Reading MATAR SO Complete PART 2 by MAI DAMBU Chapter 8 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Hmm mutumin nan gwanine a rashin kunya lokaci gida Mai nasara ya birkice min, nima kuma bakina bawai ya mutu bane, sai dai nasan zan kwaci kaina.
Duk yanda nazo dakatar da al'amarin yawucce tunanina dan bai ji a ranshi ya kyaleni ba, sai da yabiya bukatarshi. Kuka nake sosai kamar raina zaifita haka ya jiyarda kanshi daɗi, da farin ciki dakyar na mike. Na ɗaura zanina Allah yaso da under dasu nagoge gurin da muka ɓata, yana magana amma ban saurareshi ba nayi cikin gida kamar munafuka na shige ɗakinmu, dake Aunty na ƙitchen wanka nayi tare da tsarkake jikina, ina kuka.

Fita yayi a gidan rashin sawai sai wani nishaɗi yake ji a ranshi, gidanshi ya nufa. Ya sami balkisu a falo kallonta yayi yaga ta mike, sai kunyarta ya kamashi. Murmushi yayi sannan yace.
"Yau naje gidansu maryam tana gaisheki."

Ganin yanda yake farin ciki, yasata fahimta duk yanda akayi Yunus yasami maryam kamar yanda yake so.

Wanka yashiga yayi, sai murmushi yake dokawa, yana gamawa yafito. Sanye da jallaɓiya ya zuwa falon, abinci ta kawo mishi, aikuwa yaci sosai.

**** Bayan kwana biyu, naje gidan Aunty Hamdiya na wuni a gidan sai yamma na dawo ina dawowa nasamshi a kofar gidanmu, dake mangariba tayi shigewa nayi. A bakin mama naji wai tun huɗu yake kofar gidanmu, sallah nayi ina idarwa na mike. Zan fita mika min turara Mama tayi na goga a jikina, sannan tace.
"Don Allah ku fahimci juna dashi, babu daɗi zama haka ace baki da auren da karancin shekarunki ki fahimci Ummarki."

Shiru nayi ina kuka. Sannan nafita wajen shi, buɗe motar yayi ya shiga. K'in shiga nayi sai da yace.
"Don Allah kishigo, ana kallonmu."

Kamar na fasa ihu na shiga ko rufe kofar banyi ba, bai damu ba, mikar da hannunshi yayi yaja kofar ya rufe, sannan ya kunna Ac.

Shiru nayi kaina a sunkuye kirjina kamar zai fita lura nayi da jikin gilashin motar, kamar mai duhune kai kana ganin na waje nawaje bai ganinta, sannan ta gabar motar ma kusan rabinta duhu ce,

"Malam idan baka da abincewa zan fita."

Shakar kamshin yayi sannan yace.
"Duk ɗaya ne, nidai kiyi hakuri mu koma gidanmu."

"Taɓ naje kasa a cire min mahaifa, Allah ya min tsari." na faɗa mishi kamo hannuna yayi tare da kaiwa fuskarshi yace.
"Insha Allah ko yara dubu zaki haifa min ina sonsu."

"Daga baya knn, wai anyi sadaka da bazawara."
Na faɗi haka.
"Ynx kina nufin nasake ki."
"Yanzun naji batu wai an daki kwarto da buje"
Zaro idanun yayi yana kallona.
"Maryam yanzun kinfi sha'awar zawarci da zaman gidan mijinki."
"Toh miye a cikin zawarcin, ai hannun hagu ba bakon wanke kashi bane."

Tsura min ido yayi yana al'ajabin yanda nake faɗa mishi magana kai tsaƴe.
"Yanzun babu ɗan girmamawa nan maryam."
"Wai yanda baka tausaya min ba akan mi zan tausaya maka, Ina girman take? Hhh wai ancewa akuya sarkin fawa ya mutu' tace ya mutu da wukar yankanshine"

Jingina yayi da seat ɗin motar yana nazarin yanda zai shawo kaina.
Ganin babu halin haka ya kai hannunshi kan nawa na janye da sauri, take ya sake maisawa, sannu a hankali komi ya sauya da wayyo da dabara ya cima burinshi a cikin motar nima kamar wawuya bansan ya akayi komi ya faru ba sai da naji yana maida min kayana, sannan na fashe da kuka. Sosai rarrashina ya shiga yi, cikin kuka nace.
"Laifin mi na maka, a cikin gidan ubana da bani da kima da daraja kazo kake kwanciya dani, mi yasa bazaka je kanemi mata masu daraja da kima ba?"

"Kiyi hakuri mana maryam, Allah ma muna mishi laifi ya yafe mana sai mune baza mu yafewa juna ba nayi kuskure kiyi hakuri."

"Bazan iya zama da kai ba, dan nima na rokeka ka juya min fuskarka baka son ganina da abin cikina da yana tare dani da yakai matakin da zanji bugun zuciyarshi, ka kashe min rayuwata ka hanani amsa sunar da kowacce mace take buri Uwa, waya sani ko shi knn bazan kuma haihuwa ba."

Cikin ɗauki yace.
"Wallahi zaki kuma, ki zo muko ma gidanmu ki gani sai Allah ya bamu wasu."
Harara na ɓala mishi sannan nace.
"Buɗe min kofa nafita."

Ba musu ya buɗe min nayi waje abina.

.......Tun daga ranar ban kuma jin ɗuriyarshi ba,sai da muka kusan sati biyu sannan na ganshi, a lokacin yazo zai murjeni akayi rashin dace nima ina up, dole ya haɗi maitarshi amma bai ji daɗin haka ba.
Duk yanda zan kuntatta mishi ina bi dan duk da ina hutun kullum sai yazo ya matseni son rashi.
Cikin kwanakin nan wani zazzaɓi yake fama dashi, ga meeting da yake zuwa akai akai, wanda dakyar yake fita, karshe Ahmad ne ya amshi zuwa meeting ɗin.
Shi kuma ya dawo gida ya cigaba da jinya, kiran Dr Nafi Balkisu tayi. Taxo ta sanya mishi ruwa da allura.

Bayan karewar ruwa daf magrib, Aman ya kirashi yana sanar mishi da cewa.
"Yunus mun gama komi, sai tafiyarka kawai ya rage wanda muka so ɗagawa amma sunce haka ba zai yu ba, ka daure ka tafi idan ba damuwa muma munso zuwa toh a gaskiya baidace mu tafi dukkanmu ba."
Can kasar makoshinsa ya amsa sannan yace.
"Nagode."

Kallon Agogon ɗakin yayi, ya mike dakyar ya nufi ban ɗaki wanka yayi da alola, ya fito sanye da rigar wankan sannan ya buɗe gurin kayanshi yasaka kayanshi.

Wani irin bakon yanayi wanda yake ɗauke da kewata, masalaci ya nufa.
Bayanan idar da sallah, gida ya dawo ya ɗauki key sai unguwarmu.
Ina daki nayi wanka kenan zan gabatar da sallah akace wai yana sallama dani, tsuka nayi kasa kasa,
Sannan nayi sallah na, na gyara jikina. Riga da wandon pakistan mai ruwan kwai nasaka sannan na ɗauko hijab ɗina wanda bai kashi haske ba, nasaka.
Murmushi nayi a raina nace.
"Gaskiya Rahilah ta kyauta min da ta kwaso min kayana kaf, daga gidanshi."

D'aga labule Mama tayi tare da mika min kofi tace.
"Sha maza."
Kaman zan fasa ihu haka na shanye sannan na fita, sai da nashanye naji wani mugun daɗi a maganin har na isa bakin kofa na dawo nace.
"Mama ko zaki kara min wannan maganin daɗinshi yayi yawa."
Hararata tayi da sauri nafita, oho dai nasan koma ya-ya ne maganin yayi min daɗi kuma sai na koma ta kara min.

Ina fita nasame shi a cikin mota, shiga nayi nima na zauna. Ko kallonshi banyi ba na juya mishi baya, tada motar yayi kafin nasan abinyi tuni ya cillamu kan titi, shiru nayi ina tuna faɗar da Umma tayi min, yau da safe akan yan unguwa sun fara surutun naki komawa gidan mijina. Kuma muna tanbaɗewa a waje, maganar dai ba daɗi haka na shanye jinsu gidanshine dai bani komawa.

Tsohon gidanshi ya kaini, kafin nan ya tsaya a wani store yasaya mana fresh milk, can gaba kuma yasayi nama.
Har muka shiga cikin gidan, kin fita nayi a motar yazo ya kwashi kayan yayi ciki dasu, dawowa yayi ya buɗe inda nake ya sunkuceni sai cikin gidan.

A falo ya direni sai a lokacin naji jikinshi zafi, ina son tambayarshi amma na kasa, shiru nayi na cigaba da zama a kujeran dake kusada shi, kitchen ya shiga ya duba bai ga komi ba, dakyar ya buɗe dirowar kitchen ɗin. Ya ɗauko kofi da filet, buɗe famfo yayi ya wankensu sannan ya fito.

Juye namar yayi, wai zai bani ko kallo bai isheni ba nace.
"Kasan nafito gidan da aka san darajar ɗiya mace ne kuma Alhamdulillah, talakan mahaifina ya ciyar dani, kaci kayanka kawai."

Lumshe idanunshi yayi yana jin saukar maganar da na faɗa mishi, ajiye namar yayi, sannan ya mike tsaye ban gama tattara nutsuwata nasan mi zaiyi ba sai naji yayi sama dani.
"Dalla ka sauke ni, ka maidani kamar yar babyn wasan yara."
Bai tsaya a ko ina ba sai ɗakinshi, ya ajiye ni sannan ya rufe kofar, zanin gadon ya zo ya cire tare da buɗe gurin da ake adanasu ya ɗauko wani ya shimfiɗa.

"Kazo ka maidani gida, bana son abinda kake min."

Bai kulani ba, sai ma fincikoni da yayi, na fada kanshi zubawa juna ido mukayi,.muna kallon cikin idanun juna.
Sumbatar goshina yayi daga nan ya gangaro wuyana har zuwa kirjina.
Lumo nayi a jikinshi, tsigar jikina na mikewa. Zare min hijab ɗina yayi, ya ajiye a gefe. A hankali ya cigaba da bina har ya zuge zip ɗin rigana ya ajiyeta a gefe, ɓale bra ɗina yayi, sannan ya cigaba da abinda yake yi.

"Maryam!!!"
Ya kira sunana, "Hmmm" nace mishi.
Sabida ni kaina na masifar faɗawa hannunshi.
"Zaki koma gidana? Mu cigaba da rayuwarmu."
"Humhhum."
"Ki min magana mana, wannan humhum yana cutar dani."
Gyara kwanciyana nayi A kirjinsh, ina jin sakonshi na bin jinin jikina. Sonshi da kaunarshi suna ruruta min kwanyana.
Karan zuge zip ɗin wandona naji na ɗago kaina a kasalance ina kallonshi.
Lumshe idanuna nayi sannan nace.
"Yanzun dai kazo ka tasani a gaba, zaka nutsu dani. Sannan kaima kanka baka da lafiya, kuma zakayu aikin karfi, kuma nan gaba nasake dakai ka zageni har da iyay..."

Ban sami damar karasa maganar ba, sabida yanda ya haɗe bakinmu. A zafaffe ga jikinshi zafi yake karayi.
Sannu a hankali yunus yacima matsaya guda, bayan ya ɗauki dogon lokaci yana gurjeni son ranshi tare da sarafani. Tuni zazzaɓin suka fecce, sai gumi dake sauka a jikinshi.
Idan ana kiran jigata toh yau najita a hannun Mai Nasara dan sai da ya min filla filla, sannan ya kyaleni, na koma gefe nasake kuka sosai, sabida bansan yazanyi da raina ba, Yunus yayi min abubuwa dayawa, kuma sai bina yake yana yanda ya gadama dani.

Janyoni yayi jikinshi yana shafa bayana tare da bani hakuri, da rarrashi.
Kwace kaina nayi naje ban ɗaki nayi wanka, ina dab da fitowa ya shigo tare da rufe kofar, wanka yayi shima. Muka fito lura nayi da mutumin nan baisan gajiya ba, dan ina son saka kayana amma ya kwace tare da maidani gado, yayi min rumfa.
Ina ji ina gani, yasake samun nutsuwa dani, kallon a gogon ɗakin nayi naga sha biyu har da rabi, na tashi na faɗa ban ɗaki nayi wanka da alola nazo nagabatar da Isha tare da shafa'i da wutir.
Mikewa yayi shima ya faɗa banɗaki yafi.
Sallah yayi, yana idarwa na fashe da kuka nace.
"Ka maidani kamar inji ka ɗaukoni, ka kawo ni nan. Dan baka san daraj."

Saka hannunshi yayi a bakina yace.
"Maganarki tana min zafi sosai maryam."
D'agani yayi. Sannan ya cire min kayana ya zaro wata shirt ɗinshi yasaka min, muka koma gadon,

Rungume ni yayi barci yayi gaba damu, kiran sallar asuba ya tadamu, mukayo alola shi ya tafi masalaci ni kuma nayi a gida.

Yana dawowa na tada rigima, sai ya maidani gida, lallaɓani yayi cikin dabara da wayo yasake moreni, yana gamawa nasaka kayana dan ko wanka bayi ba, nace gida kawai.

Saka kayanshi yayi, muka fita ɗaukar naman yayi muka bar gidan.

Allah yaso har muka isa gidan malam na masalaci, yana tsayawa ina fita mika min laidar yayi da atm card ɗinshi da pin ɗinshi.
Da sauri na shiga gidanmu, umma da Aunty suna kitchen.
Ummana ce kawai taga shigowats,

Ban ɗakinta na wucce naje nayi wanka, ina fitowa nasameta a bakin gado, kunyace ta kamani. Nace.
"Ina kwana Umma!"
"Kiwa zuciyarki adalci ki bata abinda take so,.yau ce rana na uku da na kamaki kina wanka, maryam ni bazan hanaki farantawa mijinki ba, amma idan yazo kice ya sami Malam.ki koma ɗakinki na gaji da surutun mutane."

Cikin kiɗima nace.
"Wallahi Umma ba wannan wanka da kike tsamani bane."

"Jiya a ina kika kwana?"
Sunkuyar dakaina nayi,
"A gurinshi ko? Karki maidani yarinya maryam, kowa ya bata yasani kowa ya gyara yasani, gyara kayanka bai zama sauke muraba ba, Allah ya kyauta."

Tana fita na fashe da kuka, sosai sabida na mata musu akan gaskiyarta iyakar abinda tagani tayi min faɗa akai amma naki ji,


*****
Zarya yake a ɗakinshi duk yasawa kanshi damuwa akan matar ɗan uwanshi, ajiyar zuciya ya sauke lokacin da ya tsinci sakon karta kwana a wayarshi, dubawa yayi sannan yasake murmushi,

Sake kiran wayar yayi yace.
"Kasa ido akan komi, yau zai bar kasan nabaka wuka da nama."
Kashe kiran yayi sannan ya nemi guri ya kwanta, yana kaɗa kafanshi.

"Maryam Sajida.......Na kusan mallakarki."
Yana faɗan haka ya sake yar karamar murmushi.
****
Koda Daddy ya isa gida, ɗakinshi ya wucce da sauri. Yana rufe kofar shi. balkisu tarda a cikin ɗakin duk sai yaji ya muzanta a gabanta, murmushi tayi sannan tace.
"Daddyn Huda, ya jikin naka."
Kauda kai yayi cike da kunya yace.
"Da sauki."
Yana gama faɗar haka ya shige ban ɗaki. Fita tayi a ɗakin jikinta ba kwari, da ciwo ace mijinka ya kwana a wani gurin, saukin abun tasan duk inda zai kwana toh da Nice ko Fareeda tunda dukkanmu bama gidan...

Abinci ta haɗo mishi tazo tasamu yana shiryawa cikin black suit.

Ajiye mishi tayi sannan ta juya zata fita yayi maza ya riko hannunta, yanjota yayi jikinshi.
Tare da rungumeta kishin mijinta da kaunarshi suka karya mata zuciya, bata sannan sadda ta fashe da kuka ba, bubuga bayanta ya shiga yi har tayi shiru.
Hannunshi nakan kugunta ya kai bakinshi kunnenta yace.
"My Billy am sorry, bazan kuma ba. Amma maganar gaskiya ba halina na sauya ba ina tare da kanwarki maryam ce."

"Dama ni bance komi ba, kawai dai bana jin daɗin haka ne amma zanyi kokarina gurin samun farin cikinka."
Shiru yayi yana kallonta, tausayi ta bashi, sabida yasan bata da damuwa da fitinarshi amma yanda shi kanshi yake mantawa da cewa itama mutunce yasashi nufar gado da ita. Rike shi tayi tare da ware ido tace.
"Mi kuma zakayi."
"Shhiii."
Ya saka yatsarshi a bakinshi, daga nan kuwa lulawa yayi da ita duniyar majidaɗi. Kishi yasa Balkisu kasa ɓoye jin daɗinta har da kuka(😹)

Bayan sun dawo daga duniyarsu yana rungume da ita yace.
"Tayu idan nafita yanzun bazan dawo ba natafi kenan."

"Kamar Ya?"
"A'a nufina idan na fita zan wucce china sai nan da sati biyu zan dawo koma ya-ya ne ki kula min da kanki da kuma Yarana da Fareeda da Maryam, idan na dawo duk zan dawo dasu inyaso fareeda na kaita asibiti a dubata, ko Allah zai sa a dace. Kema sai a duba min ku."

Gyaɗa kai tayi.

Mikewa yayi ya shige ban ɗaki wanka yayi a gurguje yasa kayanshi sannan ya buɗe ma'ajin kayanshi ya ɗiba tare da shiryasu a jakarshi, ya fita.
Addu'a tayi mishi sannan ta gyara kwanciyarta,

****
Ahmad da Aman su suka mishi rakiya, airport. Kafin jirginsu ya tashi ya tura min.

*Zan tafi bamu yi sallama ba koma Ya-ya ne Ina kara baki hakuri da Kuskurena*
🌹🌹🍀
*MATAR SO*
🌷🌷🌻

*MAI_DAMBU*
*Wattpad:Mai_Dambu.*

Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai....

Sadaukarwa Ga Mai Nasara Team😂

_Wannan buk ɗin hakk'in masu shine idan kinsan baki saya ba karki karanta, mai fitarwa kuma ki duba girman Alkawarin da kika ɗauka na cewa bazaki fitar ba, tunda nace idan kinsan zaki saya ki fitar na Yafe ba sai kin saya ba_



*BOOK 2👈*
Page....9

Daga
Masoyinki Mijinkii
Kashe wayar yayi yasaka a aljuhunshi sannan ya mikawa su Ahmad hannu yace.
"Allah ya kaddara saduwarmu."
Rungume shi sukayi kamar zasu fasa kuka, shelar jirginsun zai tashi yasa shi ɗaukar jakarshi ya kai inda ake sakawa kafin a shiga jirgi.
Yana ajiyewa ya juya zai wucce suka bangaji juna da wani matashi, ɗago kai yayi ya kalli Matashi, wanda ya diririce tare da cewa.
"Sannu bansani bane."
Yana faɗar haka ya bar gurin.
Wuccewa shima yayi gurin jirgi, ya shiga jikinshi ba daɗi. Har jirginsu ya tashi ,zuwa abuja daga can zasu wucce.

****
Tunda Umma tayi min faɗa nake kwance, a gadonta jikina ba karfi. Karan wayata naji na mike na duba sakonshi, tsaki nayi nace.
"Ka kware a yaudara."
Kallon sakon nayi musaman kalmomin mijinki Masoyinki. Jifa nayi da wayar na koma na kwanta abuna.

Tuni barci yayi gaba dani sabida gajiyar dake jikina.
.......
Kwana goma da tafiyarshi Malam yakirani wai na bashi wayata, mika mishi nayi ban san mike faruwa ba, sai dai naga Umma ta fara azumi da yawan sallah dare.

Ga saukar alkur'anin da ake akai akai, oho su suka sani, dan i yanzun wani sabon lalaci nake ji. Kwanciyar kasa ya aureni, har da sadaki sakamakon zafin da jikinA yake akai akai, sai shan ruwa.

Abinda na lura an dakatar da koda jin radio ne a cikin gidanmu, sannan an hana yan uwana zuwa.
Nima kuma malam yace kar a barni na fita, abin haushi toh ina ake son naje.

....... Shiru Ilahirin familyn Mai nasara sukayi har da Fareeda da Balkisu, kuka Huda ya cika musu kunne. Cikin karfin hali Balkisu tace.
"Huda ya isa haka, Addu'ace mafita ba kuka ba."

Zaro Manyan idanunta tayi, cikin tashin hankali tace.
"Mommy kinsan halin da yake ciki kuwa? Kinsan hukuncin da zasu yanke mishi kuwa, wallahi a cikin mutane suke fille kan duk wanda aka kamashi ya shigar musu da kwaya, sharri akawa Daddyna ba halinshi bane."

Shiru duk sukayi cike da damuwa, Musaman Hajiyar shi. Mama kilishi tace.
"Allah sai ya saka mishi, duk wanda yayi mishi wannan abun."

Amin kowa yace, banda sulaiman.
****.Abinda ya faru kuwa, lokacin da suka bar naija daga abuja. Suka nufi china har sun isa a babbar birni Behjin anan garin screen aka samu hodar ibilis a jakarshi, an buɗe gefen jakar aka saka, ba'a ma rufe jakar ba.

Cikin abinda baifi dakika ba yan sanda suka tisa keyarshi zuwa ofishinsu. Nuna mishi abinda aka samu a jakarshi sukayi rantsuwa yayi musu bai dan da zancen ba, asalima shi ba bakon kasar bane.
Nan dai aka shiga musaya yana cewa bana shi bane suma suka kafe, Abokan kasuwancinsa suma suka zo aka tai gumurzu da jami'an tsaro.

Cikin awa guda har an watsa a kafar sadarwa,
*Ankama Attajirin ɗan kasuwan nan Yunus Marafa a filin jirgin Sama na kasar china sabida zargin da ake mishi na shigowa da hodar ibilis*

Take ko ina ya amsa, ya kuma yaɗu,
Gidajen talabijin na kasashen duniya suka haska, gidajen radio suma suka ɗauka.

Mr Huchug shi ya kira Aman ya fada mishi halin da ake ciki.

A kwana na biyu suka isa can har da Alhajinsu Yunus, da kuma Ammbassy na naija, abin fa ba karamin ɗaga hankalin mutane yayi ba, duk yanda akazo ayi abin cikin sauki da niman alfarma Kasar china taki amincewa sai dai ta basu wa'adin shigar da kara.
*****
Kusan wata guda kenan da faruwan al'amarin tun suna samun ganinshi yanzun an chanza mishi wani state, dole suka hakura.

Ni kuwa ina nan ina fama da

Please Login or Register in order to submit comment