Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
tsananin farin ciki sannan ya sake su suka sake rugawa wajen iyayensu wato Hasilatul Kurbas da Inmal suma suka rungumesu. Nan fa kowa ya cika da tsananin farin cikin samun su Izaima a cikin koshin lafiya. Bayan an gama farin cikin samun su Izaima lafiya sai suka dunguma gaba daya suka fice daga cikin wannan daki na biyu suka durfafi hanyar da za ta fitar da su daga cikin fadar. Sai da suka iso tsakiyar fadar sai kwatsam! Suka ga dakarun gidan suna ta fiffitowa ta ko ina rike da muggan AKIN GINI makamai iri-iri suna yi musu kawanya. Wasu makaman ma da ke hannun Dakarun ko a labari su Kurbas basu taba jinirin su ba, kuma yawan Dakarun ya kai miliyan daya darabi, sai gashi su sadauki Kurbas sun zama 'yan mitsi-mitsitamkar an ajiye bera guda daya a tsakiyar Kyanwowi dubu.Al'amarin da ya matukar dugunzuma hankalinZuhura, Kurbas, Hasilatul Kurbas, Inmal, Lahura da su izaima ke nan, suka kama kalle-kalle da waigc-waige ke nan domin sun san cewa ko aikin kirga Dakarun aka basu ba karamin jidali bane bare ace yaki za su yi da su. Wannan shi ne abinda ya faru a can sabuwar fadarSarauniya Abidatul Azmal bayan su sadauki Kurbas sun sami nasarar dauko jikokinsa su Izaima wadanda AbidatulAzmal tayi garkuwa da su. * * A L'AMARIN GIMBIYA Abidatul Azmal kuwa, lokacin da ta zama wannan katon tsuntsu ta fice daga cikin fadar ta luluka a cikin gajimare sai ta wanzu tana mai tsala matsanaicin gudu a sararin samaniya domin ta isa can birnin Nurul Kalbi a cikin Kankanin lokaci ta tarwatsa birnin gaba daya ta kashe duk wani mahaluki dake cikinsa sannan ta kamo Maharaz da hannunta a raye don ta kaishi can sabuwar fadarta inda za ta yiwa mutanensa kisan gilla a gabansa. Haka dai Abidatul Azmal ta wanzu tana ta tafiya harta shafe sa'a hudu. Kwatsam! ba zato ba tsammani sai ta hango wani farin aljani daga can nesa ya durfafota yanadauke da wani bil'adama a zaune bisa kansa ya rufefuskarsa da farin rawani, idanunsa kadai ake gani, kuma 17 Taskar Tsafi = 5 Kin Gini gaba dayan tufafin da ke jikinsa farare ne kuma ya rala wata zabgegiyar takobi a bayansa iska na ta kada komaj jikinsa. Koda ganin wannan aljani da mahayinsa sai Abida Azmal ta cika da tsananin mamakin kuma taji zuciyarıa dan buga da karfi saboda ko kadan ba ta ga wannan alja da mahayinśa a binciken da tayi na tsawon kwana bakw cikin halwar tsafinta ba. Kallo daya ta yiwa aljanin da mahayinsa ta gane c ma'abota addinin Musulunci ne saboda ganin irin yana kalar tufafin da ke jikinsu don haka ta tabbatar da abokan gabatarta ne. Tambayar da Abidatul Azmal ta yiwas kanta ita c "Anya kuwa wannan mutum ba Sarki Maharaz ban Ai kuwa idan shi ne a yau ne zan zare masa rub numfashi, sannan na karasa birnin nasu na baje koma kowa ba sai ma na kamashi na koma da shi fadata ba." Ya yin da ya rage saura bai fi kamu goma ba tsakan Abidatul Azmal wacce ta kasance a cikin siffar Kat tsuntsu da kuma wannan farin aljani sai duk su biyun su tsaya cak a cikin iska aka fara kallon-kallo. Nan ta Abidatul Azmal ta rikide izuwa ainahin kamanninta sanD ta dubi wannan farin aljani ta daka masa tsawa ta c "Wane ne kai? Kuma wane ne wannan bil'adama wand kake dauke da shi? Ka hanzarta amsa mini wanna! tambaya tawa ko kuwa yanzun nan na hallaka ka kai Ubangidan naka". ال murmushi Lokacin da farin aljanin ya ji wannan batu sai yay sannan ya murtuke fuska ya ce, "Ya ke wannan shaidaniyar Sarauniya, ki yi sani cewa wannan ubangidan 18 a nawa ruwane mai kashe dukkan gobara, kuma shi ne bakin takobi mai raba masöya. Shiine mai kawar da zálunci ya shimfida adalei,kuma shime dodon dukkanikafiran daiké wannan &inahiyansIna maiilisanar sdard kewidewa komai sammakonki shiia tafeyakerdomin Ubangijinsa ya sanar da shi dukkan shirinkisd dsllA ainisi sb swoo sb ilin вisррв Alhalin iyanzu kin boyewadansu Musulmioa can sabuwar fadarkiu dan ke dajin Shalfur, kumaikina kan hanyarki ne ta zuwa birnin Nurul Kalbi domin ki je kisbaje birnin ki kashe mutanen garin kúma ki kamo Sarkinsu a hannu a raye.T"0 t IamNA lutsbidA swoduх вy оvяwsr a Kodamaljanin ya zo nanua jawabinsa sai Abidatul Azmal ta lari numfashinsá tana mai Kara daka masa tsawa ta ce, "Ban tambayeka dogon labari ba, kawai so nake ka gabatari da kankadda kuma wandaskake daukebdasshisa garenilA x s msb imez sn syad s on ina snioiвв aikio Kafimaljanin ya buđerbaki ya cé wani abu sai jarumin daakeskan aljanin ya yayesrawanin das ya rufe fuskarsa da shi, fuskarsa ta bayyana afilizad o2 ida awoo sb lub snisT sb sXKodá Abidatul Azmalrta ga ko waye sai ta cika da tsananin mamaki/ Ba wani bane face Sarki Maharazlouoned idIB Sarki Maharaz ya dubiigimbiya Abidatul Azmal fuskarsa a murtuke babu annuri ko kadan yai ce,u"Ya ke wannansabokiyar gaba, kiyi sani cewanyau na fito ne dà fishina bisa dogaro da Ubangijina. Kosdai ki tuba ki karbi addinina ko kuma na hallakaki domin kece kadai yanzu kika zame mana matsala a wannan nahiya tamu domin gaba dayan kafiran aljanu ma isun saduda tunda an gwada 'yar káshi musidairsulesun ganes kurensu.s Da yawansulosun musulunta wasu kun sun yi hijara sun bar nahiyar ma gaba 50 19 daya. Ki sani cewa a dalilinki mun yi asarar dubunnan rayuka da dukiyoyi babu adadi. Lallai tsakaninmu da ke babu ga maciji. Ubangijina ya nuna mini duk irin makircım da kike kullawa, hatta mahaifiyata da jama'ata da kika sa aka kullesu a cikin kurkuku na gani a cikin barcina. ina tabbatar miki da cewa da izinin Allah baki isa ki cutar da su ba. Ko yanzu na ci babbar riba akanki tunda na shiga har cikin birninki na ci da yaki kuma na musuluntar da dukkan jama'arki." Sa'adda Sarki Maharaz ya zo nan a zancensa Sai hawaye ya zubowa Abidatul Azmal ta ce, "Tabbas ka das mini mugun bakin cikin zuciya wanda har na mutu ba zau manta da shi ba. A dalilin haka ne na rasa mahaifin mulkina, jama'ata da kasata. Kai ne mutumin da ya lalaia darajata da kimata a wannan nahiya. Babba bakin cikina da takaicina shi ne a baya na sami damar da zan hallakaka, amma sai na fasa saboda sharrin darsuwar sonka a cikin zuciyata. Tabbas na yi nadamar kamuwa da kaunarka a raina duk da cewa shi So barawo ne dare daya yake sace mutum. A yau ina mai battar maka da cewa zan kasheka da hannuna duk da cewa ina sonka a raina kuma na sani cewa a halin yanzu ka baro amaryarka a can birnin Nurul Kalbı tana zaune ta zuba ido ta ga komawarka. Bayan na kasheka itama zan je na kamata na kaita can kurkukuna inda za ta ci gaba da rayuwar bakin ciki a matsayin bazawara har sa wahala ka da bakin ciki sun zamo sanadin ajalinki. Yanzu sai shirya gani nan bisa kanka". Koda gama fadin haka sai Abidatul Azmal ta zare takobinta ta afkawa Sarki Maharaz da aljanin da ke daukc Taskar Tsafi 5 Madakin Gini da shi. Cikin bakin zafin nama Maharaz ya zare takobinsaya tareta suka kacame da azababben yaki. taAbidatul Azmal ta wanzu tana mai kai musu wannan sara da suka cikin mugun karfi na ban mamaki wanda kai cewa shi kansa Sarki Maharaz da kyar yake iya kareharin nata, shi kuwa aljanin da ke dauke da shi ya ma kasakare harin, a cikin dakika goma ta dankara masa kyawawansara uku a jikinsa ya shiga mugun hali ya shiga mugun haliya rinka tambal-tambal a sama zaj hantsilar da Maharaz su rikito kasa tare. Babban abinda ya daurewa Maharaz kaishi ne ya ya aka yi Abidatul Azmal ta sami wannan sabongagarumin. karfi haka aljalin a sanin da ya yi da karfinsuyazo daya shi da ita. Lokacin da Maharaz ya ga sun fara tambal-tambal a sama za su rikito kasa su hallaka shi da aljanin da ke dauke da shi sai ya fara karanta addu'o'i a cikin zuciyarsa yana mai neman taimakon Allah. Ana cikin haka ne Abidatul Azmal ta sokawa farinaljanin takobi a ciki. Nan take yai kalmar shahada ya sakifuka-fukansa ya sullamo kasa a lokacin da yai shahada. Cikin hanzari Maharaz ya daka tsalle sama daga kanaljanin kawai sai ya tsinci kansa a tsaye cikin iska tamkar yana da fuka-fuki kai ka ce tsuntsu ne. Shi kansa ya san cewa kawai Yardar Allah ce. Itama Abidatul Azmal sai tacika da tsananin mamaki da ta ga Maharaz ya tsaya a sama cikin iska domin duk irin gumurzun da suka yi a baya shida ita ba ta taba ganin ya yi irin wannan bajinta ba.Cikin tsananin fishi da Kunan rai ta sake afka masa suka cigaba da sabon dauki ba dadi a cikin gajimare. Wannan karon sai fadan ya sauya yanayi domin karfi ya sake zama 21 Taskar Tsafi = 5 Madakin Gini daya, suka ci gaba da kaiwa juna sara da suka cikin bakin zafin nama Duk sa'adda takubbansu suka hadu sai dai ka ga tartsatsip wuta yana tashi. Tsawon dakiku masu yawa suna ta wannan gumurzu dayansu bai sami nasarar komai ba. Koda ganin haka sai Abidatul Azmal ta ja da baya ta tsaya cak cikin iska, kawai sai ta saki takobinta ta sallamo Kasa sannan ta dunkule hannayenta ta ce, "Tunda mun kasa cuta da juna da makami ai sia mu gwada 'yar kashi ko?" Kasa. Da jin haka sai shima Maharaz ya saki takobinsa ta Tabbas rashin sani ya li dare duhu! Inda Maharaz san abinda zai biyo baya da ba zai saki takobin sa he domin Abidatul Azınal yaudararsa layi. Koda ta ga ya saki takobinsa sai tayi wuf ta day rigarta ta zaro wadansu masifafTun wukake guda b masu tsananin KAIFI DA TSINI. Kafin Maharaz ya ankara tuni ta caka masa wukak a kirjinsa hagu da dama, wukaken suka nutse, Maharaz ba san sa'adda ya kwallah ihu ba a lokacin da jini ya fara kwararowa daga jikinsa. Kafin Abidatul Azmal ta zare wukar tuni ya dok Kirjinta da kafarsa guda da karfin gaske. Tamkar an bug tamaula haka ta cilla da baya a sama cikin iska tay katantanwa kuma tayi kumallon jini. Har Maharaz ya yi nufin ya zare wadannan wukake guda biyu daga cikin kirjinsa sai ya fasa domin tsananın zogin da yake ji, kuma ya fahimci cewa idan ya zare sun ba karamin jini. ne zai fita daga jikinsa ba wanda zai iya janyo sanadin ajalinsa cikin kankanin lokaci saboda haka sa 22 Taskar Tsafi = 5 Madakin Gini shima ya dunkule hannayensa da kyar kamar ma ba zai iya ci gaba da fada ba. Itama Abidatul Azmal a wannan lokaci tana cikin wani irin mugun hali na galabaita sakamakon mummunan dukan da Maharaz ya yi ma ta a kirji har idanunta na lumshewa, shi kuwa Maharaz dishi-dishi ma yake gani har jiri ya fara dibarsa kawai tsananin juriya da jarumtaka ne suka sa har yanzu bai sare ba. Nan take Abidatul Azmal ta dawo cikin haiyacinta sosai kawai sai ta share jinin da ke bakinta ta tuntsure da dariya sannan ta nuna Maharaz da dan yatsanta guda ta се, "Na gama da kai ya kai masoyin raina, kuma babban abokin gabata, domin babu yadda za a yi ka tsira daga sharrin dafin da ke jikin wadannan wukake nawa. Da zarar ka zare daya daga cikin wukaken daga kirjinka gudan jini zai yi fitar burgu kuma take za ka mutu. Idan kuma ka ki zare wukar a hankali dafin da ya shigeka zai ratsa dukkan jinin jikinka." Cikin karfin hali Maharaz ya tari numfashin Abidatul Azmal ya daka ma ta tsawa ya ce, "Ya ke wannan jahila kuma batacciya, ki yi sani cewa babu mai kashewa da rayawa face Allah. Wannan dafi na jikin wukakenki bai isa ya kasheni ba face da yardar Ubangijina". Kafin Maharaz ya gama rufe bakinsa tuni Abidatul Azmal ta sake afka masa tana mai kai masa naushi da bugu cikin bakin zafin nama kuma tana kaiwa wukakenta cafka domin ta zaresu daga cikin kirjinsa. Duk da cewa Maharaz yana cikin matukar galabaita kuma dafi na kara shiga jikinsa sai ya rinka tare hare-haren 23 Taskar nata kuma ya hanata samun damar zare wuka daya daga cikin guda biyun. iaSai da suka shafe rabin sa'a cur! suna wannan artabu a sannan ne Maharaz ya sake galabaita ainun, ya zamana cewa idanunsa sun fara lumshewa, ya fara gani dishi-dishi kuma Abidatul Azmal ta fara samun nasarar gabza masa naushi a fuska. Nan da nan fuskarsa ta kumbura, ko ina jini ya duru. Koda Maharaz ya ga ya galabaita ainun, kuma ya labbatar da cewa Abidatul Azmal za ta iya samun nasarar hallakashi a ko yaushe sai ya fara kiran sunayen Allah Tsarkaka a cikin zuciyarsa yana mai neman taimakonsa. gsbFaruwar hakan, ke da wuya sai yaji wani irin gagarumin karfi ya shigeshi. Nan take ya rinka jerawa Abidatul Azmal naushi a fuskarta, kirjinta da cikinta, Nan da nan itama fuskarta la kumbura, jini ya rinka fita daga hancinta da bakinta. Cikin kankanin lokaci ta fita daga haiyacinta, kawai sai ta suma ta sallamo izuwa kasa za ta hallaka. Cikin zafin nama Maharaz ya cafota ya rungumeta da hannayensa biyu sai gashi suna saukowa kasa, a hankali daga can kololuwar sama tamkar yana da fuka-fukai a jikinsa. Yana cikin haka ne ya dubi fuskar Abidatul Azmal ya ga yadda ta kumbura tayi kaca-kaca da jini ba kyan gani sai yaji mamaki ya kamu da tausayinta. Al'amarin da ya matukar bashi babbar abokiyar ke nan, ya ce a ransa, "Saboda me zan ji tausayin gabata wacce take son ta hallakani? gashi ta caka Yanzu mini wadannan wukake masu dafi ina ji a 24 Taskar Tsafi =5 MadakinGmina? по в комка ку о906W NETSIM nidodel Eb коткNan take Maharaz yy yanke hök uney deikm nelursaoWardaararaaukd iurdewaAbidatulA/marwilya ldd ohin ya hie wanzdwartala uolon Rasd kumAMUsLARiA OS Kehaniy ar sdstm kwanciyarЧghn kc 929k s1 ilst 192 каinMahara ha dhike ua pmtiyd Nidaur Azmal akanhannayensa suna a aukowykasab Rdtaruhsd Basy" tabRasa Bayai tayaIBPIV tikaP'sadhul λευκοARARPNAEABA κu2ς oR19 Shifmidekaws Kays awa A dai-dai wannan lokaci ne adiút kadanukadanaishi res vkkU Banm Manarwandakeddrkashe bisa yiwoyinsa dgabanta 12 Abidatul Azmal taji kö fahnba aLEAPan Motact Hor hatash if shutagubawaa kasheta. Har Mahara Kama li a AP& WNsai kawai sai ya kasa. Kawai sai hawaye suka zubo masa yadubeta ya ce, "Ya ke abokiyar gaba kiyi sani cewa a iyatsawon rayowata d duniya ban taba kas ya mac ha haka kitan raakeyaken dalvathayr Cattai Kiwwba žan Tira Ba daga Kankn i amma kina braalbakhefh с y nnul & sbST BIUdDN BWiY BYkan Gama fadin hakan ke ddWüyRSA NANPAS YdUnodsnis sai yaji if уаmme. Aa tth kumadgttd lai sahm kwarin Jikahtl sabbaw25 Taskar Tsafi = 5 haka sai ta mike tsaye a fusace. Tana mikewa tsaye tayi arba da takobin Maharaz wacce ya saketa a can sama sa'adda suke gumurzu ta fado kasa. Cikin sauri Abidatul Azmal ta ruga ta dauko takobin ta dawo kan Maharaz ta raba kafafu a kansa. Kawai sai ta daga takobin sama da hannayenta biyu za ta caka a cikinsa. Bisa mamaki sai taji ta kasa caka masa ta tsaya cak kawai sai ta fashe da kuka ta koma gefe daya ta zauna tana tunani tana mai dada ci gaba da zubar da hawaye. Sai da ta shafe rabin sa'a guda cur! tana tunani da kuka kuma ta kasa yankewa kanta hukunci bisa abinda ya kamatra tayi a rayuwarta. Nan take Abidatul Azmal ta rikida ta zama wannan katon tsuntsu ta tashi sama ta luluka izuwa cikin gajimare ta bar Sarki Maharaz a wannan wuri a kwance babu abinda yake motsi a jikinsa tamkar gawa. Wannan shi ne abinda ya faru tsakanin gimbiya Abidatul Azmal da Sarki Maharaz bayan sun yi haduwar bazato a sararin samaniya sun fafata kazamin yaki. * L'AMARIN SU SADAUKI Kurbas kuwa, Alokacin da dakarun fadar gimbiya Abidatul Azmal suka yi musu kawanya ya zamana cewa sun firgita ainun da ganin yawan dakarun kuma sun tabbatar da cewa babu yadda za ayi su sami nasara akan Dakarun sai Kurbas ya yiwa Zuhura rada a kunne ya ce, "Bamu da mafita face taimakon Ubangijin Musulunci." Da jin haka sai Zuhura ta gyada kai itama tayi masa rada a kunne ta ce, "Tabbas zancenka dutse ne don haka ga 26 Taskar Tsafi = 5 Madakin Ginı addu'ar da ya kamata mu yi ta karantawa a zuciyarmu. Nan take ta rada masa addu'ar kuma ta radawa Hasilatul Kurbar ita ma sai ta radawa Inmal, shima ya radawa Lahura. Ya yin da Dakarun gidan suka ga su Kurbas suna yin rada a tsakaninsu sai suka bushe da mahaukaciyar dariya wadda sautinta ya cika dodon kunnen su Kurbas ya addabesu. Koda ganin haka sai Zuhura ta kwallah kabbara da karfi ta afkawa Dakarun ta' rinka saransu da sukarsu. Bisa mamaki sai ga ta tana daddatsa sassan jikinsu tamkar tana sassabe a gona. Ai kuwa sai Kubas, Hasilatul Kurbas, Inmal da Lahura ma suka yi koyi da ita, suka yi ta saran dakarun suna masu ci gaba da karanta wannan addu'a wacce Zuhura ta rada musu. Saboda tsananin yawan Dakarun su Kurbas basu gama kashe su ba gaba daya sai bayan sa'a bakwai. Tunda aka fara yakin Zuhura na goye da lzaima shi kuma Kurbas sai ya goya dan uwanta Uhairu. Har aka gama yakin daya daga cikin su Kurbas bai sami rauni ba, amma fa gaba dayansu sai suka zube Kasa suna haki saboda tsananin jigata. Bayan sun dan huta sai suka mike tsaye suka fice daga cikin fadar. Suna fita sai ginin fadar ya kama girgiza yana rugujewa kuma ya rinka nutsewa izuwa karkashin Kasa. Su Kurbas suka tsaya daga can nesa kadan suna kallon ikon Allah. Tabbas sun san cewa Allah ne Ya nutsar da wannan fada tunda wuri ne wanda ba a komai a cikinsa face sabon Allah da cutar da bayinSa. Taskar Tsafi = 5 Bayan gidan ya gama nutsewa sai Zuhura ta dubi. su Kurbas gaba dayansu ta ce, "Ai sai ku zo mu tafi izuwa gida can birnin Nurul Kalbi". Cikin tsananin mamaki su duka suka dubeta. Kurbas ya ce, "Ta ya ya zamu nufi birnin Nurul Kalbi a yanzu bayan daga nan zuwa can tafiya ce ta kwana da kwanaki masu yawa, kuma gashi bamu da abin hawa". Koda Zuhura taji wannan tambaya sai tayi murmushi ta ce, "Ubangijin da ya bamu nasara muka hallaka gaba dayan dakarun da ke cikin wannan gida shì ne zai kai mu birninmu a cikin kankanin lokaci. Abinda nake so da ku shi ne kawai ku biyoni a baya." Koda gama fadin haka sai Zuhura ta kama hanya ta nausa cikin daji. Ba tare da fargabar komai ba kuwa su Kurbas suka bita a baya da sauri su duka. L'AMARIN SARKI MAHARAZ kuwa, Alokacin da ya farfado daga dogon suman da ya yi sai ya tsinci kansa a cikin kwale-kwale a tsakiyar kogi. Kwale-kwalen na tafiya da kansa babu mai tukashi. Cikin firgici Maharaz yai sauri ya shafi kirjinsa sai ya ga sam babu wadannan wukake da gimbiya Abidatul Azmal ta caccaka masa kuma ko alamar rauni babu a kirjinsa a inda aka caka masa wukaken. 28 Madakin GiniAl'amarin da ya matukar bashi mamaki ke nan yamike zaune zumbur! yana hailala da godiya ga Allahda ya ga ya sami lafiya tamkar wani abu bai tabasamunsa ba. Kawai sai ya ji an yi masa sallama irin taaddinin Musulunci a bayansa. A firgice ya juya da sauri kawai sai ya yi arba dawani mutum tsoho tukuf wanda ke dauke da farindogon gemu, babu silin bakin gashi guda daya ajikinsa. Kallo daya za ka yi masa ka san cewa ya shamiya a duniya. Cikin tsananin tsoro Maharaz ya dubi tsohon yace, "Wane ne kai, kuma ya ya aka yi na zo nan, menene ya faru gareni?" Koda jin wadannan tambayoyi sai tsohon ya yimurmushi sannan ya ce, "Kwantar da hankalinka yakai Maharaz...Sunana Ansarul Mauruf." Koda jin haka sai shima Maharaz ya cika datsananin mamaki kawai sai ya rungume tsohon yanamai farin ciki ya ce, "Tabbas kafin rasuwar mahaifinaya bani labarinka kuma ya tabbatar mini da cewa kafinna bar duniya sai ka ziyarceni. Kai kuwa ina ka shiga aduniyar nan a tsawon wadannan shekaru da ka dainahidima ga mahaifina?" Ansarul Mauruf ya yi murmushi ya ce, "Ya kaiMaharaz ka yi sani cewa yau shekarata dubu arba'inina rayuwa a wannan duniya kuma na shekara sittin dabiyar kacal ina hidima a gidajen manyan sarakunan29 MadakiIN G Taskar Tsafi = 5 musulunci. Mahaifinka shi ne Sarki na karshe wanda na yiwa hidima kuma na rabu da shi ne domin na tafi yawon yada addinin Allah da JIHADI na yake-yake. Na ziyarci nahiyoyi dubu saba'in da bakwai kuma na yi yaki sau dubu goma sha daya da dari biyar kuma babu wanda ban sami nasara ba na akwar da kafirci. Akan hanyar dawowata ne na tsinceka a kwance cikin daji magashiyan tamkar ka mutu an soke ka da wukake guda biyu a kirji masu mugun dafi. Sai da na karanta addu'a ta musamman sannan na zare wadannan wukake daga kirjinka. Nan take raunikan suka warke kuma jini bai zuba ba koda digo. Wannan duk iko ne na Allah ba wai dabarar mu ba. A haka yanzu abokiyar gabarka gimbiya Abidatul Azmal ta sauka a birnin Nurul Kalbi amma ba ta kashe kowa ba, sai dai ta ritsa matarka tana jiran ka koma gida ta kasheta a gabanka. Babu abinda zamu iya yi bisa wannan al'amari face addu'a. Da izinin Allah za mu isa birnin Nurul Kalbi a cikin kankanin lokaci". Koda gama fadin haka sai tsoho Ansarul Mauruf ya shafi Maharaz da hannunsa nan take barci ya kwashe shi. Maharaz bai farka ba sai a cikin birnin Nurul Kalbi kuma a cikin turakarsa akan kujera. Yana bude ido igiya ya tamau yi arba tana da kuka. matarsa Salsirat daure akan gado da ini askаi Madakin Gini Gimbiya Abidatul Azmal ta dora takobinta akan uls vuyanta kuma ta kura masa idany tana mai zub da iemhawayfoYsYi sb Cikin tsananin razana Maharaz ya durkusa bisa guiwoyinsa ya shiga rokon gimbiya Abidatul, Azmal luteyane mai ccwa, "Kada ki kashe mini matata domin Bgibala yi miki laifin komai ba. Na rokcki da ki kasheni a majinakonta ita ki kyalcta". Gimbiya Abidatul Azınal tayi shisshikar kuka slusannanata cc, "Ya kai masoyina ka. tuna ccwa a dalilinka na rasa ubana, mulkina, kasata da jama ata. в ваня Babu Pa wani abu da zan yi maka domin na dauki TRT fansa face na kashe wannan mata taka domin yanzu ne kake son ka fara sabuwar rayuwa mafi dadi a duniya Blare da sita kuma ka san cewa nima ina matukar Kuanarka amma ba zan iya zama abokiyar rayuwarkа ba a matsayinka na babban abokin gabatala s s Koda gama fadin haka sai Sarki Maharaz ya eed fashe da matsanaicin kuka sannan ya cc, "Na ji ba zan iya hanaki abinda kike son aikatawa ba amma ki sani CIASI cewa idan kika kashe matata ba ki yi mini adalci ba tunda ni ban kashe miki miji ba abokin rayuwar da bayan iyaye sai shi." Rsтaрej ilar Koda jin wannan batu sai Abidatul Azmal ta fashe da matsanaicin kuka sannan ta ce, "Ya kai wannan Sarki kayi sani cewa taboas a yanzu na gamsu cewa addininku shi ne addinin gaskiya tunda na ga 1 Taskar Tsafi = 5 Madakin Gini zahiri da idanuna, wato tsafina ya kasa tasiri a kanku. Abin kunya ne a gareni na karbi wannan addini naku na yi watsi da wanda na gada a wajen iyayena. Ina mai yi muku fatan alkairi da jin dadin rayuwa kai da matarka". Koda gama fadin haka sai gimbiya Abidatul Azmal ta cire kaifin takobin da ke hannunta daga wuyan Salsirat sannan ta cakawa kanta takobin. Nan take ta sulale kasa matacciya. Ita kanta Salsirat sai da ta fashe da kuka sakamakon kamuwa da tausayin gimbiya Abidatul Azmal da kuma Sarki Mabaraz wanda ya durkusa gaban gawar gimbiya Abidatul Azmal yana ta sharar hawaye. a Wannan shi ne yadda karshen kafirci ya zo a nahiyar da birnin Nurul Kalbi yake. Kuma sannan ne musulunci ya yadu a ko ina. Sarki Maharaz ya ci gaba da mulki tare da matarsa mahaifiyarsa kuwa ta auri Sadauki Kurbas suka ci gaba da rayuwar Musulunci cikin kwanciyar hankali. Alhamdulillah. Karshe!. Daga mai debe muku kewa a kullum da ko yaushe. ABDUL'AZIZ SANI M/GINI. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is

Chapter 2 of 3