Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 3
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels TASTAR TSAFIABDULAZIZ SANI M/GINI Taskar Tsufl Ahdul'azit Sant M/iini TASKAR TSAFI kimanin shekaru dubu daya da dari K daya kafin zamanin Sarki lamarudu na birnin KUSA an yi wata mashahuriyar sarauniya kuma babbar matsahfiya j'yar ta'addanci mai suna ABIDATUL AZMAL. Abidatul Azmal ta kasance kyakkyawar buqurwa 'yar shckara ashirin da biyar kuma ta gají sarauta ne da tsafi a wajen mahaifinta Sarki Azmal bin Taufid wanda a zamaninsa babu wani sarki a duniya mai karfin mayaka da karfin sihiri kamarsa. Sai dja ya zamana gaba dayan sarakunan duniya da matsafa na matukar tsoronsa. A lokacin sarki Azmal bashi da wani buri wanda ya fi ya mulki duniya gaba dayanta don haka sai da ya-ci manyan kasashen duniya da yaki guda dari bakwai da tamanin, wannan dalili ne ya sa sarakuna da dama suka dinga gudu daga cikin birancnsu suna buya a cikin dazuzzuka saboda idan Sarki Azmal ya riskesu a cikin kasarsu yana yi musu kisan gilla tarc da duk iyalansu. Sarki Azmal na kan wannan sharafi nasa ne Allah ya jarrabeshi daj wata irin cuta mai muni, ya zamana naman jikinsa na rubewa da kadan-kadan, har sai da ya zamo abin gudu ga dukkanin iyalansa da hadiman sa domin kuwa jikinsa doyi yake, fuskarsa ma sai da ta zagwanye ta yi muni abin firgitarwa, magani 3 Taskur Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini babu irin wanda ba a yi ba amma a banza. A gaba dayan iyalan Sarki Azmal Abidatu ce kadai ba ta gujeshi ba saboda tsananin kaunar da take masa amma mahaifiyar ta ma gudu ta yi ta bar shi sai da ya zamana darc da rana kullum Abidatu na zaunc a gaban Sarki Azmal tana rusa kuka kuma ita cc ke yi masa komai. Wata rana Abidatu na tare da Sarknal tana dura madsa abinci a baki tana zub daaye kamar yadda ta saba kawai sai ta ga ya dubeta ya kama murmushi. Al'amarin da ya matukar ba ta mamaki kenan, ta share hawayenta ta ce "Ya kai Abbana ina dalilin wannan murmushi nake alhalin yau watanka uku kcnan rabonka da yin murmushi? Sarki Azmal ya sake yin murmushi a garcta a karo na biyu sannan ya bude baki da kyar ya cc "Ya ke 'yata ki yi sani ccwa ba komai ne ya sani wannan murmushi ba face na hango cewa ke ce za ki gajeni, lallai za ki yi shuhura a duniya kamar yadda na yi kuma za ki dade akan karagar mulki har ki tsufa har zuwa ajalinki. Hakika ke kadai cc ki ka nuna mini so da kauna fiyc da kowa tunda ba ki gujeni ba a sa'adda kowa ya gujeni haka kuma ba ki kyamace ni ba a lokacin da kowa ya kyamace ni." Sarki Azmal ya daga hannunsa da kyar ya yi nuni izuwa wata bakar akwati sannan da Abidatu "Je ki ki dafa saman akwatin can da tafin 4 Tuskur Tvafl Abdul'azi: Sani M/Gint hannunki." Cikin sanyin jiki da rashin fahimta Abidatu ta mike ta je ta dafa akwatin, ba zato ba tsammani sai ta ga akwatin ta rikide ta zama kofar wani katon kogo, mai duhün gaskc wata irin iska mai karfi na fitowa daga ciki tana kokarin zukcta. Ta kc iskar ta haddasa mikewar gashin kan Abidatu, rigar dake jikinta kuwa ta dinga kadawa kamar za ta fita daga jikinta, ba don Abidatu ta tokare kofar kogon da kafafunta ba da hannayenta da tuni iskar ta zuketa izuwa ciki. Abidatu ta rusa ihu ta waigo ta dubi mahaifinta fuskarta cike da tsoro ta ce "Ya kai Abbana yanzu ba ka ceceni ba kana gani zan hallaka?" Azmal ya ce "Ya ke 'yata ashe duk tsawon zamana dake ba kı amince dani ba. Saki jikinki ki kwantar da hankalınkı ki bari wannan iska ta zukeki domin za ta kai ki ne inda za ki samu irin matsayin da na samu kuma za ta kai ki inda wani mahaluki bai taba zuwa ba, kuma daga ke har izuwa mutumin karshe na duniya wani ba zai je ba." Koda Abidatu ta ji wannan batu sai hankalinta ya kwanta ta saki jikinta wannan iska ta zuketa izuwa cikin kogon. Take kogon ya rikide ya zama wannan bakar akwati, Sarki Azmal ya kurawa akwatin idanu har tsawon rabin sa'a sannan akwatin 5 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini ta sake rikidewa ta zama kogo, sai ga Abidatu ta fito daga ciki fuskarta cike da annuri wani irin haske ya baibaye jikinta gaba daya. Tana fitowa daga cikin kogon sai kogon ya zama bakar akwatin a daidai lokacin ne Sarki Azmal ya fara wani irin kakarin mutuwa. Al'amarin da ya dugunzuma hankalin Abidatu kenan ta ruga izuwa kan gado da Sarki Azmal ke kwance, ta zaunc daf da shi ta kura masa idanu tana kwalla ta ce "Ina ma'anar wannan kakari naka?" Azmal ya ce "Ya ke 'yata ki yi sani cewa lokaci ya yi da zamu yi bankwana. A halin yanzu kin ziyarci inda gaba dayan sirrikan tsafin duniya yakc,w anda ni kadai na mallakesu kuma yanzu sun barni sun koma gareki. Wannan wuri da ki ka je shi ake kira TASKAR TSAFI. Shin za ki iya bani labarin abubuwan da ki ka gano a cikin Taskar Tsafi?" Abidatul Azmal ta kada kai ta ce "Ya kai Babana ka yi sani cewa harshe ba zai iya bayanin abin da na gani ba, idanu ba su isa su ga abin da na gani ba, abin da zan iya cewa kawai shi ne na je inda babu irinsa a duk fadin duniyar nan kuma na ji wani sirri a cikin jinin jikina, Kashina, bargona da fatar jikina irin wanda ban taba ji ba. Ka yi sani ccwa azata bisa ina ji kamar zan iya daukar duniyar nan na tafin hannuna." 6 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini Ko da jin haka sai Sarki Azmal ya yi guntun murmushi cikin karfin hali a lokaci guda kuma ya hadiyi miyau na karshe. Take idanunsa suka kafe, gaba daya gangar jikinsa ta sandare komai ya daina motsi, koda ganin haka sai Abidatul Azmal ta rungumc gawar Sarki Azmal ta fashc da matsanancin kuka har da ihu al'amarin da ya haddasa durowar gaba dayan dakarun gin sarautar izuwa cikin turakar Sarki Azmal. Duk wanda ya shigo ya ga Abidatu rungume da gawa sai jikinsa ya yi sanyi ya kame kawai. Cikin kankanin lokaci labari ya bazu izuwa sauran kasashe dake makwabtaka da birnin kusan cewar Sarki Azmal ya mutu, ai kuwa nan fa jama'a suka cika da farin ciki domin sun san cewa sun huta dulkin zaluncin da ake yi musu sun manta da cewa an kashe maciji ne ba a sare kansa ba, domin akwai magajin Sarki Azmal wato 'yarsa Abidatul Azmal. A yammacin birain Kusa akwai wani babban gari da ake kira Babila. Sarkin dake mulki a Babila sunansa Asmaru bin Ufila. Kafin Sarki Asmaru ya hau kan karaga Sarki Zuwadu ne ke mulki amma sai Sarki Azmal ya kaudashi da karfin tsiya ya dora Asmaru. Sarki Asmaru na da da guda daya wani kyakkyawan saurayi kuma jarumin gaske mai suna 7 Himal. Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini Himal ya kasance adalin mutum kuma ga tausayi da jin kan talakawa. Wadannan halayc na sanc suka sa bai shaku da mahaifinsa ba Sarki Asmaru domin shi Asmaru ya kasance cikakken azzalumi, makctaci. A ragowar Sarki Asmaru babu abin da ya ke so sama da cin zali, kisa da kwatar dukiya ko macc mai kyau. Ita kanta mahaifiyar Himal asalinta matar wazirin Sarki Asmaru ce. A ranar da Sarki Asmaru ya kyallara idanu ya ganta ya jc har gidan Wazirin nasa ya yi masa kisan gilla ya daukota da karfin tsiya ya aurcta bisa dolc., Wannan abu ya faru ne kimanin shekaru ashirin da biyar baya kuma har yanzu Yarima Himal bai taba jin wannan labari ba, domin mahaifiyarsa ba ta bari ya sani ba. Sa'adda Yarima Himal ya fuskanci cewa ra'ayinsa da na mahaifinsa sun bambanta sai ya ja da baya ja cikin harkokin sarauta ya zama kamar ba dan Sarki ba. Kullum ba shi da tunanin hanyar da zai bi ya hana zalunci a doron kasa to amma fa ya san cewa bai isa ba, domin ko ba komai Sarkin yawa ya fi sarkin karfi. Tabbas idan ya ce zai shiga cikin irin harkokin mahaifinsa na hanashi aiwatar da zalunci, mahaifin nasa zai iya sawa a hallaka shi, tunda dai babu wata kauna da kyakkyawar alaka a tsakaninsu. 8 Tuskar Tsafl Abdul'aziz Sani M/Gini Akwai wani lokaci da Yarima Himal ya kama wani dan gari ya yi masa dukan tsiya har ya sumar da shi bisa laifin yiwa wata makauniya fyade, koda Sarki Asmaru ya sami labarin abinda ya faru sai ya tura dakaru hamsin don su kamo Himal su kaishi kurkuku. A wannan lokaci HImal na can bayan gari shi kadai yana baiwa kansa horon yaki, koda dakarunj hamsin suka afka masa da niyyar su cafkeshi sai ya hau su da duka, cikin dakiku kadan ya sumar da mutum arba'in, mutum goma kuwa suka cika wandonsu da iska. Yayin da dakaru goman suka kaiwa Sarki labarin 6arnar da Yarima Himal ya yi sai aka sake tura wadansu dakarun guda dari, suma duk a kakkarye suka dawo, al'amarin da ya fusata Sarki Asmaru kenan ya dubi Sarkin yakinsa Kurbas ibni Hamzil ba tare da ya ce dashi komai ba. Nan take Kurbas ya mike ya tafi gidansa ya yi shigar yaki sannan ya kama dokinsa ya hau yua nufi bayan gari shi kadai, hakika komai jarumtakar Sadauki idan ya ga Kurbas a cikin irin wannan shiga da ya yi dole ne ya razana. Sadauki Kurbas ya kasance garjejen kato, ya tsawo kuma ga kauri. Yana da karfin tsiya fiye da kwatancen mai kwatance domiun idan ransa nya baci, komai girman bishiya idan ya nausheta sai hannunsa ya nutse a cikinta. Idan kuwa ya doke ta da kafarsa sai ta jijjigo jijiyoyinta daga karkashin Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini kasa ta fadi kasa, in dai tsagwaron karfi ake magana babu kamarsa a wannan zamani, a harkar tsafi ne su Sarki Asmaru suka sha gaban sa yake musu biyayya bisa dole. Yarima Himal na zaune shi kadai a dokar daji bisa wani dutse ya cake takobinsa cikin kasa a gabansa ya kura mata idanu kawai. Kai da ganinsa kasan yayi nisa a cikin kogin tunani, kwatsam sai ya jiyo sukuwar doki a gabansa. Koda ya dago kai yayi arba da Kurbas cikin shigar yaki sai ya razana ya mike tsaye zumbur yana shawarar tsayawa koguduwa, tabbas yarima Himal ya san cewa Kurbas ya fi karfinsa nesa ba kusa ba domin ruwa ba sa'an kwando bane to amma da yake koda wasa basu taba jarraba fada da juna ba kowa na baiwa kowa kimarsa. Sadauki Kurbas ya iso har gaban yarima Himal bisa dokinsa. Dokin ya daga kafafunsa sama kamar zai banke Himal yana haniniya amma ko gizau Himal baiyiba. Al'amarin da ya baiwa Kurbas mamaki kenan, kawai sai ya sauko daga kan dokin nasa ya dubi Himal ido da ido ya ce "Na zo bisa umarnin sarki don na tafi dakai izuwa kurkuku, ina mai shawartarka daka bani hadin kai cikin ruwan sanyi ko kuma na tafi da kai ta tsiya tsiya." Koda jin wannan batu sai Himal yayi murmushi ya ce "Ai kuwa sai dai ka tafi dani ta 10 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gint tsiya tsiya don bazan taßa baka hadin kai ba." kafin Himal ya gama rufe bakinsa tuni Kurbas ya kawo masa wawar cafka ya daga shi sama da niyar ya fyadashi da kasa domin ya suma ya tafi dashi a saukake. Cikin zafin nama da nuna kwarewa da bajinta Himal yayi wata irin katantanwa a sama ya zulle daga hannun Kurbas ya duro a bayansa bisa duga dugansa kuma ya hankada Kurbas gaba ya tafi taga-taga kamar zai fadi amma sai ya noke ya juyo yana mai yiwa Himal tafi domin yayi mamakin wannan bajinta da ya nuna. Kurbas ya ci gaba da yiwa Himal tafi yana murmushi a gareshi. Shi kuwa Himal sai ya murtuke fuska ya zare takobinsa daga cikin kasa ya ce "Ya kai Kurbas kayi sani cewa ko ta wane hali bazan bari ba ka kaini hannun sarki ba, sai dai ka kai gawata." Ko da jin haka sai Kurbas ya bushe da dariya ya ce "Ai a raye akace na kai ka don ayi maka hukunci bisa laifin da ka aikata don haka kowa a rayen zan kaika. Yaro ka yi kuskure da kake tunanin har zaka iya yakata ko iya rufcewa daga hannuna." Gama fadin hakan ke da wuya sai Kurbas ya zare takobinsa shima ya kaiwa Himal mugun sara. Himal ya kare saran da takobinsa, amma saboda karfın saran sai daya tsugunna kasa bisa gwiwoyinsa ya ji kamar an dora masa dutse mai 11 girma; nan fa suka ci gaba da dauki ba dadi a hakan wato Kurbas na tsaye shi kuma Himal na tsugunne. Kurbas na ta kawo masa sara da suka yana kokarin karewa amma ya kasa mai da martani domin fifikon a baiyane yake, ya yinda aka dan jima kadan a haka ya zamana Kurbas bai yiwa Himal rauni ba ko sau daya shi kuma Himal ya kasa mai da martani, sai duk suka gaji kowannansu ya rinka daga makaminsa sama da kyar. Koda Kurbas ya ga wankin hula zai kaishi dare sai ya fusata yai jifa da takobinsa ya sake rarumar Himal da nufin yai masa mugun kaye ya take amma sai Himal ya sakle murguda jikinsa tamkar sifirin yayi katantanwa har sau bakwai a sama sannan ya fado kasa, Kurbas ya kai masa cafka, shi kuma ya fice fit ta tsakankanin kafafunsa. Hanfa suka kasa tsere tamkar kyanwa ta biyo 6cra, kuskuren da Himal yayi kena domin bai san ccwa ko da zaki Kurbas ya kasa tere sai ya cimmasa saboda Allah ya hore masa azababben gudu kuma ga baiwar rashin gajiya. Kurbas na iya shafe yini guda yana gudu a cikin daji ba tare da ya tsaya ba don ya huta. Shi kuwa Himal gudune dashi natsiya tsiya amma bashi da daguwar juriya. Yayin da suka sami sa'a kacal suna tseren guda duk da cewar Himal ya baiwa Kurbas ta zara mai yawa sai gashi HImal ya fara sarewa yana gudu 12 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini yana tangadi kamar zai fadi. Shi kuwa Kurbas sai ya zami kamar sannan ne ma ya fara gudun, ai kuwa kamar kiftawar ido ya cimma Himal har ma sai da sha gabansa. Koda Himal ya ga Kurbas. a gabansa sai gwiwoyinsa suka yi sanyi ya yanke jiki ya fadi gaban Kurbas yana haki, ba tarc da bata wani lokaci ba Kurbas ya kama Himal a ruwan sanyi yai masa daurin huhun goro ya azashi bisa doki ya tafi da shi. Bai zame ko'ina da shi ba sai gaban sarki Asmaru, da zuwa sarki ya yankewa Himal hukuncin dauri na shekaru uku a gidan maza, nan take Kurbas ya tafi da Himal kurkuku sai da tabbatar da cewa an sashi cikin daki an kulle sannan ya tafi. Lokacin da labari ya riski Hasilatul Kurbas wato matar Himal kuma 'ya ga sadauki Kurbas sai ranta ya baci, kuma hankalinta ya dugunzuma tayi rantsuwa da girman mahaifinta cewa sai ta fitar da mijinta daga cikin kurkuku a wannan darc. Hasilatul Kurbas ta kasance gagarumar jaruma kuma basadaukiya, saboda tsananin karfinta da jarumtakarta ne ake ganin ma kamar tafi mahaifinta jarumta. Hasilatul Kurbas ta kasance kyakykyawar gaske domin a fagen kyau ana ganin cewa ita da Abidatul Azamal 'yar sarki Azmal za su iya zama kunnen doki ko kuma daya tafi daya da kadan. Abin da yasa ba'a tantance ba shine basu taba haduwa ba a waje guda. Matsalar Hasilatul 13 Taskar Tsufi Abdul'aziz Sani M/Gini Kurbas daya ce wato rashin iya tsafi kuma bata nuna jarumtakarta da karfinta sai a filin yaki domin sau tari ma ita ce take zuwa ta wakilci mahaifinta duk sa'adda za'a tafi babban yaki wanda ake matukar shakkar abokan gaba, shi kansa sadauki Kurbas yana alfahari da Hasilatun Kurbas kuma ya yarda har a cikin ransa cewa 'yarsa tafishi karfi da jarumta. A halin yanzu Himal da Hasilatul kurbas sun haifi 'ya'yan biyu mace da namiji. Macen itace babba, yarinya ce 'yar kimanin shekaru tara mai suna Izaima, shi kuwa namijin shekararsa biyar ana kiransa Uhairu. Kafin Himal da Hasilatul Kurbas suyi aure sai da suka yi gagarumar soyayya irin wacce ba'a tabayi baa tarihin Kasar domin ansha gwagwarmaya sabodatarin yawan masoyan Hasilatul Kurbas. Sai da aka sa wata babbar gasa mai matukar wuya a tsakanin masoyannata mutum dubu daya. Yanayin wannan gasa shine an debi wadannan masoya na Hasilatul Kurbas su dubu daya izuwa tsakiyar wani daji wanda babu komai a cikinsa face dusar kankara sai kuma wasu irin muggan dabbobi masu rayuwa a cikin kankara wadanda ke da matukar girma da karfi, su dai dabbobin sun kasahce masu siffa irin ta Bauna, suna 14 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini da farata manya-manya masu tsini da kaifi tamkar na takobi. Gaba daya wadannan masoya na Hasilatul Kurbas su dubu daya an ajiyesu ne acikin wannan dajin babu mai makami ko guda kuma babu wata sutura a jikinsu face bante na fata, saboda haka ana zubesu acikin dajin suka kama makyarkyatar sanyi. Kafin ma muggan dabbobin dajin su farmusu sanyi ya fara hallaka wasu daga cikinsu. Daga nan kuma sai dabbobin suka dunga faso kankara daga kasa suna fitowa sama suna wani irin gurnani mai ban tsoro wanda ya dinga firgita jarumai dubun. Nan fa dabbobin suka rinka walima da sassan jikin bil'adama, kafin wani lokaci sun cinye jarumai dari tara da casa'in da tara saura mutum daya kacal kuma ba kowa bane face jarumi Himal, shima in ba don ya cire farcen daya daga cikinsu ba da karfin tsiya ya rukeshi a matsayin makami ba datuni sun hallaka. Nan fa aka fara mugum artabu tsakanin jarumi Himal da wadannan dabbobi kuma a lokacin ne sanyin wajen ya fara yi masa illah. Koda yaga masifa tai masifa saı ya sunkuci gawar daya daga cikin dabbobin wadda ya kashc da hannunsa ya runtuma da azababben gudu, dabbobin kuwa suka tasam masa a guje suna neman kure masa gudu. Matacciyar dabbar na ruke a hannunsa tamkar ya dauki silan kara duk da kasancewar girman ta da 15 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini dake hannunsa yana kan wanna hali na gudu, a haka nauyinta ya wuce kima sai ya shige fedeta da farce ya sami nasarar kammala fedeta ya yiwa kansa riga da fatar jikin dabbar wadda ya fede, nan take ya daina jin sanyi jikinsa ya daina karkarwar dari. Koda jin hakan sai ya tsaya cak ya waigo yai arba da dabbobin sa'adda bai wuce taku daya ba tsakaninsa da su, kamar a mafarki sai suma dabbobin suka tsaya kyma aka fara kallan kallo tsakaninsu dashi. Jarumi Himal ya kwarara uban ihu irin wanda ke razana barade a filin daga, a lokaci guda ya afkawa dabbobin da sara da wannan farce irin na jikinsu, nanfa yaita ragargazarsu suka dunga zubewa kasa matattu. Ya yinda dabbobin suka fuskanci cewa lallai baza su iya dashi ba sai suka juya da baya suka fara gudun ceton rayukansu. Lallai gaskiyar masu magana da suka ce idan kaji ki gudu sa gudune bai zoba, ai kuwa jarumi Himal bai ragawa dabbobin ba sai da ya kare musu gudu daya bayan daya yana zare musu ruhin numfashi. Kai wasu ma har karkashin ruwa ya dunga binsa yana kashe su sai da ya tabbatar da cewa ya kashesu gaba daya sannan hankalinsa ya kwanta. A sannan ne ya gasa daya daga cikin dabbobin ya ci ya koshi, bayan ya sha ruwa kuma ya huta sai yayi guzurin naman da ya gasa mai yawa tare da ruwa sannan ya kama hanya yayi ta tafiya a cikin dusar Kankarar. 16 Tasker Tsafi Abdulaziz Sani M/Gini Ya kwana nan ya tashì can sai da ya kwana goma sha daya a cikin wannan mugun daji yana tafiya sannan ya fita daga cikinsa, bayan ya sake shafe kwana tara ne ya iso birnin Babila. Dama tuni an zuba dakaru a bayan gari wadanda za su taryi jarumin da ya sami nasarar wannan gasa. Koda suka hango jarunmi Himal sanye da fatar wadan nan dabbobi na dajin kankara sai suka ruga gareshi suna shewa tarc da yi masa jinjina, nan take suka dagashi sama suka tafi dashi izuwa cikin gari. A wannan-rana aka daura auren Himal da Hasilatul Kurbas domin an yarda da jarumtakarsa an san cewa ya dace da ita. Wannan shine takaitaccen tarihin soyayyar yarima Himal da Hasilatul Kurbas.• Lokacin da bakin ciki ya yiwa Hasilatul Kurbas yawa sakamakon samun labarin daure mijinta a kurkuku har tsawon shekaru ukar zuciyarta ta kama tafarfasa. Izaima da Uhairu kuwa sai suka kama kuka, koda Hasilatul Kurbas taga yadda 'ya'yanta suka shiga matsananci damuwa sai ta shiga rarrashinsu sannan ta kira wata baiwarta mai suna Kasirat wadda dama itace tayi renonsu tun suna jarirai, tace da ita "Gasunan ta kula dasu sosai domin ita yanzu zata fita ne kuma bata sani ba ko zata dawo a raye." Ko dajin wannan batu sai hankalin Kasirat ya 17 Taskar Tvafi Abdul'aziz Sani M/Gini dugunzuwa ta ce "Ya shugabata ke kuwa ina ne inda zaki je haka har da kike tunanin ba zaki dawo a raye ba?" Hasilatul Kurbas tayi murmushi sannan ta dafa kafadar Kasirat cikin yanayin yake ta ce "kar ki damu da inda zanje ke dai kawai ki kula da -"yayana, ki rakestf amana koda a bayan raina ne." Ta na gama fadin hakan sai ta juya ta shiga cikin turakarta ta bar Kasirat nan a tsaye a tsakar gida cikin tsananin damuwa da fargaba. Hasilatul Kurbat bata fito ba daga cikin turakarta sai da dare ya raba, sanye cikin shigar yaki ta fito, ta sanya farin sulke da hular karfe a kanta, ba'a ganin komai a fuskarta face idanunta, hancinta da bakinta sannan kuma ta ratayo wata zabgegiyar takobi a bayanta. A kuibin cinyoyinta dama da hagu kuwa wadansu zabga zabgan wukakene acikin kufensu guda biyu, koda fitowarta sai ta ruga inda Bargar dawaki yake ta kwance wani ingarma farin dokinta ta daura masa siddi da sauri wannan-ta haye kansa ta zabureshi da gudu. Tana isa kofar gidan tadakawa masu gadi tsawa tana mai umartarsu dasu gaggauta bude mata kofa, in ba don sun dauki muryartaba da baza su bude kofarba domin tuni sun razana jikinsu ya kama karkarwa tun sa'adda suka hangota ta durfafosu sun a tsammanin cewa wani sarkin barayinne ya kawo musu mamaya, nan da 18 Taskar Tsafi Abdul'aziz Sani M/Gini nan maso gadin suka budewa Hasilatul Kurbat kofa ta fice sukwane, so kowa suka mai da kofa suka rufe. Kai tsaye Hasilatul Kurbat ta durfafi kurkukun garin ba tare da shayin komai ba duk da kuwa tasan cewa akwai gagarumin tsaro a cikin kurkun wanda aka yiwa lakabi Ukubatul dukkan. Shi dai Ukubatul dukkan kurkuku ne wanda yai kaurin suna a duniya saboda tsananin azabar da ake yiwa fursunonin cikinsa da kuma mugun tsaron da aka yi masa, shi dai wannan kurkuku an gina shine akan wani tsibiri wanda wani makeken kogi ya zagayeshi. Dole sai mutum ya shiga kwale kwale yayi tafiya yini guda acikin kogin sannan zai isa wannan kurkuku, shi kuwa ginin gidan kurkukun anyi shine da zallan duwatsun wuta, kofofin gidan kuwa da tagoginsu anyi sune da murtuka murtakan karafa masu tsananin kwari wadanda sai makeri ya shafe sa'a uku kafin ya iya yankasu. Dakarun dake tsaron wannan kurkuku mutum dubu dari uku ne da sittin da uku. Gaba dayansu suna sanye da jajayan tufafi kuma ruke da muggan makaman yaki, dukkanninsu sun kasance zakwakumai a fagen yaki wadanda basu san tsoro ba kuma idan bala'i yai bala'i basa ja da baya don ganin mutuwa sai dai su kara tun kararta gasu

Chapter 1 of 3