Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 2
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels Taskar Tsati A magd sant Slevti sale ABDULAZIZ SANI MYGINI Taskar Tsafi-4 > Madokin Gin TASKAR TSAFI-4 lOKACIN DA SARAUNIYA Abidatul Azmal Lta shige izuwa cikin karkashin kasa tare da su Izaima ta face bat ya zamana cewa hankalin su Sarki Maharaz ya dugunzuma ainun sun rasa abinda za su yi, sai dukkaninsu suka yi zugum-zugum suka yi shiru suna tunani her izuwa lokaci mai tsawo dayansu bai ce uffan ba. Sarki Maharaz ya dubi gawarwakin jama'arsu musulmi maza da mata, yara da kanana, sai takaici ya kainashi, bai san sa'adda hawaye ya zubo masa ba. A sannan ne ya ji ya tsani Sarauniya Abidatul Azmal fiye da komai a duniya saboda ita ce dalilin wannan asara da aka yi ta dubunnan daruruwan rayuka. Maharaz ya dubi Hasilatul Kurbas, Kurbas, gimbiya Zuhura, Himal da Lahira ya ga suma gaba dayansu duk kuka suke yi, sai zuciyarsa ta sake sosuwa ya ci gaba da zubar da hawaye cikin matsanaicin bakin ciki. Daga can sai gimbiya Zuhura tasa hannu ta share hawayenta sannan ta taso daga inda take zaune ta dawo daf da Sarki Maharaz ta zauna tana mai dafa kafadarsa suka dubi juna ta ce, "Ya kai dana ka kasance mai kwarin zuciya, domin bai kamata ace jarumi kamarka ba yana zubar da hawaye". Koda Sarki Maharaz yaji wannan batu na mahaifiyarsa sai ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Ya ke Ummina kiyi sani cewa ba komai bane ya sa ni zubar da 3 Taskar Tsafi-4 > Madakin Gini wannan hawaye ba face ganin yadda aka karar da dukkan jama'armu yanzu shi ke nan birninmu na Nurul Kalbi ya zama kango, tunda iya mu din nan ne kawai muka rage." Da jin haka sai Zuhura tayi murmushi ta ce, "Waye ya gaya maka jama'armu sun kare? Biyoni a baya ka ga ikon Allah". Koda gama fadin haka sai Zuhura ta mike tsaye ta nufi bayan karagar mulki da ke cikin fadar. Maharaz da su Kurbaz suka mike gaba dayansu suka bita cikin mamaki. Da isar Zuhura bayan rusasshiyar karagar sai tasa kafarta ta doki karagar. Nan take karagar ta balle kuma ta fadi can gefe daya, sai ga wani wakeken rami a wajen. A cikin ramin matane, yara da tsofaffi jingim sama da mutum dubu ashirin a zazzaune suna ta karanta addu'o'i. Koda ganin wadannan jama'a sai mamaki da farin ciki ya turnuke su Sarki Maharaz. Maharaz ya dubi gimbiya Zuhura ya ce, "Ya ke Ummina ya ya aka yi kika boye wannan jama'a a wannan rami a lokacin da ake ta wannan azababben yaki? Zuhura ta sake yin murmushi a karo na biyu ta се, "Nima ba dabarata ba ce, taimakone kawai daga Allah". Koda jin haka sai Maharaz ya daga kansa sama ya yi godiya ga Allah. Nan take suka kama fito da wadannan mutane daga cikin ramin har aka gama fito da kowa. A sannan ne su Tashar Tsafi-4 Madabin Glni Maharaz suka zauna suna sa magani a jikin raunikan jikinsu. Bayan kowa ya gama kintsawa sai Zuhura ta dubi Marahaz ta ce, "Ya kai dana yanzu mene ne abin yi? Wane irin mataki ya kamata mu dauka ne akan wannan babbar mikiyiya tamu? Ni abinda ya fi tayar mini da hankali ma shi ne, wadanann yara su Izaima da tayi garkuwa da su." Ya yin da Sarki Maharaz yaji wannan batu sai jikinsa ya yi sanyi ya dubi Zuhura cikin alamun damuwa ya ce, "Ya ke Ummina kiyi sani cewa duk abinda ke cikin zuciyarki shi ne a nawa. A cikin kowacce dakika guda zuciyata ta kan buga da karfi sakamakon tsoron irin tuggun da gimbiya Abidatul Azmal za ta iya kulla mana a yanzu. BAbban tashin hankalina shi ne a halin yanzu bamu san ma anda ta tafi ba da wadannan yara kuma a koyaushe za ta iya kawo mana harin sumame, haka kuma na tabbatar da cewa yanzu ba karamin gagarumin shiri za ta je ta yi ba a kanmu. Ni dai abinda na yi shawara yanzu shi ne mu tattara mu koma can birninmu na Nurul Kalbi, idan muka nutsu sai mu ci gaba da shiryc-shiryen ci gaba da yaki da wannan azzaluma, amma yanzu tunda Allah Ya sa mun ci wannan birni na ta da yaki, ba zamu barshi haka ba, zamu kafa daular Musulunci in ya so sai mu sa wakili wanda zan shugabanci birnin". Koda jin wannan batu sai Zuhura ta dubi Maharaz cikin tsananin fargaba ta ce, "Yanzu kai a tunaninka wa kake zaton daga cikinmu zai iya karbar wannan wakilci 5 Taskar Tsafi-4 => Madakin ba Gini Abidatul tare da yaji tsoron komai ba tunda a koyaushe Azmal za ta iya kawo ziyarar bazata?" suka Kafin ga Maharaz ya budi baki. ya ce wani abu sai gidajensu mutanen garin sun fara firfitowa daga cikin suna tahowa gaban wannan rusasshiyar Abidatul fada ta Azmal. Kafin wani lokaci mai tsawo gaba daya mutanen birnin sun taru a gaban su Sarki Maharaz sun yi jugum- jugum, kallo daya za ka yiwa wannan jama'a ka fuskanci cewa assirye suke su mika wuya. Hakika mutanen birnin sun yi matukar mamaki bisa ganin yadda akazo a ka ci gimbiya Abidatul Azmal da yaki har fadarta. Al'amarin da ko a mafarki ba su taba zatonsa ba. Koda yake wasu daga cikin mutanen birnin a firgice suke saboda sanin cewa har yanzu fa akwai sauran rina a kaba, tunda ba a kashe Abidatul Azmal ba, amma kuma ganin ta tsere daga yakin yasa jikinsu ya yi sanyi. Lokacin da Sarki Maharaz ya ga jama'ar birnin sun gama taruwa a gabansa mazansu da matansu yara da manya, sai ya hau kan wani dogon mumbari ya fuskancesu ya ce, "Ya ku jama'ar wannan birni kun yi sani cewa tsawon shekara da shekaru Sarkinku da 'yarsa suna yi muku mulkin kama karya, wato mulki na zalunci, wanda babu mai jin dadinsa face ya kasance Basarake, ko attajiri na jikin Sarki. Ku sani cewa Sarkinku ya kasance gagarumin matsafi, kuma 'yarsa Abidatul Azmal 6 Taskar Tsafi-4 => Madakin Gini ta kasance mashahuriyar BASADAUKIYA, wacce babu kamarta a wannan nahiya gaba daya. Yanzu gashi an wayi gari mu ma'abota addinin Musulunci mun sami nasarar yaki akansu, karfin tsafinsu da jarumtakarsu basu basu nasara ba. Ina so ku sani cewa ba komai ne ya bamu wannan nasara a kansu ba face taimakon Ubangijinmu wanda shi ne Ubangijin da ya halicci sammai da kassai da duk abinda ke cikinsu. Duk wani abu da kuke bautawa cabaninsa ba gaskiya bane. Ina kira a gareku da ku beyar da gaskiya ga Ubangijina nayi muku alkawari za ku zauna a rayuwa irin wacce da talaka da Basarake duk daya ne, babu sauran zalunci, babu ha'inci sai karamci da kaunar juna tare da zaman lafiya, wato lislama." Koda Sarki Maharaz yazo nan a zancensa sai gaba dayan mutanen garin suka durkusa kasa bisa guiwoyinsu suna masu nuna mubaya'a a gareshi. Koda ganin haka sia farin ciki ya lullube Maharaz da su Kurbas. Maharaz ya dubi jama'ar birnin cikin murna ya ce, "Ku mike tsaye ai bani za ku durkusawa ba. Abinda na kę so da ku yanzu shi ne, ku karbi addinina. Saboda haka yanzu zan biya muku kalmar shahada don haka sai ku biyata bayan na furta." Nan take Sarki Maharaz ya biya kalmar shahada, ai kuwa sai gaba dayan mutanen birnin suka amsa da muryoyinsu a lokaci guda. Muryoyin kuwa suka cika birnin gaba daya da amsa kuwwa har izuwa cikin 7 Taskar Tsafi-4 => Madakin Gini dazuzzuka. Al'amarin da ya kara jefa su Sarki Maharaz cikin matukar farin ciki ke nan. Sarki Maharaz ya ci gaba da bayani yana mai cewa zan zauna tare da ku a cikin wannan birni har izuwa lokaci mai tsawo domin na baku kariya da taimakon Allah bisa sharrin Abidatul Azmal kuma zamu koyar da ku addinin Allah." Koda jin haka sai farin ciki ya lullube gaba dayan jama'ar birnin suka sami nutsuwa a cikin zukatansu. A wannan lokaci ne Sarki Maharaz ya sauko daga kan mumbarin da yake jawabi kawai sai ya ga Hasilatul Kurbar, Himal da Kurbas sun taho gareshi fuskokinsu cike da alamun firgici. Da isowarsu daf da shi sai Kurbas ya dubeshi ya ce, "Ya kai wannan Sarki mai daraja yanzu ke nan kana nufin anan zamu barka mu mu tafi can birnin Nurul Kalbi? Ka sani cewa muna cikin fargaba bisa sharrin Abidatul Azmal kuma muna cikin tashin hankalin bisa halin da jikokina ke ciki, wato su Izaima wadanda ke can hannun Abidatul Azmal." Sa'adda Sarki Maharaz yaji wannan batu sai ya yi murmushi sanann ya ce, "Ya kai wannan sadauki ina so ku sani cewa wanda duk ya dogara da Allah to fa Allahzai iya masa duk abinda ya gagareshi. Ku fa tuni hasken imani ya ratsa jikinku su kuwa jama'ar wannan gariyanzu ne za su san Allah. Tun da har mun sami nasara shigar da su cikin addinin Allah bai kama ta mu yi nisa da su ba kuma suna bukatar kariyarmu. Idan ban zaunatare da su ba, Abidatul Azmal za ta iya dawowa a ko8 Taskar Tsafi-4 => Madakin Gini yaushe ta dada kafirtar da su. Yanzu abin da nake so da ku shi ne, ku yi shiri tare da sauran jama'armu ku tafi izuwa can birninmu na Nurul Karbi domin a dada raya birnin. Abu daya za ku ruke ku sami kariya daga sharrin abokan gaba, wato addu'a. Lallai ku lizamci addu'ar neman tsari tun akan hanyarku har ku isa can, bayan kun shiga birnin ma ku ci gaba da addu'ar kada ku sassauta dare da rana. Albarkacin wanda aka yi duniya da lahira dominsa babu abinda zai sameku. Ina son ku bani kwana talatin kacal, wannan lokaci zai isheni na koyar da jama'ar wannan birni addinin Allah kuma zan ci gaba da yin istahara domin Allah Ya nuna mini irin shiryeshiryen da Abidatul Azmal ke yi a kanmu domin mu san matakin da zamu dauka a kanta. Ya yin da Sarki Maharaz yazo nan a zancensa sai hankalin su Kurbas ya kwanta suka sami nutsuwa. Nan take suka kama shirye-shiryen tafiya. Wasu daga cikin attajiran birnin kuwa suka shiga kawo musu gudunmawa ta ababan hawa da guzuri mai yawa har su Kasim suka yi mamakin irin wannan karamci. Daga cikin attajiran da suka kawo gudunmawar mafi tsoka akwai wanda ake kira Suhairu ibini Marwasi. Attajiri Suhairu ya kasance mutum mai tausayi da jin kai kuma gaba daya mutanen birnin suna girmamashi şaboda kyawawan halayensa. Tsananin hakurinsa ne yasa mahaifin Abidatul Azma! yake saurara masa. Da yake Allah ya yiwa Suhairu karfin arziki duk abind 9 Taskar Tsafi-4 -> Madakin Gini Sarki yabukata a wajensa yana bayarwa bai taba musu ba, kuma yana matukar biyayya a gareshi Bayan su Kurbas sun gama shirein tafiya sai attajin Suhairu ya zo wajen Sarki Maharaz ya се, " shugabana ina neman alfarma guda daya a wajenka. Ina son na saukeka a gidana tunda dai yanzu an rushe wannan gidan sarauta na Abidatul Azmal babu inda za ka zauna". Koda fadin haka sai sauran attajiran garin suka taso suna cewa suma za su bawa Maharaz masauki. Maharaz ya dubesu ya ce, "Ai wanda ya fara bani masauki wajensa zan je". Koda jin haka sai farin ciki ya lullube attajiri Suhairu. Ba tare da bata lokaci ba Sarki Maharaz ya je wajen Zuhura domin su yi sallama, sai ya ga idanunta sun ciko da kwalla, al'amarin da ya dugunzuma hankalinsa ce, "Ya ke nan ya dubeta cikin tsananin damuwa ya ke Ummina ina dalilin cikar kwalla a idanunki?" subuto Sa'adda Zuhura taji wannan tambaya sai hawaye ya ma ta sannan ta ce, "Ya kai dana ka yi sani cewa kaine sai kai, kadai gashi abinda har ya rage mini a duniya, bani da kowa ganin jikina. yanzu ka ki ka yi aure bare na sa ran Haka kuma kullum rayuwarka hadari take, a ko a cikin yaushe za ka iya rasa rayuwarka. mai rokonka Ina da ka nemi budurwa ta gari ka yi aure a cikin wannan shi ne mu birni, domin ka cika mini burina. Fatana bar irin zuri'armu a doron kasa kafin cikar ajalinmu". 10 Taskar Tsafi-4 => Madakin Gini Ya yin da Zuhura ta zo nan a zancenta sai tausayinta ya turnuke Sarki Maharaz har hawaye ya zubo masa, kawai sai ya rungumeta ya ce, "Ya ke Ummina kiyi sani cewa a nalin yanzu babu wata tsayayyiyar mace a zuciyata, amma zan yi kokari na bi umarninki don haka sai ki tayani da addu'ar Allah ya hadani da wadda za ta dace da ni. laka kuma nima ina neman alfarma guda daya a wajenki". Cikin matukar mamaki Zuhura ta dubi Maharaz ta ce, "Kai kuwa wacce irin alfarma kake son nayi maka?" Maharaz ya sunkui da kansa kas ya ce, "Ya ke Ummina ina son ki sani cewa har yanzu shekarunki basu wuce na yin aure ba, saboda haka ina shawartarki da kiyi aure domin shi ne mutuncin 'ya mace, kuma samun cikar darajarta. Idan za ki bi shawarata, me zai hana ki auri Kurbas?. Koda jin wannan, batu sai mamaki ya kama Zuhura ta ce, "Me yasa kake mini sha'awar auren Kurbas?". Maharaz ya yi murmushi ya ce, "Ai ido ba mudu bane, amma ya san kima. Tuntuni na lura da wadansu al'amura da ke wakana tsakaninki da shi, zan so ace Kurbas ya zamo mahaifina na biyu a rayuwa". Da jin haka sai Zuhura ta yi murmushi sannan ta janye jikinta daga cikin na Maharaz ta dubeshi cikin fara'a ta ce, "Sai ka tayani da addu'a Allah Ya zaba mini abinda ya fi alkairi". Maharaz ya ce, "Amin". 11 Taskar Tsaofi-4 >Madahin G Nan take su Zuhura suka hau dawakansu suk bankwana da Sarki Maharaz suka kama hanya don fita d cıkin brinin. Himal da Lahura ne akan gaba bisd dawakansu a je sannan Zuhura da Kurbas, sai sauran mutanen birnin Nur Kalbi wadanda suka yi saura a yakin 'da aka fafata Sarki Maharaz da sauran jama'a kuwa, suka bisu kallo har suka fita daga cikin birnin, suka yi nisa har suk bace musu da gani. Faruwar hakan ke da wuya sai Attaji Suhairu ya kama hannun Sarki Maharaz ya jashilsuka taf izuwa gidansa. A sannan ne jama'a suka watse suka kam komawa gidajensuode dsnsy tod awao insa b пог в Sius Wannan shi ne abinda ya faru a birnib Sarauniy Abidatul Azmal bayan an fafata kazamin yaki anci garin da yaki, wato Musulmai sun sami nasara bl erIBİEZRD st Bd aut ay Aволв ве sisd nsanew gii sho переез SAndaM AL'AMARIN SARAUNIYA Abidatul Azmal DRE RY kuwa, lokacin da ta nutse izuwa karkashin avkasa dauke da Izaima, Uhairu yayan Himal, sai tsulum! ta baiyana a cikin wani makeken daji a gaban wani katon tsauni. Take Sarauniya Abidatul Azmal ta shafi tsaunin da hannunta na hagu sai ga wata kofa ta zinare ta abaiyana a jikin tsaunin. Sarauniya Abidatul Azmal tasa hannu ta bude kofar ta kunna kai ciki, sai ga ta a cikin wata luntsumemiyar fada wadda aka Kawatata da dukkan kayan kawa da kayan jin dadin rayuwar duniya. Fadar a cike take da kuyangi da bayi masu hidima, kuma dukkaninsu mutane ne babu aljan ko guda daya. 12 Taskar Tsafi-4 => Madakin Gini Koda wadannan hadimai suka ga shigowar gimbiya Abidatul Azmal dauke da yara guda biyu, sai suka rinka zubewa kasa suna kwasar gaisuwa. Ko daya daga cikinsu bata kalla ba kawai sai ta ci gaba da tafiya har ta isa kan wata kasaitacciyar karagar mulki ta zauna. Zamanta ke da wuya wani dogon mutum tsoho mai farin gemu yazo gareta ya zube kasa ya kwashi gaisuwa ya ce, "Lale marhaban da Sarauniyar duniya. Ya shugabata lafiya kuwa kika zo mana a wannan lokaci ba sa'adda kika saba zuwa mana ba?". Ya yin da Abidatul Azmal taji wannan tambaya sai tayi ajiyar zuciya sannan ta dubi tsohon cikin nutsuwa ta ce, "Ya kai Zurhus hakika zuwana wannan boyayyiyar fada tawa a yanzu ya zo ne bisa dole ba akan shiri ba, domin makiya sun bini har fadata sun cini da yaki. In ba don na gudo nan ba da nima sai sun hallakani. Wadannan yara kuwa da ka ganni da su garkuwa nayi da su domin na sami damar daukar fansa akan yarima Himal domin shi ne ya kashe mahaifina Sarki Asmaru". Koda jin haka sai idanun tsoho Zarhus suka zazzaro ya firgita ainun saboda jin cewa an kashe Sarki Asmairu. Sarauniya Abidatul Azmal ta dubi wata kuyanga ta mika ma ta Izaima da Uhairu ta ce, "Ki kai wadannan yara kurkuku a tsaresu, amma a kula da abincinsu sosai, kuma kada a basu wuya". Kuyangar ta karbi yaron ta ce, "An gama ya shugabata". Kawai sai ta tafi da su izuwa cikin wata kofa ta shige. Sarauniya Abidatul Azmal tayi shiru tana mai sunkui da kanta kas, ta shiga tunani har izuwa lokaci mai dan tsawo, daga can sai idanunta suka ciko da kwalla ta dago kai ia 3 Taskar Tsafi-4 >Madakin Gin dubi tsoho Zarbus ta сe, "Hakika abokan gaba sun mutuncina kuma sun zubar mini da kimata kuma sun yan mini farin cikina. Ya zama wajibi a gareni nayi gagarum shiri na Karshe don ganin bayan makiyanmu" Koda gama fadin haka sia Abidatul Azmal ta dauk madubin tsafinta ta dorashi akan cinyaria sannan shafeshi da hannunta na hagu sau uku. Nan take duk abind ya faru a birnin ya baiyana akan madubin tun daga lokaciтda aka gama wannan yaki kawo izuwa sa'adda SarkMaharaz ya yi bankwana da su Kurbas suka tafi izuwabirnin Nurul Kalbi domin su sake raya birnin nasu". Koda gama ganin wannan allamari sai gimbi Abidatul Azmal ta takarkare ta bushe da mahaukaciyadariya. har da faduwa kasa daga kan karagar mulkiAl'amarin da ya baiwa gaba dayan badiman fadar mamak ke nan bar ma suka tsorata. Daga can kuma sai ta miketsaye ta koma kan karagarta ta zuana ta murtuke fuskakamar an aiko ma ta da sakon mutuwa. Kawai sai ta tafahannayenta sau uku. Faruwar hakan ke da wuya sai wat katuwar kofa ta bude, wadansu irin samudawan mutan suka rinka fitowa daga ciki. Adadin samudawan bai wu dari biyu da hamsin ba, dukkaninsu sun yi shigar yaki n matukar kwarjini da ban tsoro. Su kansu hadiman wane fada sai da suka razana ainun da ganin wadan samudawa domin basu san da zaman su ba a cikin iad asalima babu wanda ya taba shiga wannan daki da suka daga ciki. Su dai wadannan samudawa sun kasance doga tamkar bishiyar dabino domin mutum bai isa ya iya tah Taskar Tsafi-4 -> Madakin Gini kafadarsu ba ma bare kawunansu, sannan suna da kauri da kuma kirar halittar jikinsu ta sha bambam da ta bil'adama tamkar ba jinsin bil'adama ba saboda kunnuwansu dogaye ne a tsaitsaye kamar na zomaye. Fuskokinsu kuwa munana ne babu kyan gani tamkar na birirrika. Abinda zai daurewa mutum kai shi ne a ina Abidatul Azmel ta samo wadannan mutane masu kama da Dodanni, wadanda babu irin su a doron kasa? Babu mai iya amsa wannan tambaya face ita kanta Abidatul Azmal din. Geba dayan wadannan samudawan sai suka jeru a layi cikin sahu-sahu a gaban gimbiya Abidatul Azmal suka sunkui da kawunansu kas cikin alamun biyayya kuma suka kame tamkar sun kasance gumaka. Abidatul Azmal ta dubi babban cikinsu mafi girma ta ce, "Ya kai Gamzuba maza ku yi hawa kai da jama'arka ku nufi hanyar birnin Nurul Kalbi za ku riski su sadauki Kurbas. Ina son ku afka musu ku kashe gaba dayan jama'ar da ke tare da su maza da mata, yara da manya. Amma lallai ina son ku kamo mini Kurbas da Zuhura mahaifiyar Maharaz a raye, da kuma Himal da Hasilatul Kurbas da Lahura ko ta wane hali ku zo mini da su nan. Amma ku tabbatar da cewa kun gusar musu da hankalinsu kafin ku kamasu in ba haka ba kuwa ba za ku iya kama su ba". Sa'adda gimbiya Abidatul Azmal ta zo nan a zancenta sai shugaban samudawan Gamzuba ya risina ya ce, "An gama ya shugabata, amma kin sani cewa wadannan mutane da kika turamu mu kamosu ma'abota addinin Musulunci ne kuma sun kasance shaidanun gaske. Wace dabara kike ganin zamu yi mu sami nasara akansu farat daya?". 15 Taskar Tsafi-4 >Madakin Gini Koda jin wannan tambaya sai Abidatul Azmel tay murmushi sannan ta ce, "Tabbas kayi hikima da ka yi mias wannan tambaya. Dabara daya za ku yi amfaní da ita. Kad. ku kuskura ku afka musu lokaci guda, dole ne ku fara t dan leken asiri garcsu domin ya ga halin da suke ciki. Idan har suna cikin karance-karancensu na sihiri ne kada ka kusancesu sai dai ku kusancesu a lokacin da suka yada zango suna barci ko dai suna wani abu sabanin irin bautarsu". Sa'adda Gamzuba yaji wannan batu sai ya y murmushi mai kama da kukan jaki, sannan ya juya ya daga kansa sama ya karanta wadansu dalasiman tsafi. Nan take kadansu manyan tagogi guda dari biyu da arba'in suka bude sai ga manyan dawakai kosassu masu fuka-fukai sun yi fitar burgu daga ciki. Gabadaya dawakan suka sauko Kasa suka dira agaban samudawan, kowa ya kama nasa ya dane a lokaci guda suka zaburi dawakan suka tashi da su sama suka fice ta saman fadar suna masu ratea tsaunin tamkar ratsawar haske. A wannan lokaci duk wanda ya ga wannan runduna ta wadannan samudawa dole ne ya razana domin kwarjininsu ya kai su hallaka duniyar ma gaba daya ba wai gari guda ba. Bayan bacewar wadannan samudawan ne gimbiya nufi Abidatul kofar Azmal wani ta mike tsaye daga kan karagar mulki ta daki dabam. ya ce, Koda "Ya ganin haka sai tsoho Zarhus yai sauri ya tarets da abokan gabar shugabata ya zamu idan wadannan samudawan sun dawo yi da su?" 16 Taskar Tsafi-4 >Madakin Gini Abidatul Azmal ta ce, "Suma a kaisu kurkuku a ajiyesu amma kada akaisu dakin da aka kai su Izaima. Nimayanzu zan shiga dain halwar tsafi ne kuma ba zan fito ba sai bayan kwana goma sha hudu domin na binciko abinda zan yi naga bayan Sarki Maharaz saboda shi kadai ne mutumin da zai iyakawo mini cikas a cikin al'amurana." Tsoho Zarhus yai ajiyar zuciya ya ce, "Ya shugabata to me zai hana ayanzu ki tura wadannan Dakaru naki izuwa can birnin naki domin su kawar da Sarki Maharaz don kada jama'armu su ci gaba da addinin Maharaz?". Koda jin wannan batu sai hawayen takaici ya zubowa Abidatul Azmal ta ce, "Ai na makara tunda har Maharaz ya musuluntar da jama'ata. Abinda zan iya yi kawai shi ne, na shiga wannan dakin balwa na binciko hanyar da zan bi na ga bayan sa, a sannan ne zan yi gagarumin shirin yaki na Karshe. Ina tabbatar maka da cewa sai na sami gagarumar nasara wacce zan kawar da musulunci da musulmi a wannan nahiyar gaba daya". fadin hakan sai Abidatul Azmal ta Karasa cikin wannan dakin tsafi. Tana shiga cikin dakin sai kofare dakin ta kulle da kanta. A CAN BIRNIN Abidatul Azmal kuwa, lokacin Ada attajiri Suhairu ya tafi da Sarki Maharaz izuwa gidansa sai ya shigar da shi har izuwa cikin turakarsa. Gidan attajiri Suhairu ya kasance babban gida ne mai wuri-wuri, sannan kowanne Gangare akwai hadiman da ke 17 Taskar Tsafi-4 Madakin Gini kula da shi. Hakika gidan ya tsaru kuma yaKawatu tamkar sarauta. gidan Da shigar su cikin turakar sai attajiri Suhairu ya kai Maharaz har kan shimfidarsa ya zaunar da shi sannan ya kirawo wata kuyanya ya umarceta da taje ta kawo musu abinci. Cikin kankanin lokaci aka kawo musu abinci na afarma sama da kala bakwai. A dai-dai wannan lokaci ne Maharaz ya fuskanci cewa lokacin sallar la'asar yayi, saboda haka sai ya ki cin abincin ya

Chapter 1 of 2