahaifina ya san halin da na ke ciki amma ya nu na halin ko in kula saboda tsoron Alaramma ko da ya ke su duk a hangensu wannan wata sabuwar fitinace da na zo da ita saboda yadda aka saba aurar da yarinya ba sai lalle ta san mijinba, ballantana ayi maganar so don haka duk inda na shiga babu mai goyan bayana. To a yauma Juma'ace da tsakar rana na dirar ma Kaka Aisha da kukana, kaka Aisha ta dubeni a galabaice cikin gajiyawa da wannan al'amari ta ce "Tabdijan nan ke yanzu da abaki hakura ba.?" "Lallai kina da aiki a gabanki to waima me ye da Sunusin ina ce yaran yana da dan abin hannunsa wanda zai iya rike mace ba shi da mugun hali me ake nema da mutum haka kawai duk kin bi kun kwarzabi kanki to Allah ya kyauta.?" Na gaji kirki kuma zuwa ki tunkareni da wannan maganar kinji na fada miki kuka ne kije kiyi ta yi har ruwan idonki ya kare.?" Nace "Ni yanzu....." na kasa ci gaba da maganar saboda kuka ya ci karfina. Kaka Aisha ta katse ni ke bari na fada miki gaskiya aure dai babu fashi in dai ba wani ikon Allah ba, don haka in zaki hakura ki hakura in kuma kin kI kije ki tayi.?" **** **** **** A daran ranar ni dai dan tsabar nace da rashin zuciya Sunusi ya sa ke zuwa ya aiko kirana cikin tsawa 9 na kori yaran nace ya tafi ya ce na ki na zo.' Nan dai Anti da ke cikin daki ta fito tana fadin tashi kije mana, ba na son irin haka Ameerah. 24 Nai shiru kai na a sunkuye ban ko motsaba ballanta in tanka mata, cikin tsuke fuska Anti ta ce yanzu Ameerahn ina yimiki magana ki na jina ko.?" Saboda kin mai dani 'yar iska, shi ne ki ka yi min shiru to walahi ba dai a gidan nan ba, don ba zaki jawo min tashin hankali ba. Don ba zai yiwu ace ni na ke zuga ki ba haka kawai. "Anti me nayi miki kuma.?" Ta ce tun yaushe nace da ke ki tashi ki je kiran da Sunusi ya ke yi miki amma kina jina ki ka yi kamar ba ki ji ni ba. Na mike cikin saurin naja mayafina akan kaure na yafa na fita. Yana soro ya na jirana na fito ya kalle niya ce sannu Ameerah duk na ji abin da ya faru ina jida kunne na sai dai ina mai baki hakurin da ki je ki daure ki bani hadin kai micimma burinmu ko in ce na cimma burina, ni kuma na yi miki alkawarin ba za ki tabayin dana sanin aure na ba tun da.... Na katse masa hanzari na се kai dakata min me ka ke san ka ce da ni, meye ya ba ka yi min ba? Haka ake son.? Ka ce dama kana sona ka kuma jefani cikin masifa da tashin hankali ka hadani da iyayena akar ka iyayena suna fushi dani ko kana nufin ka ce da ni duk a cikin da ka ke yimin ya ke.? Na girgiza kai cikin bacin rai na ce to bari na fada maka wallahi ko a mafarki ba zan aure ka ba, in kuwa ka ganni a cikin gidanka to tabbatar da cewa gawata ce aka kai. Ka ji na fada maka ya dan yt shiru kana ya share gumin daya bata masa fuska. ya ce to Ameerah naji abin da kika če amma don ki taimakamin da ruwan sha. Kanar kar naje to amma daga baya sai na canza shawara na yi tsaki sannan na juya na shiga cikin gida. 25 Na ce Anti wai ruwa ya ke san zai sha. ta de to dauki wannan (Jug) din ki dibar masa mai sanyi cikin firji na dauki kofin na debi ruwa na fita. Ban yi wata wata ba sai kawai na kwara masa а jikinsa gaba dayan ruwan ya sheke tun da ga fuskarsa har jikinsa. Cikin gaggawa ya dago da kansa ya dubeni ya dubi jikinsa ya yi murmushi ya ce Ameerah ke nan wannan kuma menene fa'idarsa.? Na kalle shi çikin harara na ce ai kafi kowa sanin fa'idarsa. Ya ciro hankici cikin aljihunsa ya fito da shi ya goge fuskarsa ya bude but din babur din ya ciro wata leda sannan ya mifonin ya re ungo wannan na kalle shi na kalli ledar in yi me da ita.? Ya ce siyo miki na yi yanzun nan da zan taho nan sai naji ina jin yunwa to shine na shiga kanti na siyo biskit din to dan naci sai na ji dadin sa shi ne na a ya kemata ke ma in sayo miki. FHuushi da takaici su ka kamani na mika hannu na karba sai na farke ledar biskit din a kasa duk na tattaka sıka zama gari sannan na tsuguna na de bi garin biskit din na watsa masa nace me zan yi da abin ka ance da kai ní ma wadayayyyiya ce irin ka.? ya ce lokacin ds ye ke kade biskits din dana zuba masa Ameerah ke nan wallahi ki na bani sha'awa kuma komai ki ka yi burgeni ki ke yi don haka na ke kara son ki ko banza dai na san na sanu matar da ba zata bari a raina ta ba, kin san wani abu kuwa? Na juya na shiga cikin gida yai ta fi vman kirana amma ko da wasa ban wai goba. *营 ****** A gaskiya na shiga wani hali da ban taba naninan shige shi ba a rayuwata sabili da haka ni 'yar gata ce awni io amma a yanzu a sanadiyar 26 Sunusi ta yi watsi da ni ko abu ne za a ba ni in mikon kafin in kai gare ta sai ta jehomin haka zalika ko mai nayi sai harara ni ba abin in ce zan koma hannun mahaifiya ta ba, to ma in na tafi can ma itama ba wai abu da yimin tunda ko hirama ba ta yadda ta yi da ni ballantana ban taba yin ko da wata 'yar doguwar magana da ita ba sabili da wai ni ('YAR FARI CE) dan haka babu ruwanta da ni, hakanne ya satun farkon fara wannannin rikici ba ta taba sanya bakinta ba. A yanzu haka ya zamo a cikin gida ba ni da abokin hira tsakanina da kowa sai kyara da tsangwama, ba ni da abinyi da ya fice kuka haka zalika a makaranta wani lokacin nakan ce to waini AMEERAH DA MЕ ZAN JI. **** **** **** A cikin wannan hali ne ranar wata Asabar ina kwance ina fama da wani irin zazzafan zazzabi da ciwon kai, ga shi duk ilahirin jikina bani jin dadinsa, haka zalika ga kunan da zuciyata ke yi wanda ya sanya a dalilin lamarinmu da Sunusi da ke damuna. Kawata Bebi ta shigo dakin da nake kwance ina rawar dari dama a yanzu komai na wa ya koma can dan tunina daina shiga cikin mutane haka nan kuma na dena karanta duk wani Littafin da ya kunshi soyayya dan ni ina ganin hakan shi ne ya fi dacewa da ni tun da ni ba masoyi ne da ni ba kuma wama zan yiwa so da har zan koya.? Bebi ta daga labule tare da kunna fitilar dakin haske ya gauraye dikin tai kiran sunana Ameerah! Ameerah!! Na amsa da kyar na amsa lafiya ki ke cikin kuryar daki cikin zafin nan ko zafin ma ba kya ji na ce Bebi shigo na yi karfin hali na ce zauna ina tarawar dari hakorana suna haduwa da junansu nace lafiya lau 27 daga ina ki ke haka? Tace a'a ina fa lafiya me ke damunki ne cikin kankanin lokaci lallai to yanzu wai ina tambayarki me ya ke damunki.? Na ce zazzzabi ne kawai ya ke damuna ta kai hannunta wuyana dan taji yanayin jikina kai kai kai haka jikin ya yi zafi to yanzu kinsha magani nace ban shaba tace amma ki ke anan yanzu haka ma baki fadawa Anti cewar ba ki da lafiya ba ko nayi murmushi lokacin da na ke kokarin kwanciya nace wa ki ke san na je na fadawa ni da ba ni da gata a yanzu? Ni yanzu ma addu'ar da na ke yi itace Allah yasa sanadiyyar mutuwa ta ce ta zo inna mutu ai kowa ya huta ko? ni in huta suma su huta da yawan yin fadan naki bin abin da su ke so. Bebi ta kalle ni cike da matsananciyar damuwa hade da tausayina ta ce haba Ameeraha komai hakuri ake yi da shi ki dinga yin hakuri da lamarin duniyar kar kije ki jefa kanki cikin wata babbar cuta kuma ki je ki illata kan ki abanża da wofi nace to yanzu Bebi ya ya ki ka san na yi da kaina ne? wai kuwa Bebi kin san kiyayya kuwa? A gaskiya da kin şani na tabbata da kin tausayawa rayuwata. A gaskiya kiyayya bala'I ce na fashe da kuka ina ta jujjjuya kaina nan da nan na ji kirjina ya yi bala'in zafi zuciyata kamar zata fito dan matsanacin zafi da na ke ji daga gare ta. Na dafe kirjina da hannuna ina cewa waiyo Allah Bebi kirjina zai tsage ki taimakamin ki danne shi can naji ina nunfashi sama - sama ban ankaraba kuma sai wani bakin abu ya sauko ya rufen idona ban san yadda akayi ba kuma sai ganina nayi akan gadon asibiti an samun karin ruwa, a hannuna na dama wata nas ce ke tsaye akaina tana rike da allura da sirinji a hannunta lokaci da ta ke kokarin zuko ruwan a sirinji. Sannu Ameerah ya -28 ya jikin naki? Na juyo la kaina jin da rayi maganar Antina ce a tsaye fuskarta cike da matsanancin tasuyina na ce da sauki Anti to Allsh ya kara sauki. Bebi yaushe ki ka zo tace ai tunda aka kawo ki muna nan dukkan muna nan tun yaushe na anan din? tace n jiya da hantsi muka kawo ki na ce na gode Bebi. Yau kwana na uku a asibiti amma iďma ka ganni sai ka zac na shekara a kwance duk na fita aga hankalina, na yi jeme - jeme na yi baki ba yi mesifa ramewa ramata ita ce zata fara baka mamaki in dai ka ganni in har ka sanni to kai da kanka zaka iya cewa ba ni ba ce Amegra da ka sari ada 'yar kwalliya. Zuwan da mijin Antina ya ke yi ko kuma na сe (БABA). Idan ay tashi zuwa ya na zuwa da mutane abokansa to rannan sunzo duba ni ne. Akoda yaushe su Antina su na asibiti wajena su ke wuni ya yin da Kaka Aisha ce ta ke jinyartawa. Yau ma kamar kullum ya zo shi da abokinsa suka shigo gaisa da kaka Aisha ya ya jikin nace jiki da alhamdu lillahi, ya ce Allah'ya kara sauki amin a lokaeinne kaka Aisha ta dauki kwanu kan da ака се abinci dasu ta je waje. Sannu Ameerah ya jikinnaki in ji mijin Anti ko in ce (BABA) na ce da saukI, Baba da yake da ma haka na ke cea da shi. Abokinnsa ma ya ce Allah ya sauwake na ce amin na gode. Ya ce amma Alhaji Bashir Ameerah ta rame da yawa. (Sunan mijin Antina ke nan) ya ce wallahi don ni wannannnn har tscro ya ke ba ni, Ameerah ta ce na waiga na kalli mai cewa na rame da yawa sai yanzu na gane abokin Alhaji Bashir ne da ma ya na zuwa gidan to dag abaya kiuma sai naji Anti ta ce ya yi tafiya zuwa Lonhdon shi ne dalilin dana daina ganinsa, kuma na 29 shi kwatá kwata sannan

Chapter 2 of 4