Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
domin komawa wajen zamansu suna gaisawa da masoyansu Wasu kuma na ɗaga musu hannu, har suka isa in da kujerunsu suke suka sake zama, zuciyoyinsu cike da farin cikin farin ciki Maral Bayan komai ya samu dai daita sai kuma tsala tsalan Isalan mutanan kuyangi suka shigo fadar dauke da farin ciki da nau'ikan kayan abinci mai rai da lafiya. HAUSABOOK.COM 38 nau'i daban-daban Wadansu na dauke da tulunan giya, Nan take aka shiga hidimar ciye ciye da tanɗe-tanɗe, wani abu da zai bawa mutum mamaki kuma ya, daure masa kai shi ne duk tarin tsananin yawan jama'ar da suka halarci bikin sai da suka yi wadata da abıncı da abin sha har suka bar shi, sannan taro ya watse kowa yayi kama gabansa, baki suka koma masaukinsu kahzib, Hilwas da Sharwas na zaune a cikin turakarsu suna hira a tsakanınsu domin debewa juna ƙewa. A cikin hirar ta su ne Sharwas ya dube su fuskarsa cike da tsananin damuwa ya ce "Ya 'yan uwana ku yi sani cewa wannan farin cıkı da muke a yanzu, HAUSABOOK.COM 39 kawai ina nuna shine ba dan zuciyata tana so ba, ta wata fuskar ma wannan farın cıkin ba shi da wani amfanı. Cike ma maganar mamakI Hilwas ya dubi Sharwas cikin murmushi ya ce, "Ya abokina shin ina dalilin wannan furici naka?" Sharwas ya sake haɗe rai ya ce, "Sanın kanku ne ke cewa mahaifanmu na raye kuma mun rabu da su tun muna yara kanana, to ina amfanin farın cikın mu tunda ba mu san halin da suke cikı ba. Ko da jin wannan batun daga bakın Sharwas sai hankalın Hilwas da Kahzıb ya dugunzuma ainun har kwallar takaici a zubo masu Hilwas ya buɗi baki da ƙyar fuskarshi cike da damuwa ya ce, "Haƙiƙa abokina ka sosa mini in da yake yi min Kaikayı. HAUSABOOK.COM 40 ka sani cewa a yau yau kafin wayewar gari sai mun gano in da mahaifan mu suke mun gana da su. Hakika mahaifa sune ginshiƙin rayuwar dukkannin wani ɗa na gari. Sa'adda Hilwas ya zo nan a zancensa sai ya fashe da kuka, al'amarin da ya narkar da zuciyar Kahzib da Sharwas ke nan suma suka fashe da kukan, Sai da suka shafe tsawon lokaci a cikin wannan hali sannan Hilwas ya share hawayen da ke fuskarsa ya mike tsaye zumbur ya fice daga cikın turakar Kahzib da Sharwas na bıye da shi. Da ya ke lokacı ne na dare sai suka huce kai tsaye izuwa kurkukun kasar, Duk in da suka huce sai dai ka ga kuyangi da bayı nayi musu musujina gamı da miƙa gaisuwa. HAUSABOOK.COM 41 Su kuwa ko kallonsu baa yi suna masu fice daga gidan sarautar, Tafiyar daƙiƙa hamsin kacal suka yi suka iso kofar kurkukun wadda ta kasance murtukekiya da aka yi ta da zunzurutun bakın karfe, duk in da mutum ya kalla a sama da ƙasan kofar tarin muggan dakaru ne shırye cikın shigar yakı. Hannayensu suna rike da miyagun makamai sai mazurai suke yi suna kai komo kamar za su ci babu, haƙiƙa komai dakewar zuciyar jarumi da rashin tsoronsa idan ya yi arba da dakarun dole ne ya firgice saboda kwarjininsu. Koda shugaban da ke kula da kofar wani garjejen basamuden kato ya hango su Hilwas sai ya tako da katafunsa ya tare su ya risına a gare su cikin girmamawa. HAUSABOOK.COM 42 Hilwas ya dubi basamuden ya ce, "Ya kai Zamaru ka yi sani cewa ba komai ne ya kawo mu nan ba sai domin ka sanar da mu shin ina ne mahaifanmu suke. ''Da jin wannan tambaya sai idanun Zamaru suka zazzaro ya dubi Hilwas cikin alamun tsananin tsoro ya ce, "Ya shugabana na roƙe ka da ka yi min rai. ka sani cewa ba zan iya sanar da kai in da sarki Shardasu ya boye mahaifanku ba, domin ina ina tsoron ka da ya halakar da ni Sa'adda Hilwas ya ji wannan batun sai ya fusata ainun har idanunsa suka kaɗa suka yi jawur, ya dakawa Zamaru tsawa wacce ta sanya hantar cikin Zamaru ta kaɗa, ya dube sa ya ce "Na rantse da rayuwar mahaifan mu idan ba ka sanar da mu in da aka ajıye mahaifanmu ba sai mun yi maka kısa mafi muni ka bƙkunci barzahu. HAUSABOOK.COM 43 Nan fa hankalin Zamaru ya dugunzuma ainun ya rasa abin da yake yı masa dadɗiA. Abuna farko da ya faɗo masa a rai shi ne, shin yanzu idan ya sanar da su Hilwas in da aka ajıye mahaifansu yana da tabbacın cewa sarkı Shardasu ba zai gane cewa shi ne ya sanar da su ba. Sannan abu na biyu shi ne tabbas idan bai sanar da Hilwas abin da ya ke bukata ba zai rasa rayuwarsa a yanzu take, Wannan fa shi ne masu iya magana kan cewa gaba tsini baya siyaki. Wata zuciyar kuma ta ce da shı koma dai dai zai zai faru gwara ka sanar da Hilwas abin da ya bukata. Domin ka TSIRA DA RAYUWAr ka a yanzu. Koda barde Zamaru ya zo nan a tunanin sa sai ya dubi Hilwas da turɓunanniyar fuskarsa kai ka ce murmushi bai taba wanzuwa a HAUSABOOK.COM 44 kanta ba. Ya buɗe tafkeken bakınsa wanda ya fi kama da kofar gari ya ce, "Ya shugabana sarkı ya ajiye mahaifan ku maza ne a can Wani gida na musanman, bayan ɗauke su daga kurkuku, domin ka da ku yi yunƙurin zuwa in da suke. Shi dai gidan ya kasance a cikin kasa, wanda i dan har aka shigar da mutum baya taɓa fitowa face dai mutuwarsa. Gidan ya kasance a can ƙarshen gidan sarauta. Mahaifan ku mata masu suna a zaune a gidan horar da mata sana'o'i domin samar wa da sarkı dukiya mai tarin yawa, Ko da jin wannan bayani daga bakin barde Zamaru sai bawa Hilwas, Kahzib da Sharwas suka ji sun kamu da sananın tausayin mahaifansu bisa jin matsanancin halin KANGIN BAUTA da suke ciki". HAUSABOOK.COM 45 Ba tare da ɓata lokaci ba Hilwas ya umarci barde Zamaru ya kawo musu ingarmun dawakai, sannan suka kama musu linzami, suna masu tsala azababban gudu Kai tsaye gidan karkashin kasa suka nufa da ke karkashın gidan sarauta domin su fara saduwa da mahaifansu maza, Tafiyar rabuwa sa'a da daƙiƙa hamsin kaɗai suka yi suka iso ɓangaren tun kafin su karaso bakin kofar wajen suka fara fafata yaƙi da dakarun da ke tsaro. Lokacin da suka iso bakin kofar kuwa sai suka cika da matukar mamaki, Abin da ya ba su mamakin kuwa shi ne duk da irin yadda sararin samaniya ta mamaye da duhu, Amma ko ina a wajen haskake yake da wani haske na musamman wanda in da allura za ta faɗi a kasa HAUSABOOK.COM 46 da zarar mutum ya duba zai ganta Kai da gani ka san aiki ne na sihiri. Dakarun da ke wajen kuwa sun kasance ababan tsoro saboda kwarjininsu sai ka rantse ka ce ba su kasance bil'adama ba, tsananin yawansu kuwa ya huce musali. Yayin da suka bayyana suka yı arba da su Hilwas sai suka zare makamansu suka tare su aka kacame da KAZAMIN GUMURZU mai matuƙar muni, ban tsoro da ban al'ajabi. Ana fa wannan gumurzu ne dakarun suka gane shayi ruwa ne ba abinci mai nauyı ba, yawansu ya zamto banza, domin duk in da su Hilwas suka sanya gaba sai dai ka ga gawarwakin su na zubewa kasa, jini kuwa ya dinga feshi, fantsama yana malala a kasa. HAUSABOOK.COM 47 Nan fa ya zamana cewa bangarorin biyu sun wanzu suna kawai juna sara da suka cikin matuƙar zafin nama JURIYA DA BAJINTA ta ban al'ajabi. Ana cikin wannan yaki ne wani daga cikin yanayin ya shammaci bawa Hilwas ya kawo masa wani nagartaccen sara da takobinsa wanda zai canza masa hannu. cikin bakin zafin nama Hilwas ya sanya takobinsa domin ya kare harin amma sai saran badakaren ya rinjaye shi ya kadɗe takobin Hilwas ta yo kasa za ta fadi. Kafin badakaren ya sake wani yunkuri Hilwas ya dunkule hannun sa ɗaya ya gabza masa wawan naushi a fuska, kuma ya miƙa ɗayan nasa ya cafo takobinsa saboda tsananin karfin naushin sai da badakaren ya banke 'yan uwansa dakaru mutum shida, HAUSABOOK.COM 48 suka zube kasa magashiyan. Tabbas jarumta da SADAUKANTAKA baiwa ce daga Allah, dukiya mulki ba sa bayar da ita face Allah. Kuma duk wanda Allah ya ba shi jarumta ya huta. In da a ce mutum zai ga yadda Hilwas, Kahzib da Sharwas ke ragargazar dakarun suna yin MUGUWAR HALAKA dole ne ya jinjina musu. Sai da aka shafe sa'a daya ana fafata baƙin artabu. sannan kuma Hilwas suka samu nasarar halakar da dakarun ba ki ɗaya, suka kutsa kai izuwa cikin gidan a nan amma sai suka yi GWAGWARMAYA da dakaru masu tarin yawa sannan suka samu shiga cikin ƙarƙashin ƙasa. Lokacin da suka shiga sai suka kama kalle-kalle da dube-dube suna masu duba dakunan da ke cikı HAUSABOOK.COM 49 domin su ga in da mahaifansu suke amina shiru babu labari sai fursunoni da suke gani maza da mata, Da ƙyar da sidin goshi suka gano a cikin mahaifan nasu suke a cikin waɗansu kejina na karfe hannayensu da kafafunsu ɗaure da sarƙoƙi. Cikın matuƙar farin ciki maral musaltuwa su Hilwas suka ruga izuwa in da kejinan suke Koda ya rage bai fi saura taku uku a tsakanınsu ba kwatsam ba zato ba tsammani sar wani wawakeken rami ya bayyana a gabansu wata irin gagarumar wuta na ci gangaganga a cikin ramin. Kuma wata irin kakkausar murya ta kece da dariya cike cike da matukar fushi da ɓacin rai Hilwas, Kahzib da Sharwas suka waiga bayansu domin su ga wanda yake dariyar. Ai kuwa koda waigawar tasu sai suka yı turus. HAUSABOOK.COM 50 Ba wani suka gani ba face sarkı Shardasu shirye cikin gagarumar shigar shigar yarima Kinzaru na tsaye a ɓarin hannun sa na dama, sarkın yaƙi Hatyal na tsaye a hagu. Waɗansu gabza-gabzan samudawan dakaru na kewaye da su cıkın shigar yaƙi mai matuƙar kwarjini, hannayensu rike da muggan makamai Sai da sarki Shardasu ya yi dariya ta ishe shi sannan daga bısani ya murtuke fuska kamar an aiko masa da WASIKAR MUTUWA, ya dubi Hilwas, Kahzib da Sharwas sannan ya buɗi baki cikin kakkausar murya ya ce, "Ya ku jarumai masu dauke da KAMBUN JARUMTA ku sani cewa tun daga lokacin da kuka fice daga cikin masaukinku har kawo izuwa nan na ga dukkannin abin da ya faru gare ku. Ina so ku yi sani cewa ku da mahaifanku gaba ɗaya kuna karkashin iko na ne har abada ɗaya daga cikin ba zai sadu da mahaifansa ba face ya amince da HAUSABOOK.COM 51 biya mini wata mahimmiıyar bukata ta. "Koda gama fadin hakan sai sarki Shardasu ya yi nuni da hannun sa na hagu izuwa bangaren bangon yamma da ke wajen. Yana mai karanto waɗansu ɗalasiman tsafi, gama rufe bakinsa ke da wuya sai hoton mahaifansu Hilwas mata ya bayyana suna zaune a cikin wani gida suna aika ce aika ce Duba ɗaya za ka yi musu ka fahimci cewa suna cikin damuwa Domin sun rame matuƙa sun yi baki tufafin da ke jikinsu ya yi datti sosai duk ya yayyage, babu wanda zai gansu a cikin wannan hali face ya kamu da tsananin tausayinsu Sa'adda Hilwas, Kahzib da Sharwas suka yi. Arba da su a sannan ne mahaifin Kahzib da Sharwas da ke zaune a cikin wannan kejin suka fara zubar da hawaye. duk da mahaifin Hilwas idanuwansa a makance suke baya gan abin abin da ke faruwa, amma da ya ji kukan ɗan sa Hilwas da HAUSABOOK.COM 52 abokanan Rauzil da Hasham sai shi ma ya fashe da kukan. Sai da suka shafe wani lokacı a cikin wannan hali yarima Kinzaru na yi musu dariyar mugunta. sannan sarki Shardasu ya sake nuna bangon a karo na biyu hoton bat! Kuma ya sanya wani duhu tsakanin su da su Rauzil ya zamana ba sa iya ganin 'ya'yansu. Sarki Shardasu ya saki guntun murmushi ga su Hilwas da har yanzu hawaye ke zuba daga idanuwan su Sannan bushe da dariyar mugunta, kana ya murtuke fuska kamar an aiko masa da WASIKAR MUTUWA, ya ce, "Ya ku wadannan ZARATAN MAYAKA ma'abota karfin damtse ku yi saji cewa idan har kun ɗaukae mini Alkawarin da za ku samo mini abin da nake ji Bukata to zan 'yantaku tare da iyayenku ba za ku kara bauta a gare ni ba. Idan kuwa ku ka bijirewa buƙata ta ku da mahaifan ku za ku kasance a cikın KANGIN HAUSABOOK.COM 53 BAUTA har ajali ya riske ku, Yanzu dai shawara ta rage ga mai shiga rijiya. Koda jin wannan batun daga bakın sarki Shardasu sa hankalın Hilwas, Kahzib da Sharwas ya dugunzuma ainun, kuma su duka ukun suka faɗa kogin tunani don samun mafita. Abin da ya faɗo musu a rai shi ne shin wace irin bukata ce za su biyawa sarkı Shardasu? An ya kuwa ba yaudararsu zai yı ba? To yanzu kuma idan ba mu amince mun biya masa bukatarsa ba za mu ci gaba da zama a cikın kuncin rayuwa, tare da mahaifanmu? Amsar tambayoyın da suka kasa bawa kansu ke nan take hankulansu suka sake dugunzuma fiye da ko yaushe. Hilwas ne ya katse shirun da ya wanzu a tsakanınsu ta hanyar buɗar bakı ya sanya hannu ya share hawayen sa sannan ya ce "Mun amince za mu bıya maka buƙatar matsawar za ka ba mu FANSAR RAYUKAN mahaifanmu. Shin mece HAUSABOOK.COM 54 ce ake buƙatar taka?" Sarkı Shardasu ya yi murmushi a karo na biyu ya ce, "Abın da kawai nake buƙata shi ne za ku tafi izuwa gidan boka Kimraz domin ɗauko mini SANDAR SARAUTAR shi Kafin ku isa gidan za ku tarar da miyagun dazuzzuka guda huɗu masu matukar haɗari. Daji na farko ya kasance mallakin wani gawurtaccen matsafin dodo da ake yi masa masa laƙabi da suna Zamzaru. Dodo Zamzaru ya kasance gwarzon mayaki, kaifi da tsini ba ya tasiri a kansa, A wannan ƙarni ba ki ɗaya, domin saboda hatsabibancinsa ne ya zamana sarakunan da ke makwabtaka da dajin suka yi kaura suka bar yanayin. Kuma an ce shi kadai ne yake rayuwa a dajin. Daji na biyu ya kasance na waɗansu irin tsuntsaye ne masu kama da tsuntsun batoyi, babu wani nau'in makami da yake tasiri a kansu face tsagwaran KARFIN DAMTSE da HAUSABOOK.COM 55 basirar mutum. Masana da bokaye sun tabbatar da cewa adadin tsuntsayen ba zai kidayu ba, Domin kullum kara yawa suke yi. Daji na uku na waɗansu fatalwoyi ne na haske, mutum ba zai taba samun nasara a kansu ba face ya kashe shugabansu kuma dukkanninsu suna da kamanni iri daya sak!. Babu yadda za a yi mutum ya iya gane wane ne shugabansu. tsakanin zafin namansu kuwa ba zai musaltu ba sai dai abin da ido ya gani. Na karshe kuwa ya kasance daji ne na waɗansu zakunan sihiri da wani shu'umin boka ya ƙirƙira mai suna Sultan ibn Hammar. Bayan kun samu nasara shiga gidan boka Kimraz kun dauko mını sandar tsafinsa sai kuma ku huce izuwa wanı daji da ke ıyaka da gidan ku ɗauko mini ƙoƙon kan boka Mannaf da ke ajiye a cikin wata tsohuwar rijiya dake fadar Sarkin bokaye na duniya, Sa'adda sarki Shardasu yazo HAUSABOOK.COM 56 nan a zancen sa sai hankalinsu Hilwas ya dugunzuma ainun, Sharwas dubi sarki ya ce, "Ya shugabana a wace nahiya dazuzzukan suke?" Sarki ya ce, "Me ku ke ci ne na baka na zuba? Ai zan haɗa ku ne da wani hadimin aljanina ya yi muku jagora." Koda gama fadin haka sai sarki Shardasu ya rintse idanunsa ya kırawo sunan aljaninsa, wata irin kakkarfar iska ta mamaye wurin wacce ta haddasa gashin kansu bawa Hilwas da rigunan jikinsu kaɗawa. Daga can sai ga wani narkeken aljani ya bayyana tsum! Tamkar an jefoshi daga sararin samaniya. Aljanin ya kasance mai matuƙar tsaho, muni, girma gami da kwarjini. Domin duk dakewar zuciya irin ta su jarumi Hilwas sai suka firgita da ganin aljanın Shi kansa sarkin yaki Hatyal da yarima Kinzaru sun razana matuka. sarki Shardasu ne kadai bai tsorata ba. Aljanin ya faɗi ƙasa ya HAUSABOOK.COM 57 kwashi gaisuwa ga sarki Shardasu. Sarki ya dube sa ya ce, "Ya kai Kubuzul Haiman ka yi sani cewa ban kirawo ka nan ba sai domin ina sai ka yiwa waɗannan jarumai rakıya izuwa dajin Darul Hashawar. Wannan shi ne abin da nake bukata." Koda jin wannan batun sai aljani Kubuzul Haiman ya risina ya ce, "An gama ya shugabana. Ba tare da wani ɓata lokaci ba Hukubul Haiman rankwafa gadon bayansa bawa Hilwas, Sharwas da Kahzib suka hau kan kansu suka zauna tare da dawakansu sannan Kubuzul Haiman ya yunkura ya tashi izuwa sararin samaniya. Kafin kiftawar ido ya ɓace ɓat a cikin gajimare, nan take sarki Shardasu, yarima Kinzaru da sarkin yaki Hatyal suka bushe da dariyar mugunta. HAUSABOOK.COM 58 Wannan shi ne dalilin barowar jarumi Hilwas, Sharwas da Kahzib daga birninsu na Baitul Na'im, domin su ɗaukowa sarki Shardasu sandar sihiri da kokon kan boka Mannal. SHIN WADANNE IRIN MIYAGUN MUSIBU SU HILWAS ZASU FUSKANTA A WANNAN TAFIYA TASU SUNA SAMUN NASARAR KETARE MIYAGUN DAZUZZUKA HUDU HAR SU ISA GIDAN BOKA KIMRAZ? KUMA SUNA SAMUN NASARAR DAUKOWA SARKI SHARDASU SANDAR TSAFI DA KOKON KAN BOKA MANNAF DOMIN FANSAR RAYUKAN MAHAIFANSU? SHIN YA SHURAIMA 'YAR SARKI HUSUBUL DINAR DA GIMBIYA LASHMIRA ZA SU KASANCE NA KEWAR MASOYANSU HILWAS DA KAHZIB? HAUSABOOK.COM 59 TSAKANIN YARIMA KINZARU DA GIMBIYA LASHMIRA WAYE ZAI GAJI KARAGAR MULKIN SARKI SHARDASU? INA LABARIN SARKI BARSUS, Sarkin marubutan yaƙi ANSAB DA SARKI HULBARU DA KOWANNENSU YA SHIRYAWA SARKI SHARDASU BAKIN TUGGU DOMIN RABA SHI DA KARAGAR MULKINSA, AMMA YA TSIRA DAGA SHARRINSU? SHIN A WANE HALI MAHAIFANSU JARUMI HILWAS YA ZA SU KASANCE NA RABUWA DA 'YA'YANSU? Mu hadu a 10 KANGIN BAUTA domin jin ci gaban wannan labarin nayataccen labari. Lokacin da su jarumi Hilwas suka yi cirko cirko a kofar shiga gidan boka kimraz Cike da matukar damuwa bisa halin KANGIN BAUTA da suka baro mahaifin su a ciki. Sai suka shafe tsawon daƙiƙa arba'in Batare HAUSABOOK.COM 60 da ɗayan su yace uffan ba. Ana cikin wannan hali ne kwatsam bazato babu tsammani sai suka hango wani mahayi bisa ingarman doki fari. Ya rataya wata sharbebiyar takobi a gadon bayan sa ya durfafo inda suke gadan gadan. Sai dukkanin su suka ƙura wa mahayin idanu suna jiran ƙarasowar sa. Sannu a hankali mahayin ya ci gaba da kusanto su, Har yazmana tazarar dake tsakanin su bata huce taku biyar sannan yaja linzamin dokin sa ya tsaya cak Yayin da suka yi arba da mahayin sai suka cika da matukar mamaki. Abu na farko da ya basu mamaki shine yadda mahayin ya yaksance ya mace ba namiji ba, Sannan ya akayi ta iya ketare miyagun dazuzzukan dake baya Wato dajin fatalwoyi na haske, dajin dodo zamzaru da kuma dajin zakunan sihiri masu ɗauke da fuka - fukai , HAUSABOOK.COM 61 Wanda su kansu sai da suka sha bakar wahala sannan suka samu nasarar ketare dazuzzukan. Amsar tambayoyin da suka kasa bawa kansu kenan Shi kuwa Sharwas sam bai ma san da wannan zancen ba, Domin tuni ya shagala da kallon kyakkyawar budurwar, domin lokacin da ya fara arba da ita sai yaji zuciyar sa ta buga wa karfi wani abu ya soki ya soki zuciyarsa a karo na farko yaji ya kamu da matukar kaunar ta a zuciyar sa, Tsawon daƙiƙu ana wannan kallon kallo tsakanin su Sharwas da Mahayin, Sannan daga bisani hilwas yayi karfin hali yayi gyaran murya ya dubi budurwar yayi gyaran murya yace" yake wannan budurwa shin wace ce ke ? HAUSABOOK.COM 62 Kuma ya akayi kika ƙetare miyagun dazuzzukan dake baya har kika iso nan?. Sannan mene ne ke tafe da ke izuwa gar mu. Sa'adda budurwar taji wannan batu daga bakin hilwas dai tayi gyaran murya cikin tattausar murya mai daɗin sauraro tace" yakai hilwas ɗan makaho rukaisu kayi sani cewa da farko dai ni suna na Husnat bintu abu-husein Na fito ne daga gabashin duniya a wani birni da ake yiwa lakabi da Darul--imfidal, Game da amsar tambayar ka ta biyu kuwa shine, Na samu nasarar ketare dazuzzukan dake baya ne bisa taimakon Ubangiji mahalicci,shine wanda ya halicci duniya da Abin da ke cikin ta, HAUSABOOK.COM 63 Amsar tambayar ta karshe ita ce bakomai ne ke tafe dani izuwa gare ku sai domin na taimaka muku da izinin Ubangiji na domin ku samu nasarar abin da kuka fito nema. Kuma na kuɓutar da mahaifan ku daga makircin azzalumin sarki sharadi, Sa'adda Kahzib, hilwas da Sharwas suka ji wannan batu daga bakin Husnat sai suka cika da ɗumbin al'ajabi da mamaki, Kahzib yace "yake wannan jaruma taya ya za ki iya taimaka mana wajen cimma burin mu bayan cewa mu ɗin Jarumai ne zamu iya nasara akan dukkan abinda muka sanya a gaba, Sannan naji kin ambaci wani Ubangiji shin dama akwai wani abin bauta bayan namu?. HAUSABOOK.COM 64 Husnat tayi ƙaytaccen murmushi da ya ƙarawa fuskar ta kwarjini sannan tace " na yar da cewa tabbas ku sadaukai ne kuka kuma zaku iya cimma nasara akan abinda kuka sanya a gaba Amma ina so ku sani zan taimaka muku ne wajen mallakar abin da kuka fita nema cikin ruwan sanyi batare kun sha wata wahala ba, Sannan ina so mu haɗa karfi da ƙarfe wajen rushe mulkin zalunci na sarki shardasu domin ku sani cewa koda mallaka sa abubuwan dake bukata sai ya ci amanar ku bazai taɓa baku fansar rayukan mahaifan ku ba, Sannan zan roƙi Ubangiji na ya warkar da lalurar dake samun iyayen ku, Amma sai idan kun ɗaukar mini alkawarin cewa zaki bayar da gaskiya ga Ubangiji na HAUSABOOK.COM 65 Sa'adda Sharwas, Kahzib da hilwas su ka ji wannan batu daga bakin Husnat sai jikin su yayi sanyi, Suna masu zurfafa izuwa cikin Kogin tunani Daga bisani sai Sharwas yace "Ɗan bamu Lokaci zamu tattauna da yan uwa na, Koda gama faɗin hakan sai shaewas da yan uwansa suka koma gefe guda suka yi ƙusƙus a junan su sannan daga bisani suka dawo izuwa inda Husnat take, Hilwas ya dube ta yace" yake Husnat haƙiƙa mun amince zamu zamu karbi addinin ki, Matukar kika cika alkawarin da kika ɗauka na taimaka mana wajen mallakar abubuwan da muka fito nema, HAUSABOOK.COM 66 Sannan idan har Ubangijin naki ya warkar da mahaifan mu, Munyi miki alkawarin cewa zamu taimaka miki wajen yaɗa addinin ki a wannan nahiya baki ɗaya, Koda jin wannan batu daga bakin hilwas sai jaruma Husnat ta cika da matukar farin ciki maral misaltuwa, Kawai sai ta kama linzamin dokin ta ta sauko ta durfafo ƙofar gidan boka kimraz Da isar ta sai kawai ta sanya hannun ta akan Mabudin kofar tayi bismillah ta tura ƙofar bisa mamaki sai gashi ta buɗe Al'amarin da yayi matukar bawa su hilwas mamaki kenan kuma ya ɗaure musu kai, Domin dai ko da a tarihi basu taɓa ganin jarumin da yayi wannan bajin ta ba. HAUSABOOK.COM 67 Domin kofar tana da kaurin gaske wacce in da za'a sanya karti majiya karfi mutun sattin ba za su iya ture ta ba, Batare da fargabar komai ba, Husnat ta zare sharbebiyar takobin dake gadon bayan ta ta kunna kai izuwa cikin gidan tana mai yafito su hilwas da hannunta tana nuna su biyo bayan ta, Batare da gardamar komai ba hilwas ya zare takobin sa ya bi bayan ta da sauri, Kahzib na rike da mashin sa mai baki biyu, Sharwas na rike da kwari da bakan sa suka shige izuwa cikin gidan, Wannan shi ne abinda ya faru da su bawa Hilwas akan hanyar ta zuwa gidan boka kimraz domin ɗauko wa sarki shardasu sandar sihiri. HAUSABOOK.COM 68 Acan birnin baitul-na'im kuwa al'amarin gimbiya lshamira da gimbiya shuraima yar sarki Husubul-Dinar kuwa, Tun sa'adda suka ji abinda ya da yafaru da masoyan su wato bawa Kahzib da hilwas, Sai suka kasance cikin tsanin damuwa yana zamana cewa sun kamu da rashin lafiya domin ko abinci basa iya ci, Koda sarki Husubul-Dinar yaga abin da ya samu yar sa sai ya yanke shawarar ya tafi izuwa Birnin sa domin yi mata magani, Amma sai sarki shardasu yace yayi hakuri har zuwa lokacin da zasu samu lafiya ayi musu magani tare da gimbiya, Al'amarin mahaifan su Kahzib maza da mata a cikin kurkuku kuwa sun kasance cikin kinci da damuwa dare HAUSABOOK.COM 69 da rana bisa tunanin halin da ya'yan su ke ciki. Suka ji sun tsani sarki shardasu fiye da komai a rayuwar su . Wannan shi ne abin da yafaru da su gimbiya lshamira da mahaifan su Kahzib. Mu haɗu a KANGIN BAUTA Littafi na 11 domin jin cigaban wannan kasaitaccen labari. Daga mai ɗebe muku kewa a kullum da ko yaushe Lokacin da su jaruma Husnat dasu bawa Hilwas suka shiga izuwa gidan boka kimraz, Sai suka tsinci kansu a wani makeken fili mai tarin rairayi, Sai suka ci gaba da tafiya Husnat tana mai dawo bayan su, HAUSABOOK.COM 70 Saboda ta lura yadda Sharwas ke satar kallon ta a fakai ce, Yayin da taga hakan sai ta dube sa ta sakar masa tattausar murya a lokacin da ya waigo ya haɗa idanu da ita ɗin. Koda yaga irin murmushin da Husnat ke yi masa sai yaji zuciyar sa ta buga da karfi, Kawai ya mayar da duban sa zuwa kan hanya yana mai tambayar kansa a cikin ran sa yana mai cewa shin Mene ne ma'anar wannan murmushi da Husnat tayi mini shin ko ita ma ta kamu da soyayyata ne. Amsar tambayar da Sharwas ya kasa bawa kansa kenan. Haka dai aka cigaba da tafiya sai da aka shafe tsawon Sa'a ɗaya ana tafiya batare da an haɗu da wani abu mai cutar wa ba, HAUSABOOK.COM 71 Ana cikin wannan hali ne kwatsam bazato babu tsammani sai aka ga waɗansu irin dakaru na taso wa daga cikin rairayin tamkar yadda danshi ke tsattsafowa daga cikin ƙasa, Dakarun sun kasance girɗa-girda tamkar samudawan farko suna dauke da siffa guda biyu, Tsagin jikin su na dama na karfe ne tsagin hagun kuwa na na haske ne Suna dauke da miyagun makamai masu barazana ga rayuwar bil'adama, Suna dauke da idanuwa jajur kwaya ɗaya jal a tsakiyar goshin su, Hancin su da bakunan su irin na gwaggwan biri ne, Haƙiƙa waɗannan dabaru sun kasance munana kuma ababan tsoro, HAUSABOOK.COM 72 Babu wata halitta mai numfashi walau mutum ko aljan da zayi arba da miyagun dakarun face tayi nadamar wanzuwar ta a doran ƙasa, Sa'adda su jarumi Hilwas sukayi arba da dakarun sai suka ɗimauce, Tamkar ace kyat su zura da gudu,amma saboda juriya irin ta zaratan Jarumai sai suka dake, Jaruma husnat ce kaɗai bata razana ba ita ma saboda tana karanta sunayen Ubangiji tsarkaka ne a cikin ran ta yasa hakan, Yayin da dakarun suka kammala yiwa su hilwas ƙawanya sai aka fara kallon-kallo tsakanin su, Daga can sai dakarun su ka zare makaman su suka yi ihu da kururuwa mai firgitar wa suka ruga izuwa kan su. HAUSABOOK.COM 73 Ko da ganin hakan sai jaruma Husnat ta zare takobin ta ta kwala kabbara da karfi ta ruga izuwa kan dakarun, Sharwas, Kahzib da hilwas sukayi koyi da ita ta hanyar zare makaman su, Lokacin da aka haɗu sai aka ruguntsume da azababban yaƙi mai matukar kwarjini muni daban tsaro, Kowa ne ɓangare su ka wanzu suna kaiwa juna miyagun hare hare cikin matuƙar zafin nama juriya da bajinta tagaban kwatance, Wohoho ana fara wannan artabu ne wani abun mamaki ya fara guda domin kuwa duk irin zafin nama na su jarumi Hilwas yazama abanza, Domin kuwa duk sa'adda suka sari jikkunnan dakarun da makaman su sai suji tamkar dutse suka sara domin wani irin tartsatsin wuta ne HAUSABOOK.COM 74 yake tashi gami da kara marar daɗin sauraro. Al'amarin da yayi matukar dugunzuma hankalin su kenan suka fahimci cewa idan aka Cigaba da wannan artabu a haka dakarun zasu iya samun nasarar hallaka su. Abangaren jaruma Husnat kuwa tuni labari yasha bambam, Domin kuwa Husnat ta zamo gagarabadau a tsakiyar dakarun, Duk in da ta sanya a gaba sai dai kaga dakarun na zubewa ƙasa matattu tamkar tana sassabe a gonar auduga. Tabbas jarumtaka baiwa ce daga Ubangijin halitta ba'a siyan ta kuɗi ko mulki, Komai hassadar Mutum idan ya ga Yadda Husnat ke ragargazar dakarun doka ne ya jinjina mata ya HAUSABOOK.COM 75 tabbatar dacewa ta cika mace mai kamar maza kuma jarumar Asali, Nanfa ƙarar karafniyar ƙarafa,ihun mazaje haɗe da kururuwar dakaru ta cika dodon kunne, Sassan jikkunnan dakarun suka dinga shawagi a sararin samaniya suna zubowa ƙasa tamkar ana ruwan su ne daga saman, Jini kuwa ya dinga kwaranya, tsartuwa gami da feshi yana zubar a ƙasa tamkar an balle Teku, Sai da aka shafe tsawon Sa'a ɗaya ana wannan fafatawa babu sassauci, A sannanne dakarun suka fahimci cewa Husnat tayi musu muguwar barna. Domin ta kashe fiye da rabin su, Nan fa hankalin su ya dugunzuma ainun,kuma suka fusata ainun HAUSABOOK.COM 76 zukatansu suka dunga tafarfasa tamkar zasu kone, Kawai sai suka zage damtse suna cigaba da kaiwa Husnat hare hare ta ko ina, Al'amarin su Bawa hilwas kuwa sa'adda su ka ga irin gagarumar bajintar da Husnat ke yi sai suka cika da matukar mamaki suka ce a cikin ransa anya kuwa Husnat bil'adama ce, Taya ya za'ayi ce zaratan Jarumai kamar mu mun kasa samun damar hallaka koda badakare ɗaya amma Husnat ta kashe fiye da rabin su, Lokacin da sa'a biyu ta shuɗe ana wannan fafatawa a dai dai wannan lokacin ne Husnat ta hallaka ba ki ɗaya dakarun dake gaban ta, Kuma ta hango irin mawuyacin halin da su Bawa hilwas ke ciki, HAUSABOOK.COM 77 Domin dakarun sun galabaitar dasu basa iya mayar da martani sai dai ƙoƙarin kare kansu. Wasu lokutan idan dakarun suka kawo musu hari suka kare da makaman su

Chapter 2 of 3