Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 4
jin kalamin ta ya cс "То ango yana fita unguwa ya dade nc? Kin kuma san ni mai yawan shan...." Nana ta yi maza ta ce "Na sani amma in dai don wannan ne ina zuwa. Nan ma gidanc Zuwairiyya arniniya ta ce bari in je in kawo ma akwai maganar da nake so mu karasa don muhimmiya сс." Ya ce "To babu laifi." Ta tashi ta koma dakin "Ni Zuwairiyya ba ki gaida angona ba balle ki kai musu ko da ruwan sha ne haka ki ke yiwa bakin Umar in sun zo?" Zuwairiyya ta tafe baki ta ce "Kin san ba na shiga falon nashi, shima duk abinda yake yi in ya ganni bari ya ke yi ya tsuke fuska sai ya ga na fita sannan ya ci gaba ke Nana ba ki fa san abinda yakemun ba ne wulakancin tsiya ne fa dashi, ran nan fa da su Ramla suka zo baya shigowa nan wurina amma har kofar dakin nan 47 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodang! ya zo ya tsaya ya cemusu kai ku fito nan. Muka yi shiru, sai ya daga labulen ya ce da ku fa nake, ku yi waje yana tsaye a wajen bai tashi ba sai da ya ga sun fita sai kuma ya ce idan na sake ganinku a gidana duk abinda na yi muku ku ku ka jawa kanku." Da sauri Nana ta ce "Yana da gaskiya saboda ya san su suke kara zugaki zan kuma gaya miki in har baki yiwa kanki fada ba, za su iya yi miki ingiza mai kantu ruwa, suna zuwa suna tayaki zagin mijinki su kuma kara miki shawarwari na abinda za ki rinka yi kina musguna mishi to da kuma hali zai yi ya ce yana son wata daga cikinsu da kin sha mamaki don kuwa aureshi za su yi da kuma kin kwashi kashinki a hannu kuma tunda ba ki iya karbar bakin mijinki ba to kin ga tafiyata don ba zan zauna anan ina zuba zance in bar mijina ya takura ba dama zuwa na yi in gaya miki ya ce zamu tafi garinsu." Zuwairiyya ta biyota tana tambayar yaushe? Ita kam tuni ta nufi falon Umar hira ta samu suna yi, amına tana shiga ta ce mishi "Mu tafi." Shima bai bata lokaci ba ya mike Umar ya biyosu don yi müsu rakiya, har jikin tasin da ta 48 Da Kamar Wuya 2_ Hafsat . Sodangi kawsu ita kuwa Zuwairiyya biyosu ta yi tana tambayar Nana yaushc ne tafiyar taku? Nana ta ce cikin satin nan da na zo ne in gaya miki in kuma roki Umar ya bar ki ki yi min rakiya, tunda akwai masu tafiya-da yawa to amma na janye tunda na lurakina da aminan da suka fi ni masu ba ki shawara kina dauka." Zuwairiyya ta ce "Wacce sharawa suke bani?" Nana ta kalleta a nutse ta ce "Taki 6atawa mijinki mana. Kina nufin shi bai san abinda yake yi ba ne da ya koresu a gdianshi? Ni ko mugun kallo ban taba hadani dashi ba nima kuma kawarki ce ta dalilinki muka san juna ni dashi inda haka kawai yake korar mutane da nima yakoreni, kuma tunda na gane'ni tawa shawarar da nake baki ba ta miki amfani ba kya ma gwda aiki da ita don ban kai matsayin hakan ba, a wurinki to zan kame kaina." "Ba haka ba ne Nana kin san ko kana son yin wani abu ma fa sai ka ga fuska."- Nana ta ce "A'a ba don Allah ki kayi niyya ba ki yi don kin san Allah zai yi sakayya akan dukkan al'amuranmu ki ba shi hakkinshi da ya hau kanki shima in ya dama ya ba ki in bai 49 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi gani ba wannan tsakaninshi da Ubangijinmu shi kenan to shi kenan Nana yanzu dai zan tambayeni in zo in miki rakiyar." Ta yi maza ta ce "Na fasa ban gayyaceki ba, randa ku ka shirya in ki ka gaya mishi zia kawoki." Ta yi tafiyarta, ba tare da ta tsaya sun yi wata doguwar sallana ba. Da daddare Nura ya shiga dakin Umma ya sametatana zaune, shima ya nemi wuri ya zauna suna hira. Umma ta kalleshi tace "Ni jibi ne ai tafiyar taku ko?" Ya ce "E Umme:" Ta ce "Iko sai Allah, Allah Ubangiji ya nuna mana lafiya yakuma ba ku sa'a." Nura, ya kalleta cikin murmushi ya ce "Ku ba za ku rakamu ba ne Umma ke da Baba?" Umma Talatu ta yi maza ta ce "Rakiya? Na ji fa an cehar da shiga jirgin sama ko?" Nura ya ce "E, Umma to ku ba za ku hau jirgin ba?" Ta ce "To na ga ana ta hidimar yara wa ke ta 'yan tsofaffi?" Nura ya yi maza ya ce "A'a Umma tsoho kuw. aai shinne yakkamataa yis ta tashi ai mu addininmu ya mutunta tsoho ya kuma ba shi 50 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi daraja mai girma don haka wanda bai san abínda yake yi ba shi ne bai san darajar tsoho ba." Umma Talatu ta yi maza ta ce "Ai fa haka ne Nura kai kam ba mu da abinda za mu ce maka sai dai mu roki Allah ya saka maka da alheri. Tun daga zuwanka gidan nan al'amura suka sauya mana, rashin lafiyar da Malam yake ta fama da ita na ciwon kirjinshi duk ya daina ashe dama duk wahala ce ta yi mishi yawa, mu kam mun gode da zuwanka yanzu kuma in kun tafi ko sai yaushe oho?" Nura ya yi murmushi ya ce "Ai kun riga kun zama iyayena Umama ba zai yiwu a ce na tafi na daďe ban zo na dubaku ba, har da hakan nema ya sa nake ganin yana da kyau in tafi tare da ku don ku ga wuri akwai 'yan abubuwan da nake so in shirya muku to amma hakan zai zamo bayan na sake zuwa ne kar kuma ki yi zaton zan dade, tunda ma ai ga 'yar unguwar na aura. Kin kuma san ba zai yiwu Nana ta dade ba ta zo ta ga Antinta da yara ba." Umma ta yi murmushi ta ce "Ai fa Allah ya sanya kauna mai yawa a tsakanin su." Kwana biyu bayan nan Nura ya kammala shirye-shiryenshi na komawarshi gida, ita kanta 51 Da Kumar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi Umma Talatu ta gayyaci aminiyarta mai kuli kamar yanda Nuran ya gaya mata ta nemi wata cikin aminanta ta yi mata rakiya. Tun safe ren nan a ke ta hidimomi tamkar wani sabon bakin akc sakewa yara sun cika gida sai koke-koke suke yi kowa na fadin zima zan bi ka Nura, ya tarasu ya yi musu nasiha sannan ya gaya musu zai tafi da mutum uku a cikinsu don su bi shi su gano garinshi amma ba zai zabi masu tafiyar da kanshi ba zai yi rubutu ne ya watsa cikin kwali kowa ya sa hannu ya dauka wanda ya dauki tafiya za mu tafi tare dashi wanda ya dauki hakuri zai bakura ya zauna sai wani lokacin idan na zo." Gaba daya suka amince akan hakan, nan danan ya koma dakinshi na zaure da da yake ciki ya soma rubutu a guntayen takardu yana nannadewa ta yanda ba zai bude ba sai in budewar aka yi, sai da ya rubuta adadin yaran gaba dayan su sannanya watsa cikin kwali ya fito ya ajiye a tsakar gida ya koma can gefe ya zauna kan turmi yana kallonsu suna zuwa daidai da dai-dai kowa ya zo ya dauki guda daya ya koma gefe yana jiran agama a bada izinin budewa, don kowa ya ga abinda ya dauka, sai da 52 Da Kamar Wuya 2 Hafsar C. Sadangi suka gama gaba dayansu sannan Nura ya kawar da kali ya sake kawo wani kwalin da shi kuma ya cika shi da mikakkun cnvelope da ya lillikcsu ya ajiye a inda ya dauke wancan kwalin ay sake komawa kan wannan turmin ya zauna ya cc musu "Yanzu zan ba ku umarnin ku bude don muga abinda ku ka dauka, amma kar kowa ya cс zai yi kuka ko ranshi ya baci don ya bude ya ga hakuri sai kawai ya wuceya sa hannu cikin wancan kwalin ya dauki envelope guda daya kun gane?" Suka ce e sun gane ya ce "To maza a fara." Nan da nan suka shiga bude takardunsu suna ganin abinda ke rubuce sai su wuce su dauki envelope su koma gefe su tsaya har aka gama mutane uku da suka dauki tafiya suka ware a gefe sauran kuma suma suka tsaya a gefe rike da envelope a hannunsu. Nura ya kallesu cikin nutsuwa ya ce musu "Na gode muku bisa bin maganata da na yi muku ga shi mun gama dukkanmu babu alamar bacin rai a tare damu ko ba haka ba nc?" Suka ce "Haka nc." Ya ce "To wannan cnvelope din da ku k 53 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi rike dashi ku je gida ku kaiwa iyayenku kudin da ke ciki a yi muku amfani dasu a wajen biya muku kudin makaranta, kun gane?" Da iyakacin karfinsu suka amsa "Mun gane yaya Nura mun gode Allah ya saka maka da alheri." Suka yi waje da gudu suna rige-rigen tafiya gidajensu don kaiwa iyayensu alherin da Yaya Nura ya yi musu, su gani shi kuwa ya wuce ya ci gaba da shirye-shiryenshi yayin da sauran yaran uku suma suka nufi gidajensu don shirin tafiya. A gidan Hajiya Salma kuwa nan ma tamkar wani bikin ake yi, 'yan uwa da abokan arziki sun hadu sai ciye-ciye da tande-tande suke yi masu tafiya kuma suna ta shirye-shiryen tafiyar su sai da aka ci aka sha sannan aka dunguma cikin motoci don zuwa airport, shima Nura da tashi tawagar can aka samesu. Tun kafin su tashi Nura ya yi waya ya sanar a gida don a san yana nan bisa hanya tare da jama'a don haka suna isa babban filin jirgin saman garin nasu suka samu an dade da isowa don taryensu suna sauka a jirgi motocin gidan su Nura ne suka dauke su zuwa asalin babban gidan 54 Da Kamar Wнуа 2 Hafsat C. Nodung! su inda 'yan uwa suka tarye su cikin murna da farin ciki irin yanda aka samu gidan cike da masu yiwa Nura murnar dawowa ya isa ya tabbatarwa wadanda suke tare dashi wafanda ba su san ko shi wayc ba irin asalin gatan da yae da ita ko da baa tsaya an yi musu wani bayani ba, tunda aka sauki su Hajiya Salma da su Umma Talatu a wasu fakuna guda biyu da suke kallon juna ake ta shiga da fita da nau'o'in abinci, iri-iri ita kuwa amarya ko sanin nda aka sauketa ba su yi ba tana can tare da angonta da kuma su Rahma ita kam Hajiya Salma ita kadai ta san yanda take jin zuciyarta don dadi ganin irin daular da 'yar uwarta ta shigo, in ban daAllah wa ke ni'ımta bawa da irin wannan ni'imar a rana daya? Ita kuwa Umna Talatu mamakin Nurane ya kamata, yanda aka yi ya iya zama cikin dan tsukakken dakin, zauren da suka ba shi mai yawan shirgi sai daga baya ne ma suka kwashe shirgin nasu suka hbar mishi dakin a haka. Ita kam Umma Talatu a wurinta ba ta tabaganin mutum mai rashin girman kai da tawali'u da iya mu'amala da na kasa dashi irin Nura ba, tsawon zaman da ya yi dasu bai taва nuna wata alama da za ta iya ganc shi din wane 55 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodungi iri ba ne, ta soma tunanin ta ko wane hali shi din ya fito daga babban gida ne ta dalilin yawan alherin da yake musu ita da mijinta, dama wadanda yake yiwa a waje masu shigoa suna yi mata godiya, saboda zaton da suke yi ita din uwarshi се. Nana kuwa tana can a inda aka yi mata masauki ita da Rahma a dakin uwar mijinta Hajiya Kubra ga 'yan aiki sun kewaye ta kowane motsi ta yi sai sun tambayeta ranki ya dade kina bukatar wani abu ne? Ta ce musu a'a nan kuwa babu abinda take so cikin zuciyarta irin ta samu kebewa tare da Antin ta don su samu zantawa kan wannan abin mamaki da suka samu kansu a ciki sai dai ta rasa yanda za ta yi ta yi haka din. Hajiya Kubra da kanta ta sbiga dakin da ta sa aka sauki su Hajiya Salma bayan da aka nutsu ta samu wuri ta zauna cikin fara'a da nuna girmamawa a garesu suka gaisa cikin dan takaitaccen lokaci suka saki jiki da juna har suka yi hira saboda irin yanda ta nuna musu cewar ita din mai matukar fahimta ce. "Amma dai ai za ku dan mana kwana biyu ku dan huta kafin ku tafi ko?" Ta yi tambayar bayan ta mike za ta fita. 56 Du Kamar Wuya 2 Hafsal C.Sodangi Hajiya Salma ta ce mata "A'a mu kam in so samu ne ai kuma gobe sai mu koma garinmu." Ta ce "Gobe-gobe, haba ai idan ma ba za ku tsaya ku ga komawar amarya gidan mijinta ba sai ku bari sai jibi ki dan huta kadan tukunna ba su yi musu ba suka amsa da to Allah dai ya nuna mana ta ce musu amin.ta fita. Cikin kwanaki biyun nan da suka yi babu abinda akeyi sai hidimar biki ga 'yan uwan Nura sun cika gida maza da mata harkarsu kawai suke yi duk wanda ya zo kuwa sai ya shiga wurin da aka sauki su Hajiya Salma ya gaishesu cikin girmamawa ya kuma tambaya ina Umman yayan take? Ace musu gata nan a nuna musu Umma Talatu ita kam Umma gajiya ta yi ta cc kai in ka ga ma dai maikudi yana wulakanta talaka ko yana wani jiji da kai to shima arzikin nashi bai kai ya kawo ba nc, tunda ga Nura da 'yan uanshi da iyayenshi a wurinata baata taba ganin masu arziki irinnasuba bata kuma taba ganin mutanen da suka kaisu sanin darajar dan adam ba da kuma girmamashi kwana biyun da su Hajiya Salma suka yarda zasu yi suna cika aka yi musu sallama ta girmamawa alherin da aka yi musu nai matukar yawa ne,cita kam Umma 5757 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi Talatu ma Nura ya s ne ta yi zamanta zuwa wani 'raci da shi din zai samu zarafin da zasu taho tare don ya shirya musu abinda yake son yi musu wanda ya ce sai ya dan samu nutsuwa tukunna zai yi. Ta ce mishi a'a gara dai ta je gida tunda ba ta nemi izinin dadewa wurin tsohon mijinta ba, don haka bai dace ya ganta shiru ba sai kawai ya ji labari a wurin wadansu Nura ya ce "Haka ne Umma Ubangiji ya sa muma mu yi koyi da halayenku a zamantakewar aurarrakinmu na wannan zamani." Ta ce "Amin dan nan amma kai kam ai ina ganin ka dace da damun mace ta kirki mai tarbiyya da sanin darajar mutane, to kai ma kuma haka kake don haka in Allah ya yarda ba zaka samu matsala a gidanka ba sai dai kawai mu yi muku fatan Allah Ubangiji ya ba ku zuri'a wacce take dayyiba." Nura ya ce "To Amin Umma." Ya sake kawo wani alherin bayan abinda ya san mahaifiyarshi ta yi musu ya ba ta ya ce "Wannan rikewa za ki yi a hannunki Umma kina tafiyar wa a hankali ba na so in zo in samu ke ko Baba wani ya sake shiga wani hali na wahala." 58 S KB ta Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi Tana murmushi tana fadin "Wahala kam ai mun fita daga cikinta tunda ga ranar da Allah ya kawo mana kai." Gaba daya aka debesu aka kaisu filin jirgi don su koma garin su, babu abin da bai yiwa Nana dadi ba irin dagewar da Antinta ta yi kan sai ta tafi da Rahma a cewar ta wai in dai Kananan yara Nana take so, to gasu nan cikin dangin Nura don haka in har ta kyautata mu'amalar ta dasu to kullum sai sun cika mata gida. Kwana ku bayan nan Nana ta tare a gidan mijinta wanda ya sha gyara aka kuma kawatashi ta yanda zai dace da abin da Nuran yake bukata. Dawowarsu cikin danginshi ya kara bayyanar wa Nana wane irin miji ta aura, Nura mutum ne mai yawan 'yan uwa mai yawan harkoki mai yawan jama'a, amma hakan bai hanashi ba ta hakkinta na zama tare da ita ya yi hira ya yi. wasa da ita ya kula da dukkan al'amuranta kamar dai yanda shari'a ta bukaci namiji ya yi wa matarshi wadannan halaye nashì sai suka kara sawa itama Nana at kara himmatuwa wajen ganin ta kyautata mishi ta bi umarniusii ta faranta mishi rai, ta girmama 59 Da Kumar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi iyayenshi ta yi mu'amala mai dadi tsakaninta, tunda shi da yake namiji yake sanar da ita ya san ya girmamata ya ba ta hakkinta to ita kuwa a matsayinta na matarshi wacce take zaune a karkashin shi me zai hana ta yi mishi biyayya takuma kyautata mishi? Watanni biyu bayan nan Nana tana zaune. tare da mijinta a falonshi hidimar abin karyawarshi take yi, inda ta shirya mishi speedy orange cake Nura sai kallonta yake yi yayin da ita kuma ta maida hankalinta kan hidimarshi da take yi zuwa can ya gaji ya ce mata. "Ni Nana ya ya muke ne?" Ta yi maza ta juyo ta kalleshi tare da tambayarshi "Na me fa?" Ya sake kallonta cikin nutsuwa, hakan ya tunatar da ita abinda yake nufi ta yi maza ta kawar da kanta ta ci gaba da abinda take yi, ba tare da ta sake tanka mishi maganar tashi ba, ya kammala hidimominshi ya gama shiri ya yi mata sallama zai fita ta ce "To a dawo lafiya Allah ya bada sa'a." Ya amsa cikin jin dadi ya fita ita kuma ta dawo ta ci gaba da ayyukan gidanta da ta saba yi kullum duk da 'yan aikin da take da su, Nana ba 60 Da Rumar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi ta amince da bar wa 'yan aikinta dukkan hidimomin gidanta ba ta fi amincewa da ta tsare hidimomin mijinta in ya so sauran ayyukan su su yimata.Sallamar da aka yi ce ta dawo da nutsuwarta zuwa wurin da sallamar ta fito, ganin Zuwairiyya a tsaye ya sa Nana ta kurma ihu nan tke kuma ta daka tsalleta isa wurin da Zuwairiyya ke tsaye ta kankameta cikin murna da farin ciki ganin aminiyarta abinda ba ta taba zato ba, a wannan dan Kanknain lokacin. "Zuwairiyya." Nana ta sake fadi cikin matsanancin farin ciki, ta kamo hannunta sukа wuce ta tsakiyar falon zuwa inda falonta yake kai tsaye har cikin dakin kwanciyarta ta kai ta kan ta ce matakomai sai Zuwairiyya ta kalleta ta ce mata "Yallaßan fa yana waje?" Nana ta kkalleta ccikin onutsuwa tana tambayarta "Wanene yallabai?" Zuwairiyya ta yi murmushi ta ce"To wa ki ke zaton zan kira yallabai a yanzu in ba Umar ba." Nana ta kyalkyale da dariya ta så hannu ta rike baki ta ce "Haba ke ki ce mun duniya ta yi dadi, gaskiya mana na ganki kin wani canza mun $61 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi to bari in gayawa Nura isowarku sai in ji abinda zai fadi." Nan da nan ta jawo wayarta ta sanar da Nura zuwan su. Nan da nan Nura ya bar abinda ya ke yi, ya taho gida don taren bakon nashi, Nana ta isa falon mijinta cikin sutura mai yalwa da hijabi, don ta yiwa mijin aminiyar tata barka da zuwa ta. kuma gabatar musu da dan abin tabawa kafin ta kammala shirya musu abinda zasu ci, tana dawowa dakinta ta ce "Ke Zuwairiyya ai zuwa za ki yi mu shiga kicin don mu shirya abinda zamu ci." Zuwairiyya ta ce "Ni da ko gama hutawa ban yi ba za ki sani wani aiki." Ta ce "Mu je in ba ki kujera ki zauna ni in yi aikin ban ce sai kin tayani ba." Та се "Тo wannan kuwa." Suna shiga. kicin din Zuwairiyya ta ce "Waw Nana ya ya za a yi a gaji da girki a cikin wannan kicin din?" Nana ta yi murmushi ta ce "Hala kicin din ne zai hana gajiya?" Zuwairiyya ta ce "Kwarai kuwa ta sa hannu ta dauki wani lafiyayyen tumatur da ya ba ta sha'awa ta wankeshi ta soma sha, Nana ta dan 62 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi kalleta ta ce "Hala mai son tumatur muka samu?" Zuwairiyya ta yi tsaki ta ce "To daga an shirya kuma sai a fara cewa an samu an samu? Shima yaliabai din ya wani tasani a gaba wai bai yarda ba ya ga alamar da wani abu a makale." Nana ta yi dariya ta ce "To ko ke fa Zuvairiyya daga shiryawarku dubi yanda ki ka canza amma da kına zaure a gida kun wani takurawa rayuwarku kuma duk laifinki ne." Zuwairiyya ta ce "Babu wani laifina shima ai miskilanci ta sake mika hannu ta dauko wani tumaiur ta ci gaba da sha Nana ta ce "A'a bale da alamar maigidan yana da gaskiya akwai wani abu a makale bari a yi mishi cushen tumatur da kwai. Zuwairiyya ta kara matsowa kusa ta ce "To ni dai ai kin san na fi son a gaya mun kayan hadin kafin a soma girkin." Nana ta ce "Haka ne ga abubuwan da muke bukatar nan kın gansu na kammala su wuri daya tumatur masu tauri gwargwdon yawan iyalinkin kamar n da yake mu hudu ne zan yi amfani da guda takwas, kwai takwas, nama dakakke cokali takwas, butter cokalf uku sai kayan kamshi ta ci gaba da harhadawa yajin da 63 Da Kamar Wuya 2 Hufsat C. Sodangi sakaci gaba da hirarsu ta dauko, ke ki ce min dai kawai maigidan gara yake sha, Zuwairiyya ta fadawa Nana, Nana ta yi murmushi ta ce "To ina arafanin ka iya girki ba ka ciyar da mijinka abinci mai dadi ba?" Zuwairiyya ta ce "Kina da gaskiyar ki Nana, ai nima yanzu shawarar taki nake bi." Nana ta yi murmushi ta ce "Ke ki ce mun zama ya yi dadı." Zuwairiyya ta tayata murmushin ta се "Ai wannan tafiyar ma ba tawa ba ce ta Umar ce cewa ya yi wai in yi mishi rakiya ya zo ya yi miki godiya kan irin shawarwarin da ki ka rinka ba ni wai ya san in ban da ke da har yanzu muna nan muna irin wannan zaman da da can muke yi." Nana ta ce "To in ban da ke Zuwairiyya miji in an riga an yi aure ai ba a irin wannan zaman dashi tun da kin riga kin dawo karkashin zamanshi in kin gyara zaman kin gyarawa kanki ne kamar yanda in ki ka bari zaman ya lalace za ki tarar mafi yawancin lokaci macen ce a wahala mai yawa, to balle ke da tun farko ba wai ba kya son Umar bane kwata-kwata ke dai kawai wasu daga cikin halayenshi da dabi'unshi ne ki ke 64 Du Kamar Wuyu 2 Hafsat C. Sndangi anin ke ba su yi miki in ki ka kyautata mu'amala tsakaninki da shi za ki iya canza mishi wasu daga cikin halayen daba kya son abinda yа gagara kuma sai ki yi hakuri dashi a kansu." Zuwairiyya ta cc "Ai ni a farkon zaman priskilancinshi ne ya kara sawa na Kara Kin shiga harkarshi tunda ina ganin tamkar zai iya wulakantani duk da dái na sani tun farkon wana gidan babu abinda ba ya yi min na akkina da yake kanshi in ban da bai shiga harkata bayan tafiyarki kuma da na yi mufin yin vani saboda shawarwarin da ki ka bani sai na auki matakin in na yi girki in zuba mishi, in kai mishi in ajiye mishi a falonshi, in yi tafiyata na ki mishi abin karyawa da safe, bai tababa na jc dáuko lokacin da na kai mishi na rana, shima nmaajecna ajiye mishi na dáre na samu bai taba haş, naz ajiyes wandaa na kais mishi: naa dauko wannan har na dawoo dákinaaina tunanin in har obe ma na wuni ina ajiye mishi bai taba ba zan diinaa dom ba zan iya lamuntar hakam ba, sai gashi ya turo kofaaya shigoxfakina wandá hakan shi ne karoona farko tum zuwana gidan idan ma wataa magana zai yi daga bayan labule yake bayawa, ya gaya min, ina ganin shigowarshi na 65 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi yi kamar ban ganshi ba, sai na ji ya yi magana cikin murya mai cike da nutsuwa, ni abincin da ki ke ajiyewa a falo na wane ne? Ban daga kai na kalleshi ba na ce mishi naka ne, ya kara sakin fuska ya ce to haka ki ka ga ya dace a yiwa maigida Zuwairiyya aje a dangwarar mishi da abinci kawai a tafi ba tare da an tsaya an ga ya ci ko bai ci ba? Ban amsa mishi ba, sai ya ce ai tunda dai ki ka gane ina da bukatar abincin naki to sai kawai ki karasa aikin naki don ki samu cikakken ladanki, ban kula ba sai ya miko hannunshi ya kamo nawa ya daganiyana fadin mu je ki zuba min abincin in ci, ban yi musu ba, na biyoshi muka taho falon nashi muka zauna na soma zuba mishi, maimakon ya soma ci sai ya ce sai dai mu ci tare don bai ga lokacin da nima na ci wani abu ba, tun daga wannan lokacin sai kuma ya zama duk lokacin da ya ganni zan shiga. kicin zai biyoni mu shiga in ina girki shi kuma yana tayani da wani aikin har sai mun gama mu dauko mu zo falo mu zauna mu ci tare, bamu fi kwana uku a haka ba sai kurna ya bijiřewa kwana a dakinshi shi kadai, tun daga nan şhi kenan sai kuma komai ya wuce al'amura suka daidaita, yanzu kuwa kinga kullum cikin cin 66 Da Kamar Wuya 2 Hafsat C. Sodangi amarcinmu muke. Jiya tun safe ya ce mun in shirya zamu taho ya zo ya yi miki godiya, kan irin shawarwarin da ki ke ba ni." Nana ta ce "To ko ke fa Zuwairiyya me ya fi zaman lafiyatsaanin mata da miji dadi." Zuwairiyya ta ce "Gaskiya babu." Suka kammala girkin da suke yin Nana ta shirya musu abin sha gaba daya suka kwaso suka kawo falo inda Nura da Umar suke zaune suna hira tare da dan motsa baki, Nana ta sake ajiye musu cushen tumaturin da abin sha а gabansu ta kuma nemi wuri ta zauna kusa da mijinta tana kula da abinda yake ci yayin da itama Zuwairiyya ta matsa kusa da nata mijin "Ni fa yanzu wani ji da ni ake yi." Umar yana cia abirci ya ke maganar. Nura ya yi murmushi ya ce "To ai an kyauta dama can abinda ya dace a yi maka kenan." Uman ya sake wani mrumushin ya ce "A to ban samu, hakan ba sai da Madam dinka ta sa baki tukuna aka

Chapter 3 of 4