Reading MATAR SO Complete PART 2 by MAI DAMBU Chapter 7 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

min hakuri da yarda da kaddara, umma kin koya min abubuwa umma miyasa baki koya min fitar da damuwata zuwa gareki ba, umma na haɗiye bakin ciki dayawa. Don Allah ki kwatar min yancina, karki juyawa al'amarina baya, ki kwatar min yancina."

"Maryam!!! Mi kike bukata daga yunus?"

D'ago kaina nayi ina kallon hajiya cikin zubda kwalla nace.
"Hajiya kiyi hakuri,,, zama dashine bana so."
"Miye ne na bada hakuri, ai hakkinki ne. Yunus ka sawwake mata."
Tace mishi.
A gigice ya ɗago kanshi yana girgizawa cikin tashin hankali yace.
"Hajiya don Allah, kuyi hakuri ina son matata, maryam kiyi hakuri na sauya halina karki rabu dani wallahi ina sonki sosai."
Girgiza kai nayi cikin kuka nace.
"Ai nima haka na rokeka da karka zubda min farin cikina, wayasani ko shiknn bazan kuma samun wani ba, ka zubda min shi. Kaje mun barka da Ubangij...."

"Maryam!!!"
Umma ta buga min tsawa.
Tsabar tashin hankali baka hangi komi a idanun Yunus.
Kuka na fashe mata dashi nace.
"Ni..."

Gaban Umma yazo ya dukar da kanshi cikim mugun yanayi yace.
"Kiyi hakuri, ku bani damar karshe."

"Abaka damar kashe musu y'a ƙo wacce irin dama kake bukata." Inji Alhaji.
Hannuna na ɗaura akaina ina kuka nace.
"Umma!!! Cewa yayi fa bani da daraja da kima, sabida an bashini a banza ko?"

Cikin ko in kula tace.
"Eh toh nima dai naga rashin kimarki da darajar, ina suke? Ina darajarki take? Ina kimarkin take?"
Rike bakina nayi tare da kallon Umma, wani irin ajiyar zuciya nake saukewa tsabar tashin hankali da ɗimauta.

Murmushi tayi sannan tace.
"Idan D'iya ta garice ko tari bazatayi ba, sai dai tajira hukuncin da zamu yanke mata. Ina guje miki aikin danasani ne kar wata rana ki zubda kwallar da tafi wanda kike zubdawa, ita rayuwa ba'a binta a guje. A nutse ake binta tafi daɗin ganuwa."
Mikewa nayi tsabar bakin ciki in dakeni an hanani kuka. Ko gani banayi. Nasa kai zan fita ji nayi an rukoni,
"Dawo nan Mamana."
Inji Malam zuɓewa nayi ina wani irin haki, hawayen ya kafe sai zuciya zalla da take aikinta.
Kwantar da kaina yayi akan kafarshi yana shafa kaina tare da tofa min addu'a. Sai da yaji numfashina ya daidaita sannan ya ɗago kanshi ya kalle Yunus cikin damuwa tace.
"Wallahi baka kyauta min ba, dan tunda nake ban taɓa jin an rabata faɗa da kowa ba, bata taɓa kawo min karan wani ba nasan halin duk Yarana amma nata halin dabane, hakurinta daban ne, adalci ɗaya zan iya maka nabaka dama ka gyara tsakaninku, idan haka bai samu ba toh zan iya baka hakuri ka sallam...."

"Malam..." Mama ta kirashi raunane.
Dakatar da ita yayi, cikin murmushin ya cigaba da cewa.
"Ban goyi bayan Maryam ba, sai da na fahimci har ynx hasina bata kaunarta, kiga yanda take numfashi, idan ita bata son Maryama ni ina sonta, kuma zan tsaya mata, ai duk sauran mazajen ba haka suke ba, haka mijin Rahilah yake? Yaron da ko gidan nan Rahilah tazo yana makale a kofar gidan nan, Mijin Rahimah nine nan nasanya shi yajanye ɗaure da yayiwa uwargidanshi, sabida kimar da muke dashi a idanunshi."

Murmushi Malam yayi sannan ya kalli Alhaji yace.
"Manyan mutane irin Yunus, basu san darajar mace ba, sabida cuɗanya da turawa. Zuciyarshi ta girmama alamarinsu, kayi hakuri Alhaji Y'ata Lu'ulu'u ce, kima take dashi da daraja, yaje ya shawo kanta idan ya samu damar haka zan iya duba al'amrin da idon basira amma bazan miki mishi maryam ba, dan tana da kima. Duk laifin da yayi bai basu kai wannan muni ba. Ku gafarceni banyi haka akan zubda cikin ba nayi ne sabida kalmar bata da kima da daraja, ka duba yanda take bana son na zama silar lalacewarta, nafi son ta koma rayuwarshi dan kanta badan mun tirsassata ba da fatan kun fahimceni."

"Wallahi babu komi, malam ai kun mana dattako, tunda baku dubi girman laifin zubda ciki ba, wanda nake jin abun har cikin zuciyata, Insha Allah zan sashi ya sawwake mata, itama tasamu ingantacciyyar rayuwa ina kara baku hakuri da abinda ya faru."

Gyara zama sulaiman yayi wanda yake zaune cike da damuwa tunda aka fara rikicin yake kallonmu,*Allah kaga zuciyata ɗaya nake son Maryam Allah nagode maka gwara akashe auren nina sameta.* Ya faɗa a ranshi kallon Alhajinsu yayi cikin zakuwa yace.
"Hmm Alhaji, idan bazaka damu ba kasashi ya sauwake mata da wuri, in yaso ni sai na shiga niman aurenta, kuma zan riketa da kima, zan ɗaga darajarta a idanun duniya, Wallahi zan riketa fiyye da ruk....."

Tauuu.Yunus ya tsinke shi da mari, bai damu ba yace.
"Wllahi sai ka saketa na aureta, kasan kana kishinta da sonta ka zubda mata da cikinta, kai d kanka kace min, idan ka tuna yanda take rokonka sai hankalinka ya tashi, kayi biriss da ita zuciyarka tana ingiz...."

"Sulaiman zan kasheka."
Ya riko wuyar Baban arif, mikewa iyayenmu maza sukayi ran hajiya ya ɓaci, aikuwa tana mikewa ta shiga kifawa daddy mari takowani fuska, sabida bacin rai, tace.
"Sake shi, kuma sai ka rabu da maryam, Insha Allah sulaiman sai ka auri maryam."

Kallon hajiyarshi yayi tare da sake baki hawaye na sauka daga cikin idanunshi ya sauke kanshi kasa yace.
"Hajiya ina raye zaki rabani da farin cikin rayuwata, itace mafarkina fa, duniyata rayuwata hajiya karki min sassarin da bazan iya kwacewa ba."
"Allah sai ka rabu da ita, azzalimi, mugu maha'inci. Ina tsoron ganinka cikin sakayyar Ubangiji dan hakkin rayuka bazasu barka."

........Dakyar aka shawo kan hajiya, faɗa Alhaji yayiwa sulaiman da kar ya sake abinda yayi.

Rufe taron akayi da addu'a sannan suka fita daga ɗakin aka barni dashi ina kife a kujeran da Malam ya tashi, da sauri yayo kaina zai taɓa ni nace.
"Koda wasa! Karka fara taɓa ni, dan zan maka wulakancin da baka taɓa tsamanin ba, mi yasa bazaka rabu dani ba? Mi yasa bazaka fita a rayuwata ba? Nifa bana sonka bana kaunarka, don Allah ka kyaleni."

Ina gama faɗar haka na mike nabarshi a gurin ko magana naki bashi damar yi min.

Zaman dirshan yayi ya kama kanshi da hannunsa duk biyu. Ina fita ɗakin Mama na wacce, na kwanta har lokacin jikina da numfashi na basu daidaita ba.
Dakyar yaja kafarshi ya fita a gidanmu duk sun tafi, koda ya shiga motarshi kifa kanshi yayi tare da sauke kwalla masu zafi. Mi ya aikeshi aikata abinda zai zame mashi tashin hankali.

Kamfaninsu ya wucce a gigice, yayi parking. Yana shiga gurinsu Ahmad ya zube musu akan kujera tare da dafe goshinsa yace.
"Ku taimaka min, zasu rabani da matata."
A tsorace suka ɗago kai tare da cewa "kamar Ya?"

Zama yayi ya shiga basu labarin abinda ya aikata da irin hukuncin da...

"Alhamdulillah, karshen tafiyarmu tazo yunus, nasan ban kaika samu da kuma buɗi ba, amma na hakura duk wani haɗakar dake tsakaninmu zan cire kaje ka zauna da Aneesah da ta baka shawaran sannan ita kuma maryam Allah yakarɓa mata sakinta a hannunka taje ta auri wani, ashe duk hiran da mukayi ka zauna kabugi cikina ne, lallai kayi kuskure ni ko sau dubu Rahilah zata haifa min yarana ina so, kuma bazan taɓa gajiya da ita ba, ada dan matsalata na aureta a yanzun kuma dan ta zame min wani yankin rayuwata ce, koda wasa bazanyi kuskure rabuwa da ita ba ko kuma naja dalilin da zasu rabani da ita ba, yayi maka kyau."

Inji Aman, yana gama faɗar haka ya tattara kayanshi yabar ofishinsu baki ɗaya.
Bakin ciki ya hana Ahmad magana, kayanshi ya haɗa ya bar Yunus shi ɗaya. A ofishin duniya tayi mishi zafi kowa ya juya mishi baya, ji yake kaman ya haɗiye ranshi ya huta amma ba halin haka..

Daga zaria kullum sai Alhaji ya buga mishi waya akan sakin, ga Hajiya ma da ta sakashi gaba. Mama kilishi ce take kulawa da lamarinshi idan akwai.
Idan yaje gurin aiki ba kowa a ofishinsu sai shi ɗaya, duk su Aman sun daina zuwa, sai dai yaje shashin ma'aikata yayita kallon yanda kowa ke farin ciki, da walwala, toh.mi yasa shi baida farin cikin mi yasa ya rusa nashi farin cikin. Yana cikin ɗimuwa,

****
Tsautsayi ya rufta da Aneesah, suna cikin aikinsu tare da abokiyar aikinta wacce take cikin damuwa, kallonta Aneesah tayi sannan tace.
"Rita mike damunki, naga kwanan nan kina shiga damuwa."
Juya kujeranta rita tayi cikin cunkushewar fuska, tace.
"Bari kawai Neesah, kinsan mahaifina sojane toh burinshi na auri soja irinshi, ba'a bukatar naja miki labarin. Yanzun dai sojan da ya nima min, zan aura shine muka ɗanyi making love da shi, tsautsayi yasa bamu saka goldenring ba, yanzun ina da cikin 2month na rasa yanda zanyi da cikin dan a coci ɗinsu Papa ba'ayarda da ka amshi cikin da za'ayishi daga waje ba yankan zama masifa da bala'i a cikin family da society."

Dariya Aneesah tayi sosai, sannan ta kalleta tace.
"Yanzun sabida Allah sabida ɗan karamin cikin da kika ɗauka shine kika jefa kanki cikin damuwa yo Allah na tuba ina zan saka damuwa a raina, ciki ko na wata nawa ne zan iya cire shi ba tare da nayi nazarin ya zanyi dashi ba, idan kin shirya muje na kaiki a cire miki."

Kamar rita ta fasa ihu dan murna, ana tashi a bankinsu suka suri jakarsu sai Rigasa.

Koda suka isa, dr nacan yana aikiwa wata sai ihu take sabida burge mata cikin da yake.
Suna zaune yafito sharfan da zuba hankalinshi tashe, ya nufi ofishinsa ya kira nurse aka fito da Yarinyar da aka burge mata ciki kamar matacciya, dake da uwarta suka zo nan ta riƙeta suka fita,
Yana zaune ya dae goshinsa kimanin sati huɗu knn tun da yake fama da ɗimauta da zaran yaje cire cikin da aka zo zubdawa sai ya saka injin ɗin yayita aiki fiyye da kima yana ganin jini na gudu a jikin macen.

Koda su Aneesah suka shiga ɗakin kallonta yayi cikin fara a yace.
"Madam barka da zuwa, ya aiki."
Yatsina fuska tayi tace.
"Ga aiki nan, amma ina ganin allura za'a mata, dan ni bana son wannan burge cikin allura yafi sauki."
"Ok ba damuwa bari nakira nurse tayi mata kinsan kuɗin alluran dai 25k ne."

Kuɗin ri ta ciro tabashi, kiran norse yayi a waya can sai gata. Faɗa mata abinda zatayi yayi taje tazo da alluran, tayiwa rita sannan sukayi godiya suka tafi.

Babban Rita babban sojane anan kaduna,Yaransa maza huɗu sai rita mace ɗaya tal jida ita yake kamar rai ɗaya.

Koda ta koma gida, ɗakinta ta shige, takwanta sabida yanda cikinta yake ciwo. Har dare bata fito ba dakanshi ya shiga ɗakin ya sameta kwance cikinta ya kumbura, ga jinin dake fita ta hancinta da bakinta.

Kiran yayan ritar yayi Nike, yana shigowa ya cincinɓeta sai waje aka fita da ita sai cikin mota, inda suka nufi asibiti.

Dakyar aka amshesu sai da mahaifinta ya fida id card ɗinsa na babban soja suka karɓeta.

Nan likitoti suka shiga aikinsu tun takwas har karfe biyun dare sannan suka fito da ita, aka kaita ɗakin yan ɓari.
Bin bayansu Babanta yayi har aka sauya mata gado, kuma zuwa lokacin jini bai daina zuba ba, bayan fitar wanda suka kawota tabuɗe idanunta cikin wahala tace.
"Am sorry Papa, naci amanar tarbiyan da kaimin, gashi nayo ciki a waje wai dan karka sani naje zubdawa ashe nice zan mutu."

"Wani likitane yayi miki wannan alluran?"
Dakyar ta iya buɗar bakinta tace.
"Kawata Anee."

Jinin ne ya fara zuwa ta baki tana amayar dashi, tun tanayi.a hankali yar yaci karfinta karshe dai Rai yayi halinsa.

A kiɗime Uban ya fasa ihu. Yana kiranta.

D'ago kanshi yayi idanunshi, yana kallon Yayanta, jikinshi na rawa tsimin sojar ta motsa. Nurse aka kira suka rufe gawarta, aka kai inda ake ajiye gawa.

Gida suka komo, uwarta da suka faɗa mata mutuwar Rita ihu take tana dukar kirjinta.
Washi gari Aneesah ta nufi bankinsu, tun kafin ta isa taga yanda sojoji suke cin uban ma'aikata ana nima Anee. Tana zuwa gurin suka taso mata a gadarance tafito makale da id card ɗinta.

...... Tana fitowa suka kalle id card ɗin, aikuwa cikin hargagi suka ce ga Anee ɗin. Wani basamuden cikinsu yace.
"Kece kawar Rita Uchenna."
Jikinta narawa tace.
"Eh"
"Ok muje kace ubanka."

Suka tasa keyarta cikin motarsu, sai barrack suna kaita aka turata wani ɗaki inda aka zuba kartin mata sojoji, rufe da fuskarsu aka buɗe mata hayaki maisa tari da kwalla bayan cin ubanta da suke da bulala. Ta ko ina suke zaneta sai da suka mata likis sannan Baban rita ya shigo ya kalli yanda ta koma zama yayi cikin zafin rai yace.
"Zaki faɗa min, inda akawa Yarinyata allura ta mutu."

A firgice ta mike zaune tare da dafe kirjinta ta fashe da kuka,tace.
"Ritaaaaa! Ce ta mutu, wayyo Allah na shiga uku wallahi bansan zata mutu ba, ce min tayi tana da ciki kuma bata son ta ɓata maka rai shine nace akwai inda nasani ana cire cikin, shiɓe tace na kaita wallahi Papa bansan zata mutu ba,da nasani bazan fara zama sanadin mutuwarta ba."

Mikewa yayi yace.
"Kufito da ita muje asibitin."
Kamar kayan wanki aka suka kwasota aka watsata a hilux, har rigasa suka isa, lokacin ana wani tashin hankali, dr yaje cire ciki wata budurwa ta mutu, shine abin ya zama rikici har da yan sanda. Ana cikin wannan sai ga su Aneesah.

Nuna musu dr tayi gyaɗa kai Baban rita yayi take sojoji suka sauka, har inda yake suka rufeshi da mugun duka, tare da nurse.

Dukanshi suke tun yana ihu har ya daina, haka suka masa mugun duka suka kuma jefashi cikin mota aka wucce da shi barrack.

.......
Duk wanda yaga yanda na koma sai ya sake kallona, dan gyarani mamah amarya take tare da min nasiha akan hakuri nayi kiba daidai misali.
Kullum sai daddy yazo nikuwa naki zuwa, idan suka ga van fita ba sai su fara min faɗa, ni kuwa sai naje kofar gida nayi zamana a ɗan barandar malam, dake gurin a kewaye yake gurin idan na zauna bana gurin sai naji tashin motarsa nake fitowa.

****
Zaune yake shida Huda ya zuba tagumi, cikin damuwa tace.
"Daddy kayi hakuri, Aunty Mom zata sauko. Dole tayi fushi amma kayi hakuri."

Murmushi yayi sannan ya mike yace.
"Ba damuwa."

Haka yabar makarantar zuwa masaukinshi,
Washi gari ya nufi kaduna inda ya samu muguwar labarin abinda ya sami Aneesah.

Nan aka tashiga da fita, iyayensu dashi kanshi, da farko sunbi baban rita cikin ruwan sanyi, ya nuna musu karfin kakinshi shine su kuma suka nuna mishi karfin kuɗi da sanaya, inda aka shiga aka fita karshe haka juya case ɗin kan Dr. Ita kuma akace shawara aka nima a gurinta ta bayar kuma bata da laifi.

Sai dai tunda ta dawo, itama ta shiga firgici sabida mafarkan da take, wani lokacin idanunta biyu zatana ganin jini, yana gudu ko kukan babys. Lokaci guda ta sambatu da ihu.

"Wayyo dasu nan zasu shige min jiki." sai aka ɗauka ko zafin bugun da tasha ne. Amna da suka sami labarin halin da Yunus yake ciki take suka mike da niman taimako,

Na yunus ya haɗu masa da zafin tashin hankali da yake ciki. Karshe sai da balkisu tayi magana da su hajiya aka maidashi zaria.
Dan kamar zai haukace, koda maganar yazo min taɓe bakina nayi nace.
"Allah ya kyauta nima haka suka hanani farin cikina can da yawarsu."

......... Dr kuwa asibitinshi ranar gwanati ta kwace, inda aka shiga ciki aka samu abin mamaki, wani gurin da yake tara, ɗiyoyin da yake cirewa a cikin mata, yana bawa wani katon karen tsafinshi yana cinsu. Ganin girman kare, yasa jami'an tsaro suka juya da baya, karshe suka cinnawa asibitin wuta.

Yana can ya fasa ihu, tare da zabura da karyayyan kafarshi. Yana yaga rigar jikinshi. A bangaren nurse kuwa ba'a cewa komi.
****
Addu'a malam sa'idu yayi ya mikawa Alhaji, aka saka mishi abaki dakyar yasha tare da cewa.
"Don Allah karku rabani da ita."

"Bazamu rabaka da ita ba, ta lafiyarka muke." Inji Malam.

Shiru sukayi Aman da yazo har zarian ya rikeshi tare da Sulaiman. Kwantae da shi sukayi,
Ya rike hannun Sulaiman.
Cikin raunaniyar murya yace.
"Karka rabani da ita don Allah, dan uwana."

"Bazan rabaka da maryam ba, tunda kana son abarka."

Yana gama faɗar haka ya fita a gidan, motarshi ya shiga tare da kifa kanshi. A jikin sitiyerin yana magana cikin damuwa. Yace.
"Wannan wata irin kaddara ce haka? Mi yasa suka min haka? Ni na dace da Maryama nina fara ganinta, amma suka ɗauketa suka m bawa wanda bai san kimarta ba mi yasa bazasu min adalci ba, su gane cewa nina dace da ita."

Haka yayita surutunshi a gurin.

****
Bayan yan kwanaki gane ganen da Yunus yake yanzun ya daina, sai dai damuwar da yake cikin ranshi a kaina, a ynz su Hajiya sun janye maganar saki sunce yayi kokarin mun daidaita.
A cikin kwanakin ya dawo kaduna, inda ya cigaba da zuwa gidanmu ni kuma ina surfa mishi rashin mutunci dan banajin zan iya hakuri da abinda yayi min, ina zaune a tsakar gida, yaron makotanmu ya shigo wai.
"Baban Huda yana sallama da maryam"

D'if na ɗauke wuta nayi banza da yaron na cigaba da chtt ɗina, sai da Umma ta leko cikin faɗa tace.
"Allah ya shiryeki ynx mutum yayi magana malam yace ana k'inki toh tashi mara kirki ki shigo dashi falon baki."
Tura bakina nayi cikin jin haushi nace.
"Wallahi nikam bazan koma gidanshi ba, gwara ya daina zuwa min. Mutum sai kace mayye."

Kwalllll naji an kwaɗa min abu a goshina aikuwa na fasa ihu wanda sai da Mama ta gintse addu'ar da take tafito ganina dafe da goshina yasata cewa.
"Kaiii Maryam, dalla kimana shiru sai kace an yanki da wuka. Dalla saka hijab kije ki shigo dashi."

Figar hijab ɗin nayi, cikin kuka na fita. Nafita har waje yana jingine da mota, babu sallama cikin masifa nace mishi.
"Yau zaka sallame ni dan nagaji da zama da aurenka, idan kuma jikina kake bukata toh wallahi sai dai ka mutu, idan yayi maka kashigo dan kasan Iyayena kima ne dasu, da sanin darajan bakonsu tunda sunsan darajar kansu."

............Chaiiiiiiiii
🌹🌹🍀
*MATAR SO*
🌷🌷🌻

*MAI_DAMBU*
*Wattpad:Mai_Dambu.*

Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai....

Sadaukarwa Ga Mai Nasara Team😂

_Wannan buk ɗin hakk'in masu shine idan kinsan baki saya ba karki karanta, mai fitarwa kuma ki duba girman Alkawarin da kika ɗauka na cewa bazaki fitar ba, tunda nace idan kinsan zaki saya ki fitar na Yafe ba sai kin saya ba_



*BOOK 2👈*
Page...8
Cikin gidan nanufa yana biye dani a baya har falon baki, dama banshi gaba na koma cikin gidan na zauna abuna, fitowa Umma tayi ta ganni a zaune ranta ya kara ɓaci, ciki tashige ta ɗauko wyar caja sai ji nayi ta tsulla min da gudu na mike har ina faɗuwa bata fasa bina ba, har kofar falon bakin ihu nake ina kuka,, dakyar na samu na shige falon ashe shi ya buɗe kofar da niyyar kwatata.

Na faɗa jikinshi ina kuka, mai da kofar yayi ya rufe kuka nake sosai ina jikinshi sam na manta da rigimarmu, shafa inda bulalar suka kwanta a jikina yayi, cikin matsanacin kewata.
Zaunar dani yayi a kujeran yana kallon kalabar kaina, wanda suka zubo har kirjina dan na wancakalar da ɗan kwalin garin gudu.

Kuka nake sosai ina mamakin mi yasa umma take tsanata akan yunus.
Zaman da yayi kusadani yasashi jin bazai iya jure har na dawo gareshi ba, sai jin ya cusa hannunshi a cikin rigana.

A firgice na dawo hankalina, tare da niman kwace kaina amma ina, ya min mugun riko wanda bazan iya kwatar kaina ba da hannu ɗaya, ɗayar hannun kuma tana cikin rigana yana shagalinshi da ita.

Kuka na saka tare da tureshi nace.
"Kyaleni ko natara maka mutane."
Murmushi yayi sannan yace.
"Nima zanso haka, kinga zasu fahimci matata na biyo."



Please Login or Register in order to submit comment