ya iso wajen a sukwane bisa doki, da zuwa ya fadi gaba Sarki Haidar ya yi
34
gaisuwa, yayin da duk wanda ke wurin ya bishi da idanu, yayin da ya ke sanar wa da Sarki Haidar
ccwa, ga rundunar mayaka nan tafe zuwa wannan
birni. Ko da rufc bakinsa kuwa, sai suka hango kura
daga bayan birnin ta yi sama, suka dinga jiyo ihu da
kururuwar mutane. Nan da nan Sarki Haidar ya yi
umarni ga mutanensa da su tashi su yi shiri, da duk
wacce suka zo za su tare su da ita. Kafin wani
lokaci sai ga rundunar mayakan birnin Humar sun
wanzu ciki da wajen birnin cikin shirin yaki. A
wannan lokaci shi ma kansa Sarki Haidar din da ba
shi da isasshiyar lafiya, amma kasancewar jarumi
sai ga shi akan dokinsa cikin shirin yaki irin na
mazan jiya.
A nan fa aka fito sauraron isowar rundunar
mayakan nan dake tafe.
Can sai ga wani barde a sukwane bisa doki ya
doso sansanin mayakan birnin Humar, da zuwa ya
ja turjiya ya tsaya, yayin da yake bin mutanen birnin
Humar da kallo. Can kuma sai ya fara magana yana
mai cewa.
"Gare ku masallatan birnin Humar, ku fito
mazan ku da matanku ku mika wuya ga rundunar
Sarki Haiman kafin mu shayar da ku gidauniyar
mutuwa, kada kuyi girman kai ko yunkurin jan daga
da rundunar Sarki Haiman, lallai idan ku ka yi haka,
to za ku dandani ukuba mai tsanani....." Kafin ya
35
a gama rufe baki, sai jin saukar kibiya ya yi
goshinsa, tsinken kibiyar ya 6ula kokon kansa ya
fito ta bayan keyarsa, nan take ya fado daga kan
dokin yana mataccc. A daidai lokacin ne kuma
tawagar rundunar makafirta bisa jagoranci
Shugaban runduna, sarkin yakin mayakan Sarki
Haiman.
Aka ja tunda aka tsaya, kowanne shashe yana
nazarin dan'uwansa, shashen Musulmi suna kallo
tare da nazarin sashen kafurai, yayin da suma
sashen Kafurai suke kallo tare da nazarin sashen
Musulmin.
Rana ta tafi faduwa, yayin da aka gabza yaki
mai tsanani, rayuka suka mutu da dama, ciwuka
suka wanzu da dama a jikin mutane, yayin da aka
ribace wasu da dama daga cikin mayakan sarki
Haiman, wanda a ciki har da shugaban rundunar
madugu uban tafiya, Sadauki Jaudaru, kafiri uban
makafurta (kirarinsa kenan). Yayin da wasu da
dama daga cikin mayakan Sarki Haiman suka juya
domin kufutar da rayukansu, suka koma izuwa
birnin Baidar domin sanar da Sarki Haiman abin da
ke wakana.
BABI NA HUDU
ayin da iskar nan da ta dauke Sayyar ta bace,
ao i hadimin Aljani ne wanda ya
wanzue da sihirin Boka Ashfar wanda tun
wani lokaci ya wanzu yana kulla kullallan sihirinsa a
bisa umarnin makafircin Sarki, Sarki Ukashatu, domin
ganin ya wanzar da Sayyar din cikin tashin hankali da
kuma kuncin rayuwa, wanda a karshe zai hallaka.
Bakin Aljanin nan ya ci gaba da keta hazo da
gajimare da Sayyar bin Haidar, yayin da shi kuma а
wannan lokaci tuni ya dade da suma a hannun bakin
Aljanin.
A can kuma cikin turakar tsafin Boka Ashfar, ya
na kallon duk abin da ke wanzuwa game da hadimin
Aljaninsa ta cikin wata bakar tukunyar tsafinsa wadda
aka cika da wani jan ruwa. Yayin da hadimin Aljanin
nan ya yi nisa, sai Boka Ashfar ya yi magana cikin wata
irin murya mai ban tsoro.
"Ya kai Hadimil Ashfar, maza ka ajiye Sayyar bisa
tsuburin Jazfar dake kudancin birnin Yaman." Tamkar a
gabansa yake, sai kuwa Aljanin nan ya sauka kan wani
katon tsuburi dake cikin wani uban daji mai bishiyoyi,
ya sauke Sayyar. Ravan va sauke shi, sai Boka Ashfar
ya umarce shi da ya tashi ya bar wajen, tashin Aljanin ke
da wuya, sai Boka Ashfar ya dauko wata bakar buta ta
karfe, ya girgiza ta, sannan ya kira sunan Sayyar sau
uku, ya rufe idanu yana wasu sabbatu tare da juya
hannuwa yana fifita su kamar yadda tsuntsu yake yi idan
ya tashi sama. Bai gushe daga wannan siddabaru nasa
37
ba, sai ga kamannin Sayyar suka juyc suka kuma wani
kyakkyawan tsuntsu mai kyawun sura, zuwa can kuma
sai tsuntsun ya tashi ya lulluka a sararin samaniya.
Boka Ashfar ya kyalkyale da dariya, sannan ya
tashi yana mai kokarin fitowa daga dakin tsafinsa.
Wata 'yar Sarki tana zaunc a bakin gabar wani
ruwa mai gudana cikin wata katuwar gona, tare da
Kuyanginta suna shakatawa. Yayin da iska mai dadi ke
busawa a cikin safiyar wannan lokaci tare da wani irin
yanayi mai sa nishadi da walwala a zukatan al'umma.
Jefi-jefi ta kan sa hannu ta na dibar ruwan tana wasa
dashi, kallo daya idan ka yi mata zaka fuskanci tana
cikin nishadi mai yawa.
Kyakkyawa ce a cikin kyawawan mata, Allah ya yi
mata kyakkyawar sura ma'abociyar daukar hankali, tana
da wushirya a bakinta, wadda idan ta yi murmushi sai ya
rudar da wanda ya kamu da begenta. Su kansu
kuyanginta dake tare da ita, tana birge su, duk wani
motsinta suna kula tare da kiyayewa da ita.
Gimbiya Anisa kenan, 'yar Sarki Haiman tare da
kuyanginta suke taya ta shakatawa kamar yadda ta saba
kullum a cikin babbar gonar da Sarki' Haiman mahaifinta
ya sa aka gina mata domin ta dinga shiga tana debe
kewa a duk lokacin da ta bukata.
Suna nan zaune tare da kuyanginta, suna
hirarrakinsu kamar yadda suka saba a duk lokacin da
suka wanzu tare da ita a cikin wannan waje, yayin da
walwala da annushuwa ke lullube da fuskokinsu a
38
wannan lokaci, musamman ita Gimbiyar Anisa. Can sai
kuyangin nata suka lura da ita, hankalinta ba akansu
yake ba, balle kuma hirar da suke yi. Don haka baki
daya suka juya tare da kai kallonsu in da take kallon.
Wani tsuntsu suka gani yana tahowa daga bayansu.
Babu wanda ya fauke idonsa daga kan dan tsuntsun har
zuwa lokacin da ya sauka kusa da su bisa ciyayin dake
bakin ruwan.
Gimbiya Anisa ta yi murmushi tare da kura wa
tsuntsun idanu, taga tunda take a rayuwarta bata taba
ganin kyakkyawan tsuntsu irin wannan ba, haka nan
kuma sai ta ji so da kaunar tsuntsun ya shiga ranta, don
haka sai ta tashi da kanta ta nufi inda tsuntsun yake da
nufin kama shi. Cikin nutsuwa ta sa hannu ta dauke shi
tana murmushi, sannan ta dawo inda kuyanginta suke
zaune tana cewa.
"Na samu abin begena, wanda zai fi komai debe
min kewa a rayuwata."
Kuyangin nata suka bita da kallo tare da girgiza
kai.
Gimbiya Anisa ta kura wa tsuntsun idanu tarc da
rungume shi a jikinta, sannan ta yi magana tamkar tana
yi da mutum.
"Ka kwanta bisa jikina sosai, ka zo wajen wadda
zata kaunace ka, zata nuna maka kulawa, kuma za ka sa
ta farin ciki a zuciyarta dare da rana, daga yau ka zama
abin begena, kuma sirrin zuciyata."
Kuyangin nata dai bin ta suke da kallo, amına
izuwa yanzu abin ya fara daure masu kai, musamman
39
idan suka yi la'akari da irin lafazin da yake fitowa daga bakinta.
"Mu gani ranki shi dade." Daya daga cikin kuyangin nata ta bukata tare da mika hannu da nufin ta
bata tsuntsun ta gani.
Gimbiya Anisa ta girgiza kai.
"A'a ki yi hakuri, ba zan ba kowa abin begena ba,
domin daga nan sai cikin kejina, wanda zai zama gidansa, amma ba zai je hannun kowa ba.." Yanzu aka fara labarin.
Mai karatu ka dakace ni a cikin littafin KAMBUN
KARFE Na biyu.
Dan'uwanku A Musulunci;
NAFI'U SALISU MUSA 08081643197
Kafan daga cikin littafin: RIGAR SAKI
"Za ki iya yi min alkawarin ba za ki taba sauraron
kowa da nufin soyayya ba, ba za ki mallakawa kowa kanki da
soyayyarki ba fa ce ni.?"
Cikin muryarta mai ratsa dodon kunne da sanya
nutsuwa ga wanda yake saurare, ta amsa mishi da cewa.
"Na amince Salim, ba zan kula kowa ba sai kai, ba zan
saurari wani da namiji da nufin soyayya ba, sai kai. Kai kadai
ne wanda na mallaka wa soyayyata, kai kadai ne a zuciyata,
da koda yaushe tunaninka ba ya gushewa daga cikinta....."
Sun kulla alkawarin ne a tsakaninsu, cewar kowa ba zai
saurari soyayyar waninsu ba, sai dai junansu kawai, duk da
cewa ba su taba ganin juna a zahiri ba.
NAFIU SALISU 40 08081643197
GARBA
MUHAMMAD
BOOKSHOP
KasnwaoSabon Gai, Kana
08036555794-08069382816
e
GBS
S
BOOKSHOP
Tsarin Bango:
SALISU JAWOTA GRAPHICS
07090490491
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels