Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 4
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels Ameerah RABI MASIDI ABUBAKAR (Hajiyar Birni ) (Mrs Ayuba Yahaya Ibrahim ) Hakkin Mallaka (m) Rabi Nasidi 2003 Copy Right (c) Rabi Nasidi 2003 Shekarar Bugu 2003 Kamfanin da ya yi dab'І Tare da Tsata rubutu a Na'ura Mai Kwakwalwa Mashi Printing & Publishing co. NDneji Qtrs, S/titi Mandawari Kusa da Sehad Storss Kano. Tei-064 331928 Godiya Dukkan godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki tsira da aminci su tabbata ga Annabin tsira (S.A.W) Ina godiya ga Allah da ya bani damar Rubuta muku wannannnn dan Littafi. Ina mika godiyata ga Haj. Halima Yusuf (ummi) Yakasai saboda muhimmiyar rawar data taka wajan ganin littafin ya kammalu gami da bada shawarwari gyare- gyare da ta yi babu abin dazance mata sai dai ince Allah ya sakamata da alheri ya kuma buda mata basirar rubutu Amin, HajiyaHalima Yusuf Ummi (Ni ko ita) (Lokaci ne) na gode na gode na gode. SADAU KARWA Na sadaukar da wannan Littafi ga mijina Ayuba Yahaya Ibrahim, saboda goyan bayan da ya bani na gode Allah ya barmu tare. GAISUWA Ga kanwata Maryam Nasidi Abubakar da Sameeran Rabi'u K/Ruwa da .Zainab Uba Sameerah Mustapha Baba kusa da Jamila Sulaiman, Hauwa Usman Maryam Muhd da Amina (Ummi). MUHIMMIYAR GODIYA Ga Mahaifana saboda kulawar da suka yimin na gode Allahu ya sakamusu da alheri Amin, TAKU RABI'ATU NASIDI ABUBAKAR (Hajiyar Birni) 3 meerah ki hanzarta kije a kitsemin kanki kada Aya yi tsami ke dama gaki da jin zafin kitso.... Ina daga daki na amsa to anti dama yanzu nake da niyar tafiya na dan tsaya ne ingyara miki dakin kafin intafi, Anti ta danyi murmushi kana ta ce indai gyaran dakina ne, dan yau daya abarshi na yafe zo kije ayi miki kitson diyata, na ajiye dan hankicin dake hannuna wanda dashi ne nake goge- gogen kana na nufi inda man kitso na ke ajiye na zari mayafina na nufi waje. Da jefa kafata cikin zauren farko mukayi kacibus da kakata wadda muke kira da Aishat, ta sako kai tunkis-tunkis na sheke da dariya kana nace Lah, barka da zuwa kakalena (haka nake kiranta idan naso yin tsokana) yau kace a gidan namu, kaka tadan tsaya ta dubeni ita ma dai cikin sakin fuska ta soma fadin ta berange ina zuwa haka da La'asariyya? Nasan dai baki da saurayi ballantana ince shine yazo koda yake yanzu kin kusa ki huta da gorina tunda munyi miji....... Cikin matsanan cin mamaki game da firgita na tsirawa kaka Aishat idanu, bansan lokacin da nayi subul da baka nace ke kaka wane irin miji? Ana zaune kalau nida bansan yadda ake fadin ba ballantana muce ga wanda zan aura, maimakon kaka Aishat ta bani amsa sai ta dan gogeni ta wuce tana fadin ke ni bani waje in shige bansan shirman nan naki ko ma menene kyaji a bakin uwarki......kaka Aishat tayi cikin gida abinta, nayi kamar in juya inbi bayan ta, dan a zahirin gaskiya zuciyata na hakIkance mani cewa akwai bukatar inyi cikakkiyar tambaya a game da maganar da kaka Aishat.... Ma'ana suna Bukatar karin bayani. 4 To amma a yanzu idan na koma zatayi kamar nayi tsaurin ido dan haka sai na zarce gidan kitson, zuciyata nacike da tunanin game da ınaganar da kaka Aishat wadda na sanya mata alamar tambaya? ******* ******* ******* Har zuwa lokacin da Habi mai kitso ta fara yimin kitson ni dai zuciyata nacan cikin tunanin maganar data firgitani, a zuciyata na yawaita yiwa kaina tambaya game da shin me kaka Aishat take nufi da fadin munyi miji?.....haka zalika me take nufi da fadin koma menene kyaji daga bakin uwar ki, na kada kai tabbas akwai alamar tambaya cikin maganar kaka, tabbas muna wasa da kaka aishat amma tunda nake bata tabayi min irin wannan maganar ba, idon har zanyi la'akari da rin al'adar gidan mu saboda su tun farko suna da wata gidauniyar akida wadda ta samo asali tun daga kan kakan kakan mu. Har zuwa yanzu da daukacin gidanmu muke karkashin ikon kakana wanda ya haifi mahaifin mahaifiyata, kuma shi din nan dai ya haifi mahaifiyar mahaifina ma'ana iyayen nasu idan mace da dan namiji Mal. Musa wanda akafi sani da Alaramma sh mutum ne mai tsattsauran ra'ayi wanda idanya ce e! to babu wanda ya isa yace a a kuma ya zao tunda gasu kansu ya samuo asalin auren zunci akayi sai dai a hada 'y ar wanna da dan wvana batare da su kansu yaran da za'a hada auren sun sani ba, sai dai kawai ranar maulidi yari na zaune taji an daura mata aure kuma dole ta hakura ko tana so ko bataso to tunda dama shi na.niji ya hakura ke mace ai dole ki hakura. Ni kuma gashi Kaka Aishat abin da take fada dole ne hankali na ya yi masifar tashi Allah Allah nake Habi mai kitso ya gama min kitsan inje inji abin daake shukawa acikin gidan mu ana gama kitsan na mike tsaye Habi ta ce tsaya mana in tufke miki kitson mana nace barni Habi ina sauri ne kawai aikin dana tuna zanyi kuma banyi ba nake saurin inje in yi shi to shikenan. Na isa cikin gida amma zuciyata take da fargabar to me ya kawo Kaka Aishat gidan nan da yamma ina yin wannannnn tunani ananma na kuma tabbatarwa da kaina ni dai a sani na ban taba ganin kaka Aishat da maraice haka ba sai yau. Nayi sallama na shiga kaka Aishat tana kokarin ta yarda kabbarar sallar magariba nima naje nayi alwala nazo na fara bada farali Kaka Aishat ta rigani idar da sallar sai da na idar da tawa na juyo sai naga kamar ni take jira akwai bayani a tare da ita na kalleta kawai ni yau na sake miki kamane sai kallona kike yi? Ta gutsuri goron banun ta ta miko ungo ni in zaki ci a'a Allah ya kivaye sai kace wata ke. Anti na shigowa itama ta nemi guri ta zauna ta mika hannu ta rage karar TV ta jiyo ta kalleni Ameerah na juyo na kalleta Na'am inason zan tambaye ki ne bance komai ba illa kallon ta kawai da nake kinsan wani Sunusi nayi shiru a'a bansan shi ba nace da ita ina nufin duk cikin samarin ki ba mai wannan sunan nace A'a babu suka kalli juna ita da kaka Aisha suka yi shiru suna tunani da mamaki. Ras gabana ya fadı da na tuno da wani wanda muka taba haduwa da shi yace dani sunan sa Sunusi laliai na tuna, dashi in dai har shine to in kuwa shine ma Sunusi yake nufi dani tunda tun farko nace dashi 6 banason sa asalima yau kusan wata biyu ko uku da rabuwar mu dashi. Ya naga kina gumi ne Antina ta ce dani na kalleta, ko kinsan shine na share gumin da yake fuskata natuna dashi amma yanzu bama tare dashi shi dama muke san muji kin sanshi ko baki sanshi ba kuma tunda dai kinsan shi ai shikenan magana ta kare inji Kaka Aishat. To shi Sunusin ne ya dauki kudin aure ya kai gidan Alaramma yau kwana shida kenan da kai kudin ko da yake su iyayen nasa sun jene akan dan Allah abaiwa dan nasu Izinin neman auren ki don haka suka kama kafa da manyan ki to cikin sa'a kuma lokacin da suka je sai suka yi sa'a yasan wan baban shi sunusi. Bayan sun gama gaisawa ne sai shi wannan baban Sunusin mai suna Alhaji Muktar sai ya fadI abin dake tafe dasu to nan da nan Alaramma sai ya yi farin ciki da jin wannan bayani nasu yace ai ba wani abu kar kuji komai kuma kuce dashi yaron kar ya damu ya cigaba da zuwa wajenta indai Ameerah ce na bashi ita, indai da rammu kamar ya aure ta ya gama naji dadI kwarai da gaske wannan abin ai duk na gida ne. To ganin haka shi wan Baban Sunusi Alhaji Muktar yasa hannu a aljihun ya fiddo da kudin aure ya bawa Alaramma shi kuma- Alaramma bai yi wata wata ba ya sa hannu ya karbа. Bakin ciki da takaici suka hadar mini cikin kukа nace ni wallahi banason shi kuma ni bazan auri wani wai shi Sunusi ba. Ban gane nufin ki ba in ji Kaka Aishat ta fadI ne tana tsattsareni da idanu nace to ma wai ke kin taßa ganin yadda akayi haka kawai akarbl kudin mutum ni 7 bansan shiba kamar yaya baki san shi ba yanzu kika се da mu kinsan shi kuma yanzu daga baya kice baki sanshi ba kuma in ban dake-cikin zuri'ar mu waye ya taba sanin mijin da zai aura basai dai in an daura auren yaji ba cikin matsanan cin kuka na cigaba da fadin ni wallahi bana Kaunarsa na amince ku hada ni dako wanene amma banda Sunusi Anti ta dubeni a fusace ta jinjina kai kana ta ce Ih! lalle to wallahi ko dashi wanda zaije ya fadawa Alaramma bakyason shi? Ko kina tsammanin ni zan iya tare Alaramma da wannan tatsuniya. Na yi kuka ya ishe ni lalle in ko haka ne an hadani da bala'in da ko a mafarki ban taba tsammanin zan shige shi ba wai Sunusi zan aura sai yanzu ne hoton lokacin da muka hadu ya fado min arai. Ba zan taba mantawa ba ranar juma'a ne da dan hantsí anti na ta aikeni gidan wata kawar ta, toni ga aladata nariga na saba bana sanyin tafiya ni daya, sai na nemi dan rakiya koda kuwa yaro ne. To ayau ma sai na kira Ummi diyar Anti na mai kimanin shekara hudu tazo ta rakani. To muna cikin tafiya ne sai yarinyar ta nuna ta gaji da tafiyar ta ce lallai sai na dauketa ni kuma nace bata isaba nakI na dauke ta. Take yarinyar tasa kuka nay lallashin duniyar nan akan tayi shiru amma taki takuma ja ta tsaya taki yin gaba ganin haka sai nayi gaba na barta da niyyar intaga kamar zantafi inbarta to zata biyoni to dai dai inda muke kusa da wani shago ne don haka lokacin da Ummi ta sake tsanyarewa da kuka sai naga anturo kofar shagon an bude wani saurayi dan dogo dashi ya fito yana murmushi ya kalleni ya kalli yarinyar ya dan 8 matsa inda take ya kama hannun yarinyar, yi hakuri Kanwata Antinki ce takI ta dauke ki ko? Ummi ta daga kai alamar Eh! Yaci gaba to yi hakuri in kinje gida saiki fada azaneta ko? Da sauri yarinyar ta amsa to, yasa hannu a ajjihu ya ciro biskitya ce ungo naki ne ke kadai kada kibawa Anti kinji ko? Ta gyada kai kana yà dan dago kai yana wani irin murmushiya ce matsomana Anti ki rike hannun ta mana, take azuciyata na soma raya cewa .....kai wannan mutum da kirki yake ko kuma ince da son yara yakeе. To sai dai kuma ga mamakina ban idar da wannan tunani ba, sai naga an daga labulen shagon wata yarinya ta dan leko da kanta tana fadin wai ina katafi ne ka shanyani gaskiya kazo ni tafiya zanyi kada ayimin fada agida yadan juya cikin murmushiya ce yi hakuri kijirani minti biyu yanzu zanshigo. Duk wannan abu dake faruwa ina kallonsu tashi farko tunanina ya fara ayyanamin duk yadda akayi wannan saurayin yana daya daga cikin irin lalatattum samarin nan da nake jin labarin su masu yaudarar 'yanmata suna lalatasu. Don haka take naji matsananciyar tsanarsa ta dira azuciyata hara ya zamto ina la'antarsa acikin zuciyata dashi da mesu irin halinsa: Nan danan na riko hannun Umma da niyar mukama gabanmu tun wani bai ganni tsaye wurin ba. To a lokacin yadan dada mat..owa yana fadin 'yan mata ya va zaki tafi baki fadaram sunanki ba, nadan kauda kai na ce idan na fadamaka amfanin mai zai yi maka? Yavi murmushiya ce ai amfanin ba mai musaltuwa bane sou haka bansan yadda zan kira shiba, tuni na juya ina fadin kayi hakuri wannan sunan ba mai facduwa bane. 9 Nan da nan ya sha gabana yana fadın don Allah ki tsaya mana koda minti biyu ne ina so zanyi magana da ke, nadan tsuke fuska nace wace irin magana kuma daga haduwar kan hanya?ya ce don Allah ina son insan gidan ku gabana ya fadI nace acikin zuciyata a awai mai wannan mutumin yake nufi dani ne? take dabara ta fado min nace sunana Hadiza nai masa karya haka zalika nai masa kwatancen karya wanda kwata kwatama bai shafi unguwarmu ba. To azuciyata ina Allah Allah na bar wajen cikin murmushin jin dadī ya ce nikuma malama Hadiza ba aso asan nawa sunan ne? cikin ko sawa dayin maganar da nake dashi nace bahaka bane nasan zaka fadamin shiyasa ban tambaykea ba,ya ce ya ya akayi kika sani? Nace kaga duk wannan iambaya bata taso ba kai dai kawai fadamin sunanka sauri nakeyi kada aga na dade ayimin fada, kwarai kuwa kina da gaskiya nima ba zanso evi miki fada ba, to ni dai sunana Sunusi Ibrahim Hashim. ******+* ********** kwata-kwata na manta da mun hadu da wani shaf a rayuwata, na manta dashi in yawan bin hanyar tunda Antina tana yawan aikena gidan kawarta amma na manta dashi saboda baya gabana na hangeshi yana yimin murmushi naji bakin ciki yake mani sai yanzu na tuna dashi nace lallai yau yaya zanyi na fada cikin raina, take dabara ta fado mini nasha mur saboda ina da tabbacin sai yaga fuska zai sami damar yimin magana to amma da yake irin wadannan mazan be zuciya gare su ta tuni ya hau murmushi haka zalika ina matsowa dab dashi yadan daga murya yana fadin ina godiya fa akan kwatancen bogi da akayi min naje na bige da shan 10 wahala nayi kamar ban ji shiba nama kawar da kaina daga bangaren da yake abin takaici wai sai ma ya taso ya biyoni ya jeru dani yana malama Hadiza yaya akai naje gidan da kika kwatanta mini har wajen sau uku amma ana cewa ba gidan bane cikin takaici wannan naci da yake nuna mini na juyo na dubeshi a fusace kana nace to kana bina bashi ne ko me naci ban biya ba da har zaka matsu lallai sai kasan gidan mu ya dan girgiza kai cikin yake ya ce babu ko daya Hadiza illa iyaka dai so da kauna. Naji wan: kuna a zuciyata yadda kika san ya ci ka min kibiya a zuciyata bansan lokacin dana furta... ka gani tun wuri ka fita daga harka ta idon kuma kakI wallahi zan dau mataki akan ka naja wani dogon tsaki mits!! A tunani na zai ji haushi hakan dana yi masa ya rabu dani amma mai makon haka sai naga ya yi murmushi kana ya ce kiyi hakuri Hadiza bana nufin in bata miki rai illa yaka na shiga wani matsanancin hali na tsabar kaunar ki don haka bazan taba damuwa ba da duk wani mataki da zaki dauka akaina, ba kuma zan gaji da birki sannu a hankali ba har sai naga burina ya cika na samu hadin kanki, dan haka ki daure ki sanar dani inda zan same ki a tsiwace to shikenan ni dakai aga dan halak nayi gaba ban ko sake saurare sa ba. Bayan na koma gida ne Anti ke cewa dani amma dan yau kin dade da yawa, nace wallahi da naje na tarar bata nan ta shiga makota sai dana jira ta dawo shine ya sa kika ga na dade Anti ta ce to iceko dai kinyi sallah ko? nace la Anti nayi sallah mana yama za'ayi in kai har iyanzu karfe wajen biyar banyi sallar la'asar ba. 11 A daran ranar ne dai ina gindin famfo ina wanke hannu na bayan na gama cin abunci, wani yaro ya shigo yace wai ana sallama da Hadiza nayi gaggawar juyowa, nace da yaron nan gidan babu Hadiza kaje ka sanar wa da wanda ya aiko ka, ya juya ya fita ni kam tuni na shiga tunanin magana... bana ko tantama ire-iren samarin da nake yiwa karyar chenjin suna ne wani yazo.... ban ida tunani ba sai ga yaron ya dawo yace ance wai to ke kizo. Nace kai wai waye ne wannan ke aiko ka? yace nima ya takura min da aike, ba nan ne gidan su Hadizan da yake nema ba to menene na koma na sake aiko ka? kuma kaima ai nasan kasan cewa a duk gidan nan babu wata Hadiza ko ba nan Unguwar kake ba? ya ce na fada masa yace wai shidai alallai nan ne gidan, ya kuma tambaye ni wai yaya ne sunan yarinyar da take nan gidan....... Na katse yaron da fadin shine kai kuma dan baka da hankali ka fada masa ko?. To menene kuma nayi wa yaro fada amira dan aike ai bashi da laifi.... Anti ce ke magana tana tsaye ne a bakin kofar dakin tana kallon mu. A raina nace shikenan ta faru ta kare dama bana kaunar Anti taji to yanzu kuwa ta riga taji dan haka zance ya kare nasan cewa za tayi dole sai naje, Nace Anti bafa ni yake kira ba yaron ne da shir manshi, Anti ta ce duk da haka yafa mayafim ki kileka kiyi mashi bayani in yaso sai ki koma. Nadan marei raice nace Anti bafa ni yake nema ba kuma ni sai in fita? Ni gaskiya ina ganin bai dace in fita ba tunda bani bace Hadizan da yake nema ba, Anti ta gyada kai game da fadin duk da haka ki dai daure ki leka da kanki kiyi mashi nasan 12 magana zaifi yadda da maganar ki akan ta yaron ba mamaki idan yaron ne ya koma ya sake dawo dashi, na kalli Anti cikin haushi nace toni yanzu idan naje mai zance dashi, Anti ta shiga daki tana fadin Oho miki ni dai ga abin da nace dake kiyi in zaki yi to in kuma ban isa ba ne ya rage naki. Dole ne na zari mayafi in fita ina kumburi, na isa gareshi na taddashi sai faman murmushi yake yi ina karasawa inda yake naji gabana ya fadl bakin ciki game da takaici suka rufe ni. Ada da farko dana fito ban sheda kowa ye ba to amma yanzu dana karaso har inda yake na fahimce mai kiran Hadizan, ba wani bane illa Sunusi (Sarkin naci) mutumin da nayi wa cin mutunci dazu dazun nan. To amma ga mamaki na sai gashi tsaye a zauren gidan mu, tunani na farko shine..... yaya akayi ya gano gidan? lallai wannan ya isa akirashi basara kan naci.....ya katsen tunani na da fadin barka da dare Malama Hadiza yaya ki kazo gida? Koda yake na lura kina cikin mamakin ganina. Na dubeshi na kauda kai a zuciyata nake cewa....lalle wannan mutum ya zama dole inyi da gaske akan shi tunda wurwuri tun bai jawo min wata bahaguwar rigimar ba, abin nufi kar tafiya tavi nisa nzo in rasa yadda, zanyi dashi dan haka ya zama wajibi a gareni inyi maganin shi a yau din nan ya fita harkata. To mu gaisa mana ya mutanan gida? Lafiya lau na bashi amsa yace hadiza sai kuma kika ganin yanzu ko? Nason zakiyi mamakin ganina kina iya cewa da zumnan fa inuka rabu dashi amma gashi yazo gidan mu kina iya cewa koda ma yasan gidan ne yace dake bai sani ba. 13 Ya cigaba da zuwa kamar kanyar din ya ba dadl, yace ai da zunnan bayan mun rabu dake sai nayi tunanin fushi ba nawa bane kamata ya yi in biki in ga gidan ku tun da kinki fada min, tona biki a baya har muka zo nan kika shiga sai nace da wani yaro nanne gidan ku? Saiya ce dani Eh nan ne nayi farin ciki sosai, da sai gobe nayi niyyar zuwa to amma sai naji zuciyata ba zata yi hakurin sai gobenba gara dai nazo yau tunda dai nasan gidan, ina zuwa dana aika yaro sai ya dawo ya ce wai ba Hadiza a gidan, har hankali na ya tashi sai ak tula sni nace yace kize tunda na tambaye shi -- cewa waya fada masa yace wata budurwa ce. Tuni haushi ya rufe ni duk ya cikani da surutu bai masa ni a tsayiwar da nake kamar kan kaya nake ba dak nake gara na bar wurin, sai ci gaba nai sauri na daga masa hannu nace ya isa haka na juyar dakai gefe gud ya kalleni cike da mamaki lafiya kuwa? Ya tambayc ni nace lafiya illa dai sauri da nake yi kawai sai dai duk da saurin ba zai hana iu tsaya in fada maka gaskiya ya ce to ina sauraren ki, naci gaba. A gaskiva ni dai yezu bani da lokacin yin soyavya dan haka sai kai hakuri dan karkace na yaudare ka, ban iya yaudara ba kuma ban san a yaudare ni shi yasa na fada maka gaskiya danni kai ma na taba tsayawa dashi nayi zance dashi dan haka ni dai inay maka addu'ar Allah ya baka wadda ta fini Ameen. Ya yi shiru har anayin zaton ma ba zai iya cewa dani komai ba na kauda shirin da cewa to sai anjima ya dago da kanshi cikin sauri minti biyu, kamar karna tsaya sai dai na juyo ina sauraren abin dazai ce dani, ni ina ganin duk wannan bawani abin damuwa bane idan har kin amince dani Juk bazai gagara ba koda kuwa 14 shekara nawa zaki yi kina karatun zan iya jiran ki fatana dai ki soni ki kuma bani hadin kai ta yadda zamu cimma burinmu na aure, dan a gaskiya ina cikin matsanan cin hali nasan ki tun ran da Allah ya hadani dake, kuma wallahi Allah kadai yasan halin da nake ciki ki taimaka, ni dai nasan sonki Allah ne ya jarrabeni da shi ta yadda banajin zan iya hakuri dake, na galla masa harara lallai kana cikin wahala toni bari ka jima kwata-kwata ana kaunar ka bana son tunda dai haka kake son kaji ko? Nayi maka hannun ka mai sanda ka gani ka wane irin mutum ne banajin ko ana yin dole? Ban ma tsaya naji me zai ce dani ba na shige cikin gida na basrshi yana faman kirana. Anti ta ce har ya tafi nace eh ya tafi ta ce bake bace? Eh bani bace to ai kinga haka yafi ni dai na shiga daki na barta anan gudun karta gane cewa raina a bace yake tun daga ranar bai kuma zuwa basai kuma gashi yau Akaka Aishat ta zomin da wani labarin daban, tun lokacin da Kaka Aishat suka fadamin wannan maganr kwata-kwata na rasa abin dayake yi min dadı, hankali na a tashe yake kullum cikin kuka bani da aiki daya wuce kukan, hakanan bani da inda zanje inji dadI inba wajen kawata Bebi ba. * lallai Idon ki kenan sai yau akeganinki yau kika tuna dani ko dai batan kai kika yi ne? nai dariya nace kai Bebi wadannan tambayoyi haka ai sunyi yawa, wanne irin batan kai zanyi sai kace wacce bata san gidan ba, ai gani nayi kwana biyu kin yada ni ne? wallahi Bebi ina son zuwa kinsan komai sai Allah ya yi, yanzu ma wata gagarumasr matsala nake fuskanta shiyasa nazo kiban shawara. Ameerah ta kwashe duk halin da ta shiga ta gayawa Bebi tai ajiyar zuciya ta ce Ameerahwallahi ni nama rasa abincewa hakIka kina cikin babbar matsala, to amma ina ganin mai zai hana ki nemi goyon bayan Atinki,tunda naga tana jida ke, na dafa kirji na nace bebi rufan asiri duk yanda kike zaton wannan lamari ya wuce nan, Anti fa da bakinta take cewa wai indai na bijirewa wannan maganar wai zamu raba gari ba ni ba ita don bazan janyo mata musiba ba tana zaune lafiya, Bebi ta ce ito dama maganar iyaye ai ba abin bijirewa bane Ameerahshawarar da nakeso inbaki shine kibi maganar iyayenki

Chapter 1 of 4