Mahalakhshmi takeyi ba, zan bawa kowa damar sararawa da y'an mata ba tareda hukunci ko doka ba,
Amma fa bayan wannan babu wani abu me sauk'i, hukunci na kuma sai yafi nata tsauri"
Waziri yace, "idan ka zama sarki ita kuma ya zakayi da ita??"
Kai tsaye yace, "zan maida ita baiwa ta ko kuma na kulle ta a kurkuku ko Baba??
Ko kuma ta zauna a me kula da matata"
Waziri ya shek'e da dariya yace, "lallai d'ana mulkin ka zo ze da abun mamaki, ina son ganin wannan ranar ni kaina sai na dinga gwangwajewa ta"
Arveen yace, "karka damu baba"
Wani matashin ba fade ne ya shigo yana kai gaisuwa suka amsa tareda bashi umarnin ya fad'i abunda yake tafe dashi.
Da sauri yace, "ranka yadad'e Shugaban mu na gobe wato Aruuful Ansaaar dai ya aikawa Masarautar marudha wasik'a akan neman sulhu a yanzu zancen nan da muke Sarauniya Sameena ta amince da hakan haka itama Sarauniyar mu ta amince yanzu gaf suke da had'e hannayen su guri guda su zama tsintsiya mad'aurin ki d'aya, sannan wannan Aruf Ansar da kuke gani makirin mutum ne yanzu ya riga ya gama mamayar zuciyar sarauniyar mu, abubuwa da dama shine yake tsara mata yadda zatayi, sai kun tashi tsaye a kansa idan ba haka ba ze baje tsarin ku kuna zaune, kuyi hanzarin sanin abunyi ranka yadad'e"
Tini zuciyar Arveen ta fara tafasa yayi kicin kicin da rai.
Waziri ne ya kalli bawan yace, "yanzu ka zo da labarin da ya fusata d'ana dan haka ba kai ba samun kyauta yau ka tashi kaje"
Sim sim ya tashi ya fice, ko babu komai ya isar da abunda yake son isarwa.
Waziri ya kalli Arveen cikin son kwantar masa da hankali yace, "haba jarumin d'ana be kamata abu kad'an ya dinga fusata ka ba,
Zamu san abun yi"
A harzuk'e yace, "kar in bari abu kad'an ya fusata ni wannan kake kira abu ka d'an??
Haba kace ka samo mana mafita ashe hanyar da bata 'bullewa ka kai mu,
A memakon masarautar Marudha ta tarwatsa ta yanzu sai su had'e kai dan temakon juna? Meyesa hakan???"
Yayi tambayar a tsawace.
Waziri ya dafa kafad'ar sa tareda cewa, "yi hak'uri d'ana kwantar da hankalin ka ni nasan hakan ma baze yuwu ba"
Maharani tana zaune Ansaar ya iso inda take, ba tareda ya jira umarni ba ya nemi kujera ya zauna kusa da ita.
Ido ta zuba masa tana jin wata irin kibiya tana sukar zuciyar ta.
Da d'an murmushi akan fuskar sa yace, "ba abu ne fa me wuya ba Lakhshmi, ki bawa masarautar Marudha hak'uri baya nufin kin fad'o, domin kuwa shi shugaba da son zaman lafiya aka san shi, hakan da zakiyi shine ze k'ara kankaro martabar ki a wajen wasu, kiyi k'ok'arin danne zuciyar ki karki bari girman kai yasa ki fad'a halaka, ki rubuta wasik'a yanzu yanzu Lakhshmi,
Gobe ki tashi mutanen ki suyi tafiya zuwa can domin isar da sak'on, kiyi komai da tsari kuma da mutuntawa"
Daga haka ya tashi yana shirin barin wajen.
Sunan sa da ta kira ne yasa ya fasa tafiyar ya juyo yana kallon ta.
cikin murmushi me cike da shauki tace, "Aruuful Ansaar, Tumhara har kaam bahut khub hota hai"
(Aruuful Ansaar Ko wane aiki naka yana kyau)
Murmushi yayi tareda d'an rissinawa.
Hakan ya sumar da ita a zaune, yau ne rana ta farko da ta ta'ba ganin ya risina mata, hakan ya sata cikin nishad'i, ita kad'ai tayi ta murmushi tana tunanin irin yanayin sa da d'abi un sa.
Da daddare ta kaiwa Ummee ziyara,
Cikin sanyi ta zauna kusa da ita tareda rik'i hannun ta, a marai-rai-ce tace, "Ummee na yak'i dawowa gare ni gashi har wani yana nema ya gaje fadar sa, ko dai ya mutu ne??"
Girgiza kai tayi alamar a'a ko kuma bata sani ba.
Murmushi tayi tace, "Ummee mutum d'aya ne ya ta'ba sanya shauki a cikin tunani na bayan shud'ewar wani lokaci"
Duk da irin yanayin da take ciki be hana kyakkyawan murmushin ta bayyana ba, ta lumshe ido tareda had'iye wani mugun yawu.
Maharani tace, "zan iya tafiya?"
Gyad'a mata kai tayi.
Ta tashi tana murmushi ta koma turakar ta.
Hadima Urmi ce ta shigo hannun ta rik'e da Abdulkareem wanda yayi wayo ya girma har ya fara irin gwaranci na yara.
Tana ganin sa fara'ar ta ta k'ara fad'ad'a da sauri ta taso ta kar'be shi tana cewa, "Abdulkareem!!
Ido ya zuba mata ko k'iftawa baya son yi.
Ta saki murmushi tareda hura masa iska a fuska sai kuma ya k'yalk'yake da dariya.
Sake rungume shi tayi tareda sumbatar goshin sa tace, " ina fatan nasara wa rayuwar ka Abdulkareem "
Uwar Hadimai Urmi tace, "Ranki yadad'e naji kamar yana buk'atar ganin ki ne shiyasa na shigo miki dashi ina godiya k'warai da gaske da ya kasance kin dawo damu kusa da ke, anan zamu fi samun kwanciyar hankali"
Ta murmusa tareda cewa, "uwa urmi ai wannan ba komai bane gareki, kije kawai yau zan kasance tareda Abdulkareem"
Tayi godiya sannan ta fice.
Yau ta kasance rana ce wadda ake lullumi babu rana sai hazo da hadari da suka zagaye sararin samaniya iska tana kad'awa kad'an kad'an,,, sakamakon Albarkar shuke shuke da tsirrai da suke dasu a yanki yasa k'amshin su yake tashi yana bazawa ko ina.
Cikin nutsuwa take shiryawa cikin wani Sari ruwan makuba (coffee ) wanda aka yiwa ado da ruwan gwal (golden ) yayi matuk'ar dacewa da jikin ta yayi mata kyau sosai,
ta d'auki wata dank'areriyar sark'a ta zuba a wuya har sai da ta kai kan cikin ta kallo d'aya zakayi mata ka gane ta madarar gwal ce sai shek'i da walwali take, haka tayi ta saka kayan ado ta ko ina sosai tayi kyau kamar sabuwar amarya, tana gama shiryawa ta zura takalmin ta,
Wajen taga ta nufa tana lek'awa, sassanyar iskar da take kad'awa ta shak'a taja numfashi kafin ta sauke ajiyar zuciya, murmushi ta saki saboda tunanin da ya fara bijiro mata,
A duk lokacin da yanayi ya kasance irin wannan takan kasance a mak'ale dashi domin kuwa tana matuk'ar jin dad'in irin wannan yanayin yayin da ta kasance a tareda shi, idan bazata fita ba haka shima bazata barshi ya fita ba sai dai ya rungume ta kawai, tayi bacci ta farka shi kuma yana ta gadin ta, idan kuma zata fita ko a ina take ko a wane yanayi take ko yawan mutanen da suke guri baya hana ta shigewa jikin sa, amma sauyin rayuwa ya sa itace me fita ko wane irin lokaci ana ruwa ana rana ana sanyi ko ana iska baya hana ta fita domin al'umar ta.
A take wata muguwar kewar sa ta tsirga mata tin daga sama har k'asa , idanun ta suka cicciko da k'wallah, tafukan hannun ta tasa ta goge su kafin ta fara takawa cikin nutsuwa tayi hanyar waje.
Ko ina ta ratsa d'iban gaisuwa ake da mik'o jinjina, da kyar take iya amsa musu saboda yanayin da ta tsinci kanta a ciki,
Haka ta cigaba da ratsawa har ta isa bayan masarautar,, bakin tank'amemem ruwan da yake gudana ta tsaya tana kallon furrai da tsirrai tana matuk'ar jin dad'in daddad'ar iskar da take gudana.
Ta dad'e anan tana tunanin rayuwar baya da kuma wadda zata kasance nan gaba, tana jin zuciyar ta na mata barazana akan irin abunda yake shirin faruwa, duk da tana da k'warin guiwa amma tana matuk'ar tsoron wannan Azzalumar masarautar domin kuwa d'aukar fansa ce zata dawo dasu wajen ta.
Tana cikin tunanin taji an rungume ta,
Wani bahagon numfashi ta fizga tareda zazzaro ido a razane.
Muryar sa ce ta daki dodon kunnen ta cike da kulawa yace....
(Su o'o har an baza kunnuwa aji me yace hhh😂😜😜a dena sa ido😎)
*INDO CE..*
[26/03, 10:41 a.m.] INDO CE..: *🎠🎠🎠 TAJMAHAAL🎠🎠🎠*
(Masarauta)
Mallakin
*INDO CE..*
🌼ELEGANT ONLINE WRITER'S🌼
*Page~16*
بسم الله الر حمن الر حيم
*Ga masu buk'atar shiga group na musamman domin jin k'arshen Labarin Naira 100 ne kacal😂 ku hanzarta ku mallaki naku kar a barku a baya🤣 domin k'arin bayani ku neme ni tanan 👉🏻 08146838480*
"Mad'aurin rigar ki ne ya kwance shine zan gyara miki"
Duka ta tattaro k'arfin ta ta bangaje shi, a zafafe ta yarfa masa wani shigaggen mari, fuska a had'e tace, "ka shiga tai-tayin ka Aruuf,,
Maharani Mahalakhshmi ni ba kamar ko wace mace bace, bana buk'atar gigi, ban amince wani ya kusanci kusa dani ba shine zakayi min irin haka saboda ka samu fuska?"
Hannun sa dafe da kumatun sa cikin wata sassanyar murya yace, "kenan har ranki ya 'baci!?? Bana son hakan kiyi hak'uri, a bisa kuskure ne na aikata hakan nima kaina na sa'ba doka da k'a'ida ta, wannan baya d'aya daga cikin d'abi'a ko ak'ida ta ina neman afuwar ki"
A tsawace tace, "rufe min baki Ansaar!!! idan zuciya ta ta riga ta buga batajin magiya bata gane meye hak'uri bare ta tausayawa mutum iya abunda ta sani kawai hukunta duk wanda yayi mata kuskure, ka cancanci mummunan hukunci sai dai bazan iya yi maka shi ba, kuma hakan ya samo asali ne saboda ina mutunta addinin ka da kuma duk wani mabiyin addinin banda haka tabbas kai da kwanan farin ciki daga yau sai dai tarihi, Aruuf"
Kallon ta yake ido cikin ido a dake yace, "tabbas nayi kuskure amma irin hukuncin da kike yankewa mutane wani laifin sa be kai girman hukuncin ba, kin mayar da zubda jini tamkar ado ko kuma wani abu me kyau,
Na tsani wannan d'abi'ar taki,
Mutum ya aikata kuskure kad'an kiyi masa hukuncin kisa kin mayar da takobi abun k'arar da rayuka,
Ki jaraba koda sau d'aya ki dena irin wannan hukuncin ki samu jituwa da kusanci da jama'ar ki na tabbata hakan ze sa kiji sauyi sosai a tareda ke,
Bayan wanda kike so kuma kike jiran zuwan sa kin kasa sakin jiki da kowa,
Ba dole sai ahalin ka ne zasu ji'banci lamuran ka ba idan da kina jansu a jiki sosai nasan zaki fi haka samun salama domin nasan zaki samu masu d'ebe miki kewa ba adadi,
Nayi bincike akan mahaifin ki wato Sarki Ganesh, tabbas shi shugaba ne me adalci wanda yake iya zama yaci abinci tareda bayin sa, yakan zauna yayi hira ta fahimta dasu ya d'auki kowa a matsayin d'an uwa yana kyakkyawar kyautatawa gare su baya zargin kowa haka ya d'auki yarda ya bawa kowa, tunane tunane ba aikin sa bane ya mik'a lamarin sa ga ubangiji, meyesa bazaki kwaikwayi baban ki ta wasu 'bangaren ba??"
Shiru tayi tana nazari kafin ta girgiza kai tace, "baka san komai ba dan haka ka janye jikin ka, duk da cewar na d'an yi mamakin yadda ka zayyano min wasu daga cikin halayen mahaifi na, amma wannan kad'an ne tunanin ka baze iya d'auka ba kwanyar ka bindiga zatayi idan aka fara karanta maka tarihi na da na mahaifi na har ma da mahaifiya ta Sarauniya Rukhshah, Rukhshahnaa, tunani kuma abu ne wanda ya zama wajibi ga wanda yake tafiya ba gaba ba baya kuma hanya ta k'ure masa ya zama dole yayi nazari akan meye mafita, ka dinga tunanin abunda ze yuwu Bin Abu Ansaar "
Daga haka ta fara takun ta me matuk'ar jan hankali da shagalarwa da nufin komawa ciki.
Cikin zafin nama ya rik'o hannun ta tareda finko ta tayi baya, dai-dai inda wata k'orama take kwararar da ruwa ya tara ta,
Sai da ta jik'e jalaf har ta fara kakkarwa saboda sanyi da kuma yadda ruwan ya ratsa k'ok'on kanta sannan ya sake ta.
Cikin hanzari ta fito tana girgiza kanta tareda k'ok'arim shak'ar kyakkyawan numfashi, ta d'auki lokaci kafin numfashin ta ya dai-dai-ta sai sauke ajiyar zuciya take a kai a kai ta furzar da wata sassanyar iska ta bud'e idon ta garass a kansa tana binsa da wani kallo me cike da tuhuma da kuma tsantsar 'bacin rai.
'Dan murmusawa yayi yace, "Lakhshmi nasan ba lallai idan kin fahimci me hakan yake nufi ba, ni nayi ne dan na sa kiji sanyi har cikin zuciyar ki ba da wata muguwar niya nayi ba,
Ranki ya 'baci sosai a dalili na be kamata in bar hakan ba, kuma yawan tunanin da kike ya jefa ki a damuwa hakan ne ma yasa nazo gareki domin nema miki salama, tin zuwa na da haka naso in iso miki sai dai kuma ban samu damar hakan tin farko ba,
Idan kika d'aga murya kece zakiji dan kuwa mutanen ki zasu raina girman ki,
Idan kuma kika koma cikin Tajmahaal a haka mutane zasu d'auka kinyi wankan Al'ada ne na addinin ku, ni kuma nayi ne kawai dan rage miki damuwa, na barki lafiya"
Daga haka ya juya ya bar wajen cikin takunsa irin na cikakken jarumi.
Ido ta bishi dashi take tunani ya k'ara bijiro mata, a zahiri tace, "yanayin takun sa yanayin salon sa haka ma tafiyar sa murmushin sa da kuma yadda yake gudanar da komai cikin kyakkyawar manufa da k'wak'k'warar hujja Sakkk,.
Murmusawa tayi tareda cewa, " na k'aunaci hakan Aruuf, kuma salon ka yana burge ni"
Wani shauki ne ya shiga d'ibar ta sai murmushi take ita kad'ai,,
Cikin nutsuwa ta shiga cikin masarauta kamar yadda ya fad'a kuwa kowa yayi zaton tayi wankan Al'ada ne shiyasa suke ta kwasar tabarraki,
Gaf da zata shiga sashin ta tayi karo da Gimbiya Jusiyya hannun ta rik'e da wani d'an abu na zuba wuta, fuskar ta d'auke da murmushi ta saka mata Albarka sannan taja hannun ta suka shiga ciki,
Kaya ta ta d'akko mata ta bata tareda cewa, "y'a ta kisa kaya kinji ko!? Kar sanyi yayi miki yawa"
Gyad'a kai tayi ta kar'ba tana murmushi.
Cikin hargagi Arveen yace, "Baba wai me yarinyar can take nufi da mu ne a wannan masarautar??? Ta d'auki wancan k'azamin bawan tamkar wani abun bautar ta, kusancin su yayi yawa, ina jin zafin hakan Baba"
Waziri yace, "yaro na? Nace ka dena saurin fushi dan kuwa mutum me saurin fushi be cika tunani ba,
Ka zauna kayi nazari sosai akan abu shine mafita ba kai ta fusata ba, karka damu d'ana"
Tsaki yayi yace, "haba Baba na, haka kake ta cewa kar na damu gashi yanzu duk ka lalata komai kwata-kwata ma yanzu ba ta mu take ba, zanyi abunda nake ganin shine dai-dai fa"
Waziri yace, "d'ana kwantar da hankali bana son ganin 'bacin ran nan naka, na gaya maka sannu sannu bata hana zuwa"
Arveen ya juyar da kai tareda cewa, "haka dai"
Gimbiya Jusi ce ta kalle ta cike da kulawa tace, "Maharani?? Naga kwanan nan kina cikin damuwa duk kin canja me yake faruwa ne?? Me yake saki irin wannan yanayi Maharani??"
Lumshe ido tayi tareda kamo gefen le'ben ta ta taune shi, kamar baza tayi magana ba sai kuma tace, "Mama Jusiyya masarautar da muka yak'a a baya tana son dawowa garemu domin d'aukar Fansa na tabbar yanzu magajin masarautar ne yake k'ok'arin tinkara ta abun bazeyi kyau ba domin kuwa nasan ya girma ne da muradin fansar jinin mahaifin sa"
Gimbiya Jusi iya tashin hankali ta gama kaiwa k'ololuwa, ko motsin kirki kasa yi tayi sai girgiza kai da take idanun ta sun cicciko da k'wallah.
Da sauri Maharani ta dafa kafad'ar ta tareda cewa, "Haba Gimbiya Jusi meyesa kuma zaki tashi hankalin ki haka shiyasa fa nak'i fad'a muku gara na shiga tashin hankalin ni kad'ai k'anwata Farhana ma ban gaya mata ba saboda bana son ku shiga irin rud'anin da nake ciki ina fata a cikin wannan k'adamin masoyi na ya dawo Gimbiya Jusi daga nan ne duk wani k'warin guiwa ta ze dawo, rashin sa ya sa rayuwa ta ta samu babban nakasu, Mama Jusi dan Allah ki dena damuwa babu abunda ze faru sai Alkairi, ubangiji baze basu ikon cin nasara a kan mu ba, domin a koda yaushe gaskiya itace a sama"
Gimbiya Jusiyya ta share k'walla cikin tausayi da juyayi tace, "y'ata ke me nasara ce kuma zaki cigaba da nasara a rayuwar ki, har yanzu jinin masoyin ki yana bibiyar jikin ki, akwai abu me matuk'ar daraja a tsakanin ke dashi, darajar wannan abun baze bari ya nisan ta da ke ba, yana tareda ke y'ata"
Murmushi ne ya su'buce mata ta lumshe ido a k'asaice tace, "naji dad'in hakan Gimbiya Jusi"
Farhana tana zaune gefen sa suna hira kad'an kad'an mafi yawanci ma tambaya ce yake mata sai ta bashi amsa,
Wannan budurwar me rufaffiyar fuska ta shigo kai tsaye Kumar ta fara kira,
Yayi saurin bud'e mata hannu ta fad'a jikin sa tareda sauke wata zazzafar ajiyar zuciya.
Cike da kulawa ya rungume ta yana kallon ta cikin muryar sa me cike da jin kai yace, "kyaa hua??"
Numfashi ta sauke kafin tace, "masarautar da ta dad'e tana bibiyar Maharani itace yanzu take k'ok'arin jefo harin ta gidan nan, yanzu lokacin da ze d'auki fansar sa yayi"
Kece yayi da dariya, har sai da yayi me isar shi sannan ya tsaya, cikin k'warin guiwa yace, "ban damu da kashe kashen da za'ayi ko 'barnar da za'ayi ba, ban damu ba idan an rushe masarautar nan ni dai buri na a wulak'anta Maha"
Farhana tace, "wannan gaskiya ne Khumar nima babban buri na shine naga an tarwatsa ta, ban ta'ba muradin mulki ba kawai naga an kawo k'arshen ta shine cikar buri na"
Devi tace, "shikenan to yanzu me kuke ganin za'ayi??"
Khumar yace, "baku da damuwa a kan wannan yanzu hukuncin da na yanke shine za'a bi zanyi nazari naga abunda ya kamata, sai mun cika muradhen mu"
Zaune take a bakin gado ta rufe fusksr ta da tafukan hannun ta duka biyun, ta dad'e a haka kafin ta tashi ta fice.
sashin da aka mayarda Hadima Urmi ta nufa, ta tarar da ita zaune tana yiwa Abdulkareem wasa.
Tsayawa tayi tana kallon sa har cikin rai tana yaba wa irin mugun wayon da yaron yake dashi, a hankali ta tsungunna dai-dai shi cikin sassanyar murya ta kira sunan sa, ya dawo da kallon sa gareta yana fara'a.
Murmushi tayi tareda shafar kansa tace, "zanje kurkuku na duba Ummee na ko zaka raka ni??"
Hadima Urmi ta murmusa tareda cewa, "me zamani y'ar mulki yaro Abdulkareem be iya magana ba, zan iya amfani da yawun sa??"
Kallon ta tayi ta kauda kai sannan tayi mata alamar eh.
Hadima Urmi tace, "godiya nake uwar marayu ta dai Abdulkareem yana son ya bi Ummeen sa alamun sa ma sun nuna hakan"
Hannu ta mik'a masa tana murmushi tareda cewa, "kana da son yawo kenan??
Yanzu ma kaci girman da zaka fara sanin ciki da wajen masarauta zan dinga d'aukar ka nayi komai tareda kai dan ka fahimci komai"
Shi kuwa cikin sauri ya mak'ale mata sai rarraba ido yake.
Hadima Urmi tace, "Abdulkareem ya gode haka ma me rainon Abdulkareem ta gode"
Bata kula ta ba ta d'auke shi suka fita.
Tana kwance can gefe ta tsakure sai d'an numfashin ta da yake fita a hankali ne ze tabbatar maka da tana da rai.
A hankali ta k'arasa ta durk'usa a gaban ta, cikin sanyi tace, "Ummeen mu!!! Ki tashi nazo ki tashi kiga Abdulkareem, cikin hanzari ta bud'e ido tareda mik'ewa ta zauna tana kallon su.
Mik'a mata shi tayi tana cewa, " daga Udday da Surekha"
Rungume shi tayi tareda gyad'a kai cikin nuna kulawa da zallar k'auna, sumbatar goshin sa tayi take waye suka shiga jerangiya akan fuskar ta kamar famfon da ya lalace.
Maharani bata hana ta ba sai ma nata hawayen da suka fara zuba.....
*INDO CE..*
[27/03, 11:08 a.m.] INDO CE..: *🎠🎠🎠 TAJMAHAAL🎠🎠🎠*
(Masarauta)
Mallakin
*INDO CE..*
🌼ELEGANT ONLINE WRITER'S🌼
*Page~17*
بسم الله الر حمن الر حيم
*(WANNAN SHINE K'ARSHEN SHAFIN KYAUTA DAGA YAU NA GAMA FREE PAGE. KI BIYA KI KARANTA CIKIN AMINCI😊)*
*Ga masu buk'atar shiga group na musamman domin jin k'arshen Labarin Naira 100 ne kacal😂 ku hanzarta ku mallaki naku kar a barku a baya🤣 domin k'arin bayani ku neme ni tanan 👉🏻 08146838480*
Cikin sanyi ta dafa ta kafin ta share k'wallar ta tana murmushi tace, "ba kuka zakiyi ba Ummee Addu"a zakiyi mana wata rana muma zamu haifa miki y'a me kama da ke nasan zakiyi farin ciki sosai musamman idan ta kasance me sunan ki, nasan zatayi irin halin ki da kyawun ki Ummee, kuma zata kasance jaruma sak jinin mahaifin ta, ina son ganin Murmushi a fuskar ki ba hawaye ba, idan ina ganin kina kuka nakaniji gaba d'aya bazan iya yafewa kaina ba,
Gashi kin k'i magana Ummee kin kasa fad'a min kin yafe min ko kuwa??
Duk da ko kin yafe min ba lallai ubangiji ya yafe min kuskure na ba, Ummee idan kinso zan iya bada raina fansa akan abunda nayi, Farhana ta kasance me karaga nasan koda bana raye indai hakan ta faru tabbas ruhi na ze samu salama Farhana nasan zatayi fiye da abunda nayi a wannan k'asar bare kuma da temakon ki, za'a shimfid'a mulki na adalci, Ummee meyesa baza ki za'bi hakan ba?? Meyesa sai zaman kurkuku kika za'bawa kan ki?? Mu kuma iyalin ki meye makomar mu Ummee??
Dan Allah ki dena kuka kiyi farin ciki a koda yaushe nasan wannan yaron tabbas ze zamo Fansar wasu daga cikin rayukan da muka rasa, ki kalle shi sosai duka yanayin jinin Abdulkareem ne dashi hakan ne yasa naji ina k'aunar sa domin kuwa Ahalin Abdulkareem ba abun k'i bane,
Kiyi Murmushi Ummee na"
Share hawayen ta shiga yi sai dai tana sharewa wasu suna k'ara zubowa, ido ta zubawa Abdulkareem wanda yake kallon ta kamar wanda yake mata kallon tuhuma, wani yalwataccen Murmushi ne ya buwayi fuskar ta, jinjina kai tayi tareda mik'awa Maharani shi, cikin ranta tanaji kamar tayi magana sai dai bakin ta yayi nauyi ya rik'e gamm baza ta iya motsa shi ba indai da sunan tayi magana ne, girgiza kai kawai take yayin da wasu zafafa hawaye suke kwararowa daga cikin idanun ta, tabbas tana da abun fad'e tana da muhimman abubuwan da ya kamata ta sanar mata sai dai k'addara ta hana ta wannan damar"
Jin tana neman fashewa da kuka ne yasa tayi saurin tashi tana rungume da Abdulkareem ta fice daga wajen tana tafiya cikin sanyi da tsanani tausayin rayuwar su"
"Lakhshmi"
Muryar sa ce ta doki dodon kunnen ta,,, tsayawa tayi cak ba tareda ta juya ba kuma bata cigaba da tafiyar ba.
K'arasowa yayi cikin nutsuwa da kamala yace, "Lakhshmi bana jin jefa kanki cikin wani k'angi shine mafitar damuwar ki, da haka me yasa baza ki baza sojojin ki ba tinda suna da yawa su je su nemo miki wanda kike so???
Kuma ina so ki tattara nutsuwar ki guri d'aya indai baki yi hakan ba banajin zaki iya yin tunani me kyau,
Akwai jarrabawa a rayuwa haka kuma akwai k'alu bale, wani tashi k'addarar zalla ce wani kuma tayi gauraye, rashin nutsuwa yana gusar da hankali kuma idan hakan ta faru k'arshe bata bada abu me kyau,
Ya kamata ki dinga nutsuwa ki bawa zuciyar ki damar yin tunani me kyau"
Sai da ya gama maganar sannan ta d'ago idanun ta wanda suka cika tafff da hawaye zuba a kansa ta d'an kwashi lokaci tana kallon sa kafin ta bud'i