Reading AUREN BAZATA BY ZAINAB YAKASAI SHUKRA Chapter 8 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ki fada min wani abun amma banda wanda bazan samu a nn ba "


" To naji na canja Dan - Malele zanci "


" Safeer kamar zeyi kuka yake ji, Tabarar Shukrah ta soma damunshi, "ynx fisabilillahi Shukrah a ina zan samu wani Dan -Malele a nn"


"Toni shi zanci "


" Shiru yayi mata be kara cewa komai ba ya janyo plate din ya fara cin abincin sa "


" Shukrah ganin ya kyaleta ya sata fasa masa kuka sosai har tana bubbuga kirjinsa, Rike hannayenta yayi da nasa guda daya yana cigaba da cin abincin sa har anan bece mata komai "

" Shiru tayi ta kara lafewa a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya har bacci ya dauketa "


" Sai da ta gama cin abincin sannan ya kwantar da Shukrah a kan gado sannan ya dauki plate din yakai kitchen ya dawo ya kwanta a kusa da Shukrah bayan ya musu addu 'a, Da tunanin rigimar Shukra bacci ya dauke shi "




" Cikin dare yunwa ta damu Shukrah ta mike ta fara bubbuga Pillow' n safeer, Bude idonsa yayi ya sauke su kan Shukrah da tayi kalar tausayi tana kallonsa "

" Ya akayi? Ya tambayeta da muryan bacci "

" yunwa nakeji ta fada tana jan hannunsa "


" Mikewa yayi ya fita, kitchen ya je ya hada mata Tea sannan ya dawo ya samu ta shiga Toilet "


" Tana fitowa ta nufi inda yake da sauri ta karfi cup din hannunsa bata damu da zafin da tea din yake da ba ta kafa kai ta fara sha, Bata ajiye ba sai da ta shanye tsat, Ta zauna bakin gado ta rufe idonta tana maida numfashi, Wani tausayin ta yaji yana shigarsa sosai "


" wani zafi Shukrah taji tana ji sai gumi take, Ganin da yayi tana gumi ne yasashi shiga toilet ya hada mata ruwan wanka, Ya dawo ya daga ta ya cire mata rigar jikanta ya dauketa cak sai toilet, Da kansa yayi mata wanka sannan ya dauko ta ya dawo da Ita ya kwantar kan gado shima ya kwanta sai bacci "



" Sai da Daddy yayi 1week a San Francisco, sosai yayi wa baby siyayya shima sannan Y soma shirin komawa Nigeria, Shukrah yar Rigima wae sai ta bishi,jin safeer be ce mata komai ba yasata yin shiru da maganar "



" Ranar da Daddy ze koma dukansu ne suka rakashi Airport sai da su kaga tashin su sannan suka koma gida suma "



" Yau ake taro bude Company 'n Ahmad, Sosai manyan mutane suka halarci taron kasan cewar Ahmad shahararre kuma fitacce a San Francisco state, Bayan gaishe gaishe, ciye ciye Ahmad ya gabatar da Safeer a matsayin Manager' nsa, sosai abun ya bawa Safeer mamaki don be taba tunani ba kuma koda wasa Ahmad be fada masa ba, "


" Se bayan da aka kammala taron ne Safeer ya samu kebewa da Ahmad inda yayi masa godiyar wannan alherin da yayi masa "


" Nan Ahmad ya nuna masa ba komai ae duk daya ne, Saf
[4/22, 11:55 AM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻





WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA





Dedicated to Miemie bie 😘




2⃣8⃣



"Safeer ya kira Mamah ya fada mata irin Alherin da Ahmad ya masa, Nan Mamah ta bukaci Safeer ya hada ta da Ahmad din, Ya bashi wayar kuwa inda Mamah tayi masa godiya sosai sannan tayi masa Addu 'a, Sosai Ahmad din yaji dadin yadda Mamah tayi masa "


" Yau saura kwana Biyar su Shukrah su koma Nigeria, Sosai Ahmad da Azeeza suke musu tsaraba wanda yawanci kayan Babe ne, Azeeza ce ma tayi wa Aysher da Miemie tsaraba, inda Ahmad yayi wa Mamah da Ammii tsaraba shi kuma "


" Ana gobe zasu koma cikin gidan ba wanda yayi bacci suna tunanin rabuwa (sabo turken wawa), Jirgin bakwai da rabi zasu bi hakan yasa koda su safeer suka dawo daga mosque wanka ya shiga bayan ya fito ne itama Shukrah tayi "


" 6:40am dukansu suka fito suka shiga mota Sai Airport, Cikin mota Shukra da Azeeza sai kuka suke sun rungume junansu, Suma su Safeer kawae dauriya suke irinta mazaje amma suna jin ba dadi a ransu wannan ne dalilin da yasa basu hana su kukan ba ma "


" 7:30 aka fara kiran sunansu, safeer da kyar ya janye Shukra a jikin Azeeza bayan ya mata alkawari zasu sake dawo wa kafin ta haihu tunda shine manager 'n company' n Ahmad so akwai bukatar zuwansa San Francisco akai akai "



" Sai da Su kaga tashin su sannan Ahmad yaja Azeeza mota wadda har anan kukan take (Sabo da dadi rabuwa ba dadi) "




" A Nigeria Miemie da Aysher ne a kitchen suna ta girki kala kala, Dama Mamah ta nemi alfarmar Ammii kan tazo gidanta su tari su Shukrah gaba daya "


" Ammii bata watsa kasa a idon Mamah don tun 9:00am sukazo ita da Areef "



" To cikin jirgi Shukra sai kukanta take Safeer na Aikin lallashi, Da kyar ya samu tayi bacci sannan hankalinsa ya kwanta "




" 2:00pm Jirgin su yayi landing a Airport na Malam Aminu kano, Suna fita Safeer ya kira Haiydar ya fada masa sun karaso sannan suka koma gefe suna jiran zuwan Haiydar din "


" Bayan kamar minti ashirin sai ga Haiydar ya zo ya fito ya tayasu zuba kayan su a booth ya jasu sai Farm Centre "


" Miemie najin tsayawar mota ta fito da gudu dai dai sanda Shukrah ke fito da ga motar Haiydar, Miemie tayi tsalle ta Rungume shukra cike da murnar Ganinta, ita ma Shukra da murnar ta ta rungume miemie suka shige gidan gaba daya "

" Shukrah na ganin Ammii ta fada kanta ta rungume hade da sakar mata kukan shagwaba "


" Baki Ammii ta saki tana kallon Shukrah da mamaki
"Kukan na meye to Shukrah"

"Na dadi ne Mamah ta bawa Ammii Answer "


" Sai Anan Safeer da Haiydar Suka shigo gidan Nan fa aka shiga gaishe gaishe kowa fuskar sa dauke da fara 'a, Bayan an gama ne Aysher ta shiga kawo musu drinks "


" Ruwa kawai Safeer yasha suka tafi Mosque shida Haiydar, To itama Shukrah Sallah tayi sannan tazo tace Miemie ta bata abinci taci don ita cikin nn harda wani mugun ci yasa mata "


" Coconut rice da Egg sauce Miemie ta zuba mata sai mixed fruit ta ajiye mata a gaban ta, "


" Ae Shukrah na kai Spoon din baki taji zuciyar ta ba tashi ta yarda Spoon din da sauri tana kokarin mikewa, Amma kafin ta mike tuni ta fara Amai a inda take "



" A tare dukansu suka nufeta Aysher ta rike ta tana mata sannu jikinta sai rawa yake

"Aysher ki dauke wannan abincin banason ganinsa Shukra ta fada a wahale"


"Sai da Aysher ta dauke abincin takai kitchen sannan ta dawo ta fara gyara gurin "


" Mamah ko rike Shukrah tayi suka shiga daki ta taimaka mata ta dauraye bakinta ta hada mata ruwan wanka ta shiga sannan ta dawo palour inda Ammii "


" Sanda Safeer ya dawo gidan sai dube dube yake yanason ganin Shukrah Amma bai ganta, Kiran Miemie yayi da hannu ta dawo kusa dashi ta zauna "

" Shukrah fa? Ya tambaye ta kasa kasa "


" Nan miemie ta masa bayanin komai, aiko yayi saurin ture plate din gabansa ya shige dadin Mamah "


" Tana kwance a kasa da alama fitowarta a wanka knn idonta a rufe kamar me bacci ya kara sa kusa da ita ya zauna, Shafa fuskarta da yayi ne yasa ta bude idonta da sukayi ja alamar tana jin jiki sosai "


" Mikewa tayi ta shige jikinsa don ba abinda take bukata a halin yanzu sai shi, Tana so taji dumin jikinsa "

" Kara rungume ta yayi tsam kamar za a kwace masa ita yana shafa gashi kanta har zuwa bayanta, yana mata rada a kunnenta "



" Kara shigewa jikinsa tayi tana lumshe ido, ita kadai tasan abinda takeji a jikinta (Nace wannan ko sun manta a gidan Mamah suke) "


" kokarin kunce towel din jikinta yake aka bude kofa ya juyo da sauri yana kallon kofa, miemi ya gani a tsaye ya watsa mata harara "

" ME ya shigo dake cikin dakin nn? Ya tambayeta rai a bace "


" Ammii ce tace in kira kaci abinci "

" Dalla fita k bani guri ya fada yana nuna mata kofa "


" Fita tayi da sauri dan tana tsoron bacin ransa "


" Wayarsa ya ciro yana snapping fuskan Shukra, Kafin kuma ya shiga kiran Aysher "


" Da Sallama tashigo cikin dakin Amma ganin a yanda suke yasata saurin juyawa "


" Dariya yayi sannan ya ce ta daukowa Shukra kaya tasa "


" Fita tayi bata wani dade ba ta dawo kanta a kasa ta mika masa kayan ta fice da sauri"


"Da kansa ya saka wa Shukra kayan kafin ya soma lallabata kan tazo suci abinci amma tace bata san cin komai, da kyar ta yadda zata sha Tea "


" 4:15 pm Ammii tace itafa gida zata tafi, Safeer ne ya maidata gidan sannan ya dawo "


" Sai bayan Magrib Abbah ya dawo suka gaisa da Safeer ya kara masa murnar zama manager a San Francisco "


" Shukra ma tazo suka gaisa da Abbah inda yayi ta samata albarka yana addu ar Allah ya sauke ta lafiya ya bada nagari "



" Sai da sukayi Sallar isha sannan suka musu rakiya har mota suka tafi gidansu, Gidan tsaf yake don Aysher da Miemie sun zo jiya sun gyara"


"Shukrah ce ta fara wanka tana fitowa ta kwanta sai baccin gajiya, Safeer ma da ya fito daga wankan kwanciya kawae yayi ya musu addu a sai bacci............


SAFIYA TA GARI






SHUKRA YAR GATAN MIEMIE BIE 💞💞
[4/22, 7:37 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻





WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA


Dedicated to Miemie bie 💞


Wishes to show my appreciation to you Bilkisu galadanchi $Safiyya galadanchi for your luv, care and advice giving to me, I wish you Success where ever you may go more power to your elbows ❣

2⃣9⃣



"Washe gari Safeer beje ko ina ba a gida ya yini, Sai bayan la 'asar ne Haiydar yazo, Sosai suka yi hira, Shukrah ta fito daga daki da gani a bacci ta tashi, Tana ganin Haiydar ta saki ranta suka shiga gaisawa cikeda girma ma juna, Kallon Safeer tayi taga ita yake kallo "


" Ta bata rai tana harararsa' Zani gidan Ibtee tace tana turo baki "


" Maida kallon sa yayi kan wayarsa yace 'Bazaki ba' "


" Tafi minti biyu tsaye tana kallonsa kafin tasa kukan shagwaba harda bubbuga kafa a kasa kamar karamar yarinya "


" Ganin ko kallonta yaki yi yasa ta zuwa gabansa ta Fisge wayar hannunsa

"Ni wallahi sai ka kula ni"

"Dariya Dukansu kusa sa ba kamar Safeer da yakeyi tsakani da Allah harda Sakkowa daga kujera "


" Abin ya kara bata haushi dama yanzu abin haushi ba wuya yake mata ba, Ta kara fashe wa da kuka tana kallon Haiydar wanda yake kokarin tsayar da dariyar sa "

" Harda kai ko? Nagode "

" yi hakuri Shukra, Ki rabu dashi kinji, yi tafiyar ki gidan Ibtee ki tawo min da Amal in zaki dawo, Safeer ya fada kamar bashi ya gama mata dariya ba yanzu "


" Bazani ba ta fada tana hullar da wayarsa a kasa sannan ta wuce dakinta ta rufe kofa harda key ta fada kan gado tana cigaba da kukanta "


" A parlour Haiydar ya kalli Safeer "wae kae meye hk ne zaka sa yarinya a gaba kana mata dariya"


"Dariyar ya kuma yi kafin yace ae mu biyu mukayi mata dariyar naga "inji Safeer


" Amma ae taka tafi bata mata rai, wae meye ma abin dariya "


" Ni mamaki ta bani Duk fa yau bata kulani ba in nayi mata magana sai tamin Shiru ko kallo ban isheta ba, shine ta bani dariya yanzu ae tazo tana wani bata rai wae zata gidan Ibtee "


" Murmushi me kyau Haiydar yayi sannan yace me kayi mata taki kula ka?

"wallahi ban mata komai ba rigima ce kawai irin tata "


" To Allah ya kyauta Haiydar ya ce tana kallon wayarsa da ta shiga vibrating, Sanda Haiydar ya daga wayar shi kuma Safeer mikewa yayi ya shige Dakin Shukrah "


" Tana zaune tana charting a bakin gado ya karasa kusa da ita ya zauna sannan ya karbe wayar Hannunta "



" ME zaki ci, Ya tambaye ta yana kallonta "


" Murya can ciki tace bakomai "


" kamo hannayenta yai duka biyun yana kallon cikinta daya dan turo kadan dan ita shukra dama cikinta a shafe yake, "Haba Mana Shukrah Cute ya zaki ce ba zaki ci komai ba, ki daure ko tea kisha"


"Ni bazan sha ba ta fada wane zatayi kuka "


" Ni Gidan Ibtee zani tayi min Tuwo "

" To Alhamdulillahi tunda zaki ci tuwon tashi na rakaki gidan Ibtee, Ya fada yana nikam da ita, Hijab ya dauka a kan gado ya sa mata ya rike Hannunta suka fito parlour inda tayiwa Haiydar sallama don ba da wuri zata dawo ba "


" Har bakin gate din su Ibtee yakai Shukra yace ze jira ta ta kawo masa Amal, Tana shiga parlour taga Amal tana wasa ta dauketa takai masa sannan ta koma cikin gidan "


" sanda ta shiga gidan taga Ibtee tana leka bayan kujera, Shukra ta hade rai don batason yin dariya "


" Lafiya Ibtee, Meye a gurin shukra tace tana lekawa itama "

" Ke banga Amal ba kuma fa wallahi yanzu na shiga daki na dawo kuma ban ganta ba Ibtee tace hankali tashe "


" Shukrah ta gimtse dariyar ta ba tare da Ibtee ta gane ba tace to waye ya shigo gidan ya dauketa? dama baki rufe parlour ba? "


" Inafa na rufe, keni zo mu fita Dalla ta fada sanda tasa Hijab dinta "


" Ai kuwa bamuga ta zama ba Shukrah tace sannan tana hannun Ibtee suka fito "


" Fitowarsu tayi dai dai da fitowar Haiydar da Safeer, Amal na hannun safeer ya bata wayarsa tana wasa da ita "


" wata Nannauyar ajiyar zuciya Ibtee ta saki ta kalli Shukra, Shukrah ta tuntsire da Dariya harda rike ciki "


" Ibtee takai mata duka 'bakida kirki Shukrah dama kinsan tana gidanki baki fadamin ba kikasa na tashi hankalina"


"Har anan Shukrah dariya take taja hannun Ibtee ni zo muje kimin Tuwo shi nake so wallahi, "


Kin jawa kanki ae bazan yiba"


"Haba Ibtee Swthrt, matar abu turab, uwar gida sarautar mata daga ke ba kari, Maman Amal Beauty, dan Allah kimin tuwon kinji Shukrah ta fada sanda suka shigo parlourn "


" To naji zanyi shknn Ibtee tace tana karasawa kitchen, ita kuma Shukrah tayi zaman ta a parlour dan in ta shiga kitchen taji kamshin miyar baxata iya ciba "



" Sai ba adi salamu magrib sannan Shukrah ta koma cikin gidanta inda ta dauko Amal ta dawo wa da ibtee ita ta koma ta samu Safeer zaune a palour yana Aiki a system dinsa "

" Ya Safeer zo muci tuwo ta fada tana ajiye flask din hannunta a kusa dashi, Ta wuce kitchen dauko plate da spoons ta zuba musu, Ta mike ta bude fridge ta dauko musu lacasera ta ajiye tana kallon Safeer "


" Sai da ya kammala abinda yake sannan ya switching off system din sannan ya sauko suka soma cin abincin "



" Washe gari gurin 11:00 Safeer yace Shukra ta shirya yakai ta gidan Ammii daga nan su biya su gaida Hajiyar Haiydar, Shukra harda dan tsalle ta shige toilet don yin wanka "

" Safeer ya juya ze fita kenan ya hango wayar Shukra dan dressing mirror, Da sauri ya karasa ya dauka Kai tsaye contact dinta ya fara dubawa cikin sa 'a kuwa yaci karo da wata Number anyi saving as MY NUMBER, Da sauri ya dauko wayarsa ya dau Number yasa yayi dialing, Tana fara ringing yayi saurin Rejecting yayi mata Saving number sa as "HUSBY"

"Sannan yayi saving tata number as "WIFEY"


"Koda Shukrah ta fito da sauri ta shirya ta samu Ya Safeer a parlour suka kama hanyar gidan Ammii"


"sanda suka isa Safeer ne ya dauko wa Shukrah tsarabar su Ammii suka shiga a tare cikin sa a kuwa suka tarar da Daddy na gida "

" Safeer ya dade sosai yana hira da Daddy sannan Y musu sallama ya tafi "


" Misalin karfe hudu da rabi wayar Shukrah dake hannun Areef ta soma ringing, mika mata yayi da sauri
"Baki sake take kallon number ita dai tasan ba ita tayi saving number nn ba, Tana ta mamaki har kiran ya katse wani ya shigo, Sai anan ta dauka da Sallamar ta"
"Jin muryan Safeer yana Answer mata sallama yasata sauke ajiyar zuciya"


"ki fito mu tafi gidansu Haiydar"


"To kawai tace sannan ta shiga dakin Mamah tayi mata sallama ta fito ta samu Safeer a motar sa suka tafi Gidansu Haiydar "


" Sosai Shukrah ta samu karba ta musamman a gurin Hajiyar su Haiydar, Don Hajiyar Haiydar mace ce mai kirki da son mutane duk da kasan ce watar ta mai kudin gaske amma kudinta be sa mata girman kai ba "


" Sai da sukayi sallar isha sannan suka koma gidansu inda Hajiya ta cika Shukrah da tsaraba, sosai Shukrah ta shiga ran Hajiyar don har tana tambayar ta sanda zata sake zuwar Mata.........





SHUKRA YAR GATAN MIEMIE BIE 💞
[4/27, 1:53 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻




WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA





Dedicated to Miemie bie 😘






3⃣0⃣



Three Months later


"Shukra zaune a dakinta ta sa akwatuna a gaba tana duba wa zallar kayan Babe ne aciki, a zuciyarta tana mamakin irin wannan soyayya da iyayen ta, iyayen Safeer kai harma da Hajiyar Haiydar suke nuna wa babynta, takai one hour tana aikin kayan kafin ta ture kayan ta jingina a jikin gado tana shafa cikin ta dan wata shida wanda ya yayi girma sosai sai kace dan wata tara, Mamaki da tsoron girman cikin ya hana mata nutsuwa a yan kwanakin nan ga nauyi kamar me "



" Tana cikin haka Safeer ya shigo cikin dakin yana Waya da alama da friend dinsa suke wayar, Sai da ya gama ya juyo yana karawa Shukrah kallo wadda gaba daya ma hankakinta baya wajensa, janyota yayi jikinsa yana shafa kanta "

" Shukrah meye matsalar??

"Tsoro nakeji ya Safeer ta bashi Answer kamar zatayi kuka "

" Dago kanta yayi yana mata kallon mamaki kafin yace tsoron me?


"Wannan cikin mana yayi girma da yawa kamar wadda zata haifi guda goma "


" To Shukrah ae lafiya ce, kuma ma ko guda goma kika haifa ai ba matsala bane indai Allah ya baki lafiya ko "



" Kuka kawae tasaka masa wae ita BAZATA haifi guda goma ba "



" Safeer dae yana mamakin Shukrah yanzu ba dama ayi magana sai tasa kuka, ayi mata wasa ta dauka da zafi, lallashinta yashiga yi yana cewa insha Allah daya zata haifa mai kama dashi tunda batason goma "


" o o ni me kama dani zan haifa tace tana turo baki "


" To naji Allah ya sauke ki lafiya shike nan "


" A a "

" Sai me kuma "

" Sai da ta dauke kai kafin tace ni gidan Ammii zaka kaini "


" Kema dae kya ji kunya Shukrah jiya fa har 10:00pm kina gidan Ammii kuma yau ma wae sa rai kike na kaiki "


" Kukan ta ta cigaba wannan karon har tana hadawa da kaimai duka "


" Ganin Abin Shukrah ba me kare bane yasa Safeer saurin ture ta a jikinsa ya mike ya fice, ita ko Kukan ta take tsakani da Allah a haka dae bacci ya kwashe ta a gurin "



" Sai bayan sallah magrib sannan Safeer ya dawo gidan Shukra na zaune a parlour tana cin gireba, suna hada ido ta daure rai ta maida kallon ta jikin TV"


"Yammata na, yanzu kina kallona na shigo cikin gidanki amma ba sannu da zuwa ba komai "


" Ban iya ba tace ba tare da ta kalleshi ba "

" Baki iya gaisuwa ba Shukrah ya fada sanda ya karaso kusa da ita yana binta da kallon mamaki "

" To kaima baka iya dubiya ba ta fada tana murguda masa baki "


" iye Shukrah ya Safeer din kike yiwa haka? Yayi maganar irin abin ya bashi mamakin nan "


" komai ba tace ba sai ma juya masa baya datayi tana cin gireba hankali kwance "


" Ya dade a tsaye yana mata kallon mamaki kafin ya girgiza kansa ya wuce dakinsa a ransa yana cewa

"Shukrah dae ta zama a lallaba"



"Shukrah na nan zaune har 9:00tayi, wayarta ce tayi ringing tayi saurin dauka kamar me jira DR WAHEEDA ta gani jikin screen din sai da tayi murmushi kafin tayi picking, tayi mata Sallama ta answer "


" Bayan yan gaishe gaishe ne, waheeda tace Shukrah bakida kirki wallahi ace kin samu cikin har 6 Months amma baki fada min ba "


" Shukrah wadda kunya ta rufe tayi murmushi batada abinda za tace shiyasa tayi shiru "


" Kinyi Shiru Shukrah ko bakya jina ne? Waheeda ta tambaya "

" Da kyar Shukrah ta ce mata kiyi hakuri ae nayi tunanin ya fada miki "


" Inafa ya fada min, Ae zan gamu dashi ne kedai Allah ya sauke ki lafiya, Badai wata matsalar ko?


"Ba matsala wlh "


" Daga haka dae Shukrah yi sallama Shukrah dae har anan bata dena jin kunya ba, Don sosai take jin nauyin DR Waheeda hakan nema ya hanata sanar mata tun farko "






" To kamar yadda Safeer Yayi wa Shukrah alkawarin zasu sake zuwa San Francisco haka kuwa akayi don yau Safeer Bayan ya tashi daga office Golden season travelling agency ya nufa kai tsaye yayi musu visa shida Shukrah da Miemie "



" Sanda ya shigo gida tarar wa yayi Shukrah tayi baki wasu yan uwansu sune na katsina suka zo, Tsayawa yayi suka gaisa sannan ya wuce, Shukrah kamar bazata tashi ba tayi zamanta ta cigaba da hirar ta sai da wata Auntyn ta Aunty Nabeehart ta harare ta
" Kin tashi kin bi mijin ki ko sai na kwada miki mari tukun na"



"Turo baki Shukrah tayi ta tashi tana cewa Aunty fa banida lpy sannan ta shige dakin Safeer "


" Sanda ta shiga ta samu har ya shige wanka saboda haka sai kawae ta fito mai da kaya tayi kwanciyar ta kana game a wayar sa "


" Sanda ya fito gaban dressing mirror ya nufa ya dauko cream ya dawo kusada Shukrah ya zauna, Tana ganin haka tayi saurin minimizing game din ta ajiye wayar ta mike, sai da ta karbi cream din hannunsa sannan ta kalleshi ta fara magana kasa kasa

"Ya Safeer ka dawo lafiya ya office?


" Alhamdulillahi, Yau na zo miki da albishir "

" Cikeda zumudi tace ya Safeer menene dan Allah "?


" Inna fada miki me zaki bani as a gift "


" Duk me kake so zan baka wallahi "

" Are you sure! Yace in between laughter dan shi kadae yasan tanadin da yayi mata "


" Absolutely sure inji Shukra don bata me yayi ba,

"To shknn zan fada miki koma menene amma ba ynx ba sai dare "

" me yasa sai dare Shukrah ta tambaya cikeda rashin fahimta

"banason tambaya tayi yawa tunda nace sai dare ae saiki hakura ko"
"Shukra bata sake cewa komai ba har dae ta gama shafa masa cream din ta koma wajen bak'in ta "


" Da daddare bayan Safeer ya fito daga masallaci be wuce ko inava sai gidan Mamah inda yayi mata bayanin tafiyar tasu, ya kuma fada mata tare da Miemie zasu tafi "



" Miemie da tunda ya shigo cikin gidan ta rufe idonta kamar me bacci wae don karta gaishesa ta fasa ihu hade da duro wa daga kan kujera "

" Ya Safeer dan Allah dani zaka tafi San Francisco wayyo dadi, Wayaga Miemie a cikin turawa wai! A gaskiya ka gama min komai wallahi God bless your unborn Babe ta karasa harda yar rawar ta "


" Baki

Please Login or Register in order to submit comment