Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 4
sassauta mun shi ya sa na zo in yi godiya." Gaba daya uka yi dariya. Wuni suka yi suka kwana sannan washegari da safe suka kama hanya suka tafi 67 Hafsat C. Sodangi Du Kamar Wuya 2 bayan Nura da matarshi sun yi musu alheri mai yawa. Watanni shidan farko na zaman Nana cikin dangin Nura ta yi amfani da hikimominta wajen janyo 'yan uwanshi a jikinta ta yi matukar yin kokari wajen kyautata mu'amala a tsakaninsu don haka sai ya zamo an samu shakuwa mai yawa a tsakaninsu ta kuwa zamo mowa kwarai a wajen mahaifiyarshi kullum a cikin yi mata aike take ita kuwa Nana duk abin da ta girka sai ta aike mata dashi nura ya yi matufar jin dadin yanda Nana take tafiyar da al'amura tsakaninta da 'yan uwanshi. Ita kuwa Nana ta na ta Gangaren ba ta da wata miskila tsakaninta da mijinta da kuma 'yan uwansu in ban da wasu da ta riga ta fahimci babu wani abin da za ta yi ta burgesu don kuwa a zahiri suka nuna mata ita din sun tsaneta don haka babu wani abinda za ta yi ta burgesu tana zaure tare da Nura da hantsi cikin furanni, shan iska suke yi Nana ta kalli Nura cikin nutsuwa da girmamawa, ta ce "Ni in ba za ka damu ba in tambayeka mana." Ya zuba mata ido yana kallonta cikin sakin fuska ya ce "Haba Nana me za ki 68 Da Kamar Wuyu 2 Hafvat (. Sodangi tamabyeni ni kuwa in samu damuwa akai." Ta cc "Ni da so nakc in san me ke tsakaninka da Naja'atu?" Nura ya kalleta ya cc "Mc ki ka gani?" Ta dan dago ido ta kalleshí ta yi kamar ta gaya mishi abinda ta ganin sai kuma ta fasa ta ce "Babu komai ni dai kawai na dan yi zaton ko akwai wani abu ne shi ya sa na ce barí in tambayeka." Ya ce "To babu komai Nana kc dai kawai in kin ga wani abu ne sai ki gaya min haka nan in ta miki wani duka kina iya yi min bayani." Ta ce mishi ba ta mun komai ba suka cі gaba da hirarsu. Naja'atu ta ci gaba da zama matsalar Nana a dalilin yawan shiga sabgoginta da take yi sai dai in Nana ba z ata shiga cikin gidan su Nura don gaida mahaifanshi ba, sai ta san abinda ta yi mata na wulakanci, in kuma magana ta yi to za ta san yanda ta yi ta karyatata duk kokarin Nana na ta gyara mu'amalar a tsakanin su abin va gagara tun abin baya damunta sosai har ya soma damunta a dalilin ba ta san menene laifinta a wurinta ba, ana cikin haka kanwar Nura karama Nusaiba wacce take sakandire aji uku ta zowa 69 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi Nana hira ta dawo daga makaranta tana falo tare da Nana suna hira lokacin da ta ga Naja'atu ta shigo cikin gidan kai tsaye ta wuce falon Nura ba tare da ko kallon inda suke ta yi ba balle ta gaishe su, Nusaiba ta bi ta da kallo ta ja tsaki tare da zobara baki Nana ta ce "Lafiya irin wannan tsakin?" Nusaiba ta ce "Haushinta nake ji lokacin da ake so a hadata aure da Yaya Nura kememe ta ki amma yanzu ta ga ya je ya auroki sai bakin ciki take yi, tana wani kamun kafa a wurin Hajiyarmu don ta matsawa Yaya Nura ya yarda ya aureta, itakuma Hajiya ban san dalili ba duk abinda take so itama sai ta tayata son shi." Nana ta kalleta cikin nutsuwa ta ce "Dama ba Hajiyar ce ta haifeta ba?" Nusaiba ta ce "A'a ba ita ba ce ita 'yar Kanwar Babanmu ce amma a wurin Hajiyar ta girma lokacin da ta ce ba ta son Yaya Nura ita Hajiyar ce ta ce kar a matsa mata yanzu kuma ta dawo tana so kuma wai tana tayata." Nan da nan kishi ya kama Nana sai dai ta yi kokarin dannewa ba tare da ta yarda Nusaiba ta gane ba, lokacin ne kuma ta ji dadewar Naja'atu wurin mijin nata ya dameta nan take ta 70 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi mike tanufi falon mijin nata don ta ga abinda take yi sai kawia suka gamu a hanya tana fitowa, yayin da ita kuma Nana take shiga ciki, murmushin da taje ta tarar a fuskar Nura shi ne abinda yakara bakanta mata zuciya, maimakn ta zauna sai kawai ta juyo za ta dawo wurinta da sauri Nura ya kirata "Zo mana Nana kin shigo kuma kin juya, ba tare da kin ce min kmai ba, ina ce dama wurina ki ka zo?" Ta ce "A'a na dai shigo ne kawai." Ta ci gaba da tafiyarta, ya yi maza ya tashi ya bi bayanta ya lamota "Zo mana Nana zo ki gaya min me ya fata miki rai na ga yanayin fuskarki " ya caıza. Ba ta amsa mishi ba haka nan ba ta iya dago fuska ta kalleshi ba saboda takaicinshi da ya kamata. "Menene bebina?" Ya fadi hakan cikin muryar rarrrashi "Zo ki ji, zokı gaya min abinda ya dameki ni ne? Ni ne na yi miki laifi?" Та се "Вa ka mun komai ba kawai dai mu'amalar da ke tsakaninmu ne na ga kana nema ka canzata." "Da na yi me bebina?" Cikin sauri ya yi tambayar. Ta dai bar maganar ta ce mishi "Mu 71 DàKamar Wuya 2 Hufsat C. Sodangi bar maganar kawai." Taljuya ta nufi kicin dinta, "Zo Nusaiba, zo mu je ki tayani girki kin ji." 20 d Nusaibu ta bi bayanta da sauri yayin da shima Nuraya shiga kicin din "Jeki gida Nusaiba yi sauri in kin je ki ce da Hajiya ina gaishe ta, nima ina nan zuwa." Nusäiba ta ce mishi "To." Tana fita Nura ya kalli Nana ya ce mata akwai alkawari a tsakaninmu 'Nana na gayawa juna gaskiya don haka ban ga dalilin da zai sa in ganki a wani yanayi da ban saba ba sannan in tambayeki menene ya faru ki ki gaya mun gaskiya, kin ga ke nan ke ce ki ke nema ki kawo wani canji a tsakaninmu in kuwa ki ka yi haka ina ganin ba ki yiwa zamanmu adalei ba." Nana ta daga ido ta dan kalleshi nan da nan kuma ta kawar dá fuskarta ta ce "Idan ma na yi-hakan bani ce na canża yanayin zaman ba kai ka fara don kuwa kaine farkon wanda ya fara boye min gaskiya don haka kmai na yi tayaka na AOMI BES 8ទ ចទ G បបយ Ta ci gaba da aikinta, yana taimakonta har kemala Kamar kullum ta jawo foodflask fita inai kyautå bude ta cikashi da abin da ta 72 Da Kumar Wuya 2 Hafsar C. Sodangf girka sannan ta kira mai aikinta ta mika mata ta cemaza a je a kaiwa Umma ta karba cikin sauri takama hanya, ta fita ta jc kaiwa ita ma Nana ta dawo kicin din ta debe abincın ta je ta shirya a falon Nura ta dawo mata falon ta baro mishi abincin shi kadai tana zaune tana tunanin maganganun da Nusaiba ta yi mata, sai kawai ta sake ganin Naja'atu ta zo za ta sake wucewa ta shiga inda nura ya ke sai kawai ta mike cikin sauri ta ce mata "Ji mana baiwar Allah rinka yin abu kamar kina da hankali kin ganc? Daina shigo min gida haka kawai babu sallama." Naja'atu ta tsaya ta yi mata wani lalataccen kallo ta ce mata "Gidanki fa ki ka ce min? Kina nufin nangidannaki nc?" Nana tace "Kwarai kuwa ina,kuma da yancin hanaki shiga cikinshi musamman da yake na lura ba ki da hankali." "To ai kuwa yanzun nan zan nuna miki rashın hankalina." Ta daga hannu da nufin kaiwa Nana mari a fuskarta ta yi maza ta cafe hannun nata ta murdeshi da iya Karfinta har sai da ta kwallara kara abinda ya sanya Nura fitowa cikin! sauri yana zuwa ya ga abin da ke faruwa cikin sauri ya ce "Saketa Nana ba ta yi musu ba la 73 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi saketa, yi maza ki fita min daga gida ya baiwa Naja'atu umarni "Ko ba ki ji abinda nake fada ba na ce yi ki fice min daga gida in daina ganinki." Ba ta Gataloakci ba ta sa kai ta fita tana sharar hawaye a dalilin wai Nura ya shigar wa matarshi fadan. Nana ta koma wurin zamanta ta zauna shima Nuran ya bi ta ya jeya samu uri ya zaına yanı mata magana "Kar ki rinka daka ta wannan yarinyar Nana in kin lura da kyau za ki ga ita din tamkar daban take a cikin gidan." Ba ta tanka mishi ba ta yi shiru har yayi ya gama ba ta ce mishi komai ba ta tashi ta tafi wurinta. Kwana biyu bayan nan Nana ta yi mata tana zaune a gabanta cikin ladabi yayin da Naja'atu ke kwance a jikin ta tana ta faman shagwaba, Hajiya Kubra te kalli Nana, fuskarta a daure ta ce mata "Kiranki na yi in ji shin da gaske ne wai kin hana Naja'atu zuwa wurin wannan yaron?" Nana ta sunkuyar da kanta kasa ta yi shiru ba tare da ta dago kai ta kalleta ba balle har ta bude baki ta ba ta wata amsa. Sai ta ci gaba da cewa. 74 2 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangl "Shi mijin naki bai gaya miki abinda yake tsakaninshi da Najar ba ne? Ita Naja'atu da ki ke ganinta ko babu aurc tsakaninta da shi wantane don haka babu wata matar da ta isa ta shiga tsakanin su to balle ma kuma auren ki da ya yi ba zai hanashi auren 'yar uwarshi ba, tunda suna son juna ko jiya kuma da na tuntubeshi a kan maganartaya amince da auren don haka daga yau sai yau kar in ji kar in gani kar in sake jin wata magana ta sake tasowa na cewar kin hana wani shiga gidan balle kuma Naja, wacce itama nan ba da dadewa ba za ta shigo, in kin kalli wannan yaron ma da kyau ai kin san ba zai yiwuya zauna da ke ke kadai ba kamar yanda ki ke zato tunda dangine dashi bila adadin tun daga wurin Babanshi har nawa to ya ya za a yi a ce ya rasa auren kowa a cikinmu sai ya je waje ya auro bare? Kuma ace wai da ita kawai zai zauna ai aurenki dashi kawia an tayashi so ne saboda shi dan yau tayashi son abinda yake so ka ke yi in har kana son zama lafiya da shi in ya so daga baya in an nutsu kaima sai ka sashi ya yi kaima kan da ka ke so din don haka kar in sake jin wata magana a tsakaninku, gara tun wuri ki yi tattalin da za ku zauna lafiya in ta zo in kuwa ba 75 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodungi ki yi hakan ba to duk abin da ya biyo bayan haka ke ki ka jawo in fatan kin ji ni?" Nana ta amsa "Na ji Umma na gode." Ta mike za ta fita, Naja'atu ta yi maza ta cc mata "Ai tashi za ki yi ki fita tun ba a sallamcki ba?" Ba ta saurareta ba ta yi tafiyarta tana shiga cikin falnta Nura ta samu a tsaye yana ta faman zirga-zirga a falon alamar dai cikin bacin rai yake yana ganinta ya kara tsuke fuska cikin muryar tashin hankali ya soma tambayar ta "Ina ki ka fito?" Kan ta ce mishi komai sai ya ce mata "Juya kawai ki koma inda ki ka fito don ba zan lamunci irin wannan sakarcin ba." Nana ta tsaya ta yi galala tana kallonshi cikin mamaki da kaduwa ya sake daka mata tsawa mai tsananin karfi ya ce "Kauce daga nan ki bani wuri na ce ko ba ki ji ni ba." A hankali ta bude baki ta ce mishi "Na ji, yanzu kuma zan yi hakan." Tana fadin hakan ta yi maza ta juya cikin hanzari ta fita ta bar gidan. Mu littafi na uku don jin karshen labarin. gamu a Sai an jima, Taku Hafsat C. Sodangi. 76 AKARA CITY OKSHOP 027614161 Tsarin Bango: ANKA - GRAPHICS FAGGE 07030319787 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 4 of 4