Reading AUREN BAZATA BY ZAINAB YAKASAI SHUKRA Chapter 11 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tamasa gwalo tace cikeda shagwaba Mamah yaushe zaki haifar mana twins muma adena min gori "


" dariya sukayi dukansu sannan safeer ya fice yasa Aysher Da Shukrah su kaiwa Daddy twins"




WASHE GARI


Tun asuba mutane suka fara cika gidan duk da cewa a tourist camp za ayi taron sunan amma kafin7:00 gida ba matsaka tsinke, ba ayi girki a gida ba kasancewar an riga anyi order a can tourist camp din snacks kuma anyi order a me. Biggs, Drink ko Wata Aminiyar Mamah ce Hajiya Maryam Anas ce tadau nauyi "


°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

12:00pm na isa tourist camp gurin ya cika sosai da yan uwa da abokan arziki, Bayan bude taro da Addu ' a da wata babbar Malama *safiyya* *yakasai* da tayi ne kuma aka vukaci D. J Yasa sauti nan fa yan *SHUKRAH NOVELS suka zage sai rawa suke ba kamar Safiyya* *Galadanchi* da *Zee* *zee*, sai da komai ya lafa sannan aka fara rabon Mutane sai karba suke, can nagano wasu mutane sun koma gefe sunata dura abinci da lemo a jaka kara matsawa nayi don ganin ko suwaye, wazan gani inba, *MEELA* *SOFTIE* *EESHATULLAH* *MAMAH* *SKY* *FEUXER* *MARYAM*& *NURIYYA* ba, suna ganina suka fara raba ido, Haka dae taro ya watse mutane sae sawa twins albarka suke "




" Sai wajen 11:00pm safeer ya samu kubewa da Shukrah, fitowarta a wanka knn tana shiryawa yakarasa ya rungume ta taba ya a tare suka sauke ajiyar zuciya, yace mata a cikin kunnen ta

"Bazan taba gajiya da yimiki godiya ba Shukrah kinmin komai a rayuwa ta, Allah ya miki Albarka kinji, yanzu ki fadamin duk me kike so insha Allah zan miki "


" Shukrah tai Saurin juyowa tana kallon shi sannan tace da gaske ya Safeer "


" Yace Da gaske "



Tace Aiki nake so na fara, yace wannan shine yafi komai sauki, akwai wata kawar Mamah tare sukayi Uni Maid insha Allah zan mata magana itace me *MARYAM* *CLINIC* Din can... .
[5/15, 7:48 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻 *AUREN BAZATA*👮🏻




*WRITTEN BY*
*ZAINAB YAKASAI*
*SHUKRAH*






Dedicated to *MIEMIEBEE*





3⃣8⃣



" *SHUKRAH* tace karka cemin *AUNTY MARYAM ANAS*, *Safeer* ya kalleta cikeda mamaki sannan yace karki ce kinsan ta?

" *SHUKRAH* ta mishi hararar wasa sannan tace lallai yaza ayi ace bansan taba tare fa sukayi secondry skul da *Ammii* fa kuma tana zuwa gida sosai, *Safeer* yayi murmushi mai kyau sannan yace Masha Allah ynx inna fita zanyi wa *Mamah* magana insha Allah komai zaizo da sauki don *Mamah* tana bani labarin saukin kan *Mummy Maryam Anas* tun suna uni maid haka take duk da kasancewar ta over roller amma bata da girma kai, *SHUKRAH* ma murmushi tayi sannan tace Allah sarki Allah dae ya shige mata gaba, kuma nagode sosai da Amincewar dakayi *PAPA'N TWINS*, matsowa *Safeer*yayi ya rungume ta sosai sannan yace kinfi karfin komai a gurina wallahi *SHUKRAH* Allah dae yayi miki Albarka ya kuma kara miki lafiya ya kare ki daga sharrin masu sharri, sosai *SHUKRAH*taji dadin addu 'ar tasa saboda haka ta manna bakinta akan nashi ta soma kissing dinsa sundau lokaci sosai a hk kafin *LABEEB*ya fasa kuka sukayi Saurin janye wa haka kuma suka nufeshi da sauri,, *SHUKRAH* C tayi nasarar daukan sa Tasan yunwa yakeji don duk basu zo hannunta ba, shiyasa tayi Saurin yaye rigarta tasoma feeding nashi"

"sanda *Safeer* ya fita a dakin gurin *Mamah* yaje yamata bayani yadda sukayi da *SHUKRAH* kuma hakan ya mata dadi at last dae zata taimaki mutane da yawa kuma ta mishi alkawarin zatayi, *Mummy Maryam Anas* maganar a yau ba sai gobe ba, nan *Safeer* yashiga godiya sannan sukayi sallama da *Mamah* da kanshi ya kai Hajiyar *Haiydar* gida sannan sukaje ya samu *Haiydar a gida saboda hk suka zauna sunata hira Safeer* sai
Tsokanar *Haiydar* yake wae za ayi masa *AUREN BAZATA* Sai da *Haiydar* ya bata ransa sannan *Safeer* ya kyaleshi sanda ya masa sallama ma ko answer wa ma beyi ba haka *Safeer* ya tafi ya nayiwa *Haiydar* dariyar mugunta"


°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°


*Hajiyar Haiydar* T samu yayar ta *Hajiya Safiya* kan tana son hada *Haiydar* & *Zafeera* Aure kuma Alhamdulillahi maganar ta tasamu karbuwa a wajen *Hajiya safiya Da Alhaji mai kano* mahaifin *Zafeera* kenan Don Alhajin cewa yayi nanda wata biyu za ayi bikin acewarsa ae su suka haifi yaran kuma sunada hakki akan su haka kuma suna da ikon zaba musu abinda yayi dai~dai da rayuwar su, saboda hk ba bukatar tambayar *Zafeera* ko bata sonsa"



" *ZAFEERA* Itace 'ya mace guda daya tilo a gurin *Hajiya Safiya* shiyasa ta dauki son duniya ta dora mata"

"hajiya kawae dauriya take don sam bata son abinda zai taba *gudaliyar ta*,kuma tana tunanin yadda zasu kwashe da *Zafeera* DUK da dae tanada saukin kai kuma tasan bazata ce A a ba, Amma tana ganin dae kamar an shiga hakkin ta, da kyar ta iya bude baki tace Allah dae ya sa komai yazo da sauki "


" Ameen Hajiyar Haiydar tace "

" Shiko *Alhaji Mai kano* cewa su kashe kansu in anyi AUREN, daga nan dae ya mike ya fice, To itama Hajiyar Haiydar sallama tayi wa Hajiyar Zafeera ta fice "



" Da daddare har Zafeera ta kwanta Hajiya ta shigo ta kwashe duk yadda sukayi da Hajiyar Haiydar ta fada mata sannan tace
"kuma Baffanki yasa bikin Nan da wata biyu,"

"Zuciyar Zafeera ta bada wani *Dum Dum Dum* tanason Hajiyar ta, kuma bata jin zata iya watsa kasa a idanun soyayyar da Hajiyar take mata uwa uba kuma tarbiyyar da Hajiyar tamata, Saboda hk tace *TO* Asanyaye "

" Sosai Hajiya taji tausayin 'yar tata amma saboda batason maganar tayi nisa har tasa *Zafeera* kuka yasata mikewa tace kiyi Addu' a *Angel* sai da safe "

" nanma *To*kawai tace mata sannan ta kwanta"


"Duk wannan Abun da ake Haiydar be Sani ba don Hajiyar bata kuma yimasa maganar ba, cikin sati biyu magana ta kankama don har ta isa katsina dangin su Haiydar din kenan, Hajiyar Haiydar da Hajiyar zafeera sun shirya staf zasuje Dubai don hado lefen *Zafeera*, koda *Haiydar* ya tamvayeta inda zata cewa tayi ina ruwansa "

" Sati daya kawae su Hajiya sukayi suka hado kaya masu yawan gaske uwa uba kuma ga kyau da tsada, Sai bayan da suka dawo ne Hajiyar tace wae yazo yaga lefen shi, ko kallon kayan beyiba yayi fice war sa don wani mugun takaichi ne ya durar mishi"


°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°


"yau kwanan su *LABEEB DA LABEEBA* 40 A duniya amma *Ammii* bata taba sasu a idanun ta ba sai dae ko a picture shidin ma sau biyu ne, Ranar da *AREEF* Yaje ganin su yayi snapping dinsu ya nuna mata sanda ya dawo sai kuma sanda *SHUKRAH* tayi mata sending a WhatsApp "

" Wannan dalilin ne yasa *Mamah Shukrah Aysher da Miemie* suka shirya mata ziyarar *BAZATA*.. . .





*SHUKRAH YAR GATAN MIEMIE BIE*💞
[5/16, 1:15 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻 *AUREN BAZATA*👮🏻
( *An unexpected marriage*)


*WRITTEN BY*
*ZAINAB YAKASAI*
*SHUKRAH*



*DEDICATED TO MIEMIE BIE*💞



3⃣9⃣



" *AMMII* Na daga cikin daki ta jiyo sallamar su, ta fito da sauri ta tare shu da fara 'arta
"Sannunku da zuwa, wannan irin zuwa na bazata haka, da kun Sani kun kira ni kun cemin zakuzo ae"


" *Mamah* ta dan harare ta sannan tace to in an kira picking kike, ae ina sane na shirya wannan zuwan bazatan sai da na kira *AREEF* Ma na tambaye shi ko kina nn ya tabbatar min kina nn din sannan muka tawo "


" Murmushi kawae *AMMII* Tayi ta wuce fridge ta kawo musu drinks, *Aysher* ta durkusa kusa da *Mamah* tana gaida *AMMII*, da fara a ta Answer sannan *MIEMIE* MA ta durkusa ta gaida ta, *SHUKRAH*ma ta gaida ta, ta Answer ba tare da ta kalle taba "

*MAMAH* Ta dawo da kallon ta gun *AMMII* Sannan tace, ae kawo muki twins mukayi tunda kinki zuwa ki gansu, Murmushi *AMMII*Tayi sannan tace ba haka bane ba, abubuwa ne sukayi min yawa, *Mamah* tace to aini gashi nan nazo da kai na"

" *SHUKRAH* ta dan kallo *AMMII* Aiko suka hada ido, Ammii tayi saurin dauke idonta, Shukrah tayi Murmushi sannan ta mike ta do rawa Mata *LABEEB* Kan cinyarta, *AMMII* Tayi saurin sa hannu ta ture shi saura kadan ya fadi Shukrah ta tare shi tana Murmushi, Mamah tace yanzu dan Allah wae sai ki ture shi haba *Ammii* gaskiya ki rage wannan kawaichin naki yayi yawa wlh ynx zamani ya canja fa, Dariya *Ammii* tayi tace to ae shi kunya, kara da kawaichi a jinin fulani yake, Amma kamar yadda kika ce na rage zan danyi kokari na rage din, yawwa ae haka akeso *Mamah* tace tana do rawa *Ammii* *Labeeba* akan cinyarta, cikeda kunya *Ammii'n* ta daga ta tana Murmushi sannan tace Allah ya raya su yasa masu jin k'ai ne"


"Hada baki sukayi dukansu wajen cewa Ameen"

"Yinin ranar duk sunyi shine a gidan *Ammii* amma *Mamah* ta kula bawata magana data shiga tsakaninsu da *SHUKRAH* a zuciyarta tana mamakin hali irin na *Ammii* kusan wata biyar fa bataga Shukrah 'n ba tun tafiyar su San Francisco gashi ynx tazo amma sai share ta take, Tana wannan tunanin ne taga *Ammii* ta mike ta shige Bed room, *Mamah*ta Dawo da kallon ta gun *SHUKRAH* tace
*SHUKRAH* tashi kibi *Ammii' nki* kuyi magana kinji "

Kamar dama jira take tayi saurin mikewa ta shige dakin da sauri, juyawa Mamah tayi azuciyarta tana dada mamakin *Ammii*, Sanda *Shukrah* ta shiga dakin lokacin ita kuma Ammi zata fito, Shukrah tayi saurin rike hannunta tace *AMMA NA* ynx kin dena sona ko? Ta fadi haka ne sanda hawaye ke fitowa a idanunta "


" *Ammii* cikeda tausayin 'yar tata tace ban dena sonki ba *SHUKRAH* ya jikin ki?


"jiki Alhamdulillahi, twins suna fushi dake tunda kinki zuwa ganin su, Dariya kawae *Ammii* tayi sannan tace ae ynx gashi nan kun kawo su ko?

Eh mun kawo su kam, sun danyi hirar yaushe gamo sannan suka fito, sai bayan sallah 'r magrib sannan suka tafi bayan *Ammii* ta cika su da tsaraba "


" washe gari da sassafe *Safeer* ya shigo cikin gidan *Mamah* ya tarar a parlour tana Karanta *Hisnul muslim* ya durkusa kusa da ita yana gaida ta, Bayan sun gama gaisawa kuma shiru ne ya biyo baya don *Mamah* cigaba tayi da karatun ta shi kuma *safeer* zama yayi yana dan Satar kallon ta, lura da hakan da *Mamah* tayi ne yasa ta ajiye littafin hannunta ta ta dawo da kallon ta gurinsa "

" Ya akayi ne *Safeer*?

"kara kasa da kansa yayi kafin yace' *Mamah* dama zuwa nayi mu tafi da *SHUKRAH* & *TWINS* Tunda sunyi Arba ' in dinko?

"Mamah ta rike ha'ba tana masa kallon mamaki sannan tace to fitsararre mara kunya ni ae nafika sanin sunyi Arba,in din, to barin fada maka baxata koma ba sai nan da two weeks don bamu gama gyaran da muke ba"

*Safeer*ya bata rai kamar zeyi kuka yace wae wannan wane irin gyara ne dan Allah, nidae kawae a barshi haka wannan ma wanda akayi mata ya isa "

" Dalla can rufe min baki mara kunya kawae sai kace bakai ake yiwa gyaran ba, ta nuna masa kofa tashi ka fita ka bani guri, haka *Safeer*din ya fita yana mita
"Wannan wace irin rayuwa ce, dan anga Mutum me hakurine sai a dinga masa yadda ake so, an cemin 40 days zasuyi na hakura amma ynx an canja magana wae sai nn da two weeks, yaja tsaki sanda ya shige motar sa ya bar gidan"


*SHUKRAH* *SHUKRAH* *SHUKRAH*, Na am *Mamah* Shukrah ta Answer sanda take fitowa daga daki, wuce kije kitchen ki dauko babbar tukunya a dora ruwan wanka, to kawae Shukrah tace sannan ta dauko ta ajiye a gaban Mamah"


"Sassaken bagaruwa Mamah ta zuba sannan ta matse lemon tsami akai tace Aysher tashi kije ki ta fasa, in yayi saiki jiya ki kira Shukrah ta shiga ciki"



"Sanda Shukrah ta fito a wanka Mamah tasa Aysher ta dauko kaskon turaren wuta da bucket na karfe, Mamah tasa Kaskon cikin bucket din tazuba angurya(wanda ake samu a jikin audiga) tazuba bawon (kwanson) citta Shukrah ta zauna akai, Bayan an gama wannan Mamah ta kara zuba wani turare da wata kawar ta ta kawo mata daga Senegal "

" T haka dae rayuwa ta cigaba da tafiya kuma yau Shukrah tayi sati biyun da Mamah ta kara mata, Mamah tasan halin Safeer sarai shiyasa ma bata kirasa ta tuna masa ba, Amma ga mamakin ta har bayan magrib Bai shigoba, abin ya damu Shukrah sosai shiyasa ta faki idon Mamah ta shige dakin ta fara kiran wayarsa, bugu biyu tayi yayi picking "

" Hello *Papan Twins*


"Yap *Mamin Twins* ya kuke?

"Lafiya kalau muke, kai muketa jira dae"

"Murmushi Safeer yayi wanda har Shukrah na iya jiyo sautinsa yace ke bakin biyewa Mamah ba kin share ni, nifa da har na fara tunanin dama akwai wata yarinya teemerh luv tana masifar sona to da har nayi niyyar zuwa gurin Dad nata in nemi AUREN ta nanda two weeks in za ayi bikin Haiydar a hada namu kawai "


" Shukrah ta saki kukan shagwaba tana bubbuga kafa Ni wallahi bazan yarda ba, Ni wallahi kawai kazo mu tafi ko in tawo da kai na "


" Kukan da Shukrah take ne yasa Mamah ta shigo dakin, jin abinda Shukran ke cewa yasa Mamah ta fahimci da wanda suke wayar, saboda haka ta ta koma ta ta samu Miemie aparlour

"Miemie je ki kiramin Aysher tazo ku kai Shukrah gidanta, to Miemie tace sannan taje ta kira ta, Mamah da kanta tayi wa Shukrah bayanin Su Aysher zasu rakata, Bayan kamar minti goma sha biyar Shukrah ta shirya tsaf haka ta shirya twins, Aysher da Miemie suka tayata sa kaya a booth, Mamah dae tana tsaye sai da taga fitar su ta koma ciki... . .





*SHUKRAH YAR GATAN MIEMIE BIE*💞
[5/17, 4:49 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻 *AUREN BAZATA*👮🏻
( *An unexpected marriage*)




*WRITTEN BY*
*ZAINAB YAKASAI*
*SHUKRAH*



*DEDICATED TO MIEMIE BIE*😘





4⃣0⃣


"Cikin Mota *SHUKRAH* tayi wa *SAFEER* Text tace masa tana hanya, zo kuga murna gun sa don beyi tunanin *Mamah* zata yarda ta barta ta tawo ba, saboda tsabar zumudi zaman cikin gidan gagarar sa yayi saboda haka ya sa jallabiyya ya fito ya zauna gurin gate man, jefi jefi suke hira, Zaman kamar minti goma sha biyar yayi yajiyo horn a, ko ba a fada ba yasan su *SHUKRAH* ne shiyasa ma yayi Saurin mikewa yaje get din da sauri da nufin bude musu, get man yayi Saurin karaso wa "

" Ranka ya dade, kabari za a bude yace yana kara sawa jikin get din"

"Yi sauri ka bude dae, ba surutu nace kayi min ba *Safeer* yace cikeda kaguwa"

"Nan get man ya bude musu, Aysher ta shigo da motar, yayi Saurin ban bayan motar, Tun kafin Aysher ta gama Parking *SHUKRAH* ta bude ta ziro kafarta, kadan ya rage *labeeba* ta fadi a hannunta, Da sauri *Safeer* ya karaso ya hada ta da *labeeba* ya rungume su cikeda so da kaina, sam ya manta ma dasu *Miemie*(Baki abun magana) suna tsaye "


" Aysher tayi Saurin dauke kanta, *Miemie* ta tabo Aysher, Aunty Kinga ya *safeer* din nn ko kunyar mu ma beji ba, lallai ", Aysher ta buge mata baki tace kin cika surutu wallahi, bazaki iya dauke idonki ba"

"Duk wannan maganar a kunnen *SHUKRAH*sukeyinta shiyasa tayi Saurin ture *Safeer* din tace su *miemie* na kallon muda, dariya kawae yayi sannan ya daga kafada irin ko a jikin sa din nn, *SHUKRAH* ta kallo *Aysher*, *Aysher* tayi Saurin dauke kai, ita Shukrah dariya ma aysher ta bata tace Bazaku shiga bane kuka tsaya wae, Aysher tayi Saurin kallon ta ta girgiza kai tace baxamu shiga ba Aunty dare ya fara yi kuma ban iya driving din dare ba"


"To Kawai *SHUKRAH* Tace sannan *MIEMIE* ta mikawa *Safeer* *Labeeb* dake hannun ta, *SAFEER* Tsabar mugunta sanda ya karbe shi sai da ya murde hannun *MIEMIE* yace fitsararriya kawai, Allah ya sa dae kina karatu don naga har ynx kanki yana rawa "

" Yar kara *Miemie*ta saki sannan ta kallo shi da fuskar tausayi tace Eyya ya *Safeer* akwai zafi fa, cika mata hannun yayi yace wuce ki bani guri ni, harda dan gudun ta ta wuce ta shiga mota *Aysher* tayi musu sai da safe sannan ta shiga motar tayi reversed T fice a gidan"



10:15 *Safeer* ya samu *SHUKRAH* a dakinta tana shirin kwanciya, ya karaso ya rungume ta ta baya yace mata a kunnen ta kinsan fa yau ke amarya ce, hope you are ready "


*SHUKRAH*ta danyi murmushi tace twins dae suna jinka ni ba ruwa na, Dariya shima yayi ya juya ya kallon su, bacci suke hankali kwance, ya dawo da kallo shi gurinta yace Bawani nn wayo kike son min, ae sun riga sunyi bacci, Dan ture sa *SHUKRAH* tayi sannan ta ja hannunsa suka kwanta suna fuskantar junansu "



" *safeer* ya kara matsowa jikinta yace mata *i luv u Babe beyond your expectation* "Murmushi *SHUKRAH* tayi tace kayi shiru bacci zamuyi, Matseta *Safeer* ya kuma yi sannan yace tunda nake da ke ban taba jin kince min i luv u ba, kodai har ynx bakya sona ne"


" *SHUKRAH* tayi Saurin matse hannunsa dake cikin nata haka kuma ta runtse idonta don tana masifar jin nauyin kalmar nan, dakyar ta iya bude baki tace

*My feelings for you are so strong and deep that i cant convey them in words, because i found no word strong enough to tell you how much i luv u, You are more than amazing, my heart is all yours*~i luv u~"



"tana kaiwa nn ta kifa kanta jikin pillow tana dariya kasa kasa, *Safeer* fa be taba tunanin jin wannan maganar a bakin taba though he's quit sure tana sonsa, tunda dae alamu sun nuna hkn, Saurin dago kanta yayi ya zira harshen sa cikin bakinta ya fara tsotsa cikeda so da kauna da kuma kewarta, kara shigewa jikinsa tayi don tayi missing dinsa sosai 54 days basa tare fa, haka dae suka raya wannan daren"



~~~~~~~~~~~~~~~~~~~




"yau saura kwana biyar bikin *Haiydar* amma bemasan me ake ciki ba, don *hajiya* kobi ta kansa batayi ba, duk wani abu da yakamata da *Safeer*take hatta kayan da zesa suna gidan *safeer* haka ma invitation cards suna gurin sa "


03:25 pm *safeer* ya shigo office din *Haiydar* da sallamarsa ya ajiye envelop kan desk sannan ya zauna yana fuskantar sa, ko kallo *Safeer* be ishi *haiydar*don yana kula da take~takensa, kuma sam zuciyar sa bata aminta da yawan zuwan da *safeer* din yake gidan su "



" *Haiydar* ga wannan invitation cards din ka ne ko zaka bawa abokanka na gida, don na office na gama basu *Safeer*yace yana nuna masa envelop din daya kawo "



" Murmushin takaichi *haiydar*yayi yana bin *Safeer*da mugun kallo tsawon lokaci sannan ya dauki envelop din ya mika masa yace cikeda takaichi karbi ka fitar min a office kafin ranka ya baci, kuma wallahi ka cire hannunka a maganar nan don gudun bacin rai"

"Dariya Safeer yayi sannan ya mike yace ni bazan karba ba don bana bukatar su, kuma ni bana gudun bacin rai indae akan wannan maganar ne "


" Fita Dalla malam kafin rai na ya gama baci don wallahi komai yana iya faruwa " *Haiydar* yace yana nuna masa kofa, Dariya *Safeer*
Yayi sannan ya fice yana cewa ba lefin ka bane wallahi nanda wani dan lokaci zaka dawo dai dai ae *Auren Bazata Alheri ne*


" Kwanaki sunja kuma gobe za a daura Auren *haydar*amma *Miemie* bata samu labari sai yau din da taji Aysher da Mamah suna maganar, ta zaro ido sannan tazo da sauri ta durkusa kusa da Mamah tace ki kace wae bikin ya Haiydar za ayi da wata banida ta fashe da kuka tace wallahi ina sonsa ina kaunar sa Mamah ku rufa min asiri zan mutu wallahi"



"Aysher ta harare ta tace Dalla can rufe mana baki wae, ina sonsa ina kaunar sa, ke har kinsan wani so "

" Mamah ta janyo miemee jikinta tace yi hakuri kinji Kinga ynx makaranta kike kuma wadda zai aura yar uwar sa ce, kema inkin gama school zai aure ki ae"

"Miemie ta turo baki tace ni wallahi bana son kishiya sai dae ya sake ta ya aure ni, Mamah tace yawwa hk za ayi ke dai ki kwantar da hnkl 'nki kawae, ynx kitashi kije daki ki dauki ankon ki kan bed ki gwada"


"Mikewa tayi ta nufi dakin tana bubbuga kafa' ni wallahi bazan je bikin kishiya ba... .






*SHUKRAH YAR GATAN MIEMIE BIE*💞💞
[5/23, 11:43 AM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻 *AUREN BAZATA*👮🏻
( *An unexpected marriage*)



*WRITTEN BY*
*ZAINAB YAKASAI*
*SHUKRAH*




*DEDICATED TO MIEMIEBEE*



4⃣1⃣


"Friday 26 october 2015 da karfe hudu na rana daukacin al'ummar musulmai suka shaida daurin auren *ALIYU KABEER DAN KASA* ( *HAYDAR*) Da amaryar sa *KHADEEJA ABDALLAH MAI KANO*( *ZAFEERA*) Kan sadaki naira dubu dari da hamsin, daurin auren da ya samu halartar manya manyan mutane daga fadin Nigeria kai harma da mak'otan Nigeria, "





Da daddare akayi kayatacciyar dinner ta gani ta fada, abokan haiydar duk sun halarchi dinner din haka ma kawayen zafeera guri ya cika har ba masaka tsinke kasan cewar harda yan gayyar sodi ma sun je, haka akaci aka sha aka tashi mutane sai sawa auren albarka suke "
" Washe gari akayi yini da daddare kuma Aka kai amarya dakinta, misalin karfe goma sha daya na dare haiydar yana mike a dakinsa na gidan Hajiya bama shida niyyar fita, a bangaren amarya Zafeera kuwa har ta gaji da jiran ango ta kwanta ta fara bacci kuma generator ya mutu saboda zafi ya dameta, mikewa tayi ta leko palour amma duhu ya gauraye gurin da kyar ta lallaba ta leka dakin dake kusa da nata, wanda take kyautata zaton na Haiydar ne amma ga mamakin sai taga baya ciki, parlour ta dawo ta zauna amma tsoro ya hana mata sukuni sai take ganin kamar Mutum ne ke giftawa ta gefen ta hakan yasa ta mike jikinta na rawa ta shige bedroom dinta ta dau wayar ta, number Safeer ta nemo tayi dialing, Allah ya taimaka mata kuwa ringing biyu tayi yayi picking


"Hello Safeer "Zafeera tace murya na rawa, ba tare da ta jira yace wani abu ba ta cigaba
" Safeer dan Allah kazo ka kunna min generator wallahi tsoro nakeji "

" Shi Haiydar din yana ina? Safeer ya tamvayeta cike da mamaki"


"Nina wallahi ban Sani ba, dan Allah kazo, Zafeera ta Bashi answer tana fashewa da kuka, dan har ga Allah tsoro takeji tunda a gidansu bata saba zama cikin duhu ba "


" To shknn gani nan zuwa ki dena kuka, tare ma zamu tawo da haiydar din kinji safeer yace sanda ya mike ya dau car key dinsa, dakin Shukrah ya wuce ya mata bayanin komai, ta mishi Allah ya kiyaye hanya sannan ya fice da sauri "

" Gidan Hajiyar Haiydar ya wuce direct don ya tabbatar Haiydar yana can, Sanda ya karaso gidan dakin Haiydar ya tura, ae ko ya ganshi kwance yana ta bacci abinshi, Safeer yaja tsaki sannan ya karasa ya fara buga mishi pillow 'nda yake kai da karfi, don iya haushi yau haiydar ya bashi "


" Bude ido Haiydar yayi waze gani in ba Safeer, ya hade rai yace lafiya zaka tashe ni ina bacci "

" Ba lafiya ba Haiydar kai kazo nan hankalinka a kwance kana bacci kabar yarinyar mutane a cikin duhu ko, to wallahi ko ka taso mu tafi ko kuma inje in kira hajiya Safeer yace yana hararar Haiydar "


" Haiydar wanda yasan in aka kiramai hajiya tasa ta kare yayi Saurin mikewa yana hararar safeer sannan yace muje cike da kulewa, tabe baki Safeer yayi sannan yayi gaba, shima Haiydar din takalmi kawae Yasa ya bi bayansa, "


" Cikin mota ba wanda yace da dan uwansa ci kanka kowa sai cika yake yana batsewa, Sanda

Please Login or Register in order to submit comment